Reading adon dawa Chapter 20 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

teburin ma'aikata ta duba da ke daf da kofar shiga har yanzu masifaffun
matan nan ne akan aiki ta dube su ta fada cikin gadara ina takardar maganin nan?
Kubani insayo sai taga sun turus da alama suna mamakin kalam kaltum,
can daya daga cikinsu tace kibarshi an bar matashi kyauta, kaltum ta wuce tana gyara
jibgegiyar ledar da ta shako da kayan dadi yayinda duk gadon da tazo giftawa marasa
lafiya da masu zaman jinyar su suka bita da kallo,
dadi yakama kaltum ta huce takaicin bakin cikin talaucin da ya addabesu , ita ma
yanzu zata jera kayan shayi akan lokarsu kamar yadda kowanne gado ake jerawa,
kallon ta suke ita ma tana baza ido tana dubansu duba irina ku kallah da kyau nice dai ta
dazu wacce ba ta da guntun sabulun wanki,
yanzu Allah Ya hore mata abunda yafi sabulunku,
dadi ne yayiwa kaltum yawa hartayi batan kai
tarasa gadonda kalah ke kwance kokuwa idone yayi mata yawa tafiya take hartakai
karshen dakin bataga gadon kalah ba saita juya ta kara tahowa tana baza ido dukka
bangarori hagu da dama saigata abakin kofar fita mamaki marar misaltuwa zaka iya gani
afuskarta ta fada abayyane ko ba dakin bane?
yayinda ta kara duban fuskokin yan dakin da ma'aikatan, hakika yan dakinne dan haka
daki ma shine babban abun tambaya ina gadon kalah?
Ina kalah ?
Shine kokarinda kaltum takeyi gashi babu wanda yace mata uffan
.ADON DAWA 23
.
TRUE LIFE STORY
.
masu son zaman kasarkuba dayawanmu
kaddarace muma badason ran mu ba dolece,
a bakin bandaki aka tsatstsaya ana kallon su kaltum yayinda mamaki ya rufe yan kallo
suna tambayar meyake faruwa ne meyakawo zancen zama akasar sudan?
kaltum ta wuce wajen fomfo batare da ta iya tsayawaba tabasu ansa ba Aisha ce ta
tsaya tana bayanin abunda yafaru, gaba daya suka bawa kaltum gaskiya suka bawa
ma'aikatan da yan dakin rashin gaskiya koba yan kasa bane ba ai musulmai ne,
wulakanci bashi da dadi kuma yan sudan nawa ne a nigeria sunacin arziki abun duniya
suke tarawa a Nigeria su dawo sudan suna zagawa,
akwai auratayyah asakaninsu dan haka
anzama daya,
aka cika bandaki ana bawa kaltum hakuri akanta karbi bokiti da omo tayi wanki taki
karba tace ai ta rantse indai bokitin yan dakinne bazatayi anfani dashiba
saida wata tabata sabulu sannan ta karba na
aishane bazata karba ba tunda tana dakin tana ganin wulakancin da akeyi mata bata
fitar da ita kunya ba sai daga baya zata biyota saboda kar yan dakin su tsaneta kome?
kaltum rigima da kyar ta karba sabulun ta wanke taje ta shanya igiyanda dake gaban
dakinsu tashigo dakin tana kallon kowa daya bayan daya jira takeyi ayi magana tayi
tsiwa babu mai iya hada ido da ita domin Aisha
takawo musu labarin abunda kaltum tafada abandaki
ta isa gadon kalah har yanxu shirkif take cikin barci, ta fada abayyane cikin harshen
larabci kalah zantafi cikin gari insamo miki abunda zakici nabar amana agurin ALLAH
domin Shi Ya halacci talaka Ya halacci me kudi ya halacci dan sudan ya halacci dan
Nigeria
sai kowacce tayi kiri-kiri tana duban kaltum sunsan magana ta yasar musu ta wuce kere-
kere ba mayafi kasancewar taraba mayafinta gida biyu ta rufa kalah
ma'aikatar daya ta dubi kaltum ta gyada kai
tace lalle yarinyarnan batada mutunci ashe.
kaltumta murguda baki ta fice yayinda suduka suka bita da kallo kaltum nashiga gidansu
matan gidan sukayo kanta suna tambayan yaya jikin kalah an sayi magungunan kuwa?
Wannan tambayan nasu ta bata mata rai don haka bata basu amsar tambayarsu ba ta
kada kai tayi daki,
buhun kayanta ta jawo ta bude ta daura wata lafayan tacire ta jikinta, yau zancen wanka
babushi tafice ko wacce taja bakinta tayi shiru babu wacce ta sake tambayarta komai
sunga ranta yabace kuma sunsan basu kyauta ba kallonta sukeyi harda lekenta akofar
gida su ga inda zata nufa asibiti ko
kasuwa,
hanyar kasuwa ta nufa don haka suka gaskata neman kudi zataje
nan suka dasa kujerar gulma cewa banda
yarinta ma meyasa kaltum zata damu kanta akan kalah, matarda ta cuceta takawota
Khartoum ta wulakantata ita da yarta , kaltum babu abunda basuyi mataba na wukanci
fatsumace ta hango kaltum ahanya yayinda tafito daga wani gida ta bullo da gudu ta iso
inda kaltum ke tafiya ta dafa bayanta firgigit ta tsorata ta waigo da sauri sai taga
fatsumace sukayi murmushi alokaci guda fatsuma tace yaya jikin kalah, kin san fa tsoron
asibiti gareni shi yasa banbiku asibiti ba,
kaltum ta tabe baki tace bai kamaki bane dole dakinje,
fatsuma tace banda abunkima inake ina zuwa duba kalah duk irin muguntan da tayi miki
mezakije kiyi mata koda mutuwa tayi ma ina ruwanki?
kaltum tayi murmushin karfin hali tace muna yiwa Allah laipi muroke Shi Ya yafemana
meyasa bazan yafewa kalah ba?
yarta lami ta mutu meyasa bazan taimaketa ba tunda bata da kowa?
fatsuma ta tabe baki tace lallai kaltum dama haka kike da tausayi kamar lokacin
Sahabbai?
kaltum tayi daria, saboda na hadu da lalurar rashin lafiya nima Madina ta taimakeni
yayinda sauran suka gujeni shiyasa na kudiri niyyar taimakon duk wani mara lafiya
acikinmu tunda muna kasar da ba namu ba, babu iyaye babu dangi,
fatsuma tayi ajiyar zuciya tace gaskiyane yanzu ina zakije ?
Kaltum tace kasuwa zanje na nemo wa kalah abinci kafin magariba fatsuma ta yamutse
fuska tace mezaki sayar kisami kudi?
kaltum tace bara zanyi .
fatsuma ta dafe kirji tafada a bayyane cike da fargaba bara?
Bara fa kikace kaltum to Wallahi ba'a bara anan sai akamaki akaiki Chad ko maiduguri
ayar, nan ba bur sudan bace babban birninsu ne ba a wannan rashin hankali kame akeyi.
kaltum tayi kasake tana tunani to in banyi bara to mezanyi na sami kudi tunda sana'ar
tamu ta sassafene kawai muma sau daya samu muci abinci ko sau biyu saikuma wata
goben....
fatsuma ta katse tunaninta tace yanzu nan da ganni daga cen gidan nafito nasami sabon
aiki da yamma zandinga zuwa kuma kudi da abinci matar tace zata dinga bani kullum.
kaltum ta tambayeta cike da fara'a wanne
irin aikine ?
*fatsuma tayi murmushi tace gidan kunshi ne
da gyaran jiki (alewa da dilke )matane dankar suke taruwa ana bin layi ita kadaice don
haka aiki yayi mata yawa take neman masu tayata kamar masu yi mata aikin gida da
masu wanke wa mutane lalle da shafa mahallabiya nidai renon jaririyarta neke yi mata
yanzu ma aikena tayi insayo mata mahallabiya akasuwa zo muje ki rakani saimuje gidan
tare ki dinga tayani aiki idan kikaci sa'a kema saita daukeki aiki,
tafiya sukeyi fatsuma hira takeyiwa kaltum yayinda ita kuma addu'a kawai takeyi
azuciyarta tana fatan Allah Ya taimaketa matarnan tadauketa aiki asirinta yarufu ,
akusa da mai sayar da mahallabiya akwai masu sayarda madarar turare anan ne kaltum
tahadu da wani farin saurayi mesuna Abbas,
kallo daya ya wa kaltum yaji zuciyarsa taharba ta tsansar kaunanta ya dinga shisshige
mata yana tsoma baki acinkin cinkinsu ko kallo bai isheta ba domin ita duk abunnan da
akeyi hankalinta na gun aiki da tunanin halinda kalah ke ciki, saida Abbas
yamiko mata kwalbar turare sannan ma ta daga ido ta dubeshi ta sa hannu takarba
batare datasan manufarsaba ta manta ana godiya idan anwa mutum kyauta ta kada kai
tayi gaba fatsuma tace ta tsaya tana surutu dasu sannan can ta taho suka tafi a hanya
take shaidawa kaltum cewa Abbas ne ya tsaryar da ita yana tambayarta gidansu wai
kaltum yakeso,
kaltum ta tabe baki ta fada a yatsune au shine yabani turare ai danasan manufarsa da
bazan karba ba,
fatsuma ta zungureta tace ke wawuya ce ki so shi kawai yadinga zuwa zance yana kawo
mana kudi, abinci,sutura da kayan dadi,
kaltum tace Allah Ya sawake na so wannan.
fatsuma ta harareta tace yafiki kyau fa, balarabene fa kobaki kare masa kallo bane?
kaltum tace bai dameni bafa ya kyaleni,
haka dai suke tautauna harsuka isa gidan me kunshi katafaren tsakar gidane aka malale
da kafet hade da manyan fululluka mata birjik kowacce a kishingide an yarda mata
kunshi a laulausan fatarta da alama mai kunshin ta bunkasa domin matan manyane duk
a wajen daga dukkan alama motocinsu da direbobinsu a waje kofar gida suna jiran su,
kallonsu kawai kaltum keyi tana sha'awar baiwarda Allah Ya yi musu dama nice nasami
kwanciyan hankali da daula irin wannan, kaltum tafada azuciyarta dai-dai lokacinda ta
durgushe gabansu tana kwasar gaisuwa.
fatima wannan fa?
ina kika samo yar kyakyawan kawa itama yar
nigeria ne ko yar mali?
Inji Jawahir me kunshi.
fasuma tayi dariya tace kawatace kasarmu daya gidanmu daya kaltum sunan ta,
gaba daya suka zubawa kaltum ido sai ta sunkuyar da kanta kasa ta fada cikin
marainiyar murya hajiya kitaimake ni ki bani aiki mahaifiyata na asibiti akwance abinci
na
fito nemar mata,
sai hawaye ya kewa kaltum gaba daya suka tausaya mata harda masu tayata kuka,
kankace kwabo sunfara bude jaka ana zaro
sabbabin kudi ana mika mata sadaka tamike tana bi tana karba tana tarawa ta durkushe
a gabansu tayi godiya gami da kwawawan addu o I,
Jawahir takara mata da albishir da daga gobe tafara zuwa aiki ta dauketa aiki zata dinga
biyan ta,
kaltum tayi sauri ta dubi fatsuma farin ciki ya lullubeta su kayi dariya lokaci daya sannan
sukayi godiya tare,
kaltum tamike tsaye ta kara godiya tace zan koma asibiti wajenta gobe zan fara zuwa.
Jawahir tayi murmushi,
Ta ce Allah Ya kaimu kiyi mata sannu Allah ya sauka ke.
kaltum ta amsa da amin ta fice tana murna yayinda tafara kidaya kudinta metan wa
tamanin jine ma'ana dari biyu da tamanin saita kyalkwale da daria saboda farin ciki
tashiga tunanin abunda zata sayawa kalah wanda zataci tana tafe tana tunani saita
yanke shawara taje restourant ta sayo mata gasheshshiyar kazar da ake gasawa a inji
mai laushi da tiriri, marar lafiya zaiji dadin taunawa don haka kai tsaye ta wuce al-amana
resturant ta sayo wata dankwaleliyar kaza gashesshiya mai zafin gaske har tiriri takeyi
ta ashara jine tashiga super market ta cefano kayan shayi na hamsin wa ashirin jine fal
leda ta nupi asibiti ta ayyanawa a ranta cewar yan dakinsu na asibiti zasu sha mamaki
idan sukaga ta tilowa kalah wadannan kayan dadi a gaban ta kamar ba yanzu suka gama
mata wulakanci ba akan guntun sabulu saita yi murmushi ta gode wa Allah daya dubeta
Ya turo mata kudi nan mai dimbin yawa cikin dan kankani lokaci tsaka nin la'asar da
magrib, Allah Shine abun godiya kaltum ta fada abayyane tana shiga cikin get din asibiti
saita nufi dakin da kalah ke kwance ta duba igiyar data yi shanya saitaga an kwashe
zannuwan data shanya saita yi mamakin wayezai kwashe zannuwan nan bata tunani
sace wa aka yi tafi zaton
bushewa suka yi aka kaimusu kan gadon kalah,
tashiga dakin teburin ma'aikata ta duba da ke daf da kofar shiga har yanzu masifaffun
matan nan ne akan aiki ta dube su ta fada cikin gadara ina takardar maganin nan?
Kubani insayo sai taga sun turus da alama suna mamakin kalam kaltum,
can daya daga cikinsu tace kibarshi an bar matashi kyauta, kaltum ta wuce tana gyara
jibgegiyar ledar da ta shako da kayan dadi yayinda duk gadon da tazo giftawa marasa
lafiya da masu zaman jinyar su suka bita da kallo,
dadi yakama kaltum ta huce takaicin bakin cikin talaucin da ya addabesu , ita ma
yanzu zata jera kayan shayi akan lokarsu kamar yadda kowanne gado ake jerawa,
kallon ta suke ita ma tana baza ido tana dubansu duba irina ku kallah da kyau nice dai ta
dazu wacce ba ta da guntun sabulun wanki,
yanzu Allah Ya hore mata abunda yafi sabulunku,
dadi ne yayiwa kaltum yawa hartayi batan kai
tarasa gadonda kalah ke kwance kokuwa idone yayi mata yawa tafiya take hartakai
karshen dakin bataga gadon kalah ba saita juya ta kara tahowa tana baza ido dukka
bangarori hagu da dama saigata abakin kofar fita mamaki marar misaltuwa zaka iya gani
afuskarta ta fada abayyane ko ba dakin bane?
yayinda ta kara duban fuskokin yan dakin da ma'aikatan, hakika yan dakinne dan haka
daki ma shine babban abun tambaya ina gadon kalah?
Ina kalah ?
Shine kokarinda kaltum takeyi gashi babu wanda yace mata uffan.
ADON DAWA 24
.
Babban abin tambaya shi ne, ina gadon kallah? Ina kallah ta ke? Shi ne kokarin da
kaltum take yi, ga shi babu wacce tace mata uffan, Kallonta suke tamkar a talabijin take
ba a zahiri ba. Ta koma ta dawo, se ta je kansu ta tsaya, tana musu duba irin na mamaki
da Al'ajabi. Can taetambaya, "don Allah ina mai gadon nan, kallah? "
Caraf ta ji an dafa bayanta, sai ta yi farat ta juya a tunanin ta kallah xata gani da kafarta
tana tafiya ko bsndaki ta shiga da kanta, juyawar ta, se ta ga masipappiyar ma'aikaciyar
jinyar nan ce, mamaki ya kama kaltum matuka ta bude baki tana dubanta.
Matar ta fada cikin marainiyar murya, "kaltum ki yi hakuri Allah Ya yiwa kalah rasuwa
dazu dagafitar ki,ko get baki kai ba. An leka da gudu ba a ganki ba.... "
Duk wannan dogon bayanin da matar ke yi bai shiga kunnen kaltum ba, kalmar da ta
rike ita ce, Allah Ya yi wa kalah rasuwa.
Rim! Ka ke ji ledar hannunta a cike da gwangwani ta bare, yayin da lakar hannunta ta
saki sai ga himilin kudin da takunso damke a hannunta sun watse a kasa. Ita kuwa sharaf
tafado akan ma'aikaciyar sai suka tare ta. A kasa ta mike zunbut kamar mai suma,
amma ba suma ba ce, tsabar tashin hankali ne ya tayar mata da mutanen boye jikinta
masu naci, ashe ba su bar ta ba.
Kan ka ce kwabo an kinkime ta an dora ta akan wani gado an kira likita ya hau aikin ceto
rayuwarta. Idanuwanta a kafe amma duk abun da ya soka mata sai ta fusge, kuma
magana take barkatai ga tsananin karfi, sai ta yi tazubar damasu danne ta. Masana suka
shaidawa likita ya daina wahalar da kansa, wannan ciwon ba layinsa ba ne, aljannu ne
don haka aka gewaye ta ana tofa mata addu'a.
Sai bayan sallar isha'i ta farfado, ta tashi zaune daram zuciyarta cike da mamakin ganin
yadda jama'a suka zagayeta, mata da maza, ta lura da an burbursina mata wasu
abubuwa a kofar hancinta, sai ta tuno matsalar bugun aljannun da take da su a baya.
Sannan ta gaskata su ne suka tashi, sai dai tambayar da take yiwa kanta, me ya tayar da
aljannun? Tana tunanin
ADON DAWA 25
.
TRUE LIFE STORY.
.
Tunanin matsananciyar rayuwar da ta tsinci kanta a ciki. Ba ta son khartum haka ba
dadin xaman garin take jib a, dama-damarta dan ta hadu ds fatsima kawa mai kaunarta,
mai karfafa mata gwiwa. Ba don fatsima bad a rayuwa ta kara yi wa kaltum xafi a
khartum kasancewar BABU RUWAN WANI da rayuwar wani , babu taimako ko kadan a
xaman gidan nan.
“ya na yi miki Magana”. Fatsima ta xunguri kaltum a lokacin da suke tsugunne a bakin
katuwar bola suna tsintar kayan miya.
Kaltum ta daga idanuwanta da sauri ta dubi mutumin da ke tsaye a kanta, Abbas ta gani
tsaye a kanta yana murmushi sanye da jallabiyarsa fara tas! Da rwaninsa fari kal irin na
larabawan sudan. Murmushi ya sakar mata gami da cewa, “marhaba kaltum.”
Sai ta ji ranta ya dungunxuma y abaci, bakin cikin day a dankare xuciyarta ya sake
karuwa. Kallon fuskarta kawai xaka yi ka tabbatar da labarin xuciyarta. Ya yi ta Magana
ko daga idonta b ata yi ba balle tab a shi amsa. Da ya dame ta, sai ta yanke shawarar
hakura da tsintar kayan miyar, gara kawai ta bar masa wajen. Ta kinkimi kwandonta aka,
ta yi tafiyarta ko fatsima bat a yiwa sallama ba saboda ta fuskanci ita ke goyon bayansa.
Sai da ta yi nisa sannan ta ji fatsima ta kwalla mata kira. Kaltum ta juyo sai tag a fatsima
a guje tana murna.
Ta iso inda kaltum ke tsaye ta mika mata kudi, kaltum ta mika hannu ta karba a
sanyaye, sannan ta tambaya cike da mamaki, “waye ya bani”!
Fatsima ta yi dariya ta xaro nata kudin t ace, “ashara jine ya bani, ke kuma ashirin jine y
ace in kawo miki.”
Kaltum ta tabe baki sannan ta yi mata tambaya, bad an bata ta sani ba sai don ta ja
mata kunne.
“waye ya ba mu kudin!”
Fatima tace, “Abbas mana”.
Kaltum ta ci gaba da Magana cikin fushi da cewar, Abbas ya fita harkarta, ba ita bas hi,
ya sami dama ne daga wajen fatsima dab a xai ci gaba da nace mata ba.
Fatsima t ace, ita kuwa ko yanxu idan ya bas u kudi sai ta karbo musu sai dai idan ta
bata ta xubar.
Fatsima ta ci gaba da yiwa kaltumtsiya tana cewa, “duk wnnan fadan da kike yi, ban ga
kinyi wurgi da kudin ba a damke a hannun ki yake.”
Sai kaltum ta sake damke kudinta b a tare da ta kara cewa uffan ba. Ba ta son Abbas,
amma tana da bukatar taimakonsa.
Fatsima ta dinga yi wa kaltum tsiya don t ace bat a son kudin, amma shiru kake ji bat
ace komai ba. Suka isa famfo suka wanke kayan miya, sannan suka nufi kasuwar adare
don su sayar. Yau bas u dmu da sai sun siyar da tsda ba, saboda aljihunsu da nauyi,
kudin da Abbas ya bas u ya ishe su cin abincin yau hard a nama da lemo.
Da rana suka tafi gidan jawahir mai kunshi kamar yadda ta umurce su bayan sallar
axahar xa su dinga xuwa saboda mai gidanta bai yarda ta fara xaman kunshi ba sai t
agama aikin gida kakaf.
Jawahir tana murna da xuwan kaltum matuka, saboda kaltum ta iya kitso ashe, tabbas
xata kwashi kudin kitso. Kaltum da fatsima suna taya ta aikin gida, ko rainon yaranta,
suna tayata da wanke lalle idan ya yi da shafa mahallabiya, ko su hura mata garwashi
idan xata yi wa mata dukkan.
Ba sa barin gidan jawahir sai bayan sallar isha’I, bayan tab a su abincin dare sun cika
cikinsu, sun share mata gidanta tas! Sannan su nufi gida.
A halin yanxu sun rage tafiya markadi tsintar rubabbun kayan miya, saboda dan kudin
da suke samu daga wajen jawahir. Babu laifi tana biyansu duk da dai aikin da suke
shirga ya fi kudin aikin yawa, tana bas u abinci anda shi ne babbar matsalarsu. Kaltum
mai farin jinni, ladabinta da kwaxon aikinta gami da fara’arta sun sa wadanda ta ke yi wa
kitso da wankin lalle suna kaunarta, har suna yi mata kyauta akai-akai.
Allahu Akbar! Allah ma ji rokon bayinSa, Allah Yana taimakon duk wanda ya tashi ya
neama, haka Yan a bawa duk wanda ya roke Shi. Babu talaka sai mai matacciyar xuciya.
Allah ba Ya hana bawanSa lomar da xai kai bakinsa.
BABI NA GOMA SHA DAYA.
BUR SUDAN.
Rayuwar mambela da madina a bur sudan ta xama tamkar gayan tuwo ne marar miya
cinsa haka babu dadi. Haka suke rayuwa amma xukatanu babu dadi saboda rashin
kaltum din su.
Mambela ya fada ya sake maimaitawa, yyin day a lailayo rantsuwa yam aka a cikin
bayanansa a dai dai lokacin day a tara ‘yan gidan su madina kakaf kofar gidan su da
sanyin safiyar wannan rana. Yana Magana hawaye na yi masa tsartuwa, hakika daga jin
kalamansa xaka tabbatar a cikin matsanancin fushi yake Magana da matukar damuwa.
Tabbas babu maganar wasu a cikin lafaxansa, Magana yake cikin gadar da basu
tabbacin xartar da hukunci mai tsanani akan duk wanda ya karya masa doka. Ba wai
rokarsu yake das u bi abunda yake umartar suba, har ya fi son kada su bi don ya yi was
an kura das u.
Ya dube su daya bayan daya ya kawar da ido gefe, yayin day a runtse ido ya xubar da
hawayen day a cika masa ido, ya fada cikin harshen larabciwanda yake tunanin
kowannen su xai gane, wanda bai gane sosai bad an uwansa xai fassara masa.
Ya ce, “yan Nigeria da niger a da ina sonku fiye da yadda nake son yan kasata sudan.
Amma a ynxu bna son ganinku, ban ki in bude idona in ga an kwashe ku ba kada a bar
mutum daya saboda xamanku a kusa da ni babban fami ne a cikin xuciyata.
A duk lokacin da nag a irin ku, ko na ji yarenku na hausa sai gabana ya yanke ya fadi, in
ji xuciyata ta buga saboda kuna tuno min da KALTUM. Da xarar na fito da safe na hango
ku kun fito da kayan sana’arkukamar haka, sai in ga kamar xan hango kaltum a tsugune
a can tana wanke-wanke.”
Se ya nuna gefen da madina ke xaune, yayin da kuka ya kece masa, kuma ya kecewa
madina.
(NIMA SE DA MAJINA YA KECE MIN)
Mambela ya cije leben ya ci gaba da cewa, “kun ci manata da ku ka bar kaltum ta tafi
Nigeria, aka rasa mutum daya da ai tashi ya ruga ya xo ya sanar da ni halin da ake ciki,
haka kuka kori yarinyar nan, ku kuma kuka mike kafa a kasarmu. To ba ku isa ba, yadda
kaltum ta bar sudan sai kun bar sudan, yada na rasa farin cikin rayuwata, sai kun rasa
farin ciki kuma.”
Hankalin kowannensu ya tashi, kana dudan idanuwansu xaka ga sun firfito waje don
fargaba.
Kalmar “ma’alesh, ma’alesh ya mambela”. Suke Ambato.
Ma’ana kayi hakuri kai mambela. Sai Kalmar ta xame masa tamkar ashar suke danna
masa saboda masu iya magan na cewa, da xarar an fara ba ka hakuri to tabbas an cuce
ka.
Ya daka musu tsawa cikin fushi, y ace, su rufe masa bakin su, bay a bukatar bada
hakurin su. Tsit kake ji ko tari babu wanda ya sake yi.
Ya share hawaye y ace, “ba ku da imani, ba ku da tausayi, ko wannenku yasan tsakanina
da kaltum kun san babu abun da na fi so a duniya irin kaltum ba ni da Magana sai ta
kaltum, haka ba ni da wurin xuwa sai ajen kaltum. Ina kwance ba ni da lafiya kaltum ta o
ta duba ni, a ranar na kai ta wajen mai martaba ya yaba da hankalinta, tya amince min
in aure ta. Mun fara shawarar yaya xamu je kasarsu saboda madina t ace, sai na je
gaban iyayenta xan aure ta, tana barin gidan mu kuka tura keyrta ku ka kore ta.
An fada min tana kuka bata so ta tafi, madina kika hada mata kyat a tafi, to ku sani babu
ku babu xaman lafiya a garin nan. Kaltum ta tafi ta bar ni, ban san ta inda xan fara nemo
Nigeria ba, da garin da kaltum ta ke a Nigeria.
Ni mambela na yi alkawarin takura muku, kun daina walwala kamar yadda na daina,
ciwo nake yi a kwance a ranar da kaltum ta xo duba ni, na warke da nag anta, daga
lokacin da na ji an dauke ta a lokacin ciwona ya dawo har yau na kasa samun lafiya. To
daga yau kun daina xaman lafiya don duk sai na kakkarya kafafuwanku daya bayan
daya.”
Kiri-kiri suke yi da ido, yyayin da kowannensu yah au kammala sangalalinsa kada a fara
ta kansa. Madina kuwa ta yi tsuru a gefe kanta a sunkuye a kasa, tasan kowanne
hukunci xai xartar daga kanta xai fra, don haka ta fara tunanin inda ake siyar da sandar
guragu, gara tun da wuri ta tanada.
Mambela ya ci gaba da Magana cikin kakkausar murya, y ace, “babu sana’ar sayar da
komai a kofar gidan nan, haka kada inga kafarku a bakin kogi, wajen kamun kifi. Haka
kada inga kafarku a kasuwarmu jim arab, kad a wata ta xo garinmu bara, sai na karya
duk wanda ya saba wannan doka. Sannu a hankali idan yunwa tai she ku xaku tarkata ku
tafi inda kuka fito, yadda kaltum ta tafi ta bar ni.”
Malam nura wani tsoho daga cikin su madina xai yi Magana, mambela ya dunkule hannu
xai kai masa bugu, abokansa da ke tsaye a gefensa suka rike shi. Suka ja shi suka tafi,
da kyar mambela yake daga kafarsa don tananin tashin hankali. Ya rasa akan wanda xai
huce, takaicin rashin kaltum amma ya fi jin haushin madina wacce ta hana su su yi aure
tuntuni. Sannan da yaradarta aka dauke masa kaltum dinsa.
Suka rushed a kuka suna kiran, sun shiga uku sun lalace, ya ya xa su yi su rayu idan ba
sana’a, ba bara! Madina ta mike a fusace ta fara Magana cikin fushi.
Ta ce, ‘haba jama’a kamar ba musulmai ba, kun manta Allah ne mai rayawa, Shi ne mai
kashewa!kun manta Shi Ya ke tsare mutum, Ya yi masa Katanga da duk wani mugu! Ko
gexau ban yi bad a mambela ya hana mu sana’ar da xamu ci abinci, Allah da Ya
haliccemu Shi xe fito mana da wata hanyr da xa mu ci abinci mu rayu. Jahilci ne ku dinga
kiran shiga uku, ku kira Kalmar “inna lillahi wa’inna ilaihi raji’un Allah Xai yi mana jagora.
Ko me ya samu bawa mukaddari ne, shan ruwan kaltum ne yak are a bur sudan dole ta
tafi, da shan ruwanta yak are a duniya da wayar gari xa a yi a tarar ta mutu ma karewar
tafiya Nigeria.’
Sai suka ji xuciyar su ta yi dan sanyi, sannan kowannensu ya dinga kinkimar kayan
siyarwarsa yana shiga gida don kada mambela ya xagayo ya iske su a kofar gida sana’ar
yau dai ba a yi ba. Sai asarar da suka yi, saboda mai kosai ta yi markade, mai koko ta
dama, haka mai danwake ta kwaba, har gara ma masu shayi da biredi ruwan xafi ne
kadai da lipton suka dafa.
Kwanaki biyu haka su madina suke xaune babu mai sayar da komai, babu bara, babu
xuwa kogi kamun kifi har sun fara jin jiki.
“mambela ya cuce mu, mugu marar imani”. Kalmomin da suke ta nanataw ken an, duk
dakin da ka xo

Please Login or Register in order to submit comment