kujerar da yake zaune.
"Kukan me ye kike yi Amatullah?".
Na yi saurin kawar da hawaye da suka ɓata mini fuska kafin na sama sararin cewa"babu komai". Ya yi ɗan jim kafin can ya ci gaba da magana.
"Har baƙon nakin ya tafi?". Babu shiri na ɗago kaina ina dubansa mamaki da tsoro kwance luf a bisa fuskana ban ƙara shan giyan mamaki ba sai da ya ƙara jefa mini wani tambaya a karo na biyu da ya kusa sanya nokinan kaina suncewa take na soma haɗa gumi duk da sanyi da ni'iman Ubangiji da ya lulluɓe garin.
"Me kuka tattauna da shi?".
Na gyara zamana kafin na iya raba tsakanin haƙwarana da suka manne da junansu kamar mayen ƙarfe aka sanya a tsakanin su.
"Abba ba fa waje na ya zo ba. Baƙon Amira ne....". Kafin na ƙarisa ya ɗaga mini hannu alamar baya buƙatar sauraron jin ragowar bayani.
"Amatullah". Ya ƙira sunana cikin kaushashshen amon da ya ƙara sanya ni na sha jinin jikina ainun. Kamar kazar da aka jefa da ruwan gishiri na amsa da ƙyar.
"Na'am Abba".
"Me yasa kike so ki sauya daga yanda na san ku a baya? Shin zuciyar ba ta tausayina akan irin fafutukan da nake yi wajen ganin na inganta tarbiyan, na tsaya kai da fata don tabbatar da cewa ba ki sauƙa daga kan gwadaben da kika taso a kai ba. Amatullah ina sa burin ganin rayuwarki ta inganta na ƙayatar da ita sa ilmi da tarbiyya daga yanzu har izuwa lokacin da zan miƙa ragamar rayuwarki a hannun mijinki".
Take hawaye suka ɓarke mini ban iya cewa komai ba har ya ɗaura daga inda ya yi birki.
"Ke ce duk wani buri da fatan da nake da muradin wanzuwansa a bayan ƙasa kafin na koma ga mahaliccina. Ba zan hana ki soyyaya ko na katange ki ɗaga kula kowa ba don yanzu kin yi hankalin da za ki iya tantance abun da zai dace da ke ko akasin haka. Amma a duk lokacin da kika ji a ranki kin fi buƙatar aure akan karatun da kike yi, to kar ki ji nauyin sanar da ni haka. Ni kuma na yi miki alƙawarin aurar da ke a lokacin da kika buƙata domin gujewa afkuwar ɓarna da yin dana sani a gaba".
Wani irin gumjin kuka ne ya zo mini mai ƙarfin gaske, gabaɗaya falon ya ɗauki sautin kukan. Na ja jiki na ƙara matsowa dab da shi na riƙe ƙafarsa gam sannan na kwantar da kaina a jiki.
"Abba na tuna na yi nadama, ka ji tausayi na ka yafe miji wallahi ba zan ƙara aikata makamancin irin hakan ba. Na yi alƙawarin ba zan ƙara yin abun da zai ɓata maka rai ba".
Bai ba ni amsa ba har sai da na cire tsammani.
"Ko kaɗan ba ki ɓata min rai ba Amatullah. Sai dai na ji ciwon ƙaryan da kika haɗa kai da Amira kuka yi min wanda na san ba halin ki ba ne hakan. A ina kuka haɗu da shi? Tsawon wani lokaci ya ɗaura yana zuwa wajenki? Sannan me yasa Amira ta ce ita ya zo nema bayan sunanki aka ambata?".
Tagwayen ajiyan zuciya na sauƙe da ya tafiyar da kukan da nake yi na koma sauƙe ajiyar numfashi akai a kai, tamkar wacce ta fafata a gasar fidda zakaran gwajin dafi na tseren gudu.
Sai da na fizgo numfashina da yake maƙalewa a ƙirji kafin na amsa masa jerin tambayoyin da ya watsa mini a lokaci guda.
"Wallahi ban taɓa ganin sa ba sai yau, ɗazu ne muka haɗu a inda na kai talla shi ne muka sama matsala da wasu ƴan mata har suka zubar mini da kunun kuma suka neme ni da faɗa. Shi ya hana su dukana kuma ya biya ni asarar da suka yi mini ya dage akan sai ya rako ni don tabbatar da na iso lafiya saboda sun yi ikirarin tare ni a wani wajen. Abba na rantse maka har da Sarkin da ya halicci sammai da ƙassai bakwai ba tare da wani ko wata ya kawo masa taimaka ko ba wannan shi ne gaskiya yadda muka haɗu da shi. Kuma ko yanzu ma sai da na roƙe sa akan kar ya ƙara zuwa yana nemana na ƙara tabbatar masa ma ba zan ƙara kai talla inda muka haɗu da shi ba. Amira kawai ta taimake ni ne don ta ga yadda gabaɗaya na rikici na kasa magana".
"Na yarda da ke Amatullah ba ni da shakka ko kokonto akan duk abin da zai fito daga bakinki. Ba da son raina ko aminvewata kike wannan tallan ba amma da iznin Allah na kusa kawo ƙarshen abun. Ki kwantar da hankalinki ki dinga taka-tsantsan da mutane don yanzu duniyar ta lalace".
"In sha Allah zan kiyaye". Kansa kawai ya gyaɗa bayan ya tallafo kaina na tashi daga jinginar da na yi a jikin ƙafafunsa. Ya miƙe zai shige ciki na yi hanzarin riƙo gefen rigarsa.
"Abba kar ka je ka kwanta da tare da bakinka ya furta kalmar yafiya gare ni ba. Hakan zai jefa ruhina cikin ƙunci da rashin nutsuwa".
Kyakykyawar ajiyar zuciya ya sauƙe da har sai da na jiyo sautin fitarsa kafin ya ce da ni wani abun da ya sanyaya sashin ruhina da nake jin kamar ana watsa mini garwashin wuta.
"Ko ban yi amfani da kalmomin baki wajen furta kalmar yafiya a gare ki ba. Zuciya ba za ta yi dogon zango tana dakon fushi da ke ba Amatullah. Na yafe miki kuma daman ba ki ɓata mini ba".
Sakakken ajiyan zuciya na sauƙe ina jin kamar an sauƙe mini wani ajiyan da aka yi mini a ƙirjina na kasa magana sai kuka, lallashina ya yi sosai har na dawo daidai kafin na yi masa sai da safe na cike cikin ɗakin. Lokacin Umma har ta yi bacci, ta kwanta a gefenta sai dai sam bacci ya ƙi kawo mini ziyara sai da na raba dare kafin na sama na iya runtsawa.
Washe gari haka na tashi da matuƙar ciwon kai ko kaina ban son ɗagawa balle na buɗe idanuna. Ina kwance a inda na yi sallan asuba, Umma ta ɗago labulen tana ƙira na na tashi na zauna kafin ta fesar da abin da yake tafe da ita.
"To ki tashi ki zo ubanki yana ƙiranki". Na tashi na rufa mata baya muka fito tare, na zauna a ƙasa yayin da ita kuma ta zauna a kujerar da Abba yake zaune kusa da shi. Shuru ya ratsa wajen kafin Umma ta buga tsaki.
"Ka tara mu ka ce za ka yi magana, mun zo kuma ka saka mu a gaba kana kallonmu. Idan ba ka da abin da faɗa ne ka sallame mu, don ni ina da abin da ya fi wannan zaman muhimmanci wanda zan yi". Wataƙila da Umma ta sama tagomashin kasancewa cikin mata masu lura da karanta ma'anar shuru da rabe-rabensa da ta fahimci shuru da kallon da Abba ya yi mata, yana bayyanar da ɗacin da maganarta ta yi masa ne. Amma sai dai kash! Ko a jikinta wai an mintsini kakkaura ko gizau ba ta yi ba.
"Na tara ku duka ne domin na sanar da ku wani hukuncin da na yanke wannan yake kamar umarni ne a gare ku". Umma ta katse shi ba tare da ya dire zancen ba"to muna jiranka sai ka tafi kai tsaye ga saƙon da kake son isarwa ai, ba sai ka tsaya kana wani kame-kame ba".
"Ina so na sanar da ku a cikin satin nan za mu tashi daga gidan nan. Don haka tun yanzu ku duk shirin da za ku yi".
Tun kafin ya gama zancen Umma ta yi zumbur ta miƙe tamkar wacce aka yi wa alluran doki, ta yi sakeke tana kallon Abba baki sake. Ta toshe kunnuwanta tana cewa"ban gane abin da kake faɗa ba Manniru? Ka yi bayani da harshen da zan fahimta ƙwaƙwalwata ta gaza amsar sauƙon da kake ƙoƙarin isar mata. Mu bar gidan nan mu je ina? Ina muke da shi bayan nan? Ko kuma kawai so kake ka yi amfanin da ikon da kake da shi a kanmu ka tozarta mu a idon jama'a?".
"Yadda kunnuwanki suka jiyo miki haka na faɗa Hafsatu za mu tashi daga gidan nan tashi na har abada. Ki fara shirya kayanki tun yanzu".
"Wallahi ba ka isa ba. Ba zan taɓa zuba ido wannan abun ya faru ba, Manniru anya kana lafiya kuwa ƙwaƙwalwarka ba ta sama matsala ba?".
"Zan ga tsakanin ni dake waye yake auren wani. Na yi rantsu ba zan yi kaffara ba ki isa ki sauya min ra'ayi akan wannan lamarin ba, dole ne mu bar gidan nan don ba zan zuba ido ina kallo tarbiyan ƴata tana lalacewa ba. Duk gini da foundation ɗin da na yi don inganta rayuwarta yana rugujewa ba, ba zan laminta ba".
"Da an yi magana ka ce ƴa ƴa kamar ka fi kowa ƴa ko a kanka kawai aka fara haihuwa. Duk mazauna gidan nan ba su ce tarbiyyan ƴaƴansu zai lalace ba sai kai uban masu ba da tarbiyya. Wai tarbiyyan nan kai ne kake yin ta ko taimakon Allah ne? Manniru kar ka biye zuciyarka ka cutar da mu babu gaira babu dalili, ka sani na sani daga kai har ni duk ƙoƙarinmu wajen tarbiyya ba zai iya sa yarinyar nan ta kasance cikin amintattu ba, face sai Allah ya dafa mana. Iyaye nawa ne wanda suka kasance manyan malaman addini amma ƴaƴansu suka fi kowa kangarewa da lalacewa ba. Ga misali nan Manniru Allah ya buga mana akan Annabi Nuhu wanda shi annabin Allah ne ma amma iyalinsa suka kauce hanyar da yake. Shi kuma sai ya ce me ye a Ubangiji?".
Ɗan jim Abba ya yi don ta gama ɗaure sa da jijiyar jikinsa.
"Ko me ye za ki faɗa barin gidan nan wajibi ne. Saboda gujewa faruwar abubuwa da yawa don haka na gama magana, kina da zaɓi biyu ko ki haɗa kayanki mu tafi tare ko ki yi zamanki a nan ki ci gaba da ɗaukar nauyin kanki kamar yadda kike ikirarin kina yi". Yana dasa aya a nan ya fice ransa a matuƙar ɓace. Ihu Umma ta kurma kamar za ta yi hauka ta zube ta yi zaman ƴan bori.
"Shikenan na shiga uku na lalace! Ni kake yi wa kora da hali Manniru? Dole na tashi tsaye a cikin gidan nan. Na rantse ba za mu taɓa tashi daga gidan nan ba ko za ka haɗiye zuciya ka mutu dare ɗaya......".
Ba ta ƙarisa ba na yi hanzari tashi na je na rufe mata bakinta.
"Don Allah Umma ki yi haƙuri. Ki dinga yi salati zuciyarki za ta yi sanyi, ba daɗe irin wannan maganar ko kaɗan".
Ta ture hannuna kafin ta ce"Amatullah ya ya zan yi da raina? Idan muka bar gidan nan ina za mu dosa? Sanin kanki ne ba mu da wani matsugunin da ya wuce nan, a nan ne kawai asirinmu zai rufu amma ubanki ya dage sai ya tona mana asiri sai ya fallaso sirrinmu ga duniya. Wallahi ba zan taɓa barin hakan ya faru ba tashi ki ɗauko min hijabina na fita".
"Umma ina za ki je a cikin wannan halin da kike ciki?".
"Wajen Malam zan je don shi kaɗai ne zai share min hawaye nan take".
[7/18, 11:05 AM] Maimunatu Iyam: *DAFIN HARSHE*
©️ Maimuna Tijjani Iyam
_______________________________________
Page 1️⃣1️⃣
Ganin tana ƙoƙarin tashi ya sani saurin cafko hannunta ina yi mata magiya"don girman Allah Umma ki rufa mana asiri kar ki je ko'ina. Da bakinki fa yanzu ki ka ce Abba yana so ya tona mana asiri amma asalin tonon silili zai faru ne daga loakcin da kika je kika baje wannan lamarin a wani can da daban da yake bakewa da malunta yake aikata abin da ba shi ne ba". Zafin marin da ta sauƙe mini a gefen kuncina na hagu shi ya sani haɗiye ragowar zancen ba tare da na furzo shi waje ba, kafin na yi aune ta ƙara sauƙe mini wani marin a karo na biyu da sai da ya tursasa mini sakin ƙara. Tsabar azaba da zogin da fatar wajen yake yi mini da nake jin tamkar ruwan tafasasshen ɗanyen dalma aka watsa mini.
"Sai yau na tabbatar har yanzu ba ki da hankali Amatullah girman jiki ne kawai da ke amma hankali kam sam babu shi a tattare da ke. Don ya wulaƙanta ni sai da ya ƙira yo ki sannan ya yi wannan ikirarin, ko rantsuwa na yi ba zan yi kaffara ba wannan duk shiri da tuggun Maman Umar ne kuma sai na nuna mata ina daidai da zamaninta. Manniru kai da ka bar gidan nan wallahi sai dai a cikin makara amma zaman daram yanzu ma aka fara sai mun ga abin da ya turewa buzu naɗi".
"Umma ki tuna fa komai ya yi zafi maganinsa Allah shi ne ya ke juya dare zuwa rana. Ya yaye ƙunci ya wanzar da farin cikin a zuciyar da cikinta babu kusuni. Me zai hana ki yi alwala ki yi salla raka'a biyu ki ba shi zaɓi ya zaɓa mana mafi alkhairi". Ba ta ce da ni komai ba illa bangaje ni da ta yi gefe guda ta shiga ɗaki ta ɗauko hijabinta ta fita, zubewa na yi a wajen na kwanta na yi luf ina sakin wani maraya kuka marar sauti.
Jikina gabaɗaya ya yi sanyi ƙalau ji nake yi kamar na tashi na ruga da gudu na je na dakatar da Umma daga abin da yake shirin aikatawa, sai dai gangar jikina ya ƙi ba ni haɗi kai wajen motsa ɗaya daga cikin gaɓoɓina. Har na ci gaba da kwanciya har izuwa lokacin da Amira ta shigo ta iske ni cikin mayuwayacin hali. Cikin tashin hankali ta iso inda nake zube ta ɗago ni sai dai na kasa tashi dole na koma na zauna na kifa kaina akan gwiyoyina ina ci gaba da kukan.
"Amatullah me ye ya faru?". Ta jefa min tambayar muryarta tana rawa, rashin samun daga gare ni bai hana ta ci gaba da tambayar duk abin da take tunanin shi ne sanadi da musabbabin kukan nawan ba.
"Ko dai mutuwa aka yi muku ne?". Na jijjiga mata kaina alamar a'a kafin na yi nasarar cira kaina ina duban ta da kumburarrun idanuna da suka rikiɗe suka sauya kala zuwa launin ja.
"Da abin da yake shirin faruwa ai gwara mutuwar ma Amira. Tun da dai shi wanda ya mutu ya huta daga rikici da fituttunun duniya sai dai ya je ya tarar da abin da ya shuka".
Ta waro idanunta tar a kaina"ke kin san zafin mutuwa kuwa? Ko don har yanzu kina ganin iyayenki biyu kuna rayuwa tare? Billahillazi mutuwa ta fi komai ciwo da raɗaɗi don har yanzu zuciyata cike take da gurbin rashin mahaifina duk da ya rasu tun kafin na mallakin hankalin kaina. Kuma alhamdulillah Baba Habu mijin Umma bai bar ni na yi kukan maraicin uba ba".
"Wani babban lamari ne yake dab da faruwa ko ina ce warhaka kam komai ya faru".
"Ki sanar da ni me ye yake faruwa don Allah, kar ki bar ni cikin duhu Amatullah".
Dogon numfashi na ja na fesar kafin na zayyana mata duk abin da ya wakana ban ɓoye mata komai haka nan ban tsallake ko da layi guda ba. Ta yi shuru kamar mai tunanin wani abu kafin can ta yi magana.
"To amma ke me ye kike tunanin ya sanya Abba yanke wannan hukuncin lokaci guda haka?".
"Ban san dalilinsa na yanke wannan hukuncin ba kuma cikinmu babu wanda ya tambaye sa".
Ta gyara zamanta kafin ta soma cewa" Samu gidan hayan a ƙurarran lokaci fa abu ne mai matuƙar wuya gwara ma ina kana da kuɗinka a hannu. Kuma ko da kuɗinka ma ba za ka sama yadda kake so ba, shi yasa gaskiya ni ban ga laifin Umma ba. Me ye amfanin a yi abun da daga baya za a zo ana dana sani?". Mamaki kwance a fuskana nake bin ta da kallo saboda dukan da zantukanta suka yi wa kwanyata.
"Kina nufin ba ki ga ma rashin dacewar abin da Umma za ta yi a addinance ba kenan?".
Ta riƙo hannuna"har ga Allah ban ga ni ba, don a tunanina haƙƙin kowacce uwa ne samar da daidaito a rayuwar gidan aurenta. Kuma Umma ta fi mu tunani ba za ta taɓa yanke hukuncin da zai cutar da ɗaya daga cikinku ba don haka kawai ki goya mata baya". Na fizge hannuna"kin manta wajen wanda na ce miki za ta je ne Amira? Wannan Malamin ba da yake fakewa da addini yana aikata alfasha. Ta inda mutum kamar ta mai ƙafafu biyu zai taimaka maka bayan shi ma mabuƙaci ne a wajen Allah?".
Taƙaitaccen murmushi ta yi tana kallona da wutsiyar idonta ta furta"amma kin san aikinsa yana tasiri akan ko waye kuma an yi ittifa'i ba a taɓa zuwa masa da kukan da ya kasa gogewa mai shi hawaye ba. Bari na sanar da ke wani sirri ko Ummata da shi ta dogara wajen kankaro mutunci, daraja har da kima a idanun Baba Habu".
"Kina nufin Ummanki tana zuwa wajensa? Tirƙashi!". Na yi mata tambayar a rikice.
Ta gyaɗa mini kanta"ƙwarai kuwa har ma tana aike na na karɓo mata saƙo daga wajensa".
"Innalillahi wa inna ilaihir raji'u! Shikenan mun shiga uku!".
Na furta cikin maɗaukakin tashin hankalin gami da firgicin da yake ƙoƙarin tarwatsa zuciyar da take dashe a cikin ƙirjina. Da mamaki babu ko ɗigo mamaki balle kiɗima a tattare da Amira.
"Me ye abun cewa mun shiga uku Amatullah? Ni da wannan kalmar tsinka min zuciya take yi, zamanin ne ya lalace an daina kiwon dabba an koma na mutum. Ba ka damu da mutum ba amma shi yana can yana hana idonsa runtsawa a ƙoƙarin ganin ya ga bayanka kin ga kuwa ai dole ka tashi ka kare kanka, tun da ko Allah ma cewa ya yi sai ka tashi sannan zai taimake ka".
Takaici ya zo mini har wuya wani ɗaci ya gauraye da yawun bakina ya jirkita shi gabaɗaya ta yadda sai da na ji kamar na yi amai. Da ƙyar na haɗiye sa ta hanyar wuyana ya wuce kamar na haɗiye ƙarangiya.
"Ai ba irin wannan lamarin ake nufi ba. Ta yaya za ka je wajen wanin Allah kana neman taimakon da shi kasan in ya tsinci kansa a cikin irin halin da kake ciki ba zai iya samarwa kansa mafita ba, kina ganin akwai basira a cikin aikata hakan?". Ta taɓe baki tana jefa da wani irin kallo alamar ta soma gajiya da fahimtar da ni abin da kaina ya gaza ɗauka balle ƙwaƙwalwata ta amshe shi.
"Ni kam ban wani irin taurin kai Allah ya zuba miki ba. In da kin fito a cikin mutanen farko irin riƙaƙƙun kafiran nan zai yi wuya ki karɓi musulmci, ga zahiri nan ki na kallo amma kuma runtse ido . Amatullah ya zama dole fa mu amshi abin da zamani ya zo mana da shi, mazan ne yanzu sai da haka sai ana danganawa ga Malamai kafin a shawo kansu. Na rantse miki ba don irin wannan taimakon daga malamai ba da yanzu wani maganar ake yi ta daban mussamman Baba Habu da Allah ya yi wani irin murɗaɗɗan mutum mai wuyar sha'ani, a hakan ma yaya balle kuma an zauna haka nan".
Ni kam shuru na yi don gabaɗaya na rasa me ye zan ce da ido kawai nake bin ta har ta kai aya. Na ja wani gauron ajiyar zuciya na fesar kafin na gyara zamana, na soma ambaton Allah a cikin zuciyata.
Ina da tabbacin shurun da na yi ne ya sanya ta ta ture komai ta koma kwantar mini da hankali da kalamai masu taushi da sanyi. Har sau da na ji raina ya sanyaya, na ƙara yarda a duniya bayan iyaye da dangina ba ni da wacce take yi mini irin ƙaunar da Amira take gwada mini wanda babu sirki a cikinsa.
"Yanzu dai ki tashi mu gyara ɗakin nan. Sannan na ba ki wani daddaɗan labari".
"Fara ba ni labarin tukunnan". Na yi zancen cikin dauriya ina ƙoƙarin dasa murmushi a fuskana.
"Mansur yanzu haka yana hanya. Saura kuma in munje ki ɗaure fuska ki yi ta shan magani". Ta ƙarishe zancen tana galla mini harara.
"Allah ya kawo shi lafiya".
"Amin ta hannun dama.Don Allah ki saki ranki ke ba wani shegen kyau kike da shi ba kuma ki zo kina wani ƙara haɗe hanci da gira duk sai ki ƙara muni". Ta ƙarishe zancen tana galla mini harara.
"Ai kuwa a hakan kin san na fi ki kyau sau dubu ɗari". Ta fashe da dariya tana faɗin"kin dai fi mi auki shi ma kuma girman buredi ina gaya miki, amma ni ba ta yau ba ce". Daga haka duk muka saka dariya kamar babu wani abun da ya faru, wannan dalilin yana daga cikin muhimman dalilin da yasa nake jin Amira har ƙasan raina. Don ba ta jure ganina cikin ƙunci duk yanda zai ta yi sai ta yi ta fitar da ni daga halin da nake ciki. Tare da ita muka yi komai har na ɗumama mana ragowar abincin jiya muka ci ita ma ta amso mana waina a wajen Ummanta muka ci muka yi hani'ƙan, sai na ji duk damuwar da na tashi da shi na neme shi na rasa sa. Muna gamawa wayarta ta soma ruri ta hasko mini fuskar wayar tana faɗin"kin ga Mansur ne".
Ta ɗaga ya sanar da ita ya zo muka tashi muka fito har mun zo zaure kafin ta soma ba ta labarin yadda muka yi da Abba daren jiya. Ta ja ta tsaya riƙe da kunkuminta tana kallona.
"Kina nufin Abba ya gane gaskiyar komai? Mun shige su". Na gyaɗa mata kaina alamar e.
"Wallahi ya gane komai amma na ba shi haƙuri ya ce komai ya wuce sai dai na kiyaye gaba".
Ta murmusa kafin ta ce"Allah sarki! Abba wallahi sauƙi halinsa da yanda yake kulawa da tarbiyyanki wani lokacin yana sani kewar mahaifina sai na ji duk duniyar na yi mini zafi".
Na kai mata duka a kafaɗarta"ke dai kam ki godewa Allah don Baba Habu bai rage ki da komai ba". Ta sauƙe numfashin da har sai da na jin sautinsa kana ta ce"Amatullah ba za ki gane raɗaɗin irin ciwon nan. Babu wanda yake maye gurbin iyayen sai dai kawai a kamanta". Tana gama maganar ta yi gaba ta bar ni.
Na fita a baya muka je wajen Mansur yana tsaye a jikin motarsa tana latsa wayarsa yayin da wani abokinsa take kusa da shi, da sallama ɗauke a bakinmu muka isa wajen su suka amsa mana yayin Mansur yake tattara dukkan hankalinsa kan Amira.
"Gimbiya kin fito?".
"Ai ka san ba zan zo na bar Sarkina a tsaye ba". Ta saki murmushin jin daɗi zai yi magana na katse shi.
"Tun da na ga alama idanunka ita kaɗai yake gani, babu amfanina gwada na ja ƙafafuna na koma".
"Afuwan ranki ya daɗe. Idanuna sun ganki amma zuciyar ce gabaɗaya tana tare da ita. Ya kike ya gidan?".
"Lafiya ƙalau ka zo lafiya".
Ya amsa cike da kulawa"lafiya sai dai na tabbatar da zaran na bar nan zan zama majiyanci ne". Amira ta yi masa wani kallo da hakan ya sanya sa cewa"e mana tun da sai na shafe sati guda ban yi tozali da ke ba. Wallahi Amira ba don Alhajinmu ya matsa min akan lalle ni zan wakilce sa a wannan taron ba, babu wani dalilin da zai sa na yi nisa da ke". Jim ta yi gabaɗaya jikinta ya mutu yanayinta ya sauya ta kasa cewa komai illa kallon juna da suke yi.
Ba su dawo duniyar zahiri ba sai da abokinsa ya yi magana"ni ma tun wuri bari na san inda dare ya yi min. Don na ga alama an manta da ni ".
Mansur ya ce"Haba kai kuwa Mukhtar ni na isa na manta da kai. Kawai dai ka san an ce sawun giwa ya danne na raƙumi". Dukkan mu muka fashe da dariya sai da muka tsagaita Mukhtar ya kallo ni yana cewa"kin ga ƙawarmu waɗannan mutanen ba ta mu suke yi ba.
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 6 Chapter of 24