Abba ya amsa da shi ciki-ciki bai ko kalle inda nake ba ya juya zai bar wajen, daidai sa'ilin da Amira ta iso tamkar an jefo ta sai da ta matsa kana Abba ya wuce. Ta iso inda nake yashe ta ɗago ni tsaye sai dai na kasa tsayiwa akan ƙafafuna.
"Wai me yake faruwa ne Amatullah? Tun ina wanka nake jiyo tashin hayaniya, na fito kuma na zo na tarar da taron mutane".
Na kasa cewa da ita komai illa kukan da nake yi tamkar raina zai fita, ƙafafuna suka fara rawa alamar sun gaji da ɗaukar nauyin sanƙararren gangar jiki da ba shi da maraba da bishiyar da ta baza jijiyoyinta a ƙarƙashin ƙasa. Na kwantar da kaina a saman kafaɗunta saboda jiri da hajijiyan da yake kwasa ta yana ƙoƙarin buga ni da ƙasa.
Haka har muka iso cikin ɗakinsu muka yada zango a falo har izuwa lokacin hawaye ba su bar kwaranya daga idanuna ba. Take jikina ya ɗauki zafi gau zazzaɓi mai ƙarfi ya rufe ni babu shiri na soma rawar ɗari tamkar jinjirin kazan da ruwa ya yi masa ɗan banzan duka.
"Don Allah ki yi haƙuri ki daina wannan kukan. Ki nutsu ki yi min bayanin abin da ya faru"
Amira ta yi zancen cikin damuwar da ya bayyana har a kalamanta. Na ja dogon numfashi na fesar daga bakina ina kafe ta da rinannun idanuna da suka sha kuka har suka saduda.
"Sharri suke yi mana, wallahi ba mu aikata ba".
"Sharrin kuma? Su waye suka yi muku sharrin kuma ke da waye?".
"Yaya Alhassan".
Ta maimaita sunan kafin ta zarce da faɗin"wani irin sharri? Kuma waye ya yi muku sharrin?". Sai da na cije leɓena saboda takaicin da ya cika mini raina kafin na sama zarafin cewa"Ummi da mahaifiyarta, su yi mana sharrin aikata baɗala ni da Yaya Alhassan. Lamarin da ya fusata Abba matuƙar har ya juya baya a Yaya Alhassan, Amira zuciyata bugawa take yi wallahi". Na ƙare zancen cikin rauni haɗe da ƙara fashewa da wani irin kuka mai cin rai da ruhi, na riƙo hannunta na ɗaura a saman ƙirjina da nufin ta ji yadda yake bugawa fiye da kima a kimiyance.
Duk ƙarfin hali irin na Amira sai gabaɗaya jikinta ya yi sanyi ƙalau ta kasa cewa da ni komai balle ta iya furta kalaman rarrashi a gare ni illa kallo na da ido tamkar majigi.
"Amira zan je na yi Abba bayanin duk abin da ya faruwa. Zan je na goge zargin da ya ɗarsu a cikin ransa". Na ƙare zancen tare da yin zumbur zan miƙe ta riƙo hannuna gam.
"Kar ki je kar ki je yanzu, ki bari sai ya huce tukunnan kafin ki je masa da kowani bayani". Na girgiza kaina"ba zan iya jira ba don hankalina ba zai taɓa kwanciya ba". Na yi kai aya ina ƙoƙarin fizge hannuna daga riƙon da ta yi mini sai dai ban yi nasarar yin hakan ba.
"Amatullah ki nutsu mana. Ba ki da kalmomin da za ki yi amfani da shi a yanzu wajen fahimtar da Abba ya fahimce ki saboda ransa ya riga da ya ɓaci. Ki yi haƙuri ko zuwa gobe da safe ne sai ki yi masa magana".
Na gaza cewa komai na faɗa jikinta ina ƙara sakin wani kukan mai matuƙar sauti, haka na ci gaba da yi duk lallashin da take yi mini bai yi amfani ba. Har sai da mahaifiyarta ta shigo ta sanya baki haka na lafa ta tashi ta shiga cikin uwar ɗaka ta bar mu.
"Yanzu za ki tashi ki je ki kwanta ne ko kuma? Don kin ga Baba Habu yana gari ni zan je gidan Ta salla ne na kwana....".
Na ji caraf na katse ta"daman kina zuwa wani wajen kwana ne?".
"Ban taɓa zuwa ko ina ba yau ne dai zan fara. Don ko Umma ba ta fito ta faɗa min ba na lura akwai takura a zaman, na yanke shawarar in dai Baba Habu yana gari zan dinga zuwa kwana sanda baya nan sai na kwana a gida".
"Waye ya ba ki wannan gurguwar shawarar Amira?. Duk wata ƴa mace fa kwana a cikin gidan mahaifinta ko da kuma filin taku ɗaya ne shi ne cikar darajarta".
"Ya kamata ki fahimce ni Amatullah don ke ma a cikin wannan yanayin kike. Ki na gaji dai gidan kowa ɗaki ne da falo gare shi, in dan Baba Habu ya dawo shi da Umma suna cikin ɗaki ni kuma ina kwanciya a falo amma hakan bai hana ni sauraron duk abin da suke yi kamar a gabana suke aiwatarwa ba, hatta idan suna raya sunna ina ji yi sumbatun da suke yi. To da hakan ya ci gaba da faruwa ai gwara na nemawa kaina mafita ko?".
Kalamanta suka sanya jikin mutuwa murus, tabbas indai zan yi wa zancenta adalci da duba irin na hankali haƙiƙa hukuncin da ta yanke shi ne daidai.
"Haka ne kam ki na da gaskiya".
"Ke ma kuma zan so ki bi hanyar da na bi". Murmushin ƙarfin hali kawai na sakar mata kafin na ce"sai Abba ya sauƙo tukunnan, amma kema da kin yi haƙuri yau dai mun kwana tare a nan tun da kin ga halin da nake ciki. Wallahi ba zan iya komawa ɗakinmu alhalin na san Abba yana fushi da ni ba".
"Ba matsala kin san ina son duk abin da zai sanya ka farin ciki ai".
Murmushi kawai na sakar mata, muka yi salla ta kawo mana abinci sai dai na kasa kai koda loma guda cikin bakina haka na kwanta. Raina cike fal da tarin damuwa da fargabar abin da gobe za ta haifar.
[10/16, 12:34 PM] Maimunatu Iyam🥰: *DAFIN HARSHE*
©️ Maimuna Tijjani Iyam
______________________________________
Page 3️⃣0️⃣
Haka na ji ta juye- juye a bisa shimfiɗan bacci ya gagari idanuna, ya bushe ƙamas kamar soyayyen fikin da aka zuba a cikin mai. Ina jin Amira ta na ta hira da masoyinta Mansur a waya cikin nishaɗi da walwala.
Sun daɗe suna wayar har sai da dare ta raba kana suka yi sallama, na juya ina kallon ta duk da duhun da ya mamaye ɗakin na furta"masoya kun yi sallama kenan? Na yi tunanin ai yau soyayyar za ta hana ku bacci". Ta murmusa kafin ta ce"ai ba mu ƙi mu kwana muna wannan wayar ba, wallahi idan ina tare da Mansur ko a waya ne sai na ji duk na manta duk wani damuwar da yake addaban raina. Ina samu nutsuwa sosai daga gare shi".
Na taɓe baki"kuma duk kin san da hakan amma kika kasa sakan kowa ki kama shi. Duk da nutsuwar da kike samu daga gare shi hakan bai hana ki ganin wasu mazan ba har alaƙar soyayya ta gifta a tsakaninku".
Ta sauƙe numfashi mai zafin da har sai da na jiyo sautinsa kafin ta sama lasisin faɗin"duk na san da hakan Amatullah amma kin sa komai na rayuwar nan sai ana yi ana lissafi, sama da saurayi ɗaya ai tsautsayi ne babba idan ya juya min baya lokaci guda kuma ya ya zan yi ni ƴasu".
"Amira kenan! Ki na raina ikon Ubangiji kenan? Allahn da ya ba ki Mansur a lokacin da ba ki yi tsammani ba shi zai kawo miki wani a lokacin da ba ki yi zato ba. Ki tsarkake zuciyarki kawai ki so mutum guda in sha Allah ba za ki kunyata ba".
"Ki kwanta ki huce gajiyar da kika kwaso wa jikinki Amatullah, don wannan maganar takin ba ta da matsuguni a cikin kwanyanta".
Ta yi zancen tana gyaran kwanciyarta, taƙaitaccen murmushi kawai na yi ina sauƙe ɓoyayyar ajiyar zuciya mai nauyin gaske. Duk yadda na so baccin ya zo mini lamarin ya gagare ni wai ƙoƙarin cire wando ta kai, haka na ci gaba da juyi ina sauƙe numfaffashi tamkar wacce ta yi aikin fasa dutse.
Runtse idanuna na yi da ƙarfin gaske ina karanto ƙarin da Malam Suleiman ya yi mana yau, har aka yi ƙiran assalatu ban runtsa, ladanin yana ƙwala ƙiran sallan farko na tashi na zauna tamkar a daidai ƙofar kunnena ya ƙwala.
Na tashi Amira muka fito muka yi alwala, muka koma muka yi sallan, ina kammala azkar ɗina na miƙe Amira ta bi ni da kallo.
"Ina kuma za ki je?".
"Zan je wajen Abba ne. Don wallahi daren jiya ko runtsawa ban iya yi ba tsabar firgicin da zulumin da ya cika mini zuciya". A sanyaye ta ce"to ki dai nutsu kar ki je ki tsaya kuka kawai maimakon bayani. Kuma ki je ki dawo ki same ni don Ummi ba za ta ci banzan ba billahillazi".
Ban ce da ita komai ba don na fahimci ko na furta ba za su shiga cikin ƙoƙon kanta ba.
Ina fitowa Baba Habu tare da Abba suna shigowa sun dawo daga masallaci, na tsaya a inda nake cak har sai da Abba ya wuce ɗakinmu Baba Habu ma ya nufo ƙofar su kaina a ƙasa na gaishe shi ya amsa tamkar wanda aka yi wa dole tana ɗaure fuskarsa tamau, ajiyar zuciya na sauƙe mai ƙarfi don tun daren jiya na lura tamkar bai so kwanan da na yi tare da Amira ba, kawai dai da yake Umman Amira ta fi shi ƙarfin faɗa a ji ne a zamantakewar su, shi yasa ya saduda.
Tamkar kazar da ƙwai ya fashe mata a ciki haka nake ɗaga ƙafafuna da nake jin su tamkar ba a a jikin gangar jikina, na iso ƙofar ɗakinmu na raba tsakanin haƙwaraina da ƙyar kafin na shiga doka sallama, sai da na yi baki uku ana huɗu na jiyo muryan Abba ya amsa.
Haka kawai na tsinci kaina cikina matsanancin faɗuwar gaba yayin da nake shigowa cikin ɗakin, da ya gauraye da hasken rana tocila.
Na zaune a ƙasa zan nesa da shi kaina a ƙasa na gaishe shi fuskarsa babu yabo babu fallasa. Sai da na aro jarumta na yafawa kaina kafin na soma magana cikin sarƙafewar harshe.
"Abba wallahi sharri Ummi take yi mana ba mu aikata abin da suke zargin mu ba da Yaya Alhassan. Hasalima na bi shi waje ne don na ba shi haƙuri akan abin da ya faru, shi ne ya zaro handkerchief daga ajihunsa......". Ya ɗaga mini hannu alamar na dakata.
"Ni ma na san ba ku aikata ba Amatullah, tun kafin a haife ki na san wane ne Alhassan na kuma san ɗabi'u da halayansa baki ɗaya. Amma dole ya janye ƙafafunsa daga zuwa gidan nan na ɗan wani lokaci ko da kuwa wannan abun bai faru ba ma, ko don rashin fahimtan da suka samu da mahaifiyarki".
Na ja jikina na iso gabansa na haɗe hannayena waje guda alamar roƙo ina cewa"Abba ka yafe mini na san jinya ka kwana da ɓacin raina a cikin zuciyarka, wannan dalilin ne ya sa na kwana a ɗakin su Amira don ba zan iya fuskantan ka a irin wannan yanayin ba".
"Uwata ba ki yi min komai ba da har za ki nema gafarana, kuma ban kwana da baƙin cikinki ko takaicinki a cikin raina ba. Babban damuwata ma shi ne yadda ran Ummanki ya yi maƙurar ɓaci".
Jikina gabaɗaya ya yi luƙus jin abin da Abba ya furta na zame na yi zaman dirshan ina ci gaba da sauraron jawabin da ya ɗaura da shi.
"Allah ya jarabce ni akan mahaifiyarki har cikin raina na tsani duk wani abun da zai sosa mata rai. Na ƙi jinin duk wanda zai tsaya a gabanta ya yi furucin da zai baƙanta mata rai ko wane ne shi, kuma komai girman alaƙar dake tsakanin mu da shi zan iya yanke alaƙa da shi".
Na sauƙe tagwayen ajiyar zuciya kafin a sanyaye na ce"in sha Allah komai zai wuce Abba, amma su Yaya Alhassan kam ai ni da su mun zama abu guda a gare ka. Idan har zuciyarka za ta iya yafe mini to tabbas su ma sun cancanci hakan". Ya yi hanzarin taran numfashina"akwai bambanci ke a ni kika yi wa laifi yayin da su kuma ran Hafsatu suka baƙanta. Zan iya yafe duk girman laifi amma ban da wannan". Ban iya cewa komai ba saboda zallar ruwan mamakin da zantukansa suka shayar da ni, na tashi na fito na soma shara ina jin ciki tamkar an yi yasa don rabo na da abinci tun jiya da rana.
Sai da na gama na hura wuta na ɗaura girki ina kammalawa na ɗeba nawa na ci a wajen kana na shigarwa Abba na sa ciki. Kamar ƙaramin yaro haka ya ke cin abincin hannu baka hannu ƙwarya na yi sakeke ina kallon sa raina cike da tarin tausayinsa don na tabbatar shi ma rabon sa da abinci tun jiya, hawaye suka zubo daga idanuna na yi hanzarin kawar da su.
"Uwata tunanin me ye kike yi haka kin yi shuru?".
"Babu komai Abba, Umma ba ta tashi ba ne?".
"Ba ta tashi ba, amma Uwata tabbas akwai wani abun da yake damunki. Ki saki jikinki ki sanar da ni ko mene ne, shin ki na da wanda ya kai ni ne a gare ki?". Na jijjiga kaina cikin sanyin jiki da hakan ya ba shi damar ci gaba da cewa"to mene ne haka a ranki kike wannan dogon tunanin?".
"Abba ina so na roƙi wani alfarma ne a wajen ka".
Ya kai lomar da ya ɗauko kafin ya ce"faɗi kanki tsaye in har ina da halin yi miki to ki sa a ranki kin riga da kin samu". Na ɗan ji jim kafin na ce"daman akwai wani gida ne a nan bayan layin, matar mijinta ya rasu daga ita sai ƴaƴanta biyu kuma duk samari ne ba sa zaman gidan. Shi ne Amira za ta na zuwa gidan ta na kwana saboda Baba Habu ya dawo, zaman cikin da falon akwai takura".
Ya kare ni kafin na isa inda nake son tsayawa"yanzu dai me ke kike so?".
Na sadda kaina ƙasa kafin na sama zarafin ci gaba da cewa"shi ne nake roƙan alfarma a wajenka inda ka amince sai na dinga bin ta muna zuwa can muna kwana tare". Ya yi shuru kamar bai ji ni ba hakan ya ƙara sanyaya mini dukkan jikina, bai amsa mini ba ya ci gaba da cin abincinsa har sai da ya gama cin abincin tas ya kwance hannunsa ya yi hamdala bayan ya ɗaura da ruwan da na kawo masa.
Na tashi na tattare kwanukan na fitar wajen na wanke su kana na ɗaura ruwan zafin dama kunu, na koma ciki da nufin duba ko Umma ta tashi har yanzu Abba yana nan zaune a inda na bar shi bai ko motsa ba.
Na yi masa sannu ya amsa zan shige ya ƙira sunana na dawo na tsuguna a gabansa.
Ya kafe ni da ido yana faɗin"na yi nazarin maganar da kika faɗa na duba na ga dacewar hakan, sai dai wani gida ne za ku na zuwa kwanan?". Na yi caraf na ce"nan ne gidan Ta salla matar marigayi Alhaji Bashiru mai kwanuka".
Ya yi ɗan jim kamar mai nazarin wani abun kafin can ya ce"shikenan za mu magana da Ummanki, Allah ya sa ta yarda don in ba ta yarda ba. Ba zan yi mata dole ba, zan kuma yi bincike akan gidan ita Ta sallan".
A sanyaye na ce"na gode Allah ya ƙara girma".
Kafin ya kai ga amsawa Umma ta fito tsam Abba ya miƙe zai je gare ta, ta buga masa wani uban hararan da ya tsaya sa tsayawa cak har sai da ta iso ta zauna kana shi ma ya koma mazauninsa ya zauna, yana yi mata sannu da fitowan da ko amsa masa ba ta yi ba. Na gaishe ta ta amsa fuskarta babu yabo babu fallasa.
"Ranki ya daɗe daman wata alfarma muke nema a wajen ki". Abba ya yi zancen cikin matuƙar ƙanƙan da kai da girmamawa.
"Ina jin ka". Umma ta amsa da shi cikin isa da gadaran da ya haɗe da tsantsan izza.
"Daman ɗiyarki ce ta zo da wani batun da na yi na'am da shi, ta ce tana so su na zuwa gidan Ta salla suna kwana tare da Amira saboda yanayin ɗakunan namun. Ga shi kuma kullum yaran ƙara girma suke yi akwai abubuwan da bai dace sun ji ko suna gani ba, gare ni kam babu matsala na yarda sai dai duk yadda kika ce haka za a yi ranki ya daɗe".
Ta yi banza da shi na tsawon wasu mintuna da har sai da na ji daman ban zo masa da zancen ba, wataƙila da ban ja masa wannan abun ba. Sai da muka cire rai da samun amsarta kana ta buɗe baki ta yi magana.
"Ka san ƴar uwarka ma ta zo da makamancin wannan zancen amma ban amince ba. Duk da ba na son abin da zai sa Amatullah ta yi nisa da ni amma ina ji zan iya amincewa da wannan ko don na nunawa ƴar uwarka cewar na isa da gidan aurena kuma ina da ƙarfin gwiwan juya komai". Cikin sanyin jiki da na murya Abba ya ce"yanzu dai ki na nufin kin amince kenan?".
"Na amince".
"To muna godiya sosai ranki ya daɗe. Allah ya ƙara lafiya da nisan kwana mai amfani, Allah ya bar mana ke ki yi tsawon rai ki yi shekaru irin na dabino".
Abba ya yi kalaman tamkar zai yi mata sujjada tsabar ƙanƙan da kai da biyayya. Ni ma godiya na gabatar mata ta ce na je na dama kunun don yau ba ta jin daɗin jikinta.
Na fito waje na ja kujera na zauna na zabga tagumi, ban yi aune ba na yi an watsa mini ruwa a fuskana. Ko gizau ban yi ba don na san babu wanda zai yi mini hakan face Amira. Ta ja kujera ta zauna kusa da ni tana faɗin"me ye kuma ya faru kika zo kika zabga tagumi haka?". Na ƙi na kula ta amma hakan bai hana ta ci gaba da faɗin abin da yake ranta ba.
"Ya ya kuka yi da Abban?". Na zame hannuwana kafin na kwashe duk yadda muka yi na sanar da ita hatta da maganan zuwa na kwana gidan Ta salla da muka yi, ta yi ta murna tana zantuka cikin jin daɗi. Haka na dama kunun na gama komai na kashe wutar ina wanke tukunyar Ummi ta fito daga ɗakinsu ta ci kwalliya tana zaunar chew gum ƙas ƙas. Amira ta yi wuf ta sha gabanta.
"To tauraruwa mai wutsiya dilallalan sharri ke da uwarki. Kun yi tunanin kun yi mata sharri kun ci banza kenan ko? To wallahi bashi kuka ɗauka sai na nuna muku bambamcin dake tsakanin ruwa da wuta, sai na haɗa miƙa gurmin da duk danginku ba za su iya kawo ƙarshensa ba. Sai kin zubar da hawaye kin yi kuka fiye da yadda Amatullah ta yi".
"Ahayye nanaye. Har da su kaza a cin danƙo? Ai ko giwa ta faɗi ta fi ƙarfin kiyashi su ja ba. Sanin kanki ne ni Ummi na yi muku nisan da har a naɗe duniya ba za ku iya iske ni ba". Amira ta bushe da dariya har da tafa hannu kana ta furta"to ina abin yake wai maye ya ci jajiri, ai ke ma kin san cewa ruwa ba sa'an kwando ba ne. Kuma ko da girgiza kurna ta fi magarya zaƙi, Ummi ga fili ga mai doki mu zuba ni dake sai mu ga wanda zai kwashe. Haka za ki ƙare da saurayi guda ɗaya mai jaraban nacin tsiya babu ko sisi a aljihunsa don lalacewa ma kwanon abincin safensa, rana da dare duk yana gidanku. Ban da rashin sanin ciwon kai". Da alama maganar ya yi matuƙar girgiza zuciyar Ummi don sai ta gaza cewa komai illa cizon ƴatsan da take yi cikin takaici. Ganin mutane sun fara fitowa daga ɗakunansu ya sani tashi na je na janye Amira ina ba ta haƙuri sai ba ta fasa zazzago zancen ba har sai da Ummi ta fice.
"Ban san yaushe za ki dinga ɗaukar abubuwa a hankali ba Amira. Yanzu dai ki je ki shirya ki zo mu tafi". Harara ta banka mini ta yi shigewarta ɗakinsu ta bar ni tsaye. Sai da na gama duk abin da nake yi na shiga ciki na tambayi Umma ko za a kawo mata abinci ta ce ba yanzu ba don haka na shiga ɗaki don na ga alamar kamar akwai abin da suke tattaunawa.
"Hafsatu ki yi wa Allah ki yi Manzon da ya karɓo mana sallalo biyar da muke yi a yini. Ki cece ni sau sausauta wannan hukuncin da kika yanke ya yi min tsauri, Maman Umar kamar uwa take a gare ni kuma ta yi ɗawainiyya da ni da tun ina yaro, ta sadaukar da abubuwa da yawa da suke mallakinta domin ji daɗina. Ta kan iya kana cikinta abinci ta ɗauka ta ba ni tana son duk wani abun da nake so ko da kuwa ita a ranta bai yi mata ba. Ta kan saurare ni ta ji damuwata kuma ta magance min ita, ba taɓa zuwa wajen da wani buƙatar da ta gaza biya min ita ba. Ta ya ya kike tunanin zan iya kallon tsabar idonta na ce da ita kar ta sake zuwa gidana don matata ba ta buƙatarta?".
Daidai lokacin da nake shiga cikin ɗakin na ji zancen Abba ya sauƙa a kunnena, na shiga daga jiki na tsaya a jikin labule ina ci gaba da saurara don ba kaɗan ba zancen ya ja hankalina.
"Ai kuwa sai dai ka zaɓa ko ni ita Maman Umar ɗin. Don duk ranar da ta ƙara zuwa cikin gidan nan, to ka ƙaddara a ranka cewar a ranar a gidanmu zan kwana".
A raunane tamkar mai shirin yin kuka na jiyo muryan Abba yana cewa"kin san ko da wani mahaluki aka haɗa aka ce na zama ke zan zaɓa Hafsatu akan kowa da komai. Amma ki dubi girman Allah ki janye wannan ƙudurin nakin, na yi imanin wannan abun da ya faru ma zai sa ta taƙaita zuwan da take yi ba sai na je mata da wannan zancen ba".
"Manniru idan ba za ka iya ba ni ba, ni ka ba ni iznin na wanke ƙafafuna na je na iske ta har gida na sanar da ita". Da hanzari Abba ya furta"A'a ba sai kin je ba zan je da kaina na sanar da ita". Sulalewa na yi zuwa ƙasa na durƙushe akan gwiwoyina ina kuka marar sauti, jin motsin za a shigo ya sani na yi wuf na tashi na ɗauko kayana na fito banɗaki na shiga na yo wanka na saka kayan da na shiga da su. Don tun ranar da Baban Vector ya bankaɗo ƙofar banɗakin Ina wanka na fara shiga da kayana inna gama wankan sai na saka su na fito abin na tsaf.
Sanda na fito na iske Abba har ya fita na shirya, na yi wa Umma sallama na fito na tarar Amira har ta shirya ni kawai take jira. A zaure muka tarar da Ummi da Auwal suna zancen muka wuce su bayan Amira ta buga musu wani uban tsaki tamkar ta ga kashi.
Har muka bar cikin layinmu ban ce komai hakan ya sanya Amira cewa"ke kuma lafiyarki Madam?".
Na ja dogon numfashi na fesar kafin na ce"Amira a iya sani na a bisa addini da al'adarmu na Malam Bahaushe mace ita take yi wa mijinta biyayya. Bai dace ta ɗaga murya ga mijinta ba amma gabaɗaya Umma ba haka take ba. Yanzu Abba har shakkan ta yake yi idan zai yi mata magana har jikinsa ruwa yake yi".
"To ke me ye matsalarki da hakan?".
Na yi mata wani kallo"a ganinki hakan ya dace ne Amira?".
"Ko mai dace ba to ke ina ruwanki da rayuwar da suke yi a tsakanin su? Ke yanzu babu dama mace ta zauna da mijinta lafiya sai ki yi wani tunani na daban Amatullah. Ai so da ƙauna gami da zaman lafiya shi yake kawo hakan in ba ki sani ba na gaya miki". Ban kuma cewa da ita komai har muka isa tashan duk da kuwa yadda ta yi ta ja na da hira, ranar Bashir ma bai sama kaina ba muna barin tashan na ce Amira ta raka ni gidan Anty Sawwama ta ce kar na je yanzu na
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 17 Chapter of 24