ki".
"Babu komai na ce miki babu komai. Ki yarda da ni mana Amira". Ina ƙare zancen na miƙe tsaye na ɗaura daga inda na tsaya"kin ga ni bari na je na duba ko Umma ta dawo". Ban jira abin da za ta ce ba na yi wuf na fice.
Kai tsaye ɗakinmu na nufa sai dai kafin na kai ga shiga muryar Baban Adnan ya tursasa mini dakatawa.
"Amatullah ƴan mata, kwana biyu kamar ba kya cikin gidan nan". Maimaikon na ba shi amsa sai na rusuna na gaishe shi na yi wucewa ta cikin ɗaki da mamakina na tarar da har yanzu Umma ba ta dawo ba. Na fito na yi alwalan sallan magrib na zo na yi ina raka'ar ƙarshe Umma ta shigo cikin ɗakin ta zauna tana huce gajiyar da ta kwaso.
Sai da na iddar na shafa addu'ar da na yi kafin na yi mata sannu da zuwa ta amsa mini fuskarta babu yabo babu fallasa, so nake yi na tambaye ta inda ta je amma sam tsoro ya yi mini katutu na kasa cewa komai.
"Umma me ye za a dafa ne?"
"Ki tafasa doya".
"To".
Na amsa da shi a taƙaice ina tashi na fita na haɗa wuta na ɗaura ruwa. Yayin da na ɗauko doyar ina ferewa na zuba a cikin tukunyar. Na ɗaukar jakar islamiyyata ina duba litattafaina. Ban tashi daga wajen ba sai da doyar ta dahu ba soya manja kana na shiga ciki na zuba nawa na ci na yi sallan isha'i na fito zaure wajen yaran da suke jirana. Sosai na zage damtse na yi musu karantu duk wani ƙoƙarin manta abin da yake ta'azzaran raina na yi shi. Muna tsaka da karatun Ummi ta fito daga cikin gida ta tsaye mini a kai kamar mai karɓan bashi.
"Ummi lafiya?".
Ta riƙe ƙugunta tana yi mini kallon hadirin kaji ta ce"ku tashi ku nema wani wajen, zan shigo da Auwal".
Na cira kai ina duban ta da mamakin rainin wayon da yake tafe da ita.
"Ban gane mu nema wani wajen ba? Sanin kanki ne a ko wani daren duniya a cikin zauren nan muke yi karatu a daidai irin wannan lokacin. Sai yau kawai za ki ce mu nema wani wajen don za ki yi zancen, ai kuwa sai dai ke da shi Auwal ɗin ku nema wani wajen".
Ta yi poster tana ganina da nake da tabbacin mamakin furucina ne ya hana ta motsawa.
"Lalle Amatullah wuyanki ya yi kauri ya isa yanka. Yau zan bar ki ne kawai amma wallahi gobe ba za ku yi karatu a nan ba".
"Ba gobe ba har jibi da gata ma a nan za mu yi, ki sa hakan a cikin ranki". Ba ta tanka mini ba illa dogon tsakin da ta ja ta fice daga ciki zauren tana shuri da takalmar yaran, na raka ta da kallo har ta fice kafin na ɗauke kaina. Babu jimawa Abba ya dawo na tashi na yi masa sannu da zuwa kana ya shige cikin gida. Ƙarfe tara muka yi addu'a kowa ya watse na naɗe tabarmar na shigo cikin gidan, muka yi kiciɓus da Amira za ta fita daga ni har ita dariya muka sakarwa juna. Na matsa na ba ta waje ta wuce ina faɗin"Allah ya shirya ki ke kam".
Ta bangaje ni"ki sa munjaye Allah dai ya shirya mu". Daga haka ta fice ni ma na ƙarisa ɗakinmu.
Cak! Na tsaya na ɗaga ƙafarta ɗaya amma na gaza sauƙe ta sakamakon zancen da suka sauƙa a ƙofifin kunnuwa tamkar sauƙar aradu, take jikina ya soma rawa kamar ana jona mini wutar lantarki. Zuffa ya soma tsatstsafo wa daga dukkan mafitan gashin jikina, tsoro da firgici ya bayyana ƙarara a fuskata. In dai ba matsalar ji na samu ba tabbas muryar Abba na ji yana cewa"Hafsatu na gama ki da girman Allah kar ki yi fushi da ni zuciyata ba za ta iya jura ba, na yarda ki hukunta da ko wani irin nau'in hukunci amma ban da wannan. Na biya ta wajen Maman Umar ne shi yasa ban dawo da wuri ba ban san hakan zai ɓata miki ba da ban tun magriban fari na dawo cikin gidan nan".
"Manniru ni fa ba zan juri wannan cin mutuncin ba. Sati ba ta cika ba tare da matar nan ta wanko ƙafarta ta zo cikin gidan nan ba yanzu kuma kai da ka baro wajen aiki sai ka wuce wajenta kafin ka iso gida. In ce dai tun ƙarfe biyar kuke tashi daga makarantar amma don kuturun wulaƙanci sai ƙarfe taran dare za ka shigo min cikin gida".
Cikin wani irin yanayin na tsinkayo muryar Abba yana faɗin" ki yi haƙuri in Sha Allah hakan ba zai ƙara faruwa ba".
"Wai Maman Umar ɗin nan ita ta haife ka ne? Ko ita ta yi naƙudarka sai haka. Ni fa na gaji ba zan ɗauki wannan rainin hankalin ba".
Kamar an jawo ni haka na ji na faɗa cikin ɗakin sai dai na yi nadamar shiga ta saboda yanayin da na iske su a ciki. Umma tana tsaye yayin da Abba kuma yake durƙushe akan gwiyoyinsa ya riƙe ƙafarta.
Zuciyata ta yi wani irin harbawa sai da na ji duniyar gabaɗaya tana juya mini a lokacin. Da gudu na shige ɗaki na zube akan gado, sai dai sam na gaza yin ko ɗigon hawaye duk da suyan da zuciyata yake yi mini. Na sa hannuna na toshe dukkan kunnuwana saboda amsa-kuwwar da zancen da na ji suka yi mini a na'urar naɗar sautina.
Har Umma ta shigo cikin ɗakin ban motsa daga kwanciyar ruf da cikin da na yi ba, ba ta ce da ni ko kanzil ba ta ɗauki abin da ya shigo da ita ta fita. Ba ta dawo ba sai da dare ta raba sosai ta shigo ta kwanta.
[7/25, 11:19 AM] Maimunatu Iyam: *DAFIN HARSHE*
©️ Maimuna Tijjani Iyam
___________________________________
Page1️⃣6️⃣
Har dare ta raba bacci ta ƙi kusanta na illa juyin da nake yi raina cike da wani irin zogin da raɗaɗin da yake tasowa tun daga ƙasan raina yana mamaye mini dukkan sashin da sassan ruhina. Sai da na tabbatar da Umma ta yi nisa a baccin da take har da munshari kafin na tashi na fito na yi alwala na zo na tada salla. Raka'a biyu na yi na sallame na ɗaga dukkan hannayena sama ina yi wa Allah kirari kafin na soma zayyana matsalolina na ƙarƙare da yin addu'ar da Malam Suleiman ya ba ni kafin na shafa addu'ar cikin sanyi da mutuwar jiki.
A zaune a wajen na ƙarisa daren yau sai can gabannin asubahi na runtsa ban yi nisa ba na ji an soma ƙiran sallan asubahi, na yi figigi na tashi ina murtsule idona tare da ƙara kasa kunna don tabbatar da abin da kunnuwana suke jiyo mini. Sai da na tabbatar da cewa lalle sallan ake ƙira kafin na tashi riƙe da kaina da yake matuƙar sarawa, na buɗe ƙofan ɗakin raina cike tal da mamakin abin da ya hana Abba tashi akan lokaci.
Turus na ja na tsaya bayan na kunna ƙwan wuta haske ya gauraye ɗakin. Na hangen Abba kwance a makwancinsa ko tashi bai yi ba, na je na tsuguna a gaban sa na ɗan buga matashin take ya buɗe idonsa ya tashi ya zauna.
"Subhanallahi! Kar dai har an yi ƙiran salla?".
"Tun ɗazu aka ƙira".
"Wallahi gabaɗaya na tara gajiya ne a jikina jiya. Shi yasa tun da na wanka ko juyi ban yi ba".
Na jinjina kaina"bari na je na sama maka ruwa a buta". Zan tashi ya dakatar da ni.
"Ki fara zuba wa Ummanki tukunnan. Bari na je na tashe ta". Na sakake ina kallonsa har ya tashi ya shiga cikin ɗakin na kasa tashi daga wajen. Sai da na sauƙe gwauron ajiyar zuciya kafin na tashi kamar kazar da ƙwai ya fashe mata a ciki na fita waje. A buta biyu na zuba ruwan kana ni ma na zuba nawa na yi na koma ciki na gabatar da sallan ko da na iddar ban tashi daga kan slalayan ba na ɗauko al'ƙur'ani na soma karantawa a ƙoƙarin dawo da nutsuwar zuciyata. Ban gushe ina yi ba har sai da na jin ɗan sanyi a cikin raina kana na rufe na ajiye na tashi na soma gyara ɗakin na gyara ko'ina kana na ɗaura mana abin kari.
Na kawo wa Umma da Abba na su, ko gama ajiye wa ban yi ba Umma ta soma faɗin"A'a ni kam ba zan ci ma wannan abincin ba ɗauke shi kawai".
A hanzarce Abba ya ce"to me ye kike so ki ci?".
Ta yatsina fuska"ba na jin sha'awar cin komai".
"A'a haka kuma ai ba zai yiyu ba ace kin zauna ba tare da kin ci komai ba. Ki faɗi duk abin da kike son ci ni kuma na yi miki alƙawarin samo miki shi matuƙar dai akwai shi a cikin wannan duniyar da muke rayuwa".
"Gandan shanu nake so ci da matsatstsan ruwan rake".
Babu shiri na cira kai ina ganin Abba da ya miƙe tsam yana faɗin"yanzu zan fita neman sa ba kuma ba zan dawo ba har sai na samu miki su".
"Abba ka kawo na je na nemo mata, tun da kai ka ga wajen aiki za ka je. Kar ka yi latti ka kawo kawai".
"A'a Amatullah ni nake da alhakin nema mata duk abin da take buƙata. Don haka ki bar ni na je da kaina don sauƙe haƙƙinta da yake kaina".
Yana rufe bakinsa ya fita daga cikin falon da hakan ya yi daidai da sa'ilin da Umma take tuntsirewa da dariya mai ƙarfin gaske har da tafa hannu.
"Wa ya faɗa maka borno gabas yake Manniru?. Ai kowa ya ce bai iya kuka ba to uwarsa ce ba ta mutu ba, mu zuba ni da kai ɗan halak ka fasa". Ban san lokacin da idanuna suna fara tsiyayar da ƙwalla ba sai ɗumin su da na ji a bisa dandamalin kuncina suna sauƙa har izuwa tudun wuyana. Har na buɗe baki zan yi magana Umma ta watsa nuni wani hargitsatstsen kallon da ya tursasa mini yi wa bakina linzami.
Kalaman da ta yi mini da ƙarfin sanin halinta da na yi suka soma yi mini shawagi a tsakiyar kwanyata. Kif na rufe bakina na juya na fita ban tsaya a ko'ina sai cikin banɗaki na zauna na ci kuka kamar raina zai fita har sai da na godewa Allah.
Na fito na zauna na yi jigum na kasa shiga cikin ɗakin kuma na rasa wanda zan sanarwa damuwata ko da zan ji sanyi a cikin raina. Ko na yi yunƙurin aikata hakan ikirarin tsinuwan da Umma da yi mini idan na yi maganar da kowa sai na ji duk jikina ya yi sanyi ƙalau kamar kazar da aka jefa da ruwan gishiri.
"Amatullahi baiwar Allah. Ina fatan dai lafiya ko? Kin zabga tagumi da safiyar nan".
Muryar Baban Adnan ya dira a ƙofofin kunnuwana da ya tursasa mini cira kaina ina duban sa yana tsaye a kaina ya zuba mini idanuna kamar yau ya saba kallona.
"Ina kwana".
Na jefa masa gaisuwa maimakon ya amsa sai ta jefa muni wata tambayar ta daban da ba ta da haɗi da zancen da na yi masa.
"Murmushi ne ya fi dacewa da fuskarki ba tagumi ba". Ban ce da shi uffan ba na tashi zan shige ɗaki muka yi kiciɓus da Umma za ta fito daga ɗakin na matsa na ba ta hanya ta wuce kafin ni ma na shige ciki. Kai tsaye cikin ɗaki na nufa raina a jagule gabaɗaya na rasa gane abin da yake damuna balle har na iya siffanta shi cikin kalma guda. Duk wani addu'ar da ya zo kaina a lokacin sai na yi sa don kawai na samarwa kaina sauƙin halin da nake ciki na suya da radaɗin zuciya.
Ina kwance akan gado na ji an ɗanna mini dundun a gadon bayana ban motsa ba. Illa runtse idanuna da na yi ina cije leɓena don na san babu wanda zai yi nuni hakan face Amira. Ba tare da na buɗe idona ba na furta"don Allah Amira ki bar ni, ba na cikin yanayin da za ki yi mini irin wannan wasan. Ki bar ni da abin da yake damuna kawai.....". Kafin na rufe bakina na ji ta ɗane kan gado ya na jan ƙafata take faɗin"tashi ki sanar da ni abin da yake damun nan ki".
Na ƙare runtse idanuna"don Allah ki bar ni". Na ƙare zancen ina juya mata baya amma hakan bai hana ta aikata abin da ta yi niyya ba.
"Wallahi sai kin tashi ki yi min bayani. Tun jiya na fahimci kina cikin damuwa amma kika ce da ni babu abin da yake damun ki. Amatullah ni da ke fa yanzu mun wuce matakin ƙawayen da zaman gidan haya ya haɗa mu, mun zama tamkar ƴan uwan da suka fito daga cikin ɗaya da ba za iya ɓoyewa junansu komai".
Na ja dogon numfashi na fesar ina tashi na zauna kana na sama zarafin faɗin"tabbas ina cikin matuƙar damuwa amma ba zan iya sanar da ke abin da yake damuna ba. Iya ƙaunar da za ki gwada mini shi ne ki taya ni da addu'a Allah ya kawo mini sauƙi da mafitan halin da nake ciki".
Ta yi ƙuri tana kallona har na kammala zancen ba tare da ni komai. Ta riƙo hannuna ta sa cikin nata tana murzawa a hankali kafin ta soma cewa"in sha Allah zan taya ki da addu'a Allah ya yaye miki duk abin da yake damunki. Amma don Allah ke ma ki cire damuwa daga cikin ranki. Rayuwar nan fa kowa kike gani yana da na shi matsalar, idan kika zauna kika ji damuwa da matsalar wani wallahi sai kin yi mamakin yadda zuciyarsa ta iya ɗaukar wannan abun kuma har take iya yin dariya da walwala. Amatullah haƙuri, juriya da miƙa lamuranka ga Allah su ne kaɗai abubuwan da suke wadata rayuwar ɗan Adam da haske kowa kuwa ƙunci da baƙin ciki ya yi masa katutu".
"In sha Allah zan yi amfani da shawarwarinki Amira na gode sosai". Na ƙare zancen hawaye suna gudu a fuskana, ta sa hannu tana share mini su tana yi mini tsiya.
"Daɗina da ke ragwanta abu kaɗan sai kuka, kamar yaron da aka ƙwace wa alawa".
Dariyar yaƙe na yi ina kallonta kan ka ce kwabo ta warware mini duk ƙullin da yake ƙasan raina. Ta ja hannuna muka sauƙa daga kan gadon.
"Mu je mu ci abinci ga shi can sai mu fita tallan ko?". Kaina kawai gyaɗa mata muka fito daga ɗakin muka shiga na su, muka ci abincin tare tana ta ja na da hira har muka gama. Muna gamawa na yi wanka na shirya ita ma ta kimtsa ta fito lokacin har ƙarfe taran safiya ya wuce amma har lokacin babu Abba babu labarinsa.
Muna fitowa ƙofar gida na hango Abba ya ɓullo daga can ƙarshen layinmu yana turo keken sa hannunsa ɗaya riƙe da leda. Ina ganinsa na ji duk jikina ya mutu murus hawaye suka ciko mini kurmin idanuna ganin yadda yake ta gumi ga takalmin ƙafarsa da ya tsinke yana tafe yana tura keken da yake ƙara gaskata mini hashashen zuciyata na cewa faci keken ta yi.
Ba mu gusa ba har sai da ya iso na isa zan karɓa ledan hannunsa ya dakatar da ni.
"A'a Uwata bar shi kawai, ai na iso ma".
Cikin wani irin yanayi na karyewar zuciya na furta"sannu da dawowa".
"Yauwa sannu. Har za ku tafi kenan? To Allah ya kiyaye ya ba da kasuwa mai albarka".
Yana dasa aya ya sa kai zai wuce cikin gidan ko gaisuwar da Amira ta yi masa sama-sama ya amsa.
"Yau kuwa lafiya na ga Abba a wani irin yanayi?".
Ta tambaye ni cikin tsantsan mamakin da ya bayyana ƙarara akan fuskanta.
Na sauƙe numfashi kafin na ce"yadda kika gan sa ni ma haka na gan shi yau". Daga haka na wuce gaba tana biye da ni a baya. Muna zuwa ƙarshen layinmu na ji ana ƙira sunana, tare muka waiga dukkanmu ni da Amira muna kai dubanmu izuwa idan muke jiyo sautin ƙiran.
Na dafe ƙirjina ina waro idanuna waje"na shiga ukuna! Sarkin Aska". Amira ta bi shi da kallo har ya iso gabanmu ya zube dukkan hannayensa a cikin aljihun wandon jamfan da yake jikinsa yana kallona.
"Barka da fitowa yake tauraruwar da take haska duniyata".
"Me ya kawo ka unguwanmu?"
Ya saki taƙaitaccen murmushi kafin ya amsa mini cikin faɗin"laifi ne don na zo inda kike? Ko kin manta an ce garin masoyi ba ya nisa. Kusan kullum sai na zo nan na tsaya don kawai na ga wucewar ki hakan ya na taimakawa wajen saisaita bugun zuciyata da daidaita fitar numfashina. Amatullah ke ce sanyin idaniyata, ke ce a cikin tunanina a farke ko a cikin bacci....". Bai gama ba na ɗaga masa hannu alamar ba na ƙaunar jin ragowar zantukan da za a fito daga bakinsa.
"Ya isa haka ya isa. Ban tsaya a nan don ka dinga zayyana mini abin da yake cikin zuciyarka ba. Zan ƙara jadadda maka ka fita a harkata don girman Allah na roƙe ka".
"Ba ni da ikon akan zuciyata balle na sama damar kitsa abin da zai zauna a cikinta ko wanda zai fita. Ina sonki shi ne kawai abin da na sani kuma na yi imanin babu abin da zai sauya hakan komai wuya komai runtsi".
Tsaki mai dogon zango na saka ina wurga masa harara na ja hannun Amira muka bar wajen cikin sauti. Har muka isa tashan raina a ƙuntume kamar wacce aka aikowa da sauƙon mutuwar uwa da ubanta.
[7/29, 5:39 PM] Maimunatu Iyam: *DAFIN HARSHE*
©️ Maimuna Tijjani Iyam
___________________________________
Page 1️⃣7️⃣
Haka na zauna fuskana gabaɗaya babu annuri raina, akan idona Amira ta ware wasu ta away ta ajiye a gefenta ta ce wannan ba na sayarwa ba ne. Dafo kafaɗana da ta yi shi ya fizgo hankalina zuwa jikina na cira kai ina duban ta tare da ɗage mata ido ɗaya alamar lafiya. Ta yi mini ishara da idonta na bi inda take kallo da ido can na hango Bashir tafe ya nufo inda muke zaune, yana tafe yana washe baki kamar gonar auduga. Tsaki mai dogon zango na ja ina ɗauke kaina gefe guda na buɗe baki zan yi magana kenan ta riga ni.
"Don Allah kar ki ce komai Amatullah. Ki yi wa Allah ki yi wa annabi ki saki fuskarki a bawan Allahn nan. Ko sau ɗaya ne in ya yi miki magana i masa masa, kin san fa an ce gaida mai gaishe ka ko ba zai amsa ba".
"Don girman Allah ki bar ni Amira ki bar ni da abin da yake damuna ma ya ishe ni. Ba sai kin ƙara mini wani ba".
Ina rufe bakina yana isowa wajen ya zauna a kan bencin da yake fuskantar mu. Ya soma zuba kamar bishiyar magarya.
"Tsarki ya tabbata ga Ubangijin da yake da ikon juya dare zuwa safiya. Kuma ya yi mini tagomashin yin tozali da kyakykyawan suranki a matsayi abin mafi kyau da burgewa da na fara gani a wayewar garin yau. Da ke da na kwana a cikin ƙirjina shi yasa yau na yi ƙudurin zuwa na ganki kafin na aiwatar da dukkan ayyukan na ranan yau".
"Kan bala'i! Bash yana kashe wuta ina bin ka da fetur. Irin wannan kalaman tashin kai haka ai ni da nake gefe ma kana sawa na fice daga cikin duniyar balle ita kuma wacce ake yi domin ta".
"Babbar yarinya ke dai ki kawai lamarin ya wuce duk yadda kike tunani da zato a cikin zuciyata. Ban taɓa ɗanɗana garɗin soyayya ba sai yanzu da na faɗa kogin soyayyar Amatullah".
Raina ya cika fam zuciyata tana tafasa tamkar talgen da aka aza a bisa wuta, na gaza cewa da su komai illa hararar da nake banka musu a faƙaice.
"A zuba min kunun. Don yau na yi wa kaina alƙawarin ba zan sha komai dangin abin sha ba sai na fara shan wannan daddaɗan kunun nakin, ya ke Gimbiyata".
"Na nawa kake so?".
Na furta zancen a zaffafe kamar zai kai masa duka. Hakan ya sanya Amira kallo ni tare da faɗin"Haba! Amatullah ya haka kamar da gaba? Ki tuna wanda ya ce yana sonka fa, komai lalacewarsa ya fi maƙiyi".
"To laifi ne don na tambaya na nawa yake so?". Ta jijjiga kanta alamar a'a tana ƙunshe dariyar da yake son kufce mata.
"Ban so kika dakatar da ita ba, ko kalmar zagi da cin mutumci ne zai fito daga bakinta ina son na ga waɗannan kyawawan leɓan natan suna motsawa. Ki ba ni na ɗari biyu".
Ban tanka masa ba na zuba masa na dosara masa a gabansa. Ya ɗauka yana sha yana ta suturan da sam ba na gane kansu balle gindinsu, da na ga zaman ba zai fishshe ni ba na amshi wayar Amira ina kallon hotuna.
Muna zaune har masan ya ƙare duk wanda ya zo sayan kunun ya yi mini wata maganar ko ya yabi surar jikina, sai na fasa sayar masa na kuma buga masa rashin mutunci. Hakan ya sa ban yi ciniki da yawa ba.
"Bari na kai wa Naziru masarsa". Na bita da kallo yayin da take miƙewa tana ɗaukar take away ɗin. Na janye hannuna daga tagumin da na zagba kafin na sama zarafin faɗin.
"Ni fa Amira na lura zaman cikin tashan nan ban gishiri a baka manda ne. Sai ka mayar da kanka bolar da kowa ta kwaso jujinsa zau juye akai. Allah ya sani ba zan iya wannan rayuwar ba".
Ta tsaya tana kallona"bari na je na dawo sai mu yi magana. Kar na bar shi yana jira na". Tana dire zancen ta juya ta bar wajen wanda hakan ya yi daidai da sauƙe sakakken ajiyar zuciyar da na yi ina zabga wani uban tagumi kamar wacce aka aikowa da saƙon mutuwa.
"Yan mata adon gari idan ba ku gari ya ɓaci idan kuka yi yawa gari ya ɓaci". Kalaman da suka dira a ƙofofin kunnuwana kenan da suka tursasa mini ɗago kaina ina ƙarewa mutumin kallo tun daga sama har ƙasa. Babban mutum ne wanda a ƙalla zai kai sa'an Abbana a kwanakin duniya ya yi shigar kamala cikin cikakken jamfa har ƙasa ga jakar kaya riƙe a hannunsa.
"Me ye kike tsayarwa ne ƴan mata?". Ya kuma jefa mini wani tambayar a karo na biyu har lokacin idanunsa ƙar a kaina ba ya ko ƙiftawa.
"Kunu ne. Na nawa za a zuba maka?".
"Ga shi kuma ni ba na shan kunu. Sai dai na sha mai tsayar kunun".
Tsam! Na miƙe kamar wacce aka tsigarawa alluran doki na tsaya ƙyam akan ƙafafuna duk da rawar da suke yi mini tsabar firgicin da zancen nasan ya jefa ni a ciki.
Muryarta har sarƙewa yake yi idanuna yana kawo ruwa na soma faɗin"wani irin banzan magana ne wannan bawan Allah?. Babban mutum ne kai don haka ka ja girmanka don billahillazi idan ka yi gigin zubar da ni babu abun da zai sa ba zan sanya ƙafa na tatttake sa ba. Ni ba iskanci ne ta fito da ita daga gidanmu ba face sana'a".
Kafin na rufe bakina na ji ya ɗauke ni da mari kafin na yi aune ya ƙara sauƙe nuni wani marin a karo na biyu na ɗayan kuncina. Na ɗago kaina a gigice sai dai kafin na sama zarafin cewa wani abun tunin ya tari numfashina.
"Ke yarinya kar ki sake ki yi min rashin kunya irin na ku na ƴaƴan zamani. Ni nan da kike gani na shekaruna ɗaɗɗaya shekaru sittin da biyu a duniya. Jikata da farko yanzu haka tana gidan aurenta har da ƴaƴa, da kina da mutuncin ni ɗin nan na matsayin uba ya kamata ki kalle ni".
Na dafe kuncina raina cike da fal da takaici. Ƙirjina yana dakan lugudan tara-tara sau goma sha tara. Ruwan da ya wadaci kurmin idanuna suka kwaranyo akan kuncina.
"Ai ba ka riƙe girmanka ba ne shi yasa har na sama fuskar gaya maka ko wani irin magana". Na yi maganar jikina har ɓari yake yi tsabar ɓacin rai da ƙuncin da nake
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 9 Chapter of 24