Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
bakin d’aya daga cikin rooms d’in kana ya juyo yace, “Next room is your as long as you want.” Ya shige ciki. Haydar tashi yayi ya isa gurin da wayar take ya rubuta abunda yake so da time d’in da yake son a kawo mishi kana ya tura. D’aukan jakarshi yayi ya shiga d’akin da aka ce nashi ne, sai dai yana shiga ya fara jiyo muryoyin Faisal da budurwarsa a wani hali na intimacy wanda hakan ya takurashi nan take. Yana ajiye jakar bai ko tsaya k’arewa d’akin kallo ba ya fice cikin sauri saboda irin kalaman da suke amfani dashi ya girmi kwakwalwarshi. Minti sha biyar da haka yaji alamar an ajiye abu a bakin k’ofar ya tashi ya bud’e ya shigo da kwandon abincin. Kamar yanda ya fad’a haka aka masa chips da scrambled egg sai black coffee wanda babu cream babu sugar. Yana gama cin abincin ya tattara ya kai kitchen island da yake wani gefe a falon kamar kitchen. Bayan ya dawo ya zauna ya kunna Netflix yana kallo amma hankalinshi na kan Mamanshi wacce ya tabbatar yanzu tana cikin zullumi da kuma dana sanin auren da tayi. Kwafa yayi a zuciyarsa kuma murna yake yi da Allah ya had’ashi da Faisal a Dark Web d’insu har suka bayyanawa junansu suna da kuma inda suke, wanda ba’a cika hakan ba a duniyarsu. Yana zaune Faisal ya fito gefenshi wata yarinya ce da bazata wuce shekaru sha shida ba tana shafa k’irjinsa. Wata riga ce iya cinya a jikinta shara-shara da bata 6oye komai ba na jikinta. Kai tsaye gurin da wayar take suka yi Faisal na rubuta musu abunda suke buk’ata, Abul kuma daya lura da shigan yarinyar sai ya kawar da kanshi, a lokacin ne ya rage murnarsa domin da alama haka zai dinga ganin ‘yan matan Faisal and zasu takurashi. “Abul this is Beeba my girlfriend.” Faisal ya fad’i hakan yana zama a sofa dake kallon Abul ita kuma Beeba ta hau cinyarshi tana shafa kanshi da kunnuwanshi. Abul da bai ta6a kallon hakan a zahiri ba sai ya tsorita zuciyarsa ta fara bugawa yayi saurin kawar da kanshi gefe yace, “Hey Beeba.” Juyowa tayi ta masa kallon sama da k’asa sannan ta sanya yatsanta a bakinta tace, “Hey Bull.” “It’s Abul not Bull.” Faisal ya gyara mata yana sanya hannunshi cikin rigarta. “I prefer to call him that.” Abul da yaji haushin had’ashi da tayi da Shanu sai ya tashi ya koma d’akin da aka bashi domin ya lura kamar basu gama abunda suke yi ba. Sai daya tabbatar sun fita daga gidan sannan ya fito ya shiga band’aki yayi wanka da alwala kana ya koma yayi sallah. Yana zaune a kan sallayar yaji yana buk’atar abunda zai kawar da hankalinshi. Jakarsa ya jawo ya fara bincike ko zai samu sauran kwayarsa, yana binciken ya samu wata kwayar da sau d’aya Micheal ya ta6a bashi yasha saboda k’arfinta da tsadarta. Waye ya iya sayan mai yawa haka har ya sanya mishi a cikin jakarsa? Ya gama kaf tunaninshi bai tuna lokacin daya saya ko aka bashi ba. Ganin zai 6ata lokacinsa yasa ya d’auki biyu ya harba kana ya kawar da duk abunda zai iya yiwa kanshi illa dashi ya kwanta a kan gado yana jiran ta fara aikinta ta kaishi duniyar da babu damuwa sai farin ciki da jindad’i. Bai iya komai ba bayan ta fara wargaza masa kwakwalwa illa bud’e bakinsa da yake yi yana rufewa, can kuma sai ya rufe idanunsa sai ya bud’e yana murmushin jindadi shi kad’ai. Wani lokaci kuma zai gwada tashi amma daya duba k’arkashin gadonsa sai yaga rami ne mai duhu babu gurin takawa. Hakan yasa yayi kwanciyarsa akan gadon har bacci ya kwasheshi mai cike da mafarkai iri daban-daban. Haka rayuwarsa a gidan Faisal ta kasance, da safe kafin su tashi zai rigasu tashi yayi amfani da band’aki ya kuma yi order d’in abinci a kawo masa yaci. Daga nan kuma zai shige d’akinsa yana danna Laptop d’insa inda yake samun labarin duk wani motsi na uwarsa da mijinta. Yamma tana yi zai sha kwayarsa yayi mankas ya kwanta a kan gado yana zaro harshensa waje har bacci ya d’aukeshi. Faisal bai damu da sanin ina Abul yake ba domin shima harkar gabansa kawai yake yi da Beeba budurwarsa. Idan kuma suka had’u falo in dai ba wata babbar magana ba basa kula juna. Beeba na yawan kallon Abul tana kuma jan hankalinsa idan Faisal baya ganinta, Abul daya lura ta fara seducing d’inshi sai yayi saurin gama abunda yake yi ya bar musu falon. Yau satinsa biyu a gidan, a nan ne kuma kwayarsa mai kwantar masa da hankali da sakashi nishad’i ta k’are. Kud’insa da yake dashi ya fitar ya fito falo ya samu Faisal da Beeba a wani hali da bai so gani ba. Ya kai seconds goma yana kallonsu sannan ya kira sunan Faisal ya juyo. “What bro?” Faisal ya amsa masa ba tare daya daina abunda yake yi ba. “Ina son fita supplies d’ina sun k’are.” “Go to my Driver.” Daga nan ya maida hankalinshi kan abunda yake yi ya rufe idanunsa yana cije fuska. Abul hanyar k’ofa yayi amma bai san dalilin da yasa ya juyo ba hankalinshi na kan Beeba dake k’asan Faisal tana aiko masa da kallo mai cike da fassara iri-iri. Shi ba gwanki bane koda yana shan kwaya yana buk’atar mace a rayuwarsa, ganinsu da yayi kuma cikin wannan halin yasa yaji shima yana buk’atar hakan. Sai dai wa zai samu? A yanzu daya 6ata rayuwarsa ma baya buk’atar k’arin yin zina. Zai sha kwaya amma ba zai yi zina ba, da haka ya isa gurin da motocin Faisal suke Driver ya d’aukeshi suka fita daga gidan. Babu inda bai zaga ba amma bai samu inda ake sayar da kwaya ba, Pharmacy babba ko k’arami sun hanashi magani sunce sai da prescription. Ya fito a wani Chemist na shida da suka je ne wani ya biyoshi ya masa kwatancen shagon Imaa dake can kwararon unguwar ‘yan iskan garin marasa galihu. Da k’afarshi ya k’arasa shagon domin Driver yace motar baza ta iya shiga unguwar ba, a bakin shagon ya samu samari hud’u zaune suna busa sigari, daka gansu zaka san suna shan wahalar rayuwa. Duk abunda yake buk’ata ya saya a shagon Imaa na murna domin yayi ciniki sosai ba kad’an ba. Sai dai bai samu kwayarsa da yake sha tun zuwanshi Abuja ba. Bayan ya fito ya bawa samarin kud’i wanda ciki har da Banney dake binshi da kallo yana tuna gatanshi na da kamar Abul d’in. Godiya suka masa kana ya koma mota suka tafi gida. Abinci ya fara aikawa a kawo mishi yaci sannan ya har6a kwayoyinsa ya kwanta yana jiran ta fara aiki ta sakashi bacci. Sai dai wannan karon jinshi yayi garau babu alamun bacci a idanunsa balle nishad’i nishad’in da yake ji idan yasha waccar kwayar, wannan hauka yaji yake son yi ya wargaza komai daya shiga gabanshi. Yana zaune akan gadonsa ya fara wurgi da duk abunda hannunsa ta kama, yana tsaka da haka Beeba ta shigo d’akinsa tsirararta tana masa murmushi. Rufe k’ofar tayi ta iso gurinshi tare da zama akan cinyarsa tana tura masa k’irjinta. Hakan yasa hankalinsa ya k’ara barin jikinshi ya biye mata tana k’ok’arin rabashi da kayan jikinshi. Sai dai bata kai ga cimma burinta ba Faisal ya band’ako k’ofar ya ja gashin kanta ya had’ata da gini goshinta ya fara zubar da jini, Abul kuma daya fara gane inda hankalinsa yake yaji an naushi hancinsa ya gigice ya rasa gane a ina yake. Dukan hauka Faisal ya yiwa Abul ba tare daya ce komai ba sai furzar da iska da yake yi ta bakinshi da hancinsa. Jina-jina ya yiwa Abul sannan ya jawo kwalar rigarsa ya fitar dashi k’ofar Cabin d’in ya jefar. Komawa ciki yayi ya d’auki wayarsa ya kira wani mutum wanda a cikin minti uku ya iso yace, “Ka kaishi d’akin karnuka, kar ka bari su kasheshi amma ka tabbata sun masa illar da har abada ya gani sai yasan yaci amanata.” Yana fad’in hakan ya koma d’akin Abul ya samu Beeba na tsugunne a gurin tana kuka, gashinta ya k’ara kamowa ya kaita zuwa d’akinsu yana cewa, “You want to fuck with him? Then fuck yourself with this.” Ya nuna mata kwalbar barasa dake gefenta. Hak’uri ta fara bashi ya girgiza kanshi yana mai zama a kan kujerar dake d’akin yana fitar da numfashi cikin 6acin rai. “Na sayeki gurin ubanki da kud’ina don ki zama mallakina ni d’aya zuwa lokacin da zan gaji dake in freeing d’inki. But you want to be a real bad bitch kinyi seducing my only friend dana ta6a kawowa gidana. You ruined him for me, nima kuma zan lalataki yanda babu wani d’a namiji da zai k’ara morarki, you ungrateful bitch.” Fad’in abunda ya faru da Beeba ba’a magananshi domin sai daya tabbatar yayi ruining d’inta sannan yasa aka fitar da ita daga gidan aka je aka watsar da ita a cikin jeji wanda zata yi kwana biyu a ciki bata fito kan titi ba, that’s is in tayi rai kenan. Faisal ya cika sunansa ‘Sadistic’ wanda shine Handle d’insa a Dark Web. Kwanan Abul biyu ana turashi d’akin karnuka, sai sunyi kamar zasu kasheshi sai a fitar dashi a barshi a waje yana ihu yana kukan raunin da suka ji mishi, wanda har sun karya mishi k’afarshi baya takata. A kwana na biyun Faisal ya zo gurin da ake mishi horon ya sameshi a waje tare da fresh wounds wanda karnukan suka mishi. Tsugunnawa yayi a gabanshi kana ya zare sunglasses d’in idanunsa ya dubi Abul wanda idanunsa suka kumbura baya iya bud’esu da kyau. “I liked you Man, but sai ka nemi budurwata bayan ni mutum ne da bana sharing sex doll d’ina. I still like you shiyasa zan barka da rai but waccar tsinanniyar ta mutu babu ita babu k’ara nanewa wani namijin. Na san ita tayi seducing d’inka domin ina ganin lokacin data shiga d’akina bayan tayi tunanin na fita daga gidan ne, I have cctv cameras da babu mai ganinsu sai ni d’aya. Na d’auka ba zaka biye mata ba, na d’auka you’ll push her away ashe kaima jiranta kake yi kana muradin kasancewa da ita. Shiyasa ban ta6a trusting kowa ba sai kai, kuma you showed me yarda da mutane gangancine. You’ll live but ba yanda kake so ba. Danny ka masa allura ka kaishi can k’arshen gari ka jefar wannan shine alfarma da kuma tausayawa da zan iya maka.” Abul dake durk’ushe a gurin ya kasa koda magana saboda irin ciwo da zogin da jikinshi ke mishi. Da haka Faisal ya mik’e ya saka glasses d’insa yana cewa, “Zan je Sex doll hunting wish me luck.” Abul na jin k’arar sawayensa har ya shiga mota suka fita daga gidan. Danny da zai mishi alluran sai da ya naushi k’afarsa wacce ta karye sannan yana dariyar mugunta ya danna masa allurar wacce a take ta sakashi fita daga hayyacinsa gaba d’aya. A wata pick up da Faisal ke 6adda kama in yana son fita shi d’aya suka sakashi, sannan suka nemi abun rufe mota suka d’aura a kanshi suka fita daga gidan. Driver dake tuk’a motar shi yaji tausayin Abul ya fasa kaishi bayan gari, don haka ya kaishi unguwar daya ta6a kawoshi sayan magani wato gurin su Imaa. Duk da cewa ba tare suka je ba amma ya gane gurin da zai kaishi wanann karon har k’ofar shagon Imaa yayi parking kana ya isa gurinsu ya musu magana. Banney da bai manta alherin da Abul ya musu ba ya d’auki nauyin kula dashi bayan ya nemi kud’i gurin Drivern. Babu musu ya ciro kud’i mai yawa ya bawa Banney yana cewa, “Ban san meyasa nake tausayinsa ba, but take care of him kuma kace ya koma gidan iyayensa inji ni.” Yana fad’in hakan ya koma mota da taimakonsu suka ciro Abul wanda yake kamar matacce. “Wooo ya zaka kawo mana gawa? So kake ka d’aura mana sharrin kisa?” Fad’in Imaa yana fitowa daga shagonshi bayan yaga abun nasu bana k’arewa bane. “He is not dead but unconscious.” Fad’in Banney yana sauk’ar da Abul kan simintin bakin shagon Imaa. “Ku d’age mini wannan abun daga bakin shagona kafin ni in k’arisashi.” Imaa yayi maganar cikin zafin rai. Banney yasa baki sauran suka taimaka mishi suka d’auki Abul zuwa shagon da yake kwana suka yasar dashi a nan suka yi tafiyarsu suna cewa, “Idan ya mutu a gurinka babu ruwanmu.” Sai da suka tafi sannan ya 6arka kayan jikin Abul ya fara duba meya sameshi. Duk jikinshi ciwuka ne wanda wasu sunyi zurfin da suna buk’atar stitches yayinda wani gurin kuma fatar ta d’aye sai nama kad’ai ake gani. “You fought with a Lion Nigga?” Banney ya tambayi unconscious Abul. Fita yayi daga shagon ya isa shagon Imaa yana fad’a masa abubuwan da yake so don treating Abul. “Kud’in double zaka bayar don baka da prescribtion.” Fad’in Imaa bayan ya gama kawo masa abunda yake buk’ata. “Don’t do this Imaa, mutumin nan ya maka alheri a baya karka mishi haka a lokacin da yake buk’atar taimakonka.” “I don’t give a damn. Ka bada kud’i ko kuma kaje ka nemi wani gurin.” Banney yasan idan ba shagon Imaa ba babu inda zai je a bashi abunda yake buk’ata. Don haka dolenshi ya kirga kud’in da Drivern ya bashi ya bawa Imaa nashi. A nan ya rage Saura dubu biyar cikin abunda aka bashi wanda yake zaton dubu sha biyar ne duka. Yana komawa shagon da Abul yake kwance ya samu ya farka yana hawaye kawai baya iya ko motsi. “Ka farka kenan? Gashi bani da alluran da zan maka hankalinki ya 6ace saboda abunda zan maka will hurt like a bitch.” Banney da kanshi ya wankewa Abul ciwokanshi ya saka antiseptic kana yayi stiching wand’anda suke bukatar hakan. Duk abunda ake yi Abul in banda ihu babu abunda yake yi amma ya kasa motsa jikinshi dalilin allurar da aka mishi bata gama sakeshi ba. A cikin unguwar tasu Banney ya kira wani dattijo mai d’aurin kafa ya d’aurewa Abul kafarshi wacce yace gocewa tayi. Da sauran kud’in yake ciyar dasu har Abul ya fara tashi da kanshi yana zuwa bola inda suke Bahaya ba kamar daa da yake yi a leda Banney na kaiwa ya jefar ba. Satinsa biyu ya warware sai dai har lokacin yana d’ingisa k’afarsa wacce mai gyaran yace zai yi wuya ta dawo daidai in ba Bature ne ya gyara ba. Ko da ya samu lafiya sai ya koma harkar shaye-shayensa inda yake zuwa kasuwa da Banney suyi kwadago sannan su samu na shan kayen maye, wanda sun gwammace su sha kwaya akan suci abinci. Wannan shine tak’aitaccen tarihin Abul a Abuja bayan ya tsira da rayuwarsa da kyar. Mum Fateey 👌RUWAN ZUMA 🍯 Suwaiba Muhammad (Mum Fateey) 09023713064 (36) “Ba yanda za’a yi a aika wani sai ni?” Haydar ya tambayi Alhaji Abdul bayan ya gama fad’a masa tafiyar da zai yi zuwa Abuja. “Aikinka ne bana kowa ba.” Ya bashi amsa tamkar bashi da damuwa a duniyar. “Shikenan.” Da haka suka cigaba da magana kan abunda zai je yayi. Bayan sun gama Haydar ya koma office d’insa ya tattari kayansa ya koma gida domin a gobe zai yi tafiyar tare da wasu mutane biyu daga cikin company nasu. D’an achaba ya sauk’eshi a waje shi kuma ya biyashi kana ya shiga gidan. K’ofar falon daya zama nashi ya bud’e ya fara ajiye jakarshi a kan kujera yana kasa kunne ko zai jiyo motsin Laila duk da cewa bai ga motarta a waje ba. Yau kwana biyar kenan da yin fad’ansu wanda daga shi har ita kowa ya damu bana wasa ba. Zata mishi girki ta kawo mishi har side d’in da yake, sannan idan ya fita zata shigo ta gyara masa d’akinsa ta kuma kunna mishi turaren wuta kamar yanda ta saba. Sai dai shareshi da take yi yafi k’ona mishi rai domin ta nuna bazata bashi hak’uri ba balle kuma ta canja halayenta ba, kenan har lokacin tana kan bakanta na k’in haihuwa dashi. Daurewa kawai yake yi domin tunda ya aureta bai ta6a rabuwa da ita a makwanci ba sai wannan lokacin, sai yanzu ya gane cewa tayi tasiri a rayuwarsa yanda baya zato, domin yanda yake jinta a ranshi yanzu har yafi na daa. Sai da yayi wanka sannan ya dawo ya d’ibi abincin da ta saka mishi kad’an kamar loma uku, hakan na cikin puninshment d’inta domin yasan tana son yaci abincinta sannan ta k’i jinin yaci kad’an ya bar mata sauran. Yana zaune a falo bayan la’asar yana tunaninta wanda ya zame masa d’abi’a yaji shigowar motarta gidan. Duk da yasan cewa baza tazo gurinshi ba amma yaji dad’in dawowarta domin ko ba komai suna zaune a rufi d’aya. Yana ji ta bud’e falonta ta shiga ya kwanta a kan kujerar ya rufe idonsa yana jin zirga-zirganta tsakanin kitchen da falonta wanda ta d’aura musu abincin daren ta ba zai ci ba. Sai da Haydar ya fita sallan magrib sannan Laila ta shiga sashenshi ta samu ya cakali abincin ya bari. In ba don gudun kar abun ya wuce haka ba daa ta daina girkin gabad’aya, domin bata ga amfanin yin ba tunda ba ci yake yi ba, itama kuma damuwarta bai barta ta ci ba. Tuwon data mishi miyar d’anyen ku6ewa da tasan yana so ta ajiye mishi kana ta fita daga falon ta koma sashenta zuciyarta na k’una. Ta san da gangan yake mata haka amma yayi duk abunda zai yi domin har gobe tana kan bakanta. Shi kuma yana dawowa ya shiga d’akinsa ya fara had’a kayan da zai yi tafiya dasu gobe da asuba. Bayan ya gama ya dubi inda ta ajiye mishi abincin amma bai bud’e ba balle har yaji yana son ci, saboda shi In zai yi tafiya baya cin abinci da dare da kuma safiyar ranar gudun tsayawa a hanya ko gur6acewar ciki. K’arfe goma saura kwata yayi shirin bacci ya shiga sashenta yana jin kewarta da kuma wata muguwar son kad’aicewa da ita. A can d’akinta ya sameta kwance a kan gado kamar ma tayi bacci, hasken d’akin ya kunna idanunsa suka saisaita kan surar jikinta cikin night gown d’in da ta saka wanda ya bayyana wasu ga6o6in jikinta. Tsura mata ido yayi na wasu sakanni yanayinshi na canjawa yana jin kewarta a ranshi. Can kuma yayi gyaran murya ya kira sunanta. “Laila.” Bata amsa ba hakan yasa yayi tunanin bacci take amma daya tuna cewa da zarar an kunna hasken wuta a kanta take farkawa sai ya gane da gangan ta shareshi. Hakan yasa ya murmusa kad’an sannan ya k’ara kiranta a karo na biyu. Can k’asan mak’oshinta ta amsa sannan ta gyara kwanciyarta ya bita da ido. “Zan yi tafiya gobe zan je Abuja. Watak’ila zamu kai sati ko kuma muyi kwana biyar.” “Allah ya kiyaye hanya.” Kawai tace dashi amma ya gane muryarta ya fara rawa. “Me kika ce?” Ya tambayeta domin yana son gaskata kunnenshi. Jin tayi shiru yasa ya tsaya bai tafi ba, seconds goma da haka kuma yaga jikinta na rawa alamar kuka take yi. Babu abunda yafi karya masa zuciya irin kukan Laila kuma ya tsani ganin kukanta. Takawa yayi ya isa gurinta jin ba’asin kukanta, “Meya sameki kike kuka? Meya faru?” Ya tambayeta yana d’age hannunta da ta rufe fuskarta dashi, sai dai bata bari ya bud’e mata fuskar ba sanin ya 6aci da hawaye. “Tambayanki nake yi kinyi shiru.” “Babu.” Ta bashi amsa a karo na farko. “Haka kawai da girmanki ki fara kuka babu abunda ya sameki Laila?” “Nace babu komai.” Ta fad’i hakan tana goge hawayen ba tare data yarda sun had’a ido ba. “Don zanyi tafiya kike kuka?” Ya tambayeta yana d’aga ha6arta wanda hakan yasa ta kalli kwayar idanunshi a karon farko bayan sa6anin da suka samu kwana biyar da suka wuce. Marairaicewa tayi tare da shagala da kallonsa domin ba k’aramin kewarshi tayi ba dalilin wannan karon sun raba makwanci yanda babu mai ganin d’an uwansa. Karantar idanunsa da tayi kad’ai yasa ta fuskanci yanayin da yake ciki wanda in zata fad’i gaskiya itama tana buk’atar mijinta domin horon ya musu yawa dukansu. Tana ji ya kai hannunshi jikinta ta bada kai suka lula duniyar masoya. Bayan komai ya lafa Haydar ya koma gefe ya jawota jikinshi yana jin zuciyarsa fari tass har yana ganin wautarshi na nesanta kanshi da yayi da ita na tsawon wannan lokacin. “Komai ya wuce ko?” Ya tambayeta yana tufke mata gashinta daya kunce mata d’azu da suke wata duniyar. Gyad’a mishi kai tayi kana ya sumbaci tsakiyar kanta ya gyara musu kwanciyar dalilin baccin da yake ji sosai. Laila da kanta ke k’irjinshi taci gaba da sauraron bugun zuciyarsa har bacci ya d’aukeshi amma ita nata k’ekau tana jiran baccin nashi yayi nauyi. A hankali ta zare jikinta sannan ta zura night gown d’inta dake yashe a k’asa. Cikin sand’a ta fita daga d’akin tayi hanyar kitchen. Sai data gama abunda zata yi sannan ta dawo ta samu babu Haydar a kan gadon. Zuciyarta ce ta buga da k’arfi ba dai ya biyota ba a karo na biyu? In bata manta ba hakan ne ya jawo musu fad’a kuma gashi da alama ya sake kamata a karo na biyu. A birkice ta fito falo ta isa bakin k’ofar da zai sadata da sashen nasa, sai dai tana murd’awa taji k’ofar a gark’ame alamar an saka makulli. Jijjiga k’ofar ta fara yi tana kiran sunanshi a hankali sanin dare yayi. Duk abun nan da take yi Haydar na zaune a falo ya dafe kanshi da hannunsa biyu idanunsa sun cika da hawaye amma ya k’i bari su zubo. Bak’in cikin da yake ji ya tsaya a mak’oshinsa yana jin azabar zafi a ranshi. Wai dama Laila haka ta tsaneshi bata son had’a zuriya dashi? Menene laifinshi don yana son haihuwa da ita? Me ta d’aukeshi sannan wani irin matsayi take bashi a rayuwar aurensu? Shin anya ta d’aukeshi a matsayin mijinta ko dai ta ajiyeshi ne a matsayin mai d’ebe mata kewa ba tare da sun haihu ba? Meyasa take son 6ata soyayya da kuma auren dake tsakaninsu? Ire-iren wad’annan tambayoyin ne a ranshi wanda yaji nan take ya fara tausayinshi kanshi daya d’aurawa kanshi son tara zuriya mai yawa kuma yake son babbar mace at the same time. Meyasa bai yi tunanin Laila zata k’i haihuwa ba? “Haydar ka bud’e mini don Allah ka saurareni.” Fad’in Laila cikin magiya domin tasan yayi fushi mai tsanani wannan karon. Yana jin hakan ya tashi ya shige d’akinsa, kai tsaye ya shiga band’aki ya sakarwa kanshi ruwa ya fara wanka. D’azu bai jima ba dashi da ita duk suna cikin walwala da farin ciki amma lokaci d’aya tayi sanadiyyar wargajewar komai ta sanyashi cikin k’unci da yake jin d’acinsa tamkar mad’aci. Ko da ya fito bai ji motsinta a bakin k’ofar ba, a nan kuma zuciyarsa ta raya mishi cewa taje k’ara shan abunta ne. Wannan tunanin kad’ai yasa yaji bak’in cikinsa ya k’ara hauhawa yana son dukan abu, abu mafi kusa dashi ya d’auka yayi cilli dashi ya had’u da gini ya fad’i k’asa. Ya jima a tsaye yana nanata Lahaula a ranshi da kuma korar shaidan sannan yaji sauk’i kad’an ya zauna a bakin katifar yana tunanin wannan rayuwar daya tsinci kanshi a cikinta. Matarsa ta Sunnah ba dadironsa ba amma tana kyamar d’aukan cikinsa? Meya mata? Me zai yi? Washe gari da

Chapter 13 of 32