Reading Dauɗar Gora by Bilyn Abdull ce Chapter 1 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Downloaded From https://tknovels.com.ng ********************************************
Visit http://novelselite.com.ng for more books

About Novels Elite
Novels Elite is a website consisting of Hausa Novels Books
such as Text, Documents, Audiobooks, and Videos, the
purpose of creating this site is to Entertain, Motivate and
Educate our readers.


Novels Elite provided so many kinds of Hausa Novels of any
type, Such as Adventure, love, romance, fiction, non-fiction,
mystery, fantasy, action e.t.c.

We provided a new and old novel as softcopy from our
Authors with their permission

Zaku iya samun mu a kafafen sada zumuunci kamar haka:

Facebook: Novels Elite
Youtube: http://youtube.com/@novelselitetv
***********************************************

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)


𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻
*‫*ِبْس ِم الَّلِه الَّر ْح َٰمِن الَّر ِح يم‬
_Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._


Page 1


.........Kwanakin mako uku kenan da shuɗewar komai amma
komai ya kasa mantuwa a zukatansu. Kuzari ya samu rauni
kamar yanda dukkan karsashi ya gujema gangar jiki. Duniya
ta masu ƙunci, ƙunci irin wanda har ƙarshen numfashi da
wahala su manta. Farin cikinsu ya zama fansar damuwar
wasu, wasun da kansu kawai suka sani basa kallon na ƙasa da
su. Da ace ƙarfin iko a hanun kowanne ruhi yake a zahirin
rayuwa, da ita ce zata zama mace ta farko a duniya mai ƙarfin
ikon da zai girgiza zukatan kowaɗanne irin azzalumai. Kafin
shuɗewar makwanni uku masu ɗauke da kundun baƙin ciki
rayuwar ahalin Mal. Zayyan tamkar dutsen lu'u-lu'u suke a
cikin tsakkiyar zinare. Ba magana ake akan dukiya ba, dan
tana a cikin jerin abu mafi rauni da suke ɗauka ko amsa sunan
ko kallo farin ciki. ana magana ne akan kammaluwar ahali
masu matuƙar ƙaunar juna zunzurutu mara gauraye. Masu
kuka a yayin zubar hawayen ɗayansu, masu dariya a yayin
farin cikin ɗayansu, masu jiyya a yayin ciwon ɗayansu, masu

𝕽𝖚𝖒𝖆𝖓 babbar ƙasace a tsakkiyar wani babban tsibiri
zama komai a lokacin da komai yake abu ɗaya a hanunsu.

a wani ƙarni daya shuɗe kafin yau, ƙasace mai yawan arziƙin
zinare yankin nahiyar Africa. Ƙasar Ruman nada babbar
Daular mulki data ƙunshi manyan sarakuna masu ɗunbin
tarihi kala-kala da labaransu bazai taɓa kasancewa shuɗaɗɗe
ba a duniya. Ba arziƙin zinare ne kawai suke da shi ba, sunada
nau'i-nau'in kayan itatuwa da wajajen noma harma da kiwon
dabbobi da akan fita da su ƙasashe daban-daban ko'a shigo
cikin ƙasar a saya. Al'ummar wannan ƙasa sun kasance wasu
irin ƙyawawan mutane masu kwarjini da cikar haiba, sai dai
duk da ƙyawun da mafi rinjayensu ke da shi hakan bazai hana
a samu masu ƙarancin ƙyawun ba. Sunada yawan addinai da
ƙabilu tamkar kowacce ƙasa, sai dai mafi rinjayen ƙabila sune
masu yara yaren rumanci, sannan addinin musulinci yafi
kowanne addini ƙarfi da rinjaye. Abu mafi mamaki a ƙasar ta
Ruman shine, duk da ƙarfi da rinjayen da addinin musulinci ya
samu suna girmama al'adunsu na kaka da kakani musamman
ƙarfin iko. Ƙarfin iko nada matuƙar tasiri a ƙasar Ruman
ainun, hakama al'adu da girman masautunsu na taka rawar
ganin hana dukkan abinda turawa suka zo musu da shi taka
rawar gaban hantsi a garesu bayan ilimin boko, duk da suma
sun shiga cikin ƙangi na mulkin mallakar turawan a ƙarnin
daya shuɗe. Babu wani mulki dake da tasiri sama dana
sarautunsu tun a farkon ƙarnikan baya har zuwa yau ɗin nan
da suke rayuwa bisa mulkin mallakar sarakunan dake mulkin

𝕯𝖆𝖚𝖑𝖆𝖗 𝕽𝖚𝖒𝖆𝖓 itace babbar masarauta da
mallakar su.

dukkan masarautu ke ƙarƙashin ikonta bama su talakawa

maimakon mulkin siyasa, su 𝐃𝐀𝐔𝐋𝐀𝐑 𝐑𝐔𝐌𝐀𝐍 itace
kaɗai ba. Itace tamkar fadar shugaban ƙasa a wasu ƙasashe. A

babbar masarauta mai faɗa aji akan komai da kowa na ƙasar
Ruman, komai yana tabbatuwa ko akasinsa da ƙarfin ikon
sarki mai mulki a kujerar wannan daula. Bama gasu talakawa
ba, babu wata masarauta a cikin kasar Ruman data isa koda

mulkin 𝐒𝐡𝐚𝐡𝐚𝐧-𝐬𝐡𝐚𝐧 (King of kings). Ƙarfin mulkin
ɗaga murya a bayan idon Daular Ruman saboda karfin ikon
wannan Daula yakai a duk faɗi da ƙasar Ruman ke dashi babu
wani mahaluki da zai iya faɗar siffa kai tsaye ko kamanni na
sarkin da duk zai mulki daular ruman tun zamanin ƙarnikan
baya, saboda tsantsar girmamawa da akema sarakunan
wannan Daula ko iya ɗaga kai a musu kallon ƙurulla na kusa
babu maiyi, daga nesa kuwa fuskokinsu ababen kwarjinine
irin na masu mulki da a ranar wasan al'ada na kowanne
shekara ake iya ganinsu a zahiri daga nesa bisa keken doki. A
tsari da ƙa'idar daular ruman dukan yarima mai jiran gado
daya shiga shekaru bakwai na girma za'a ɗaukesa kowa ya
daina ganinsa, a sirrance zaiyi ilimin zamani dana addini
dama duk wata rayuwarsa irin ta kowa. Bayan cikar shekarun
girma a garesa za'a fara bayyanasa ga sarakunan sauran
masarautu cikin shigar da ƙwayar idonsa kawai zasu iya gani.
Nuna yarima mai jiran gado ga sauran masarautu na nufin
alamar mahaifinsa zaiyi murabus kenan ya ɗaurasa a karagar
mulki basai bayan ransa ba. Sarkin kuma da baya buƙatar

mutuwarsa. 𝐓𝐚𝐣𝐰𝐚𝐫 𝐇𝐚𝐲𝐬𝐚𝐦 𝐢𝐛𝐧 𝐀𝐛𝐝𝐮𝐥𝐥-
hakan bazai taɓa bayyana yarima ba ga kowa har sai bayan

𝐌𝐚𝐣𝐞𝐞𝐝 shine sarkin daular ruman daya shuɗe aka ɗora
ɗansa ɗaya tilo bisa karaga. Shi kaɗai ya haifa a duniya, shine

tarihi yazo ba'a taɓa 𝐒𝐡𝐚𝐡𝐚𝐧-𝐬𝐡𝐚𝐧 mai ƙarfin iko da
kawai magajinsa sai mata huɗu da saɗaka daya bari. A yanda

daularsa ta gagari duk wani jar fata nunawa yatsa ba
kamarsa, ya shimfiɗa mulki a Ruman dama yankin Africa gaba
ɗaya, izzarsa da ƙarfin mulkinsa yasa ba masarautun Ruman
kawai ba, dukkan masarautun Africa na biye da shi da
girmamawa da tsoro mai ƙarfi. Ya tara arziƙi mai ban tsoro da
ban mamaki, ya kuma shimfiɗa ayyuka da ba Ruman kawai

jajayen fata masu faɗa aji na tsoro da shakkar 𝐓𝐚𝐣𝐰𝐚𝐫
ba, Africa gaba ɗaya bazasu iya mantawa ba. Kaf ƙasashen
𝐇𝐚𝐲𝐬𝐚𝐦 𝐢𝐛𝐧 𝐀𝐛𝐝𝐮𝐥𝐥-𝐌𝐚𝐣𝐞𝐞𝐝. Sarki Haysam ya
raini ɗansa ɗaya tilo tamkar sauran shuɗaɗɗun sarakuna
koma fiye da su, dan saɓanin sauran yarima da tarihinsu ya
shuɗe shi wannan yariman tun a shekara uku na haihuwarsa
babu wanda ya sake ganinsa kojin labarin inda yake rayuwa.
Sai dai a kullum akanji sunansa a bakin Tajwar Haysam fiye da
sau goma, ambaton sunansa shine mafi yawan magana dake
fita a bakin Tajwar. Hakan kan saka razani da tabbatuwar shi
wannan yarima zai kasance na daban a dukkan sarakunan da

rabbata, dan kuwa dai kam da gaske 𝐓𝐚𝐣𝐰𝐚𝐫 𝐄𝐬𝐡𝐚𝐚𝐧
suka shuɗe kenan. Tabbas hasashen mutanen ƙasar ruman ya

𝐢𝐛𝐧 𝐇𝐚𝐲𝐬𝐚𝐦 𝐀𝐛𝐝𝐮𝐥𝐥-𝐦𝐚𝐣𝐞𝐞𝐝 ya zama sarki na
daban a cikin dubban sarakuna, tare da labari mai ban tsoro
da razani fiye dana mahaifinsa. Kamar yanda ƙa'idar daular
ruman take bayan cikar shekara talatin da biyar yarima
Eshaan ya bayyana a ƙasar haihuwarsa ta Ruman, sai dai
kamar kowane yarima na baya babu mai iya ganin fuska ko
suffarsa ta ainahi, hatta da idanunsa ma shi babu wanda zai
iya ganin koda ƙwayar cikinsu sakamakon glass dake sakaye
da su. Bayan gama bayyanashi ga masarautu da wata ɗaya
kacal Tajwar Haysam bin Abdul-Majeed yay murabus aka
ɗaura yarima mai jiran gado bisa kujerar mulkin daular ruman
tare da auren mata huɗu galla-galla daga mabanbanta

𝐓𝐚𝐣𝐰𝐚𝐫 𝐄𝐬𝐡𝐚𝐚𝐧 bakwai akan karagar mulki Tajwar
masarautu masu ƙarfin faɗa aji a kasar ruman. Kwanan

mai murabus Haysam bin Abdul-Majeed ya kwanta jiyya,
jiyya ce data girgiza kowa ta kuma bada mamaki, dan kuwa
kwanansa ɗaya tak yace ga garinku nan. Kwatanta tashin

ba. Ƙura bata lafa ba mutuwar ɗaya daga matan 𝐓𝐚𝐣𝐰𝐚𝐫
hankalin da ƙasar Ruman ta shigama a lokacin bazai lissafu

𝐄𝐬𝐡𝐚𝐚𝐧 ta sake bayyana, kwana ɗaya da mutuwarta
watama ta sake mutuwa a washe gari amare suka rage saura
biyu. Al'amari ya fara saka zukatan jama'a hasashen da babu
damar cewa komai. Wata biyu tsakani ɗayar matar ta uku ta
sake mutuwa saura ɗaya. Tofa babbar magana. Abu mafi

wata. Kenan matan Tajwar 𝐓𝐚𝐣𝐰𝐚𝐫 𝐄𝐬𝐡𝐚𝐚𝐧 da
girgiza zukata shine mutuwar ɗayar data rage a shigar sabon

mahaifinsa sun gama mutuwa kaf a cikar wataninsa uku da
hawa karagar mulkinsa da kuma aurensa. Abun ya taɓa
zukata aynun, sai dai babu wanda ya iya ko tari saboda tsoro.

ɗaura auren 𝐓𝐚𝐣𝐰𝐚𝐫 𝐄𝐬𝐡𝐚𝐚𝐧 𝐢𝐛𝐧 𝐇𝐚𝐲𝐬𝐚𝐦
Sai dai abu mafi tsayawa arai a cikar wata na shidda aka sake

𝐀𝐛𝐝𝐮𝐥𝐥-𝐦𝐚𝐣𝐞𝐞𝐝 da wasu matan biyu daga gidajen
masarautun kasar ruman. Labarin bai canja ba, dan kuwa
suma sun mutu ɗaya bayan ɗaya kafin cikar shekararsa guda
da hawa mulkin. Abin al'ajabi aka kuma sake aura masa wasu
biyun daga wasu masarautun, suma ɗin dai kamar ƙiftawar
ido nasu labarin ya shuɗe a cikin shekara ɗaya. Haka aka sake
ɗaurama Tajwar Eshan aure da wasu mata daga mabanbanta
masarautu da tsoro bazai barsu hana auran ƴaƴansu ba, haka
kuma suka mutu suma ya kasance duk ya auri yarinyar
kowace masarauta goma da suke da su.
Zuwa yanzu ba shakka da tsoron ɗaga murya bane kawai
a zukatan mutanen ƙasar Ruman, hatta numfashi suna
yinsane tamkar ɓerayen dake a ƙarƙashin tsaron maguna. A
tunaninku yaya sautin fitar numfashin zai kasance?😭.

★★_________★★

Sunanta shine 𝕱𝖆𝖗𝖊𝖊𝖉𝖆𝖍 na yanka, sai dai iyayeta da
dukan jama'a na mata alkunya da 𝑰𝒇𝒇𝒂𝒉. Su huɗu
iyayensu suka haifa, itace auta a cikinsu. Hanash! Shine
auta 𝑰𝒇𝒇𝒂𝒉. Sunan mahaifinsu Zayyan!, amma suna
namiji babba. Arfa! ita ke bi masa, Fariha! Itace ta uku, sai ita

kiransa Babiy, mahaifiyarsu Jamaima! Suna kiranta Ummu.
Ƙasar Ruman ƙasarsu ce ta gado tun iyaye da kakanni, nan
kaɗai suka sani, anan kuma kaɗai suke rayuwa. Kamar yanda
na faɗa muku a tun farko ƙasar Ruman ƙasace mai tarin arziƙi
nau-i daban-daban da ake kaikawo da su a cikin ƙasa da
wajenta, tun daga kan zinare, noma, kiwo, ƴaƴan itatuwa
dama wasu daban lissafo ba. Sai dai duk da wannan tarin

cikin matsayin talakawa ba. Kamar dai su 𝑰𝒇𝒇𝒂𝒉,
arziƙi da ALLAH ya basu hakan bai hana kasancewar wasu a

mahaifinsu talaka ne mai rufin asirin ALLAH. Manomi kuma
makiyayi, a nomansa harda noman zuma yakeyi. Dukkan
wani nau'in zuma zaka samesa a hannunsa, wannan yasa
yake mu'amula da daular ƙasar Ruman. Duk da ba masu arziƙi
bane su mahaifinsu mutumne mai tsantseni da taka tsantsan,
sannan ya tsaya tsayin daka wajen ganin sun samu ilimin
addini dana zamani irin na yara ƴan gata. Gidansu gidane mai
ban sha'awa da birgewa a ɓangaren mu'amulantar juna mai
cike da soyayya da ƙauna. Basu da wani buri sai na faranta
ran juna, a koda yaushe zaka samesu cikin nishaɗi dan
talaucinsu bai taɓa kasancewa damuwa ga rayuwarsu ba ko
nakasu ga farin cikinsu. Idan ɗaya na ciwo sukan kasance
tamkar su duka suke ciwon, idan ɗaya na farin ciki sukan
kasance su duka cikin farin ciki. Sune abokai kuma kawayen
junansu harda iyayensu. Sunada tarin burika na rayuwa dana
kai da kai, wasu a rubuce, wasu a ƙayyade a cikin zuciya,
wasu a bayyane, wasu a adane a ƙasan zukata. wasu sun cika,
wasu ƙaddarorinsu masu ɗaci da saka zubar hawaye dake
gudana a halin yanzun sun yanke igiyar kaiwa ga samun
cikarsu. Labarin sauyawar tasu, da yankewar tasu ya farane
daga wata rana dake dai-dai da cikar sauran kwanaki huɗu na
zagayowar bikin al'ada da ƙasar Ruman ke gudanarwa. Ranar
da tarihinsu bazai iya gogewa ba, zukata bazasu iya mantawa
ba, lissafin faruwarsu da shuɗewarsu bazai taɓa daina
maimaita kansa ba koda a bayan rai ne.😭

A kowane karshen wata Babiy ke kai zuma tulu uku
daular ruman, amma a duk bikin shekara na al'ada tulu goma
yake kaiwa dan shi kaɗai ne yardajje a manoman zuma da

zamannin Tajwar Haysam. Koda ya mutu kuma 𝐓𝐚𝐣𝐰𝐚𝐫
sarki ke iya amfani da zumar dake zuwa daga hanunsa tun

𝐄𝐬𝐡𝐚𝐚𝐧 bai daina amsa ba. Sai dai kuma duk da wannan
yarda a kullum zagaye suke da tsaro ta fannoni daban-daban
duk a dalilin zumar da Babiy kan samarwa Tajwar. A ranar
data rage sauran cika kwanaki huɗu na bikin al'ada rashin jin
daɗin jiki ya saka Babiy bama Hanash damar tafiya dasu duka
cikin ƙaton gidan gonat da yake noman zuma domin ɗurasu a
sabbin tulunan da za'akai daular ruman. Da'ace yasan
anjimarsa ko ƙaddararsa data ahalinsa da bazai taɓa barin
wannan lokaci zuwa ba koda a mafarki. Sai dai kash, ƙaddara
ta riga fata inji masu iya magana. Cike da farin ciki suka fita,
dan kuwa a shekara sau uku kacal Babiy ke barinsu shiga cikin
lambunsa. Ba lambun kawai ba, hatta fita koda ta zuwa
makarantace suna yintane cikin shiga mai lulluɓe dukkan
kamanni, domin kuwa ƴaƴan nasa na ɗauke da wani irin sirrin
ƙyawu mai ɗaukar hankalin duk wanda zaiyi tozali da su, dan
haka kullum cikin shigar larabawa suke harda niƙabi,
idanunsu kawai ake iya gani da tafukan hanunsu, a yau kam
sai suka fita a asalinsu batare da sanin iyayensu ba duk da
kuwa suna dai sanye da abayoyin, sai dai babu niƙabin. Su
kansu da'ace sun san abinda ke biye da rayuwarsu da zasu
ninka niƙabi kan niƙabi ne har sama da sau sittin idan zai
nisanta zuwan almakashin daya datse walwalin zinaren farin
cikin zukatansu.
Sun isa lambu sun gudanar da ayyukan da Babiy ya
umarcesu cike da farin ciki da nishaɗi, suka tsinko tarin ƴaƴan
itatuwa kowa da nasa da burin abinda zaiyi dashi a ranar
bikin al'ada dake tunkarosu. shigarsu gida dai-dai da isowar
tambura da bushe-bushen algaitu masu ban mamaki da
al'ajab a cikin kunnuwansu dama dukkan sauran talakawan
gari, dan abune da ba'a sabaji ba sai a wasu lokuta na
gittawar Tajwar daga can kan hanya bawai a cikin anguwa
kamar hakan ba...........✍

2

...........Cikin ƙarfin hali Babiy ya zabura hanyar soro domin
dubawa duk da halin ciwo da yake ciki. Baya yaja da sauri
saboda cin karo da suka kusayi da tawagar jama'ar Daular
Ruman dake ƙoƙarin shigowa suma. Kansa ya rissinar alamar
girmamawa a garesu. Hanash da Ummu ma a kusan tare suka
zabura. Cike da girmamawa mai haɗe da matsanancin tsoro
Babiy ya zube bisa gwuyawunsa. Hakan da su Ummu sukaga
yayi ya sasu zubewar suma tare da risinar da kawunansu,
jikkunansu na matuƙar tsuma dan abune da ba'a taɓa gani
kojin labarin faruwarsa a tarihin ƙasar Ruman ba. Babban
mutum dake jagorantar tawagar ya tsaida idanunsa akan
Babiy. “Ya kai wannan talaka dake a ƙarƙashin mulkin daular
ruman, munzo da babbar magana ne gareka bisa umarnin
daular ruman”.
Ƙasa Babiy ya ƙarayi da kansa, tare da haɗe hannayensa
waje guda. “Ina mai matuƙar farin cikin ganinku tare dani, ni
mai biyayyane ga kowanne umarninku”.
Duk da maganar Babiy ta musu daɗi babu alamar
hakan a fuskokinsu. Ya miƙe cikin rawar jiki zuwa ɗakin
Ummu. Mintuna kaɗan ya dawo da babbar tabarma sabuwa
ƙal data saya domin auren Arfa zai shimfiɗa a gabansu.
Dakatar da shi Shugaban tawagar tasu yayi cikin ɗaga hannu.
*_“Munzo nan ne domin isar da saƙo ba zama ba ya kai
wannan talaka dake a ƙarƙashin daular ruman. Umarni a
gareka daga daular ruman, taga iri a gidanka kuma tana
buƙata. Muna mai tayaka farin cikin zama ɗaya daga cikin
surukan tarihin daular ruman”_*.
A matuƙar firgice Babiy da iyalansa duka suka ɗago cikin
zabura da matasanancin rikicewa. Sai dai basu da ikon koda
motsa bakunansu balle neman ƙarin bayani. Kasancewar ba
amsa dama suke buƙata ba mutumin ya janye idanunsa daga
Babiy ya maida kansu Arfa da suka ƙanƙame hannayen
junansu.
“Wacece babba a cikinku?!”.
Kalamai huɗu masu ƙarfin razani da neman fasa zukatan mai
saurare da har abada bazasu bar amsa sauti cikin zuciya da
ɓargonsu ba suka fita daga bakin ɗaya daga firɗa-firɗan
samudawan dake zagaye da mutumin. Babu wanda ya iya
motsawa a cikinsu, dan kuwa sake dulmiya suke a cikin
duhuwa.....
Saukar sautin wata zabgegiyar bulala mai adon jikin
zakanya a jikinta ya sakasu zallo baki ɗaya. Babiy ya zube a
ƙasa saboda azaba na raɗaɗin shigar wannan bahaguwar
bulala a jikinsa, ganin basamuden mutumin dake riƙe da
bulalar ya sake ɗagawa zai zuba masa Arfa ta miƙe tana mai
fashewa da kuka jikinta na karkarwa tace..
“Nice!”.
Cikin daka tsawa basamuden hadimin yaba Fariha da Iffah
umarnin suma su ɗago. Ɗagowa sukai jikkunansu na
karkarwa ga hawayen tausayin mahaifinsu ya wanke musu
fuskoki. Idanu ya zuba musu kusan na sakan goma, kafin ya
janye ya maida ga shugaban tawagar tasu.... “Zancenta nakan
gaskiya ALLAH ya ƙara maka lafiya”. ya faɗa cikin girmamawa
ga shugaban tawagar tasu. Shugaban ya gyaɗa kansa shima
idanunsa akan Arfa “Mahaifinta da ɗan uwanta zasu zama
waliyyanta”.
Ya faɗa cike da cika umarni yana mai nufar hanyar fita batare
da wani ƙarin bayani ba......

Har aka tafi da Hanash da Babiy babu abinda su Fariha
suka fahimta, balle ma Iffah da kallon kowa kawai take.
Kukan Ummu ne ya dawo da su hankalinsu, gaba ɗayansu
sukai kanta. Ummu dake kuka kamar ranta zai fita ta haɗasu
su duka ukun ta rungume jikinta na wani irin rawa......

★★_______★★

Tafiyarsu da kamar awanni uku Babiy da Hanash suka
dawo gida da doki ɗaya da tarin kayayyaki, sai rakuma guda
uku. Fuskokinsu cike suke da firgici mai tsayawa a zukatan
masu kallo. Ba abinda sukazo da shi bane a gabansu Ummu,
burinsu susan mike faruwa? Kawai. Basu samu amsa ba daga
garesu har bayan shuɗewar wasu awanni, kafin Babiy ya basu
amsa cikin dakewa....
“Na bada aurenta ga *_Shahan-shan_*, bamu baro ba sai
da aka ɗaura musu aure, wannan raƙuman da dokin
sadakinta ne”. Ya ƙare maganar idonsa akan Arfa.
Tamkar saukar aradu mai tarnatsa haka furucin ya isa cikin
kunnuwansu, Ummu tai baya zata faɗi Babiy ya riƙota, kansa
yake girgiza mata alamar kartace komai, suma yaran ya juyo
garesu yay musu nuni da shiru ya jata suka shige ɗaki.
Umarnin mahaifinsu shine mafi girman biyayyarsu garesa
matsayinsu na waɗanda ke rayuwa a ƙarƙashinsa, badan sun
so ba suka zaɓi shiru, sai dai shirun nasu bai hanasu haɗe kai
a ɗaki suyi kuka ba su ukun. Kuka irin wanda za'a kira kuka a
duk idaniyar da zubar hawaye ke kwaranya na rashin lissafin
ƙididdiga. Mintuna sun shuɗe, hakama awannin da suka
ƙarasa kalmashe wannan yinin. Bayan sallar magrib saiga
motoci da tawagar hadimai tare da wasu hamshaƙan mata
huɗu wai sunzo ɗaukar Amarya Arfa. Kuka suke tamkar ransu
zai fita, haka sunaji suna gani suda iyayensu aka shirya Arfa
cikin shiga ta alfarma aka wuce da ita Daular Ruman.
Dare ya riski zukatansu cike da damuwa, yayinda sai
ɓarawo mafi iya satane ya samu nasarar sama musu
nutsuwar wucin gadi wato barci. Sun wayi gari kunnuwansu a
buɗe na jiran jin labarin mutuwar ƴar uwarsu, sai dai babu
wani alamar hakan har sake shuɗewar kwanakin zuwan ranar
bikin al'ada.
Babu fashi aka gudanar da bikin al'ada na ƙarshen
kowace shekara. Sai dai su a zuri'arsu babu wanda ya leƙa
koda ƙofar gida. Anyi an gama, kamar kowace shekara an
samu rashin rayuka a wasanni daban-daban, da kuma haɗarin
mota dana mashina suma a tituna daban-daban saboda
cinkoson jama'a dalilin garin shine babban birni da Daular
Ruman ke ciki. Bikin al'adar ƙasar ruman kuma yana ɗaya
daga cikin biki mai tsananin ƙayatarwa da mutane daban-
daban suke halarta daga sassan duniya ta ko ina. Shahan-
shan ya fito zagaye tamkar kowace shekara cikin shiga ta
alfarma, bashi a karan kansa ba hatta keken dokinsa ma abin
kallo ne, sai dai a wannan karon ma babu wanda zaice ga
kamanin Tajwar Eshaan ibn Haysam Abdull-majeed ɗin.

★ A haka lokaci ya ƙara turawar da kwanaki suka zama
watanni kusan uku. Shuru na waɗannan watanni bai sama
musu wata nutsuwa ba, dan a kallon farko da mai gani zaima
gidansu zai san akwai matsala tattare dasu. Komai ya sauya,
sauyawa irin wadda ƙaddara ta shigo cikin tarihinsu. Babu
mai walwala a cikinsu, komai na ƙarfin hali sukeyi, abinci ya
gagara ciyuwa yanda ya kamata a koda yaushe garesu, sai cin
ƴaƴan itatuwa, tunkan a sanar musu alamominsu sun
tabbatar da zaman makokinsu. A haka duhun wani dare na
cika watanni uku da kwana uku da auren Arfa ya sake
riskarsu, suka sake zama ƙarƙashin mulkin mallakar ɓarawo
mafi iya sata koda shiri ko babu wato (barci). Daren da yazo
ma Iffah da wasu irin munanan mafarkai masu firgici daban
tsoron.
Har rige-rigen fitowa suke daga ɗakunan barcinsu
sakamakon fitar sautin razananniyar ƙarar data karaɗe gidan
mai ban tashin hankali. Su duka huɗun suka rufu a kanta
kowa na ambaton sunanta da kai hannu jikinta. Duk da sanyi
da akeyi jike take sharkaf da zufa ga illahirin jikin nata daya
ɗauka zafi. Ummu ta rungumeta tana mai sakin hawayen da
ke kwance a cikin idanunta. Ta riga ta farka dan haka itama ta
ƙanƙame Ummun tana fashewa da nata kukan.
Ba yau ne karan farko da Iffah ke shiga irin wannan tsoron
ba sakamakon firgici a mafarki, sai dai na kwanakin nan yafi
razanarwa da saka ruɗani a zukatansu. Babiy ya kai hannu ya
shafa yalwataccen gashin kanta, murya a raunane yake
ambatar sunanta.. Kanta ta ɗago a hankali fuskata sharɓan da
hawaye, ta dubi mahaifin nasu da Yayansu Hanash da Fariha,
sassanyar ajiyar zuciya ta sauke tare da haɗiye sauran kukan
tana tashi zaune daga jikin Ummu ta share hawayen dake jiƙe
da fuskarta. Matsawa tai jikin mahaifinsu tana mai kamo
hanunsa.
“Babiy inajin tsoro, matuƙar tsoro a wannan mafarkin fiye
dana kullum. Babiy itama Nina Arfa kashemana ita zasuyi
kamar sauran matan daya aura?, itama zamu rasata na gani a
mafarki na...”
Da sauri Hanash da dukkan rauninsa ya bayyana a
fuskarsa ya shiga girgiza mata kansa cikin aro jarumta.
“Mafarki ba gaskiya bane Iffah, ki kwantar da hankalinki Arfa
na cikin ƙoshin lafiya tamkar mu insha ALLAHU...”
“Amma Akh Hanash nawa yasha zama gaskiya, a daren da
Nina Arfa zata bar gidan nan irin wannan mafarkin nayi a
kanta, yau ma shine na maimaita da ita babu banbanci a
cikinsa na rantse maka”.
Har ƙasan zukata zancen nata ya dake su, ganin bayyanar
rauni a fuskokinsu ya saka Babiy yin murmushin ƙarfin hali
yana shafa kanta. “Shaiɗanu zasu iya dawo miki da
makamancin sa ai Ibnati, dan haka ki kwantar da hankalinki
Arfa na lafiya a gidan aurenta”.
Bazata cigaba dayin jayayya da su ba, amma tana cikin
matsanancin damuwa tamkar yanda take hango tasu akan
fuskokinsu. Maimakon komawarsu barci sai duk suka miƙe
zuwa tsakar gida, alwala suka ɗauro, suka koma can runfar
dake matsayin falon iyayensu suka fara salla da miƙa kukansu
ga UBANGIJIN talikai da fatan hana tabbatuwar abinda
zukatansu ke cikin tsananin fargaba. Haka suka kasance har
sallar asubahi gaban mahaliccinmu, bayan idar da sallar
asubahi maimakon kwanciya sai suka riski kansu a zaman
jugum-jigum na jiran tsammani. Har fitowar rana babu wani
yunƙuri daga ɗayansu. Sai ko ga isowar abinda suke fargabar
ya riskesu ya iso garesun. Shigar bugun gidan a cikin
kunnuwansu ta sakasu miƙewa a zabure gaba ɗaya kuma a
lokaci ɗaya, kowanne cikin rawar jiki da fidda tsammani.
Babiy ne yay jarumtar ƙarasawa ga soro cikin jan ƙafa. Tunda
yay tozali da hadiman masarauta zuciyarsa tai wata irin
masifar wulƙitawa.....
“Kun kasheta itama ko?!”.
Da shi da hadiman suka riski muryarta a cikin kunnensu a
bazata. Sam babu tsoro ko shakka irin wadda akema duk
wani mai alaƙa da masarauta a ƙasar cikin idanunta a yau.
Sun soye sunyi jazur irin na tashin hankali. A harzuƙe cikin
hadiman ɗaya ya daka mata tsawa da faɗin, “Hattara ɗiyar
talakawa, bakin rijiya ba wajen wasan yaro bane”.
“Idan yaron ya kasance rago ba!!”.
Ta bashi amsa itama a tsawace. Shimfiɗeɗiyar bulalar
hanunsa ya ɗaga zai zuba mata Babiy ya kare cikin rawar jiki
yana mai zubewa ƙasa a kan gwiyawunsa. Sosai a zaba ta
ratsashi, ya rimtse idanu cikin aro dakiya da jarumtar dole, “A
gafarceta ita ɗin yarinyace masu nasara”. Ya faɗa cikin rawar
murya saboda azabar tasirin shigar bulalar.
Ƙasa Iffah takai durƙushe gaban Babiy tana mai fashewa da
kuka, kafin ta ɗago ta dubesu zatayi magana Babiy yasa
hannu ya rufe mata baki jikinsa na tsuma. Jikin nata itama
tsumar yakeyi, sai dai ita bana tsoro bane na tsananin baƙin
ciki ne da bushewar zuciya. So take ta amayar da abinda ke
bakinta an hanata. Batare da hadiman sun sake bi takantaba
suma suka isar da saƙon dake tafe da su.
“Kasancewarka mai biyayya da bin umarnin masarauta a
karo na biyu an sake baka damar halartar jana'izar ɗiyarka kai
da zuri'ar ka. Mun barka lafiya”.
Innalillahi wa-inna'ilaihirraji'un. Babiy ya shiga ambata,
kusan a tare Ummu da Fariha suka saki razananniyar ƙara
wadda ta jawo hankalin maƙwafta da mutanen dake tsaitsaye
a ƙofar gida tun wucewar hadiman masarauta. Dan sun san
dai labarin gizo bazai wuce na ƙoƙi ba........

*_WASA FARI GIRKI_*

Dole ne zuri'ar mal. Zayyan su ambaci rasuwar Arfa da
kalmar WASA FARIN GIRKI a jerin zaren ƙaddarar da ta kutso
a rayuwarsu mai ɗauke da almakashin da ya datse farin
cikinsu. Sun rasata tamkar labarin hikayoyin marubuta ko
wasan kwaikwayo na film. Ta tafi tafiyar da bazasu sake
ganita ba, tafiyar da babu wanda aka bawa damar yin
cikkakkiyar sallama da ita a cikinsu hatta mahaifansu. Ta
shuɗe a ƙaddararsu tamkar yanda ruwan damuna kan tafi da
duk wani yayin dakan tare masa hanya a lokacin wucewa.
Komai ya faru tamkar ba'aiba. Babu mai iya koda tari balle
bin ba'asi. Iyakarsu kukan idanu dana zuci wanda muryarsu
kan tsayane kawai iya filin gidansu ko katanga basu isa bari ta
haura ba. A yau ma dai Babiy da Hanash ne sukaje domin
jana'izarta. Suko aka barsu da amsar gaisuwa a cikin gida
wadda mutanensu talakawa na zuwa musu itane a
ɗarare.......
Kwanaki sun cikagaba da shuɗawa tamkar ba'ai komai
ba, yayinda ɗayar matar Tajwar da aka aura masa tare da
Arfa itama dai ta mutu bayan wasu watanni. Bayan su Arfa
ba'a sake jin Tajwar yayi wani aure ba, sai dai mutane na
raɗeraɗin a duk randa aka kaisu domin ziyartar turakarsa
babu fashi gawarsuce take fitowa. Hakan yasa kowa ke
danganta mutuwar matan

Please Login or Register in order to submit comment