Reading Dauɗar Gora by Bilyn Abdull ce Chapter 23 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

nemeta
amma bai samu ba. Yaci kuka har ya godema ALLAH dan
zatonsa ma ita suka rasa. Cikin rawar murya ya ambaci
sunanta duk da yaji muryarta. Amsawa tai da kuka, bata jira
cewarsa ba tace, “Sir kaji tsoron ALLAH ka sanarmin gaskiya
akan iyayena. Na rokeka karka ɓoyemun komai”. Zufa ce ta
shiga karyo masa tako ina, dan baiyi tunanin jin wannan
tambayar bazatanba a bakinta.
Shirunsa ya sake tada hankalin Iffah, ta cigaba da masa
magiyar da dole ya faɗa mata gaskiyar data buƙata. “Tabbas
na ɓoye miki Iffah, amma tun bayan barinki gida baifi da
kwanaki ba aka rasa ɗan uwanki da Babiy sakamakon......”
Ya zayyane mata labari tiryan-tiryan kamar yanda ya
bincika. Babu kuma banbanci da abinda ta gani a wancan
video ɗin na farko. Ya kare da faɗin, “Wlhy har yanzu akan
binciken inda aka kaisu ake amma babu labarinsu. Nima
kuma a yanzu haka ina yin nawa ta ƙarƙashin ƙasa amma har
yanzu ban samu wani bakin zaren ba....”
Kukan data fashe masa da shi ne ya katsesa daga jawabin
nasa. “Ba zaku gansu ba, ba zamu ƙara ganinsu ba, sun rabani
da su kamar yanda suka rabamu da ƴan uwana. Wlhy nima
sai na kasheshi kamar yanda ya kashesu. Na rantse bazan
barsa ba, bazan taɓa barinsa ba. Yanda ya halakasu da
macijin tsafi sai na halakashi da dafin maciji na gaskiya. Shima
sai ya ɗanɗa......” kuka ya sarƙeta ta kasa cigaba da magana...
Cikin tashin hankali daga can Sir Fawzan ke faɗin, “Iffah
ban gane ba. Dan ALLAH ki daina kuka kimun bayani, kaina ya
kulle dan ALLAH kiyi shiru kinji, wlhy na miki alkawarin
taimaka miki akan koma minene, koda kuwa nima zan rasa
rayuwata ne.....”.
“Babu wannan lokacin sir, bani da shi. Kai dai kawai ina zan
samu dafin maciji mai haɗarin gaske?”.
“Ya ALLAHU! dan ALLAH ki faɗamin mike faruwa? a yanda
zan fahimceki”.
“Idan bazaka samamin abinda nake buƙata ba na Barka
lafiya”.
Yana hello-hello bata sauraresa ba ta yanke wayar, koda ya
sake kira bata ɗauka ba, da taga zai dameta ma sai ta jefa shi
a black list. Kaikawo ta cigaba dayi a ɗakin tana kuka. Komai
ya cakuɗe mata, zuciyarta ta gama ƙeƙashewa da bushewa.
Ta sallama duk wani ɗan sauran rangwamenta. Abinda kawai
idonta da zuciyarta ke gani gawa huɗu ta ahalinta kwance
duk a dalilin mutum ɗaya tak, lokaci yayi da zatai abinda ya
kawota itama dan bai cancanci cigaba da rayuwa ba mutumin
nan sam, tayi alkawarin tare zasu mutu, amma sai ta kasheshi
ta kuma bayyanama duniya wanene shi.
Yanda taci kuka ta fita hayyacinta dole ta bama duk wani
tausayi, da ƙyar ta iya zaman rubuta komai da ya rage, ta
tattare ga Ajmaal, a ganinta ta gama tattare dukan abinda ya
dace ta tattare masa. Hatta ƙudirinta na kawar da Shahan-
shan ta hanyar dafin maciji bata ɓoye masa ba. Ta kwashe
videos ɗin dake wayar zuwa wayarta ta turama Ajmaal ɗin,
takumayi gajeren video da kalaman masu girgiza zuciya har
biyu. Ɗaya na Ummu da su Kaka ta roƙa ya bamawa, ɗaya
kuma na al'ummar ƙasar ruman ne baki ɗaya. Shima tai masa
godiya da fatan alheri da nasara har ƙarshen rayuwa.......


★★..... BARRISTER ★★.....

Barrister dake jin kamar ya ƙwaɗa wayar da ƙasa ya
rumtseta a hannunsa da masifar ƙarfi, a karo na farko wasu
zafafan hawaye suke silalo masa. Jarumar zuciyarsa zugasa
take kada ya yarda ya amince koda zai rasa rayuwarsa,
yayinda wani ɓangaren kuma ke haska masa iyalansa da yafi
so fiye da komai a duniya a halin yanzun. Wannan shine
tashin hankalin mafi ƙololuwar girma daya taɓa cin karo da
shi a rayuwarsa....

Washe gari da safe wujiga-wujiga ya wayi gari, amma
hakan bai saka ko gezau ga mutanen ba. Sai ma duk wani
details daya shafi case ɗin da suka dire masa. Mamaki da
tsoronsu ya sake mamayesa ganin duk wani abinda ke
hannunsa ne. Kuma ya adanasu ne a mabanbanta wajeje.
Akwai wanda a gidansa suke, akwai wanda a office suke,
akwai na mota ma. Amma abin mamaki gasu duk a gabansa
sun tattaro sun kawo masa. Tabbas ya sadaƙar, dan mutanen
nan hatsabibaine na innanaha. In har zasu iya hakan a
kankanin lokaci bayaji idan ya bijire musu iyalansa zasu tsira
kuwa....
“Barrister baka da lokacin dogon tunani, ka shirya dan a
yau oga ke son ka tattaro masa duk bayanin da yake buƙata a
wajen mutanen can. Ciki har da sanin su wanene ainahin
masu aikin, da inda suka ɓoye Abu Hanash da ɗansa”.
Karan farko Barrister ya dubeshi a razane, har ƙoƙarin
taune harshe yake wajen faɗin, “Kana nufin dama baku bane
ke riƙe da su Abu Hanash ɗin...?”
Saurayin yay ɗan waige-waige alamar baya son wani
yaji, cikin raɗa-raɗa yace, “Bamu bane Barrister. Muma
kuɓutar da su muke son yi har ma da kai kanka. Sai dai ban
san miyasa oga bai son ka sani ba ya zaɓi baka aikin a kife”.
Ba ƙaramin zabura Barrister yay ba jikinsa har rawa yake ya
matsa gab da saurayin. “Dan ALLAH kada ka yaudareni ka
faɗa min gaskiya”.
Da sauri saurayin ke masa nuni da yay ƙasa da murya kar
wani yaji, “Barrister wlhy kaji na rantse maka abinda na faɗa
maka shine gaskiya. Na kuma sanar maka ne saboda ka bani
tausayi. Amma iyalanka kansu suna zagaye da tsaro ta yanda
wani bazai taɓa iya samun damar cutar da su ba, kai kanka
kusan sati uku fa muna tare da kai batare daka sani ba. Oga
ba azzalumi bane ba, amma ban san miyasa bai son kasan
taimakonku zaiyi ba. ya kamata kaima ai ka gane hakan tun
farko musamman aikin daya baka ɗin, taya wanda zai cutar
da kai zai kuɓutar da kai?, taya wanda zai cutar da kai zai
ɗauraka akan hanyar abinda kake nema ya baka bakin
zarensa haka cikin sauƙi?”.
“Hakane wlhy ɗan uwa hakane. Kaina ne ya kulle a ruɗani
nake gaba ɗaya. Nagode nagode yanzu kam ka bani ƙwarin
gwiwa, insha ALLAHU kuma sai na bada mamaki. Dan a
wannan gaɓar sai su Abu Hanash sun fita da izinin UBANGIJI,
zan kuma gano koma wanene da hannu a kan ɓoyesu”.
“ALLAH ya baka nasara. Ni bara naje kar wani ya fahimci
ina anan har yanzu”.
Kai kawai Barrister ya ɗaga masa yana murmushi. Wannan
tattaunawa ce ta bama Barrister duk wani ƙarfi da sabuwar
himma na musamman, a yanzu kama baka iya ganin komai
sai murmushi tare da shi, lokacin da aka kawo masa abincin
rana ya buƙaci takarda da abin rubutu. Takardu aka kawo
masa bama takarda ba, hakan ko ya masa daɗi, dan ya
kwashe sauran wannan yinin da dare wajen tsara duk abinda
ya dace. Washe gari har ya fisu zumuɗin son fita ma, sauran
da basu san miya faru ba canjawar Barrister ɗin taita basu
mamaki.....

★★... KAUYEN JUMNA ★★....

Tun kammala bayanin Abu Zainab ga su Kaka jikkunansu
duk yay sanyi, Ummu ma hawaye takeyi, Barrister shine hope
ɗin su a yanzu bayan UBANGIJI masanin abinda ke fili da
ɓoye. Gashi a dalilinsu an rasashi. Idan har aka cutar da shi ta
dalilinsu bazasu yafema kawunansu ba.
Kaka dai jinjina kai kawai yake amma komai ya kasa
cewa, sai Iyyani ce cikin ƙarfin hali da sharar ƙwalla ta dubi
Abu Zainab da damuwa ke shimfiɗe a fuskarsa. “Zakariyya
kuyi haƙuri dan ALLAH, mun jefa rayuwarku a haɗari, ya
ALLAH ka bayyana Abdullahi da gaggawa”.
Ɗan murmushin yaƙe Abu Zainab yayi, cikin danne abinda
ke masa kaikawo yace, “A'a mama ai mutum baya taɓa wuce
ƙaddararsa, kuma har yanzu bamu tabbatar ba ko akan
wannan case ɗin bane muka rasa shin, dan Barrister da kike
ganinsa nan shima hatsabibin kansa ne, gaskiyarsa da
tsayuwa akan ganin tabbatar da ita yasa yanada maƙiya da
yawa akan cases daban-daban hatta a cikin abokan aikinsa
ma. Kinga kuwa zama ta iya yiwuwa ba'akan wannan ɗin
bane.....”
“Dole ya zama akan wannan ne”
Kaka ya faɗa cikin katse Abu Zainab. Duk kallonsu suka maida
a kansa. Ya jinjina kai batare da ya kallesu ba. “Ban san gaibu
ba, amma inaji a jikina akan su Muhammad Zayyanu ne, sai
dai kuma tabbas koma a ina yake har yanzu yana raye insha
ALLAHU. Inajin wannan ƙwarin gwiwar ne a zuciyata”.
Ba ƙaramin mamaki kalaman kakan suka basu ba, sai dai
kowa ya gagara cewa komai sun dai zuba masa ido. Kusan
mintuna biyu gidan shiru kafin kaka ya miƙe, babu jimawa ya
dawo da jakka a hanunsa. Su dai duk suna kallonsa kawai.
Takardar daya zaro ya miƙama Abu Zainab. “Ungo duba
wannan”.
Da sauri Abu Zainab ya amsa ya fara karantawa. Bakinsa
cike da magana ya ɗago yana duban kaka da ke kallonsa.
“Baba wannan kuma fa?”.
Murmushi Kaka yayi da kauda kansa kamar bazaice komai
ba. Sai kuma ya ɗan taɓe baki da fara basu labarin yanda duk
a kai a randa zai dawo. Ya ɗora da faɗin, “Saurayin daya
kawoni gidan nan zuciyata ta bani ba haka nan ya kawoni
ba....”
“Amma baba shine ka amince harma da nuna masa
gida?”.
Kaka yay ƴar dariyarsu ta manya. “Zakariyya kenan, to idan
baka iya kama ɓarawo ba ai shi sai ya kamaka. Ka ganni nan
barni kawai inda ka ganni. Idan na nuna nasan yanada
manufa a kaina tun farko kamar yanda naso nuna masa a
tasha ai bazan san sirrin zuciyarsa ba. Amma dana bashi
dama fa? Yanzu a tafin hannuna yake, kuma jirace nake da
zuwansa dan na tabbatar zai dawo, na masa talalar da tabbas
sai ya dawo da izinin UBANGIJI”.
Abu Zainab kam a yau Kaka ya fara bashi tsoro. Sai dai
ya danne bai yarda ya nuna ba. Kaka ma ya fahimci haka
amma ya kanne, sai jakkar ya tura ma Abu Zainab yana faɗin,
“Wannan sune kuɗin dake tare da takardar”.
Nan ma dai da mamaki Abu Zainab ke kallon kuɗin, kuɗine
masu yawa sabbi ƙal sai ƙamshi suke na sabunta. “Baba
waɗan nan mutanen kuwa anya....”
Kaka yay murmushi mai bayyana haƙora. Sai kuma ya
ɗan kalli sashen da Ummu ke zaune. Tuni ta tashi batare da
sun farga ba har Iyyani..........✍️

46


..........Lokacin da kaka yayi ma Abu Zainab rakkiya sukejin
halin da ƙasar ke ciki, dan shima Abu Zainab kasancewar
fitowar sassafe yayi sannan komai bai fasu ba. Hankalinsu
yayi matuƙar tashi dan basu san wacece a cikin matan sarkin
ta rasu ba.
“Zakariyya zama bai ganni ba, dole ne mu wuce tare
kenan, kayi haƙuri kaɗan jirani anan ina zuwa”.
Kaka bai jira cewar Abu Zainab ba ya koma gida da sauri,
koda su Iyyani sukaga a yanayin da ya shigo suma hankalinsu
ya tashi, amma tambayar duniya yaƙi ce musu komai kan
abinda ya farun, sai cemusu da yay shima zaije Daular ruman
ne.”. jin wannan furucin nasa yasa jikin Ummu fara rawa, a
hankali ta zube ƙasa dan zuciyarta ta gama bata kodai ta rasa
Iffah ko su Babiy. Dama yau kusan gabbanin asuba tayi
mafarkin Iffah na kuka da kiranta tazo ta ceceta, sai kawai ma
zuciyarta tafi karkata akan Uffan..

Su Kaka sun iso daular ruman a harmutse, dan ƴan
zanga-zanga nata da ɗa karuwa harma abin na bama mutane
mamaki. Yayinda jami'an tsaro tuni sun fito ta kowane titi na
masarauta sun tare. Da ƙyar suka samu ƙarasawa gida,
kasancewar ana aikowa gidan domin halartar jana'iza yasa
Kaka yay tunanin wannan ma indai Iffahr ce zasu aiko. Dan
haka suka shiga tambayar ƴan anguwa amma kowa na
tabbatar musu babu wanda yazo. Hankalin Kaka ya tashi fiye
da farko, dan kuwa dai bayan wannan hanyar babu wata mai
sauƙi da zai iya ji sai abokinsa dogon yaro da ke cikin
masarauta. A yanda kuma garin yake hakan abune mai
wahala a garesa kenan......

★ BARRISTER ★

Yanayin da aka wayi gari a ƙasar bai hana su Barrister
fitowa ba, sai ma lokacin shi yasan abinda ke faruwar,
al'amarin ya taɓa masa zuciya, dan ta wani fannin case ɗinsa
tamkar kacokal yanada alaƙa mai ƙarfi ne da abinda ke
faruwar. Har yaji yana tsoron ace yarinyar ce ma ta rasa ran
nata. Dan dole dai ya daure ya isa inda ya nufa. A yau dai bai
samu Sayyid Faizul-Anwar a falon ba, sai dai kasancewar an
san da zuwansa ya samu tarbar data dace. Bayan zaman
kusan mintuna arba'in Sayeed ya fito cikin shigar jallabiya,
cikin girmamawa Barrister ya gaidashi, ya amsa masa da
kulawa shima yana masa barka da zuwa. Suna tsaka da
gaisuwar cikin yaran Sayeed ya shigo ya isar da saƙon zuwan
wasu baƙin. Damar shigo da su ya bada dan yasan da
zuwansu, daga haka ya maida hankalinsa kan Barrister.
Barrister yayi matuƙar mamakin ganin baƙin, sai dai ya
danne hakan dalilin kallon da suke masa matsayin Barrister
Akeem. Gaisuwa sukai ta mutunta juna, har suna tsokanarsa
da cewa shine idonsu na gari. Murmushi yayi yana rissinar da
kai alamar girmamawa. “Kar kuji komai ranka ya daɗe, a
komai muna tare da ku kuma zamu kare mutuncin ku”.
Sosai suka nuna jin daɗi da zancensa. Nan suka shiga
kwarzantashi. Shi dai nasa murmushi ne a zahiri, a kasan rai
kuma yana matuƙar mamakin abokinsa da ɓoyayyun
ayyukansa. Dan bai taɓa tunanin Barrister Akeem zai iya irin
waɗan nan ayyuka ba.....
“Barriter ina alkawarin mu?”.
Sayeed Faizul-Anwar ya katse masa tunani. Ajiyar zuciya yaja
a ɓoye, sai kuma ya muskuta yana murmushi da taɓa bag ɗin
daya shigo da ita. “Ranka ya daɗe komai yazo hannu fiye ma
da yanda kuke buƙata. Sai dai kafin mukai ga nan ina son
nace wani abu saboda wasu dalilai”.
“Faɗi kanka tsaye Barrister baka da damuwa akan
hakan”.
“Nagode ranka ya daɗe. Bawani abu bane mai girma akan
dai shi wannan case ɗinne. Komai dai gashi na gani anan
kuma na tattaro, sai dai yanda aka bani aikin a dunƙule ina
ganin ya kamata nace wani abu duk da dai naga komai a
kansa, amma saboda nasan inda duk ya kamata na toshe a
ramukan da zasu iya yunƙurin buɗewa koma su buɗe ɗin yasa
nake son bada shawara bisa wani hangena”.
Shiru kamar bazasu ce komaiba. Sai dai sun maida
dubansu ga Sayeed Faizul-Anwar, kai ya gyaɗa musu alamar
tabbatar da babu matsala, dan haka kusan a tare suka sauke
numfashi, kafin ɗaya a ciki ya shiga faɗin. “Barrister mun
yarda da kai, sai dai ka sani koda baka san komai akan case
ɗin nan ba bazamu taɓa bari wani rami a buɗe mana ba koya
buɗe maka, zamu kasance a bayanka a kowanne lungu da
saƙo na ƙasar nan.”
“Nagode da wannan karamci”. Barrister ya faɗa da
girmamawa.
“Baka da damuwa Barrister ka cancanta ne.”
Murmushi ya sake saki tare da mikewa ya kai jakar
gabansu, cike da farin ciki suka buɗe suna mai fiddo duk
takardun ciki. Bayan sun ɗan dudduba su suka ɗago fuskoki
cike da murmushi suna yabama Barrister namijin ƙoƙarin sa.
Shi dai nashi murmushi ne kawai. Ɗaya daga cikin baƙin da
ake kira da Sayeed Harun Al-rashid, babban mutum ne a
ƙasar ta ruman, dan riƙƙaƙen ɗan kasuwa ne na gwal da kowa
ya sani kasancewar sunansa yayi matuƙar shura a wannan
harkar data zama babban tattalin arzikin su na ƙasar, dan
Ruman kam bata san iya arziƙin gwal da ALLAH yay mata ba,
shiyyasa duk wani riƙƙaƙen ɗan kasuwa zaka samu gwal ɗin
ne mafi rinjayen makaminsa kamar dai Sayeed Harun Al-
rashid. Ta wani gefen kuma yana riƙe da sarauta sai dai yafi
bama kasuwancin muhimmanci matuƙa. Zamansa ya gyara
sosai yana fuskantar Barrister. “Barrister yanzu mi kake son
ka sani?”.
“Ranka ya daɗe ba komai bane dama sai akan waɗan da
naga case ɗin ya karkata. Na duba dukkan bayanan Barrister
Abdallah Aas, sai dai a yanda na fahimta kamar ya gano inda
su mutanen dake hannun naku suke, dan kafin ma ya rasa
ransa kamar ya fito da ga ƙauyen Lufana ne wajen matar
marigayin, abinda nake son cewa anan ina tsoron yazam
bayan Barrister ɗin akwai wanda yasan wannan sirrin. In
kuwa hakan ta kasance zaman mutanen a station ɗin dana
fahimci kun ɓoyesu zai zama barazana ke nan koda anan
gaba”.

Kusan a tare sukai murmushi, Sayeed Harun Al-rashid ya
muskuta zamansa cikin nuna damuwa da zancen Barrister.
“Maganar ka nakan hanya Barrister shiyyasa tun kafin yau
muka gama maganin duk abinda kake gudun. Tun daga
farkon wannan case ɗin idanunmu akan komai suke, dan
haka ka kwantar da hankalinka. Su kuma tuni basa a police
station ɗin, dama mun kai ajiyar su ne domin ɓadda kama
bayan kwanaki kuma muka ɗauke su, amma kai a yanzu mi
kake son cewa?”.
Anzo dai-dai gaɓar da Barrister keson azo, dan haka ya ɗan
murmusa yana mai ƙara bama kansa nutsuwa. “Alhmdullh
kun fahimci inda nake buƙatar akai ranka ya daɗe. Abinda
nake son cewa kai tsaye shine ayi duk yanda za'ai cikin
kwanaki biyun nan abar ƙasar ruman da mutanen gaba
ɗaya”.
“Eh maganarka abin dubawa ce kam, amma kuma mizai
hana kawai a ɓaddasu a wuce wajen, dan abinda ya zama
dalilin zuwansu hanunmun ma an sameshi cikin sauƙi yanzu
haka”.
Barrister yay ɗan jimm dan bai fahimta ba, amma sai ya
dake bai sake musu wata tambaya ba gudun karsu zargi wani
abu. Sai dai ya cigaba da faɗin, “Ɓaddasu bashine mafitaba
ranka ya daɗe, dan a ɗan bincike da nayifa akwai babbar
matsala game da mutuwar Barrister Aas”.
Babu wanda zancen bai daka ba a acikinsu, Sayeed Faizul-
Anwar daya kafe Barrister da ido yay saurin faɗin, “Barrister
bamu fahimce ka ba, mi kake son cewa?”
“Ranka ya daɗe yanzu zan fahimtar da ku. Idan har kun
saurari dukkan labaran dake yawo har yanzu babu wani
tabbaci na samun alamar sassan mutum a cikin motar
Abdallah, wannan shine yaja hankalina tun a ranar farko
bayan nabar nan na fara nazari da bincike. Tabbas Abdallah
na raye, sai dai ya ɓoye kansa domin bada ƙafa. Na sanshi
nasan mizai iya fiye da tunaninku. Shiyyasa nake ganin kashe
mutanen a yanzu bashine mafita ba, muyi nesa da su da ƙasar
nan ta yanda babu inda zasuji ɗuriyarmu, sai kuma mu samo
wasu a madadinsu a buɗe shari'ar ta yanda zamu ƙona
Barrister Abdallah Aas da ransa batare daya farga ba”.
Dukansu gumi suke na tashin hanakali, sai dai babu
wanda ya iya cewa komai har zuwa wani tsahon lokaci.
Sayeed Harun Al-rashid ya nisa yana mai share ɗan gumin
daya taru masa a goshi. Ƙyaƙyƙyawar fuskarsa fara tas gaba
ɗaya ta ƙwaɓe alamar rashin damuwa. “Zartar da hukunci
bazai yuwu yanzu ba Barrister, amma kaje zuwa anjima zakaji
komai ta waya”.
“Babu damuwa ranka ya daɗe”. Barrister ya faɗa cikin
jimami shima, sai dai acan ƙasan ransa dariya yakeyi, yayinda
wani gefe na zuciyarsa ke tabbatar masa akwai wani babba
mai alaƙa da case ɗin bayan su, shiyyasa bazasu iya zartar da
hukuncin ba kai tsaye. Yau ma dai an rakosa da kuɗi masu
yawa har mota.......


★★... BAYAN KWANA BIYU ★★....

A kwanaki biyun nan abubuwa da yawa sun faru tako
wane ɓangare, sai dai marasa daɗi sunfi masu daɗin rinjaye.
Zuwa yanzu dai da gaske ƙasar ruman da jama'arta suke basa
buƙatar Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed matsayin
Shahan-shan. Dan tun tsirarun mutane na zanga-zanga a
wasu jahohi takai yanzu ƙasar ma gaba ɗaya ta ɗauka. Abu
mafi ban mamaki harda wasu a manyan ƙasar na nuna goyon
baya ga talakawa, ciki kuwa harda wasu Tajwar na jihohi.
Yayinda ta wani gefen kuma hankalin wasu manyan ƙasashen
duniya ya fara dawowa kan zanga-zangar dama dalilin yinta.
Babban abinda ke tunzura jama'a shine biris daga Shahan-
shan, yayinda kuma a cikin gida hankalin ƴan majalissar sa ya
rabu kaso biyu, wasu na goyen bayan ya saukan wasu na
buƙatar karya sauka dan shine kawai ya cancanta da kujerar a
ganinsu. A talakawan ma bai rasa tsirarun masoya ba, sai dai
basu da ƙarfin ja da masu boren shiyyasa suka koma gefe
sukai shiru matsayin masu kallo da ido.

*_IFFAH!_*

A kwanaki biyun nan yanda Daular ruman ke a hargitse
haka Iffah ke a hargitse. Kuka kam idanunta har sun daina
fidda ruwan hawaye. Cikin ƙanƙanin lokaci tayi wata irin rama
mai ban tausayi. Haukan da iyalan Sayeed Khairul-Bashar keyi
a masarautar da wanda jama'a keyi a waje sai ta ɗaukesa
wasan yara. Idan su da suka rasa uba kawai zasu harmutsa
masarautar haka ina ga ita data rasa ahalinta duka, a ganinta
ita ya cancanci ta hargitse ƙasar ruman baki ɗaya ma ai. Sai
dai yanda ƴan zanga-zanga ke daɗa ƙaruwa na saka mata
farin ciki, dan abin ban mamaki har wasu a cikin Tajwar na
jihohi suma sun ƙara tunzura wuta da bada goyon baya akan
saukar Shahan-shan ɗin, hankalin ƙasashe kuma ya fara
dawowa ƙasar ruman, da alama dai dama a jirace kowa yake
da wannan damar. Hakan na sake tunzura ƙwarin gwiwar
ƙudirinta.
Wutar wannan al'amari na ƙara ruruwane dalilin shirun
Tajwar Eshaan. Babu shi babu cewarsa, harma wasu sun fara
tunanin anya kuwa yana cikin masarautar ma ko?.... Duk
wannan bai damu Iffah ba a yanzu, hankalinta gaba ɗaya ya
tattara ne akan ta ina zata samo dafin maciji. Bata da wani
amintacce a cikin masarautar, a waje kam sir Fawzan ne
kawai, shima kuma zuwa yanzu ta fara shakku akansa saboda
tana ganin ya ɓoye mata abinda ya faru da su Babiy ne bisa
wata manufa. Idan tace zata fita a sulale daga masarautar
taya kuma zata dawo cikinta? Wannan ƙalubalen keta faman
mata kaikawo harya gagara samun mafita a kwanaki biyun
nan. Tana a bangarenta bata ganin kowa kowa baya ganinta,
waɗan da zasu iya ganinta hankalinsu a tashe yake dan kai
tsaye su abin ya shafa, shirunsu kuma sai ya bama Iffah
damar fassarashi da abinda zuciyarta ta gama tabbatar mata,
dan haka itama a yanzu ta haƙƙaƙe bata da lokacinsu.

Kamar yanda ta tsara bayan sallar la'asar ta shirya tsaf
cikin abaya data amshi jikinta, dan ma ta rame ga idanunta
da suka ɗan kuklumburo amalar taci kuka bana wasa ba. Duk
da masarautar a harmutse take haka ta keta cikinta
hadimanta na take mata baya har sashen marigayi Sayeed
Khairul-Bashar. Tayi matuƙar mamakin tarbar data samu dan
batai zaton irinta ba, sai dai abinda bata sani ba shine su
kallon tausayi suke mata da tabbatar da itama bawai ta tsira
bane a hannun azzalumin. Dan malamin duba da matar
Sayeed Khairul-Bashar ɗin ta ziyarta tun lokacin daya ɓata
kafin aga gawarsa ya tabbatar mata akwai ƙulli mai girma da
Shahan-shan keyi game da rayuwar Iffah shiyyasa itama bata
mutu ba a sanda aka kaita sashenshi. A ranar bata ɓoyema
ƴaƴanta komai akan zancen nan data jiyo ba, sun kuma yi
niyyar samun Iffah har sashenta da batun washe gari aka
tashi da wannan tashin hankali. Wannan shine dalilinsu na
mata tarbar data bata mamaki. Ita kuma kasancewar
zuciyarta a kusa take tana musu ta'aziyya tana share hawaye
da handkherciff. Sai hakan ya ƙara mata kima a idon iyalansa.
Yayinda ƴan uwansu kuma da basu san komai na ke jin zafin
ganin Iffahr da fassarashi matsayin leƙen wani asiri dan a
yanzu wasu a cikin ahalin masarautar su kuma suna ma Iffah
kallon wata ƴar kaɗafin Tajwar Eshaan ce tunda har ta tsira
daga kisan gillarsa..........✍️
47


.........Kamar yanda Iffah tai tunani labarin zuwanta sashen
Sayeed Khairul-Bashar ta'aziyya har ya isa kunnen surukarta
dama na jikin Tajwar Eshaan irinsu malikat Haseenat da su
Daneen Ammarah. Dan tana fitowa kiran Daneen Ammarah
ya shigo wayarta. Bata ɗaga ba, aka kuma sake kira nan ma
dai ta share kamar bataji ba. Sai da ta koma sashenta da
kusan mintuna goma sannan tai kiran Daneen Ammarah ɗin
back. A bugu biyu ta ɗaga, Iffah ta taɓe baki cikin rashin
damuwa tai sallama da fara gaishe ta. Da kulawa Daneen
Ammarah ta amsa. Iffah na jiran jin ta mata batun fitarta sai
Daneen Ammarah ta jeho mata tambayar da bata da alaƙa
ma da fitar.
“Ibnati na kiraki ne akan Abni, shirunsa na tadamin
hankali matuƙa, gashi yana ƙara harzuƙa mutane ƙasa, kinga
dai yanda ƙasar nan ke sake rikicewa. Mu dukanmu mun
nemesa a waya amma bamata shiga, na fara zargin anya ma
yana cikin masarautar nan?”.
Murmushin takaici Iffah tayi, amma a zahiri sai ta danne ta
fara magana cikin kwantar da murya. “Wannan shine tunani
na nima Mamy, sai dai ban san yanda zanyi ba ganin ku
manya bakuce komai ba.”
“Shirun na dole ne Ibnati, bazaki gane babbar sarƙaƙiyar
dake cikin masarautar nan ba ne. Amma tabbas akwai
matsala, akwai kuma gagarumin al'amarin dake ɓoye amma
yana son bayyana kansa a wannan gaɓar.....”
Cikin zumuɗi Iffah tace, “Mamy minene shi dan ALLAH?”.
“Humm Fareedah kinyi ƙarama da yawa ba yanzu ba. Ke dai
kawai abinda nake so da ke shine ki taimaka ki bincika min
idan Abni yana a gidan nan...”
“To Mamy, amma dai zaiyi wuya tunda kunce idan yana
cikin damuwa kulle kansa yakeyi baya kuma sauraren kowa.
Sai nake ganin ni taya zai saurare ni”.
Murmushi Daneen Ammarah tayi mai sauti. “Rashin
saurarenmu bashi ke nufin kema bazai saurareki ba Ibnati. Ke
dai gwada sa'arki mu gani”.
Iffah dai ta jita

Please Login or Register in order to submit comment