Reading Dauɗar Gora by Bilyn Abdull ce Chapter 2 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

da tsafi yakeyi dasu.
Wata huɗu da sati ɗaya cif tarihi ya sake maimaita kansa,
dan kuwa Fariha ta sake faɗowa a jerin matan da aka
ɗaurama Tajwar Eshaan ibn Haysam Abdul-majeed aure da
su. Batare da wani shawara ba a safiyar alhamis suna zaune
kira ya riski Babiy daga masarauta, babu wanda bai shiga
tsoro da firgici ba a cikinsu, sai dai babu wanda ya isa hana
hakan a duk faɗin ruman. Sunaji suna gani babiy yay shiri ya
amsa kiran. Tafiyarsa da awanin da basu gaza biyar ba sai ga
hadiman masarauta sunzo sunma Fariha ɗaukar amarya
itama babu wani bayani daga garesu. Ranar dai kam Iffah
bata gazaba kojin tsoro wajen gwada musu hauka, dan bata
bari an fita da Fariha ba har sai da basamuden nan ya zabga
mata bulalar dorinar hanunsa data sakata zubewa, bata tashi
dawowa hayyacinta ba sai bayan wucewarsu da kusan awa
guda. Zuwa lokacin har Babiy ya dawo. Kamar dai Arfa itama
Fariha an ɗaura mata aure da sarkin da kowa yake masa
inkiya da fir'aunan wannan ƙarnin. Sai dai a ɓoye wannan
suna ke fita a bakunan talakawan gari irinsu Iffah. Sakamakon
bulalar da aka zabga ma Iffah bayanta yay mugun fashewa
har akan mazaunanta, ga wani raɗaɗi mai azaba na ratsata
har ta kasa riƙewa sai da ta saki ƙara. Babiy da Ummu suka
rufu a kanta, hawaye suke suna jeramata sannu, Hanash na
gefe zaune idanunsa jajur alamar tsananin ɓacin ran da babu
ƙarfin ɗaukar mataki......
Tayi jiyya ta kwanaki uku, wajen ya warke, daga haka
kwanaki suka cigaba da tafiya, inda a cikar watanni biyu
itama Fariha mutuwarta ta riskesu tamkar ba'ayita ba. Sun
sake rasa Fariha a dalilin auren Tajwar Eshaan ibn Haysam
Abdul-majeed........✍😭



*_Hummmm!!😕_*

3

_____________

MAAB LUXURY HOME!! Sabuwar duniyar hamshakan mata da
ƴaƴan gata.💞

GIDAN ƙawa da ƙawata gidajen da suka cika gida.

SABUWAR DUNIYAR Amare da uwargidan data amsa sunanta
ƴar gaban goshi.

MAAB LUXURY HOME wata duniya ce ta ƙawa da ƙawata
gidajenmu da kayan ƙyale-kyale na burgewa da ɗaukar
hankalin duk wani mai kallo.

SUNYI FICE Fice irin na ɗaya a cikin tsara, sune na farkon fari,
a farin da za'a kira fari a kowace irin duniya.

A GAREMU ba sitturu na alfarma da kawa ne kawai ke
tabbatar da mu hamshakai ba. Sai mun haɗa da ƙawata
gidajenmu da kayan MAAB LUXURY HOME zamu kasance
cikakkun ƴan gata ababen kallo da nunawa sa'a koda a cikin
dubun da sukafi dubu.

MAAB LUXURY HOME sun takaita mana dukkan wahalar
nema ko order a kasashen ketare ta hanyar wadatamu da
galla-gallan kayayyakin adon gidajenmu

MAAB LUXURY HOME. Duniyar kayan Kitchen da decoration
din gida na keta raini.

INA UWARGIDA INA AMARYA!!?* Ku ziyarci shagon mu dake
No 22 Ahmadu Bello Way, Kano state. Ko kuyi order daga
shafin mu na Instagram @maabluxuryhome. Ko Facebook
@maabluxuryhome. Ko Ku nememu a lambar waya
*08034631010*.

Mai azama shi za'a kira dana farkon fari😉. Bara nai sauri
nawa suzo hannuna kafin a kwashe😁♀️

______________

.........A wannan gaɓar haukane kawai ya rage wannan ahali
suyi, dan duk dauriyar Babiy ya kasa danne raɗaɗi da zafin da
yakeji. Itako Iffah kalaman dake fita a bakinta kausasa sun
saka kowa ke ɗaukar tama zare kawai. Daga ƙarshe maganin
barci aka ɗura mata. Bata tashi farkawa ba sai a ƙauyen da
kakanninsu ke rayuwa. Wato iyayen Ummu. Rayuwa a
ƙauyen Jumna a gareta tamkar mai gushewar hankali ya
zame mata. Domin bata gane komai sai sambatu da kalamun
ɗaura ɗammarar ɗaukar fansa ga duk ahalin Daular Ruman.
Ba ƙaramin dagewa da jajircewa kakannisu da su Babiy sukai
ba a kanta wajen ganin ta samu lafiya ta dawo hayyacinta. A
cikin watanni takwas ta rasa yayunta guda biyu, wannan
babban tarihine da bazai gogu a zuciya da ruhinta ba har
karshen rayuwarta. Bayan jiyyar watanni kusan uku ta dawo
hayyacinta. Sai dai ta daina fira'a da kowa, an daina ganin
dariyarta ko farin cikinta. Babu abinda ke'a ranta sai buri da
ƙudirin ɗaukar fansa. Tama kanta alƙawarin ita da hannunta
zata kashe *_Tajwar Eshaan ibn Haysam Abdull-majeed_*.
Bayan nan idan itama an kasheta burinta ya cika na kawar da
azzalumin sarki mai mulki irin na fir'auna a ƙasarta a cikin
al'ummarta....

*_(Babbar magana. Tayaya wannan buri naki zai cika Iffah
😱? Sarki mai cikakken iko irin Tajwar Eshaan, mai amsa
sunan Shahan-shan da ko fuskarsa babu wanda ya iya sani a
cikin kasar Ruman har yanzun. Anya kuwa....? To mudaije
zuwa wai mahaukaci ya sai kura😬🤧🚴🏼)_*



★★★

“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un” bakinta ke ambata cikin
firgici da rawar jiki sakamakon farkawar da tayi daga
mummunan mafarkin daya risketa a cikin barcinta. Ta dafe
kanta dake wata irin sarawa na ciwo tamkar ana mata
luguden taɓaren daka a tsakkiyarsa, gaba ɗaya jikinta ya jiƙe
da zufa tamkar tayi wanka. Kusan watanni biyar kafin
mutuwar ƴan uwanta da fara canjawar salon mafarkainta
saɓanin na baya, abu mafi tsoratarwa kuma kusan mafarki
ɗaya ne ke maimaita kansa a kowane barcinta idan ta
kwanta. Sai dai mafi tashin hankalin a yau yayi
kamanceceniya da na wasu dare da tarihi bazai taɓa
mantawa da shi ba a cikin rayuwarsu ita da ahalinta.
“Nina Arfa! Nina Fariha!”.
Ta ambata a zahiri zuciyata na ƙara ƙarfin gudu, yayinda
hawaye suka shiga rige-rigen sauka a kumatunta. Tabbas irin
wannan mafarkin tayi a daren da suka rasa Arfa, hakama
daren mutuwar fariha. Yau kuma gashi ta maimaitashi akan
kanta. Itama kenan zasu rasata?. Kai ta shiga girgizawa wani
kuka masu ƙarfi na sake tahomata, hannu tasa ta toshe
bakinta gudun kar sautinsa ya kai ga kunnen kakanninta. Sai
dai aikin gama ya gama. Dan kuwa muryar kakanta takeji jikin
ƙofar ɗakin nata a hankali yana ambatar sunanta. Da sauri ta
shiga goge hawayen, kafin ta tashi daga shimfiɗar barcin nata
wadda karan gado ne da katifar rimi. Mayafi ta ɗauka ta
yanama jikinta, ta ƙarasa ga ƙofar ta buɗe...
“Kina lafiya kuwa ɗiyar nan?”.
Ya faɗa cikin kafeta da idanu. Kanta dake rissine ta jinjina
masa, cikin son danne kukan dake yunƙuromata ta bashi
amsa.
“Ina lafiya Kaka”.
Jin shiru bai sake cewa komai ba ta ɗago ta dubesa a karon
farko. Shima dai kallon nata yakeyi tamkar mai nazari. Sake
maida idonta tai ƙasa, hawayen da take faman riƙewa suka
ɓalle mata da gudu. Bata san ta ambaci “Kaka nima zasu
kashe muku ni ko?. Inaji a jikina nima zaku iya rasani nan kusa
tamkar yanda muka rasa su Nina Arfa”. Rawar da jikinta ta
fara ta sata zubewa a gabansa kuka na ƙwace mata. Kusan
minti biyu baice da ita komai ba, ita kuma ta kasa tsaida
kukan.. Jin saukar hanunsa saman kafaɗarta ya sata haɗiye
kukan, ya ɗagota tsaye yana ɗan murmushi dake sake
bayyana tsufansa. Gefen mayafin jikinta ya kama ya shiga
goge mata hawayen. “Fareedatu! Ki kwantar da hankalinki,
insha ALLAHU babu abinda zai faru da ke, mafarki ai ba
gaskiya bane ba. Suma su Arfa kwanansu ne ya ƙare, koba
komai kuma sun rasu a gidan aurensu. Wannan kawai ya
ishemu farin ciki”.
Kanta ta jinjina masa tana sauke ajiyar zuciya a jajjere. Ya
cigaba da shafa kanta a hankali har zuwa wani ɗan lokaci.
“Kije kiyi addu'a ki kwanta abinki da safe zamuyi magana”.
A hankali tace, “Kaka ina son zuwa naga su Ummu gobe to
dan ALLAH”.
Da sauri ya girgizamata kansa. “A'a bazai yuwu ba Iffah,
iyayenki sun kawoki nan ne domin kuɓutar dake, taya kike
tunanin zan barki komawa cikin daular Ruman?. Tun ina
ƙanƙanin yaro nake bauta wa masarautar Ruman, bayan
mutuwar mahaifina na cigaba da bautar saƙa kayan doki a
garesu kamar yanda mahaifina ya barmin gado, a haka na
haifi ƙanin mahaifiyarku shima ya mayeni, gashi har girma ya
riskesa shima yana bauta musu. Mun rasa ɗan uwan
mahaifiyarku a yaƙin kare daular Ruman, mun rasa Arfa, da
Fariha. Ke ɗaya da kika rage mana da yayanki wajen
mahaifiyarku kuma sai muyi wasa da rayuwarki? Bazai
yuwuba jeki kwanta...”
Batare daya sake bata damar yin magana ba ya juya ya
koma bayan ya jamata murfin kofar. Da kallo kawai ta bisa
hawaye na silalo mata. Duk yanda taso komawa barcin bayan
tafiyarsa hakan ya gagara, zuciyarta ta kasa fita da ga ƙangin
fargaba, da gaske tanajin matuƙar tsoro bayan rasa Fariha da
Arfa da sukai watanni ƙalilan da suka shuɗe itama su rasata,
tanaji zuciyar ahalinta bazata iya ɗauka ba idan itama suka
rasatan. Wasu zafafan hawaye suka sake silalo mata masu
raɗaɗi da saka ƙuna a ƙirji......

★★★

“Iffah! Iffah!!.....”
Sautin ƙwala kiran sunanta daga muryar kakarsu da suke kira
Iyyani ya sakata fitowa daga banɗaki data zagaya domin yin
fitsari. Turus ta tsaya tare da haɗiye maganar da zatayi tana
mai kallon ɗan-uwanta Hanash dake zaune gefen kakar tasu a
ƙarƙashin bishiyar ɗoruwa da take a tsakar gidan. Murmushin
da yakemata ta maida masa, kafin ta ajiye butar hannunta ta
ƙarasa garesa. Dab da shi ta zauna tana mai ɗan rungumesa
ta gefe da faɗin, “Ina kewarku Akhi”.
Murmushinsa ya sake faɗaɗa yana mai kallon fuskarta.
Ya kai hannu ya shafi yalwataccen gashin kanta da mayafin ya
zame mai tsaho da santsi. “Muma muna kewarki Little angel.
Gidan duk ya sake zama mana babu daɗi”.
Yanda maganar tasa ta ƙare cikin rauni itama sai idonta ya
cika da ƙwalla. Amma sai ta dannesu da murmushin mai ɗaci
tana kaɗa kanta kawai.
“Tashi ki bashi ruwa mana, k haka ake tarbar baƙo a
garinku”.
Baki ta ɗan tura gaba da kallon Iyyani mai maganar, tayi
hakane danta katse raunin data hanga a fuskokinsu. Ta miƙe
tana bata amsa cike da shagwaɓa. “Iyyani laifinkine fa, ban
taɓa ganin matar da bata tattalin mai gida ba irinki, dole
Yayana ya miki kishiya”.
Daƙuwa tamata cikin gatsina fuska. “Ungo naki nan
Fareedah, yo bandama lalacewa mizanyi da wannan faratun
mai kama da jar tsada tuzurin banza”.
Hanash ya tsuke fuska yana kallon Iyyani. Murmushi
Iffah tayi tun kafin ya faɗi abinda ke bakinsa. Dan dama inhar
suka haɗu da Iyyani sai ta hasalashi take jin daɗi shi da Arfa
akan ƙinyin aure, duk da bawani shekarune da shi ba, dan
ashirin da shida ne kawai, Arfa nada ashirin da uku, Fariha
nada ashirin da ɗaya. Iffah nada goma sha takwas....
Iffah ta dire masa abinci da ruwa ta sake kaiwa zaune
kusa da shi sannan ta dubesa. “Akhi yasu Babiy suke?”.
Ya nisa a hankali bayan ya dire moɗar ruwan daya sha.
“Duka lafiya suke. Suna gaisheki ke da su kaka. Duk da suma
dai nan da kwana kusa zamu ma dawo nan ɗin muma. Yanzu
haka nazo duba can tsohon gidanmu ne dan asan gyaran da
za'ai masa”.
Sosai ta kafesa da ido ita da Iyyani. Kafin cikin ƙarfin hali
Iffah tai magana. “Amma Yaya su Babiy basa ganin rayuwa
zata mana wahala anan sakamakon bamu sababa sam.
Sannan ayyukansu dake acan miye makomarsu? Da
karatunmu muma?. Abinda ya faru ya riga ya faru, tunda
hannayenmu bazasu iya maidosu ba, mi zaisa zukatanmu
bazasu cigaba da haƙuri ba. Barowarmu cikin Daular ruman
tamkar munji tsorone, ko sake sakin rayuwarmu a hanun
waɗanda kansu kawai suka sani.......”
“Tsoro halak ne Iffah. Bama muba mafi yawan masu yara
mata sunata barin daular ruman a yanzu domin tseratar da
ƴaƴansu daga auren jeka nayika. Karatun ƴammata yana
neman tsayawa cak, kowace na tsoron fitowa ta zama nama
a hanun hadiman daular ruman. a yanda lissafin yake a yanzu
an rasa mata goma sha huɗu fa, a tunaninki kafin ƙarewar
wannan shekarar ba'a rasa fin hakaba duk da bawai ya cigaba
da auren bane.”
Wasu hawayene masu ɗaci da ƙuna suka silalo ma Iffah,
tai saurin saka gefen mayafinta ta share tana murmushin
takaici. “Niko a ganina gudu bashine mafita ba, muryoyinmu
ya kama mu ɗaga wa duniya kowa yasan halin da muke ciki,
idan har a ƙasar Ruman babu wani sama da nasa mulkin ai a
sauran ƙasashen duniya akwai wanda suka fisa...”
“Humm Iffah ke yarinya ce har yanzu.”
“Sosai kuwa Hanash. Shiyyasa bata gane komai sai abinda
yanzu take zuwa da shi”.
“Humm Iyyani kenan”.
Iffah ta faɗa a yanayin jin raɗaɗi a maƙoshinta. Su duka
kallonta sukai, sai dai ta ɗauke kanta gefe tamkar bata gansu
ba. Daga haka babu wanda ya sake cewa komai har tsahon
wani lokaci. Iyyani ce ta canja hirar da wani abu daban har
Hanash ya kammala. Tare da shi suka fita wajen duba tsohon
gidan da kakaninsu da suka haifi Babiy ne suka rayu a ciki,
dan sudai tunda suka taso a cikin birinin daular ruman suka
san kansu duk da a ɗan gefen gari suke acan ɗin ma. Sai dai
su shigo cikin ƙauyen Jumna a matsayin duba kakannin nasu.
zuwa yanzu su duk sun rasu, shiyyasa gidan ya kasance babu
kowa. Duk ma ya rusa ya fita hayyacinsa dan ginine na jar
laka tamkar yanda duka gidajen ƙauyen suke. Sun ɗan jima
acan suka dawo, sun iske kaka ya dawo shima daga fitar da
yay tun ta safe gona ɗebo sassaƙe-sassaƙen magunguna. Ƙara
zaman tattaunawa sukayi iya su uku, ita dai Iffah bata cewa
komai. Daga ƙarshe ma tashi tai ta shige ɗakin kwananta.
Bata sake fitowa ba sai da kaka ya neme ta. Sassaƙe-Sassaƙen
magungunan daya ɗibo ɗazun ne a gabansa, kowanne ya
ɗauresa daban-daban. Ya turamata babban robar da suke
ciki... “Zaki fara amfani da su Iffah, bana son kiyi wasa dan
ALLAH. Waɗannan kuma hayaƙine, a kowacce duhun magriba
ki tabbatar kinyi turarensu, wannan kuma a ruwan wanka ne,
da kin idar da sallar asuba ki zubasu cikin ruwa kaɗan ki cire
kayanki ki tabbatar duk jikinki ya samu”.
“Tofa kaka wannan ɗin kuma duk na miye?”. Iffah ta
tambaya cikin nuna mamaki.
Idanu ya tsiramata na kusan mintuna uku tamkar mai
nazari, sai kuma ya ɗauke kansa da wani yanayi mai wahalar
fassara. “Faruwar ƙaddararmu bashi ke nuna baza'a sake
jarabtarmu ba. Idan jiya ta shuɗe da ɗaci zata iya yuwuwa
yau ɗinmu da dariya zata kasance, sai dai sanin mike a
gobenmu al'amarine mai girman gaske, damin gaibunmu ce
ita ALLAH ne kaɗai masanin mi zaizo.”
Kallon juna sukai ita da Hanash, Iffah ta ɗan ɗage kafaɗa
cikin yanayin ban fahinta ba, shima sai ya kaɗamata idanu
alamar shima hakan take. Atare suka maida dubansu ga kaka.
Amma sai ya kauda kansa alamar baya buƙatar kowacce irin
tambaya daga garesu. Iffah ta jinjina kai kawai alamar ko'oho.
Sai kuma ta miƙe tana mai faɗin, “Ni dama fa na yanke
shawarar zanbi Akhi mu koma. Tunda dai naji sauƙi gara naje
na koma makaranta anata wuceni a darasi”.
Ba karamin waro idanu Hanash yay ba, zaiyi magana kaka
ya dakatar da shi ta hanyar yin murmushi da kaɗa kansa. “Ita
rayuwa rubutacciya ce tunkan halitta, an rubutatane da
alƙalamin da ba'a goge rubutunsa, babu wani hannu daya isa
gogeta koda da ƙarfin iko. Dole ne sai anyi hakan, ko muna so
ko bama so mashin nan sai ya isa inda aka aikashi. Domin ita
*KIBIYAR AJALI! SULKE BAYA TARETA SAI TA GITTA*”.
A rikice Hanash ya tari numfashinsa. “Kaka bana gane
dunƙulallun zantukan nan naka, ka fito fili dan ALLAH ka
sanar mana mi kake son faɗa...”
“Hanash! Lokacin faɗar baiyiba ai, nima kurman baƙin
kawai na gani, fassarar sai UBANGIJI”.
Sosai Hanash ya sake tsare fuskar kaka da idanu, kamar
yanda itama Iffah tai tsai tana kallon nasa. Su dukansu sun
jima da sanin kaka mutum ne hatsabibi, dan kuwa mahaifinsa
gawurtaccen masanine da azamaninsa akan kallesa tamkar
matsafi ko wani mai gani har hanji, sai dai kasancewar bai
ajiye buzu ya zauna akan iya wannan al'amarin ba yasa ake
shakkar faɗa, yana bada taimako na magani akan abubuwa
daban-daban musamman harkar aljanu komai ƙarfinsu da
shaiɗancinsu. Sannan yana sana'arsa ta saƙa kayan kwalliyar
doki. Kaka ya gaji abubuwa da dama a garesa, sai dai shi ya
watsar da harkar bada maganin dan shima dai a karan kansa
yana ta'allaƙa sanin mahaifin nasa da bokancin, duk da dai
bai fito fili ya bayyana hakan ba kuwa, amma rashin maida
hankali akan abinda ya shafi hakan zaisa ka zargi ko haka
ɗinne. Akwai kayan aiki na mahaifinsa da yawa a killace a
wani waje da shi kaɗai ya sani, kuma tun bayan mutuwarsa
shi ya tattare su ya killace su............✍

4

.........Iffah tayi mamaki da kaka ya bari salin alin tabi Hanash
washe gari, duk da Iyyani taso borewa ita. Amma wasu lafuza
daga cuɗaɗɗun kalamansa ya sata yin shiru ta bisu da addu'a.
Kaka yayma Iffah gargaɗi matuƙa akan abubuwan daya bata,
ya kuma tabbatar mata ko guda ɗaya taƙiyi zaiji hakan a
jikinsa.
A hankali ta murza awarwarayen hannunta da shine ya
sakamata, ta sake lumshe idanunta da sakin ajiyar zuciya.
Haka kawai takejin awarwarayen da girma da kuma banbanci
da irin wanda take sakawa a baya domin kwalliya, ko miye
dalili oho.

Daga Ummu har Babiy a tsorace suke kallon Iffah da
Hanash da suka shigo. Hanash ya girgiza musu kansa cikin
sauri yana faɗin, “Wlhy ba laifina bane Babiy. Itace ta bore
akan saita biyoni, kaka kuma ya bata goyon baya. Dan a
cewarsa _(Babu wani nisa dake bada tazarar gujema ƙaddara.
A wani ajin jarabawar data biyoka ma gara kai ka tunkareta.
Dan ba kowane kogo bane ke zama kogo ga ma'abocin gudun
ceton rai)._ Babiy na kasa fassarawa, akoda yaushe
cirkuɗaɗɗun kalamai daga bakin Kaka masu tsaurine da
wahalar fahimta. Dan ALLAH idan kun sani ku fassara mana”.
Maimakon amsa daga Babiy baya sukaga yayi tamkar zai
faɗi, sai dai cikin sa'a ya dafe gini tare da dafe kansa alamar
hajijiya. Ummu ma ƙasa takai zaune jikinta na rawa, hakan sai
ya ƙara firgitasu. Da sauri duk sukai kansu suna mai
tambayarsu suna lafiya kuwa?. Da kai kawai suka amsa musu,
Babiy harda ƙoƙarin ƙaƙaro murmushi. Cikin son kwantar
musu da hankali yake kallonsu. “Kunga karku sakama
zukatanku wata damuwa, ba maganar Baba bace ba, kawai
dai bana jin daɗine kwana biyun nan dama”.
Jimm sukai alamar tunani, sai dai kuma babu damar yin
musu ko ƙin aminta da cewar tasa. Hanash ya taimaka masa
suka koma cikin runfa, Iffah kuma tana riƙe da Ummu..

★★★

Washe gari batare da sun sani ba Babiy yay sammakon
yin tafiya zuwa ƙauyen Jumna. Ya samu tarba daga surukan
nasa ko ta girmamawa....
Ƙyaƙyƙyawan tsohon da Tattarowar fatarsa ta tsufa bai
hana bayyanar ƙyawun cikar halittarsa ba ya sake kallon
dattijon gabansa a karo na babu adadadi. Murmushi ya saki a
karon farko, cikin karyar da kai da ƙanƙan da idanu ya kai
hannu bisa kafaɗar dattijon. Numfashi yaja kakkaura da
juyowa alamar dawowa hayyaci. Ya maida kansa ƙasa ya
sunkiyar saboda girmamawa ta surukuta dake a tsakaninsu
na tsahon shekaru.
“Humm Muhammadu Zayyanu!”.
Tsohon ya kira sunan tamkar mai sake bita a ranar da aka
raɗa ga mai shi. Ɗago idanu ya sakeyi a karo na biyu sai kuma
ya risinar tare da amsawa da “Na'am Baba”.
“Tun isowarka magana nake gani shimfiɗe a fuskarka
amma bakinka ya kasa furtawa, ko wani abu ya sami Hanash
da ƴar uwarsa ne a hanyarsu ta komawa gida jiya?”.
“A'a baba ko ɗaya, lafiya lau sukaje cikin ƙoshin lafiya
kuma, sai dai.....”
Sai kuma yay shiru ya kasa ƙarasawa. Kaka dake kallonsa yay
ɗan murmushi, “Sai dai baku so komawar Iffah ba ko?”.
“Hakane baba. Domin kuwa babu abinda ya canja a daular
Ruman, muna jin tsoron rasata itama kamar ƴan uwanta, duk
da bamu da tabbacin zasu sake waiwayrnmu, sai dai
kalamanka sun sakamu a ruɗani har muka kasa rumtse idanu
a daren jiya domin yin barc......”
“Hana ido barci bashi ke nufin damar iya sauya abinda
bakai ka rubuta ba. Muhammadu Zayyanu! Da ace
ƙaddararmu a hannayenmu take da kaf mutane bazasu zana
zaman duniya ba a littafinsu musamman idan sun san koda
daɗin busawar iskar dake cikin aljanna ce. Karka damu kanka
da sanin sirrin cikin dutsen da ko'a kallo abin firgitarwa ne.
Mumini yakan kasance mai azumtar yini daga UBANGIJI, ya
kuma sallaci duhun dare daga UBANGIJI domin yaye damuwa
ko samuwar nutsuwa a duniyarsa. Gaibu daga ALLAH take,
zahirin da yaso mu sani kawai yake iya nuna mana ta isharar
rayuwa ko canjawar tunanin zuciyo
yi”.
Nannauyan numfashi yaja ya fesar tare da jinjina kai,
bawai kwanciyar hankalin da yazo nema ya samu ba, sai dai
rashin zaɓi ko bakin zaren kamawa ya sashi fahimtar tsohon
na masa nuni da shiru ne kawai a zubama sarautar ALLAH ido
dan shine kawai gagara misali.....

_________________

★Kwanaki biyu kenan da dawowar Iffah gida, inda
dawowar tata ta zame mata tamkar wani famin ciwo a jikinta.
Dan a kullum takanyi hawaye sama da sau babu adadi akan
rashin ƴan uwanta guda biyu. Komai ta kalla nasu yakan
dawo mata da jiyansune mai cike da farin ciki da babu
tunanin yankewa. Duk halin da take a ciki Ummu da Babiy na
hankalce da ita, tausayi take basu matuƙa, wani lokacin
Ummu har hawaye takan share itama.
Yau ma tamkar kullum tun bayan dawowarta tai shirin
makaranta ta fice badan hankalin su Ummu ya kwanta ba.
Kawai dai dan ta dagene akan komawar. Sun bartane ko
komawar zaisa ta sake samun nutsuwa da farin cikin da ko'a
fuskarta yanzu baka hangosa. Sanye take cikin skirt golden
yellow da t-shirt fara da suka kasance Uniform ɗinsu, sai
hijjab fari ƙarami shima ta ɗora niƙab ta yanda ƙwayar
idanunta kawai ake iya gani. Bayanta goye da school bag. A
nutse take tafiya kanta a ƙasa tamkar bata son taka ƙasar har
ta iso bakin titi, tsayuwar da batafi ta mintuna uku ba ta
samu abin hawa kamar sauran ɗalibai daketa ɓillowa a
kowane kusurwa. Makarantarsu babbar makarantace mai
ɗauke da ɗalibai masu hazaƙa, domin kuwa an tattarosu ne
daga mabanbanta makarantu aka kawo nan saboda
hazaƙarsu. Kowa bata kulaba ta shige aji tai zamanta, saɓanin
da da kowa yasan Iffah mai tsiwa da surutu, gata ba'a kadata
a himma. Kauɗinta yasa mafi yawan malamai saninta ga
kuma ƙoƙari. Amma tunda ta dawo yanzu ta canjama kowa,
magana ma saita zo har a tashi batai da wani ba. Kamar
yanda malaman sukai mata uziri haka ɗaliban ma sukai mata,
dan kowa yasan tana cikin yanayin da uzirin kawai tafi
buƙata.
Duk wanda ya shigo yakan miƙa mata hannu su gaisa,
itama babu musu take miƙawa tare da amsa sallamar da
sukai mata. A haka har duk ɗaliban ajin suka kammala
shigowa malamin farko ya shigo musu. Da farko ta nutsu
wajen fara fahimtar darasin da yake musu, a hankali kuma
tunaninta ya fara janyewa zuwa ga abinda taketa faman
shiryawa da zuciyarta a kwanakin nan har malamin ya
kammala ya fita babu abinda ta ɗauka. Haka na bayansa suka
cigaba da shigowa basu darasi daban-daban, wani hankalinta
na kai wani harya fita babu abinda zatace ta saurara. Ana
tashi tana a ɗalibai sahun farko da suka fara fitowa, jitai
kawai tana sha'awar yin tattaki da ƙafafunta yau, dan haka
bata tsaya neman abun hawa ba ta miƙo titi da ƙafa ta fara
tafiya kamar wasu tsirarun ɗalibai irinta da gidajensu ke kusa
da makarantar. Tafiya tayi mai nisa sosai batare da nuna
alamun gajiyawa ba, harta kusa isowa roundabout ɗin daya
raba hanyar gidansu da ainahin titin hanyar masarauta daular
ruman. Daga roundabout ɗin ana iya hango ƙaton tambarin
ƙosashen zaki da akayisa da gold na tambarin Masarauta.
Iffah taja wani kakkauran tsaki da ɗauke kanta zuciyarta na
mata zafi. Harta kusa tsallakawa ta hango wata tsohuwa dake
riƙe da wani yaro da Uniform a jikinsa da alama titin take so
su tsallaka amma sunata inda-inda. Karan farko murmushi ya
suɓuce mata ganin yanda yaron ke jan hanun tsohuwar sai
sun tafi kamar zasu tsallaka saita fisgo yaron su dawo baya
tana masifa. Sallama tai musu, tsohuwar ta amsa mata. Ta
gaisheta da girmamawa tare da faɗin, “Ammi kuna so ku
tsalla ne?”.
Amsawa tsohuwar tai da “Eh Ibnati ”.
Iffah ta sake murmusawa daga cikin niƙab ɗinta, kafin takai
hannu ta riƙo na tsohuwar dake riƙe da yaron ita kuma. Suna
gab da kaiwa tsakkiya yaron ya fisge hanunsa ya koma baya
da gudu yana faɗin yabar abunsa a baya. Tsohuwar zata fisge
itama tana masifa da kiran yaron ya dawo Iffah ta riƙeta gam
suka karasa tsallakawa. “Ammi yi haƙuri barsa naje zan sake
tsallako miki da shi. Rufe bakin Iffah yay dai-dai da taka wani
bahagon birkin daya bada sautin ƙuuuuuu!!!. Sai sautin fitar
ƙara mai razanarwa ta biyo bayansa.
Wani irin zabura Iffah tai na juyowa dan ƙarar har
tsakkiyar kanta ta jita. Ai batama san sanda ta yaye niƙab ɗin
fuskarta ba da waro manyan ƙyawawan idanunta waje gaba
ɗaya ba tana mai ambaton sunan ALLAH ganin yaron nan
tsaye cak a tsakkiyar titi hancin wata mota gab da shi allamar
kaɗan ya hana ayi ɗanyen aiki. Kusan a tare suka isa kansa ita
da tsohuwar data fashe da kuka da ƙwala kiran sunan yaron a
matuƙar firgice.
Iffah da jikinta ke ɓari ta riƙo yaron jikinta tana
duddubashi da sauke ajiyar zuciya a jajjere, ganin babu ko
ƙwarzane a jikin nasa. Saurin sakin yaron tai ga tsohuwar
tasha gaban motar ranta a ɓace ganin mai motar ko fitowa
baiyiba ya ɗan leƙone kawai, ganin baima yaron komaiba ya
maida kansa yanama ƙoƙarin barin wajen. A fusace ta buɗe
murfin, ba saurayin daya kasance drivern motar ba hatta
wanda ke gefensa hankalinsa akan lap-top dake saman
cinyarsa sai da ya ɗago suka zuba mata idanu. Gaba

Please Login or Register in order to submit comment