Reading KALBIM BOOK 2 BY MAMUHGEE Chapter 35 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tinanin da jibon keyi shi yakeyi amma Kuma yasani a ransa a bayyane zaadens bazasu taba cutatar da yayansu ba Tinda gashinan sun kula musu dasu tamkar nasu Wanda Hakan ne ma yanzu ya saka suke kokarin auren Fatman Dan Hana a tafi da ita a mata auren kauye da Wanda bataso.

Kawu isiya Kuwa ko magana da tinanin komai baya iyayi sai kallan Nicky da Garba yana sake tsiyayo hawayen ina zai saka ransa da jika bature, Garba ya gama da rayuwansa.

Kai tsaye modibbo ya Kuwa yanke sadakin yana kallan Maheer Wanda Dad ya kalla Dan haka ya taso a hankali ya Kalli modibbon ya bude Baki yayi godiya ya Kalli su kawun suma yayi musu godiya yana koma gefe kansa na sarawa.

Ammar gurin Maheer din ya koma Shima kansa na sarawa sbd yana Jin damuwan da Dan uwansa yake ciki.

Kaman daga sama suka tsinci muryan AZIZ data sakasu duka sake dawo da kallansu da hankalinsa gabaki daya akansa ba shakka ko kwana bare lankwasa kowane zance yace

"Zan karbi muhammd a yanda yake sbd inganta rayuwarsa dan tsayuwa da kansa ya kula da 'dansa Idan an Haifa da matarsa wadda tana haihuwa zaa daura musu aure,

Muhammd zaiyi karatu ya Gina kansa da kansa ban yadda kowa tsaya Masa ba sbd dole yasan nauyin daya dorawa kansa daga shi har itama dole zata auri Muhammad din Tinda ta iya Daukan cikinsa zata iya zaman aure dashi Dan haka Muhammad zai dawo karkashin Sayd.......

Da sauri dukkaninsu suka kallesa kawu isiya a rikice yace

"Bayan wannan barnar Kuma da girmanka Garba zaa karbeka riqo??

Modibbo ma cewa yayi

"Kai baka bamu macen ba munyi renan cikin zaaka ce a baka zabgegen namiji yaje ranan cikin??
To wlh akan wannan muna Nan sai an haife cikin"

Dad ma da Dan mamaki da kame fuska yace

"Inganta rayuwar Muhammad ko da babu wannan nauyin daya hau kansa ko da akwai duka akan zaadens ya rataya sbd shi namu ne Kuma sunan zaadens yake amfani dashi a yanzu Dan haka babu buqatan zamowa karkashin wani zamu dauki nauyinta Dana babyn tin daga yanzu har lokacin da zata haihu"

AZIZ da daman Hakan yakeson ji daga bakinsu Kuma yasan yana Sanya zasu banzatar da Nicky ne Dan haka sbd ya sake sakasu a zancen sosai yace

"Bayan ta haihu zan dauki nauyin komai na aurensu tin daga gidan da zasu zauna a duk kasar da sukeson har.......

Maheer ne dayake cikin nasa juyayin ya katse AZIZ din da hanasa qarasawa yace

"Wannan ma duka nauyin mu ne zamu dauka tin daga yanzu har daurin auren da duk abinda Aysha da babyn zasu buqata zamu dauki nauyin inganta rayuwarsu gabaki daya sbd babynta Zaaden ne"

Ajiyan xuciya AZIZ LIMBA ya sauke yana miqewa tsaye fuskansa a sake yana sake tsananin kamewansa ya Kalli Dad da Maheer dasu modibbo dake zare idanuwa jajir suna jiran ta baci Dan suma a Shirye suke da zuwa kauye su kawo dukkanin dukiyar shanunsu Dan tsira da martabar iyalinsu zasu bada komai da dukiya me yawa a basu Nicky su reneta da cikinta akan su bada Garba ya tafi LIMBAs renan ciki sbd kawai AZIZ LIMBA din yafi zaadens arziki da power.

Kallan Nicky da idanuwanta sukai jajir suka kumbura har fuskanta yayi Mama ta tayar da ita ya tsayar da ita gefensa yana kallanta cikeda kulawa yace

"Babynki ya samu identity dinsa tin kafin yazo duniya,
Kina dauke da baby Zad ne Dan haka kuka ya qare tubarwa Allah zakiyi ta yi yanzu kina neman gafarar laifin da kuka aikata har Allah ya saukeki lfy"

Ajiyan xuciya ta sauke tana dagowa ta kallesa sosai da idanuwanta kafin ta bude Baki cikin tsananin sanyi tace

"Thank you LIMBA"

Murmushi me Kyau ya sakar mata yana sake kwantar mata da hankali da idanuwansa batareda yace komaiba.

Har a ranta batasan tayaya zata auri Garba ba amma sbd tanason bawa bin umarnin na gaba da ita dama ko zataga sauyi da amfanin Hakan ga rayuwanta ya sakata kasa cewa komai akan maganar auren sbd ta jira haihuwanta ta gani ko zata iya idan Kuma taga bazata iyaba zata sanar da kowa ta bawa kowa hakuri ta tafiyanta da babynta tinda dai ubansa ya yadda dashi hakama iyayensa da familynsa sun yadda da babyn Dan haka ko a Hakan ita alhmdllh Allah ya mata rahama.

Sai a lokacin bayan komai ya natsa Ummah ta samu daman saka baki tana sake bawa kowa hakuri a lamarin tareda nusar da kowa ba abin damuwa bane tinda Allah ya kawo lamarin cikin bazata da tashin hankali Kuma gashi an nema mafita a cikin sauki da rufin asiri batareda kowa ya sani ba.

Mama Kuwa ganin yanda hankalin su modibbo ya tashi akan fatma da irin abinda suke gudu ya sake biyowa baya a cikin zuria ya saka itama nata hankalin taji ya Dan tashi sosai ya Kuma karkata akan nata ahalin da Bata fata amma kaddarar Bata wuce ta fada wa wani ba a gidan gashi yanzu tana ji tana gani AZIZ ya riga ya gama karban Nicky kwata kwata a matsayin kanwarsa Dan haka dole dai itama itace uwar Nicky din kenan gashi zata fara da tarbon jika na biyu bayan Falaq da babu aure sbd cikin Nicky yana gaban na Jannah.

Kai tsaya taji hankalinta yasake tashi Dan haka ta matsu su isa gida ta yanke nata hukuncin a nata Yayan.

Babu sauran gurin sake zama ko wata firar sbd babu Wanda ransa yake a cikin dadi kowa da nauyin kirji yake numfasawa Dan haka sallama LIMBAs sukaiwa Zaadens din suka fara kokarin tafiya.

Mama ce Kai tsaye ta Kalli Jannah tace

"Jannah mu tafi ai gobe zaki dawo daurin auren tinda auren aminiyarki ne da Kuma yayanki"

Kallan Mama Jannah dake rungume da Fatma tana tayata hawaye tayi tanajin gabanta na faduwa.

Sake magana Maman tayi Wanda ya saka Jannah kallan Dad Wanda ya hade fuska sosai ya saci kallan Ummah Shima wadda tama qi kallansa sbd kada ma wani ya gano ita yake Satan kalla.

Cikin sanyi Jannah ta bude Baki tace

"Mama Dan Allah a barni anan din"

Kallanta Mama tayi AZIZ dake gap da isa kofa a cikin kunnuwansa zancen ya sauka ya Dan lumshe idanuwansa tareda juyowa ya Kalli Mama a natsensa ba damuwan komai yace

"Mama mu tafi"

Mama kallan Ummah tayi tace

"Kinji yarki tace gidansu take so bari mu barta kafin a kwana biyu a gama hidimar bikin"

Murmushin karfin hali ummah ta sake tana cewa

"Aikuwa mun gode da Hakan ana gama hidimar inshallah kawota ma zaayi har gida"

Murmushi Mama tayi tana juyawa tabi baya AZIZ Wanda ya fice tini.

Suna ficewa Jannah taji jikinta yayi sanyi tana Jin kaman ta samesa ta duba idan ba fushi zai sake yi ba.

Ummah juyawa tayi tabar palon tana yiwa kowa Saida safe ta tafi da fatma da rarrashinta akan auren da gobe zai hau Kanta.

Kowama watsewa yayi ya nufi dakinsa Banda Garba Wanda sai da kowa yabarsa a palon kansa na qasa har lokacin idanuwansa sunyi jajir sbd Kukan da yayi Kuma har lokacin ma Jin radadin komai yakeyi yana tubarwa Allah jiki a mace.

Ammar ne ya dawo ya kamasa zuwa dakinsa suka zauna ya fara basa qwarin gwiwa yana sake Masa nasihar kaddara ce da jarabawan Allah ya bayyana laifin da sukai a boye sbd ya zama izina ga wainda suke tareda su da Kuma Allah ya riga ya qaddari akwai Rabon haihuwan a tsakaninsu Dan haka rungumar nauyin daya hau kansa da zuciya daya da Kuma kauna tinda dai jininsa Kuma Ayshan ma ta saduda shine mafita da abinda ya kamacesa.

Maganganun Ammar sun sanyaya zuciyar Muhammad din sun Kuma sake bude idanuwansa akan babu abinda yanda ya iya bayan rungumar Ayshan da babynsa tinda dai har Allah ya sake taimakonsa iyayensa na nan akai Komai baida fargaban yanda zai fuskancesu a gaban da Dan gaban fatiha tindai da su akai Komai Dan haka yaji nauyin kirjinsa da damuwansa suna ragewa yana Jin kaman anzare Masa ciwon dayake kirjinsa na tin ranar da sukai abin shi da Ayshan yanzu tubarwa Allah kawai zasuci gaba da nema.
#MAMUH
07019691719


*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 78

Ummah har daki takai Fatma ta zaunar da ita ta fara rarrashinta tana nuna mata ba abin kuka bane sbd Maheer dai mijin da kowace mace zataso aurensa ne sbd yanada abubuwan so hakama rayuwarta zata inganta zatai karatu ta samu kwanciyan hankali da nutsuwa auren gida batareda taje koina ba a ciki wainda ta saba rayuwa a cikinsu tasan halaye da kyakkyawan maamalan datake tsakanin ahalin Dan haka ta dena kuka ta sakawa ranta Maheer shine mafi alkhairin da aketa jira ana fatan samu.

Jannah datake a sanyaye kasa cewa komai tayi sai sauraron Umman takeyi rabin hankalinta Kuma yana kan AZIZ dinta da batasan Wane halin suke cikiba ita dashi.

Ummah ma Bata nuna damuwan komaiba ta sake hadasu su biyun tai musu nasiha tana gamawa ta miqe ta fice tana komawa dakinta ta shige ta rufe.

Jannah ma sbd rashin dadin zuciya da son sake cirewa fatma fargaban auren da damuwa a dakin ta kwana tareda Fatma wadda Sam babu bacci a idanuwanta sallar ishai sukai suka kwanta Shiru ba me dogon motsi.


***LIMBAs Kuwa suna isa gida AZIZ ya sake maimaita maganar auren Aysha da Muhammad tareda kulawa da babynta batareda tina ta hanyar da aka samesa ba ya Kuma sake kwantar wa da Nicky hankali sbd ta sake da wannan ya gama magana kowa ya shige Nicky na Jin inama tin farko a matsayin Yayan ta dauki AZIZ LIMBA da yanzu Bata zo wannan matsayin na kaddarar datake ciki ba.

Mama Kuwa tana shigewa dakin bayan ta gama komai ta zauna bakin gado wayarta ta dauka ta bugawa baba Al'hassan waya sukai magana sosai ta sanar dashi duka abinda yake faruwa Dan haka take Shima yaji hankalinsa ya Dan tashi da lamarin Dan haka yace Shima yana Nan tafe su toshe hanyar faruwan ire Iren wainnan kaddarorin.

Wayan dashi ya saka zuciyar Maman samun sukuni Dan haka ta samu nutsuwa harma tayi bacci me nutsuwan tana fatar itama azo ayi me yiyuwa a tsakanin Sayd da Fiddausi kowama ya fidda abokin rayuwa suyi auren zaman ya isa hakanan ba aure.


Washe gari na wayewa Zaadens suka tashi da hidimar daurin auren da suke dashi a yau din Dan haka tin asuba Ammar da Saleem suke wayoyin hidimar sai Kuma gayyatar mutanensu na kusa masu mahimmanci wainda zasu samu daman halarta,

Muhammad duk da yana cikin wani halin Shima hakanan ya daure yashiga hidimar sbd auren kanwarsa ne da Dan uwansa Dan haka shine ma ya fita zuwa karbo kayan da Maheer din zaiyi amfani dasu wainda tin cikin dare Ammar ya zabesu.

Su modibbo sun kasa fitowa daga damuwansu kwata kwata Saida Dad ya sake zaunawa dasu shi da Ammar suka kwantar musu d hankali tareda rufe zancen maganar cikin Aysha da Garba akan babu me ji har acan kauye kada kowa yaji a bari ta haihu a daura musu auren kawai batareda kowa yasan ya sukai suka samu 'yayansu ba Dan haka suyi hkr su dauki kaddara tinda Allah ya kawo lamarin da sauri yaran zasu auri juna Kuma basa inda ake rayuwan saka Ido ko wani abin makamancin Hakan itama Fatma gashinan zaa yi Mata auren cikin amincin Allah da yardarsa.

Da wannan su modibbon suka samu sake zuciyoyinsu sbd daurin auren hakama Garba sun sauko Masa daga wutar da suka dauke Masa Dan ko gaisuwansa babu Wanda ya amsa a cikinsu

Maheer baida zabin daya wuce karban komai duk da Sam fatma dashi din baiga ta inda zasu fara bama amma kasancewan ko bai karba aurenbama baida lokaci ko ranar sake wani auren Dan haka ya barwa Allah zabi akan auren.

Ummah tinda ta tashi itama take wayoyi da mutanen da Mama ta hadata dasu da zasu Taho su gyara mata Fatman Dan haka itama busy take
Jannah Kuwa dole ta ajiye damuwanta gefe ta fara nuna farin cikinta da murnan auren Dan haka Bata gurin Fatma Bata gurin Maheer din Wanda nasa lamarin yasa yama manta Dana Jannah din da Bata kwana gida ba yanzu ta kansa yakeyi ta inda zai fara.

Kamar wasa sai gashi qaramar hidimar da basu shiryawa ba ta zama babba sbd yanda kowa yaketa hidimar auren daya kama ba shiri.

Koda aka tafi sallan jumaa su Mama dasu fiddausi da Falaq sun iso gidan harma dasu anty Maryam din alh saad duka sun iso sbd mama data gayyacesu daman suna son zuwa gaida Umman AZIZ LIMBA Dan haka sai gashi gidan ya Tara baqi masu aiki Kuwa aikin lafiyayyan abinci suketa yi na baqin gidan.

Gabaki daya mazan Zaadens din haka suka fara fitowa a Shirye daya bayan daya suna Jan lafiyayyun motocinsu suna ficewa zuwa daurin auren sai Maheer dinne ya fito karshe ya fice tareda Muhammad da shine zai tafi tareda shi cikin wata lafiyayyar farar Mercedes Benz S550 Muhammad ne ke Jan motar suka fice daman su Modibbo tini suka fice tareda Dad a motar Dad din driver ya jasu.

Lafiyayyan ready made lace Mai shegiyar tsada Ummah ta siya mata a acikin kudi masu yawan da aka ware na Shirin Fatman dama matan ZADs din gaba dayansu dan haka ko masu gyaran Kai da fata da fuska duka gida suka taho sukai mata komai Dan haka itama koda baqi suka iso angama shirinta tai Kyau simple ba hayaniya sai Dan glowing takeyi na gyaran da akai mata.

Jannah ma da Ummah duka dasu akai gyaran fuskan da skin din Dan haka kowannensu yayi kyansa yanda daukan ido musamman Jannah da cikin jikinta yake qarawa skin dinta Kyau.

Mama da Ummah suna dakin Ummah din suna maganarsu Maman na sanar da Ummah abinda suka tattauna da Baba Al'hassan itama ummah Naam tayi da shawarar tasu sbd gwara duka yaran a tattara ayi musu aure a huta da fargaban me zaije ya dawo Dan ita data tatace ma da har Falaq sai amata auren tinda uwarta ma ance iyakacinta Sha Biyar akai mata auren.

Mama data San zancen bama me isa gaban AZIZ bane dariya tayi tana cewa

"Ai idan kika anyi auren Falaq a yanzu ai bayan idon AZIZ ne zamuyi sa dan har gobe shiyasa baya Tina ko sunan dangin Mahaifinsa sbd auren da suka tilasta Akaiwa Ummitah da wannan shekarun.


*******Ana gama sallar jumaa aka daura auren MAHEER ZAD da FATMA JIBO ZAD Wanda mutane da yawa suka shaida anata taya murna da barin kudi wa maroqa kawai manyan mutane da manyan motoci ne keta ratsowa wasu na kokarin fita wasu na Pake anata gaggaisawa ai take su modibbo dasu kawun sukaji baqin cikinsu na yayewa suka hau farin cikin gaske anata sake gaisuwa da manyan mutane sosai.

AZIZ LIMBA ma ya halarci daurin auren Wanda ya saka tin ana yan media da maroqa suka ringa Kiransa a matsayin sirikin zaadens Wanda dole Dad ya ringa washe Baki yana farin ciki sbd yawancin manyan mutanen gasken da suka halarta mutanen LIMBAn ne dan haka a idanuwan mutane LIMBAs da Zaadens kusan ahali daya ne sbd sun zama dayan.

Ana gama daurin aure sai kusan yamma suka dawo gida sbd lafiyayyan reception da akai na masu abin duniya securities tako ina daga can AZIZ Kai tsaye gida ya koma shi Kuwa Sayd airport ya wuce yana ajiye AZIZ din gida yaje daukan Baba Al'hassan daya iso ayau din.

Tinda aka dawo daurin auren anata Dan sake taya juna murna su mama sunwa su Dad da modibbo Allah ya Sanya alkhair hakama Modibbo ya kira Fatma sun mata nasiha sosai suka Dora da maganar Garba Shima sukai fadan daya saka jikinsa sake sanyi kafin suka hakura tareda rungumar komai suka Barwa Allah.

Fatma sama ta koma Bata bari sun hadu da Maheer din ba sbd tasan dai Yana gidan tinda kowa ya dawo.

Sai magrib su Mama suka tafi gida gabaki dayansu Banda Falaq data maqalewa Jannah dole suka barta.

Da daddare kowa a gajiye yake Dan haka abincin Daren ma kusan kowa daban yaci sbd wasu a daki aka Kai musu wasu Kuma sun fito dining din koda 9 zuwa 10 na dare tayi kowa ya shige sbd neman hutawa.


Sai washe gari dukkanin suka hade a dining kowa gajiyansa ta sakesa.

Fatman ce dai kaman yanda ta saba sedai wannan Karan tana Jin nauyi yana hawa Kanta yana mata yawa ita ta saka aka shirya dining din yanda ya kamata ta qarasa gyara komai ta koma tayo wanka ta sauko a Shirye ciki riga da skirt na lace me laushi na hayaniya ta sake komawa kitchen ta hado Turkish tea da kusan kowa yana Sha ta nufo dining din lokacin kowa ya iso suna zaune.

Jin tayi jikinta na neman sanyi amma dai a daure ta qaraso tana ajiyewa ta gaida Dad cikeda nutsuwa da girmamawa kaman yanda suka saba.

Amsawa yayi cikeda kulawa yana sake jinta ta zama cikakkiyar yarsa yanzu data zama tasu har abada tinda ta riga ta zama matar Maheer dinsa.

Maheer din dake zaune sanyeda milk tsadaddiyar yadi me laushi daya Masa Kyau ta kalla cikin sanyi da mutuwan jiki tace

"Ina kwana Yaya Maheer"

Dagowa yayi daga wayarsa dayake kokarin ajiyewa ya zuba mata idanuwansa yana kallanta ita Kuma ta sauke kai ahankali tana Dan wasa da farcenta dayasha gyara jiyan yayi fes yana Dan shining.

Bude Baki yayi ya amsa a natse yana dan rage kallansa akanta,

Ammar ta gaida kafin Muhammad tukuna Saleem Wanda ya dago Dan amsawa fararen idanuwansa suka sauka akan Falaq dake tafe tareda Jannah sanye da riga da wandon Bvlgari da babu inda suka kama jikinta sunmata Kyau sosai sbd yarintarta ta fito sosai qaramar silk Louis Vuitton scarf ne a Kanta itama shi ta kalla ganin yanda yake kallanta ta juyar da idanuwanta tana bude Baki ba sauti tace

"Falaq Aziz ta fasa"

Wani mayen murmushi ya sauke yana Dan sauke kansa sbd kada kowa yaga halinda yake ciki ya Dan dago ya sake Kallanta ta sake juyar Masa da ido tana lafewa gefen Jannah.

Kansa yaji yana neman zarewa sbd Jin kaman ya janyota gabansa yayita kallan cute eyes dinta da bakinta me fadan ta fasa din.

Ganin murmushinsa dake sanyaya zuciyarta tin ba yanzu ba ya sakata sake boyayyar murmushi tana zaunawa gefen Jannah bayan ta gaida kowa cikin sanyi da yar shagwaban data taso a cikinta.

Breakfast din suka fara idanuwansa duk motsinta suna Kanta harma ta gaji cikin narkewa tace

"Saleem pls ka dena mana"

Da sauri kowa ya Kalli Saleem din Wanda ya Dan ware idanuwansa akanta yana kasa kallan kowa dake masa kallan mamaki.

Itama da maganar ta fita bakinta ba shiri saurin kallan kowa tayi tana cewa

"Sorry"

Jannah ce ta kalleta qasa qasa tace

"Me ya Miki?

Ruwa ta dauka tanasha fries din bakinta ya wuce tace

"Ze cinye wa daddy ni da ido ne"

Saleem daya ji abinda ta fada rintse idanuwansa yayi yana sake tausayawa kana da yarinyar Falaq da koyaushe yake fama da ita.
#MAMUH
07019691719*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 79

Suna gama breakfast din kowa ya bar dining Fatma Kuma ta koma kitchen Dan rage wani aikin,

Jannah gurin Dad dinta ta tafi tareda brothers dinta suka shige Palonsa suna tattaunawa sbd tafiyan da Maheer zaiyi wani business deal kwanakin gwara ya tafi da fatma kawai wadda tana dawowa zata fara karatunta.

Ummah Kuwa tana dakinta itada Falaq suna fira tana Dan hada kayanta ta dauki waya ta kira sayd Kai tsaye tace yazo ya dauketa zata zo Nan gida.

Acan LIMBAs Kuwa koda Umman ta kira suna tattaunawa ne akan maganar aure da baba Al'hassan ya Tarasu yayi musu gabaki dayansu hadda AZIZ daya kamata ace zuwa yanzu yana guri daya da iyalinsa bai kamata aceba sunada aure amma tana gidan iyayenta a zaune.

Jin Ummah na tafe ya saka baba Al'hassan din taqaitawa sbd idan taxo a sake zaman na ita sbd hankalinsa ya tashi kawai da wannan lamura tinda koshi AZIZ din me auren kwatsam kowa haka yaji cikin babu wani tarewa babu wani zance babuma Wanda yasan da sauran ran aurensa Dan haka Shima ai duk abin mamaki da fargaban ne Dan haka ya kame ya bada umarninsa me karfi na karshe akan kowa ya gabatarda abokin rayuwa ayi musu aure.

Sayd daya rasa ta inda zai fara bayani Shiru yayi har aka gama tukuna ya fice zuwa dauko Umman,

Itama fiddausi Shirun tayi tana kasa dagowa ta kalli baban Dan batada abin fada bare iya fadan waye suke tare dashi hakama itama tinda cikin Nicky ya bayyana na Muhammad ne take cikin tsoro da tsananin kame Kanta daga zuwa dakin Sayd tin suna Greece sbd Bata daukesa komaiba kaman yanda Shima be dauka komai dinba sbd turai data ratsasu daidai gwargwado.

Yanzu Sam bata zuwa ta dena zuwa sbd kaucewa kaddarar shedan Dan kila su Kam AZIZ Batama San hukuncin dazai musu ba.

Sayd na fita fiddausin ma ta miqe ta fita ta koma dakinta tana tinanin kada ace auren hadi zaa musu daban daban da wasu idan basu fada halinda suke ciki ba.

Ko da Sayd ya iso Falaq na hangosa ta window din saman ta sauko da sauri suka hade palon qasa daidai yana shigowa da sauri ta kama hannunsa tana cewa

"P badai daukana kazo ba?
Ni tareda Jan zan koma fa,
I love staying here..." ta qarasa fada tana kallan Saleem daya qaraso fuskanta da sanyayyan murmushi tana sake lafewa gefen papan nata.

Wani mayen Kallo Saleem din yayi mata yana jin tako ina yarinyar tai Masa illar da baya iya control na idanuwansa da xuciyansa idan tana guri.

Hannu ya miqawa sayd suna gaisawa cikeda sakewan datake tsakaninsu Dan wani irin shakuwa da sabo suna qarasawa ciki har lokacin tana maqale gefen Sayd din tana murmushinta.

Shakuwa ce da kulawan daya ringa bata a lokacin jinyarta da Kuma sacrifice dayayi akanta na Bata zuciyarsa wadda baa karba ba Kuma ya dage ya nace ya haukace Saida ya samo mata wadda take kirjinta ya saka soyayya shiga tsakaninsu wadda da farko dukkaninsu sun dauka shaquwa ce kawai da kulawan dayake mata me tsanani kafin daga baya daya fara zama busy suka fahimci suna cikin zuciyar juna,

Yayi kokari sosai gurin danne duk abinda yake ji a Kanta sbd taxarar shekarunsu me yawa da Kuma ganin tayi qanqanta amma Kuma shagwabanta da rashin wayonta ya saka zuciyarsa ta qarasa macewa akanta a hankali ahankali dole suka yadda da soyayyar da sukewa juna sedai ya sani zaman jiranta ne zaiyi har lokacinda zata gama duka karatunta.

A nata bangaren batasan komaiba bayan cewa Saleem Zad nata ne ita kadai,baida iKon kula kowace mace me shakaru da mara shekarun ita kadai take dashi Wanda Hakan ya saka sam Baya iya muamala da mata ko a gurin aikinsa irin sosai sbd kaucewa fitinarta da rigimarta wadda idan ta tashi Bata tina lokacinta baiyiba na irin wannan rigima take Masa sosai,

Daddynta da Sayd sunsan akwai shakuwa da kauna tsakaninsu sosai amma basusan da soyayyar data gigita musu yarinya ba bare kudirinta na batason dogon karatu saita fara auren Saleem Zad ya zama nata kafin ta qarasa karatun daga baya.

Suna qarasowa tsakiyan palon suna zaunawa Ammar ma yana fitowa a Shirye zai fita wani gurin Dan haka hannu ya fara bawa sayd suka gaisa a Mutunce haryana tambayar Yaya jikin Aysha tukuna ya fice daga Palon yana daga wayarsa da ake kira.

Ammar na ficewa fatma da Jannah suka sauko suna gaisawa da Sayd din suna kokarin zama masu aiki suka sauko da akwatinan Ummah suna ficewa dasu harabar gidan.

Gabaki dayansu miqewa sukai suna kallan kayan kafin Ummah dake saukowa hankalinta kwance fuskanta a sake tana cewa

"Aa Falaq Baki shirya bane?
Bafa zama Sayd din zaiyiba tashi ki dauko kayanki muje"

Falaq cikeda mamaki tana kasa cewa komai ta miqe tana nufar sama.

Jannah Umman ta kalla itada Fatma da Saleem da sauri tace

"Ummah tafiya zakiyi ne?
Ina zaki bansan zakiyi tafiya ba"

Saleem ma kallanta yayi yace

"Ummah lafiya dai ko?

Fatma cikowa kawai idanuwanta sukai batason ummah tayi tafiya a yanzu datake buqatanta.

Murmushi umman tayi tana kallansu tace

"Tafiya zanyi amma bama nisa zanyi daku ba gida kawai zan koma"

Tana fadar Hakan ta Kalli Sayd dayake kallanta da mamaki tace

"Muje na shirya"

Miqewa yai yana yin gaba tabi bayansa.

Dad ne ya fito daidai lokacin yaga Umman na ficewa ya kallesu ya bi bayan Umman.

A kofa ya cimmata yana saurin riqo hannunta yana dawo da ita baya kadan.

Ganin hakan kowa yabar palon
Jannah data fahimci kaman tafiyarta ne Umman zatai take hawaye suka ciko idanuwanta tafara gangarowa dasu tana son magana bama tasan me zata fada ba.

Dad dayaji zufa na kokarin keto Masa kallan Umman yayi yana sake riqe hannunta cikin nasa yace

"Fatima ina zaki tafi da kaya haka?
Meya faru Kuma?
Ba

Please Login or Register in order to submit comment