Reading KALBIM BOOK 2 BY MAMUHGEE Chapter 21 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

da zata dauka akansu zasu karba.

Maheer ma qasa ya zube a gaban Umman dake kuka sosai har lokacin tana sake qanqame 'danta.

Falaq da duk hankalinta ya tashi da ganin wannan masifun da jin asalin yanda mahaifiyarta ta rasu jikinta rawa ya dauka na tsananin tsoro da rikicewa.

Sayd ne ya iso gurinta da sauri Yana rungumeta jikinsa Yana qanqameta sbd a Karan farko da suma shida ita suka samu Kansu da tsananin kadaicin da junansu kawai suke dashi.

Fiddausi ma kuka takeyi sosai daga palo hakama fatma sbd duk me Imani yaji yanda Ummitah ta rasu daga bakin Wanda sukai aikin sai ya shiga sabon tashin hankali da kuka.

Saida Umma takai idanuwanta basa gani kafin ta dago ta kalli Ammar dasu Dad da kuka sukeyi da idanuwansu me karfi da tsananin baqin ciki ta share hawayen da suka gangaro mata ahankali ta daga hannunta dake rawa sosai ta dafa Ammar wanda ayau jin yake mutuwa yake tsananin so sbd ya huta kawai.

Dagowa yayi ta sake miqa masa hannu Wanda yayi saurin kamawa hannuwansa da dukkanin jikinsa na rawa yanason magana Yama kasa ya kifa Kansa a kafafunta Yana fasa sabon kukan samun sassaucin da bai taba tsammani ba daga rayuwarsa.

AZIZ ta kama da hannunta daya ta bude bakinta cikin muryanta data shaqe sbd kuka tace

"Dukkanin abinda sukai tsakaninsu ne da ubangijinsu na yafe sbd halaccin kaunar dake tsakanina dasu Wadda ta ginu batareda hankali na ba suma ta ginar musu batareda Sanin ni wacece ba sukai sbd Allah da bawa rayuwata kariya"

Wani nauyi me girman gaske dayake danne da kirjin AZIZ ne yaji Yana saukar masa ya zubawa Umman ido Yana ayyanawa a ransa duk duniya babu uwa mahaifiya kaman tasa.

Numfashi ya sauke me sanyi ahankali tareda lumshe idanuwansa ya bude Yana juyawa ya kalli Falaq wadda take a rude ya miqa mata hannunsa ta kama da sauri ya juya ya fice da ita Yana rungumota jikinsa sbd ya sake samun nutsuwan zuciya data ruhi dayake fatan daga yanzu rayuwarsa ta koma daidai kaman kowa.

Sayd ne yabi bayansa shima jiki a mace fiddausi ma miqewa tayi tabi bayansu suka bar bangaren gabaki daya.

Mama da ta koma dakinta ta zube qasa tana wani irin kukan da baida magani jin tayi gabaki daya ta tsani rayuwar da duk wanda yake cikinta,

Jin takeyi inama zata iya dawo da baya ta goge dukkanin wani tarihin dayake tsakani Zaadens da AZIZ me kyau da mara kyau sbd su koma rayuwarsu wadda daga ita sai AZIZ dasu Sayd inda take uwa kuma mahaifiyarsa ita kadai,..inda ita kadai duniya ta Sani a mahaifiyarsa Wadda ta haifesa wadda take iko dashi Wadda bai hada da komaiba hakama maganarta batada ta biyu a gurinsa,

Shin yanzu menene matsayin datake dashi a rayuwarsa da duniyarsa?

Waye duniya zata kira da sunan mahaifiyarsa ita ko Fatima?

Menene matsayin da zata taka a rayuwarsa da familyn LIMBAs gabaki daya?

Dafe kirjinta tayi sbd tsananin suyar dayake mata tana jin kaman ta cinnawa kanta da gidan wuta gabaki daya su mutu lokaci daya kowa ya rasa kowa ya huta.

Zaadens aka bari da Umma Wadda ta kasa dagowa ta kalli Dad kaman yanda shima ya kasa dagowa ya kalleta tsananin sonta,tausayi da kunyarta yake.

Fatma gurin Jannah dake baccin azaba da gajiya har lokacin ta koma ta zauna tana zubawa Jannah ido sbd tinanin zuciyar dake bugawa a zuciyarta ba tata bace zuciyar dashe ce.

Shiru gidan yayi bayan kowa ya koma dakinsa dan samun dawowa nutsuwa da hankalinsa.

Abincin rana da aka kammala Amina da madam Sisi ne suka jera a dining kuma suka taho Nan palon su Zaadens ma aka jere nasu a dining aka sake gyara koina aka kunna AC dasu kamshi me nutsuwa gidan ya sake daukan shiru da nutsuwa.

Babu wanda ya fito cin abinci sai kusan 3 na rana tukuna suka fito daya bayan daya banda Jannah data kasa fitowa sbd Sabon gashin da Fatma tayi mata bata iya tafiya daidai tsoro takeji na familynta zasu iya ganewa.

A daki Fatma ta kawo mata abincinta fiddausi ma taxo ta kawo mata lafiyayyan pepper turkey da warm milk taci Tasha madaran sosai ta Sha magani.

Kaya ne kaya Guda da Sayd ya taho da motar wani designer boutique aka kawo kayan sakawarsu da suka kone aka jere mata a wardrobe hakama a dakunan mazan suma duk wata suturar buqata da abin amfani angama jere musu shi duk da sun gama yanke shawarar tafiya idan komai ya dan sake lafawa sbd bazasu cigaba da zama a gidan ba ba dalilin zamansu ko daya gwara su tafi.

Doguwar riga mara nauyi har qasa sedai qaramin hannu ne da ita na vest me shegiyar tsada amma zaka dauka abar banza ce ta saka da taimakon Fatma bayan ta gama cin abinci ta miqe cikin rashin kuzari ta zira slippers din Versace din da Fiddausi ta ajiye mata gabanta ta nufi kofa da mayafin original jersey akanta data rife jikinta dashi ta nufi dakin Ummah fiddausi na tareda ita.

Suna kama hanyar dakin fiddausi tace

"Anmaida Ummah sama tana can"

Kallan fiddausi da idanuwanta masu nauyi tayi da har lokacin basu koma daidai ba tace

"Umman??

Yes muje can din"

Palon daze kaisu saman suka nufa suka hau ahankali cikin sanyi dan bata iya motsawa sosai da karfi.

Suna isa palon saman babu kowa duka suna dakinsu.

Dakin fiddausi da baida babancin komai Dana Falaq da Nicky Nan aka dawo da Umman bayan an sauya beddings sababbi masu laushi da tsada komai na fiddausi ta kwashe daga dakin ta koma dakin Falaq.

Suna isa fiddausi tayi knocking tareda bude kofar da sallama ta bawa Jannah guri ta wuce ahankali tana kafe idonta akan Umman dake kan sallaya ta idar da sallah tana addua idanuwanta a kumbure sosai itama alamar kukan data Sha.

Ahankali Jannah ta bude baki tace

"Ummah"

Juyowa Umman tayi tana kallan Jannan ta sauke numfashi me sanyi da ajiyar zuciya tana kokarin sake murmushin karfin halin daya kasa fita ta bude mata hannunta tana cewa

"UmmiJan"

Mantawa tayi da halinda take ciki ta isa da saurin gaske ta rungume Umman cikin tsananin farin ciki tana cewa

"Ummahna"

Farin cikin datake ciki kasa boyuwa yayi ta sake rungumeta tana murnanta afili.

Cikin nutsuwa da kulawa Umman ta dagota tana kallan fuskanta tace

"Bakida lafiya ne?
Meya sameki?

Shigowan AZIZ dakin qamshin na gauraye iskan dakin gabaki daya a natse sanyeda black blue Christian Dior wears da suka fiddo haskensa da kwanciyar hankalinsa sosai ya saka Umman dagowa ta kallesa cikeda kauna me sanyi tana jin babu kowane irin qunci da baqin ciki bare riqewa a zuciyarta sbd Allah ya raya mata AZIZ tagansa da idanuwanta ta hadu da abinta batareda tabar duniya ba,

Daman shi ta Sani shi ta Shaqu dashi,shine Danta kuma ubanta da guardian dinta a baya dan haka tana godewa Allah daya raya mata shi harya zama haka batareda qunci da tsanani sun rabata dashiba hr abada.

Jannah datasan shine sbd qamshinsa bata dago ba hakama bata juya ba Sedai numfashin data sauke ahankali jikinta na mutuwa sbd jin idanuwansa akanta.

Ummah dawo da kallanta kan Jannah din tayi tana sake cewa

"Meya same ki ne?
Menene ya dameki?

Zaunawa yayi ahankali Yana kallan Jannah din ya bude baki zai bawa Umma amsa Jannah tayi saurin bude baki tace

"Ummah zazzabi ne kawai Se ciwon baya kila sbd yawon danake ta yi ne jiyan"

Zuba mata ido Umma tayi ganin ta kasa dagowa ta kalleta.

Maida kallanta tayi kan AZIZ Wanda idanuwansa suke akan Jannah din yana mata kallo a natse sbd ta sauya duniyarsa gabaki daya.

"To kinsha magani kuwa?

Gyada Kai Jannah tayi tana dan kwantawa jikin Umman ahankali kafin ta dago ta kallesa da idanuwanta da suke a laushi har lokacin batada wani kuzari.

Kallan datai masa ya sakasa jin gashin jikinsa ya tashi ya zuba mata mayun idanuwansa yace

"Nan da awa daya Dr zata sake zuwa ta dubaki"

Bata basa amsaba ta fara magana da Umma ahankali tana fada mata ita batason ganin likitan.

Lallabata Umman tayi ta amince kafin ta miqe ta fice daga dakin dan basu guri suyi maganar dataga alaman zasuyi.

Tana fita suka fara magana me zurfi ta tsakanin uwa da da a natse sbd jin yanda kowannensu yayi rayuwa bayan rabuwa da juna.

Bai fito dakin Ummansa ba sai magrib Yana fitowa ya wuce masallaci tareda Sayd Wanda acan suka hade gabaki dayansu mazan gidan.

Tsakaninsa da Zaadens babu Wanda ya cewa kowa komai sbd babu Wanda yasan abinda zai fara cewa Amma dai sunsan suna kan burinsu da alkawarinsu na aurawa Ammar Jannah koda kuwa kowa ya aje makaman yaqinsa to wannan dai shi alkawarine da bazaa daga ba kuma ma da gaggawa yanzu sukeson yin hakan.

Da daddare Jannah ta daure ta fito cikin familynta suka ci abinci tare kowa yana kokarin bata kulawa sbd suma a yanzu sun samu jin wani nauyi me azaba ya sauka daga kirjinsu dan haka sun samu kwanciyar hankali tinda Umma bata gujesu ba bata kuma mance dasu ba kaman yanda bata manta ita din Matar Dzad ce ba da Aurensa akanta sedai ta sanar masa duk abinda Danta ya yanke akan aurenta shi zatabi dan hakane ma ya maidata sama dauketa daga bangarensu.

Suna gama cin abinci magani aka sake bawa Jannah Tasha suka dan zauna fira sama sama itama ta daure ta zauna har kusan after 9 kafin ta miqe ta koma daki Fatma na bayanta tana dan waskewa da hana a gane tafiyan Jannah din daya sauya.

Suna isa daki ta tube ta nufi toilet daqyar ta sake iya shiga ruwan zafi da kanta ta hawayen azaba tagama tayi wanka ta fito jikinta a tsananin sanyaye.

Zaunawa take kokarin yi fiddausi ta shigo dakin ta sanar da ita dr taxo zata sake dubata.

Faduwa gabanta yayi sbd tsoron kada wani a cikinsu Maheer yaji tinda ba amfanin zuwan likita da dare dubata.

Rigar bacci Fatma ta dauko mata me dan kauri mara tsayi ta bata ta saka ta sako dogon hijab tana cewa suje can batason dr din ta shigo Nan.

Daqyar ta isa dakinsu fiddausi acan Dr din ta dubata falaq bata dakin tana gurin Ummah dataje sake dubowa.

Suna fitowa daga dakin Nicky ta fito daga dakinta idanuwanta da suka fada sosai cikin kwana biyu akan Jannah din tana kallanta zuciyarta na jin kaman ta kamota ta rataye a bene ta mutu,

Jannah da bata lura da ita ba gaba daya tana kokarin sauka aka bude dakin Ummah AZIZ ya fito.

Fiddausi juyawa tayi Dr kuma daman ta sauka,

Idanuwansa akan Jannah din Yana kallanta ya nufota Yana isowa ya kama hannunta ahankali yakai bakinsa yayi kissing ahankali Yana saka hannu goshinta ya taba yaji Yana cewa

"Kina jin sauki??
Ko a sauya wasu doctors din?
Ya kikeji yanzu?
Akwai sauran zazzabi da ciwon haryanxu ne??

Girgiza kai tayi tana dagowa ta kallesa a narke.

Hancinta yakai bakinsa ahankali yaji kissing Yana daukanta cak dan sauka da ita sbd bazata iyaba ya Sani.

Suna barin gurin Nicky ta silale qasa a inda take tana dora hannu akai ta kurma ihun daya rikita gabaki daya gidan kowa ya fara fitowa hankali tashe ita kuma take wani irin Amai yazo mata bayan ihun.
#MAMUH
07019691719*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 47

Sake yunquro mata amai me karfi yayi ta miqe da sauri kafafunta na rawa ta nufi dakinta tana isa toilet ko qarasa isa inda zatai aman bataiba ya kufce mata ta zube gurin a qasa tana fesawa da karfin gaske jikintsa na rawa.

Firdausi da falaq ne suka fito cikin tsoron ihunta kafin Ummah itama sbd fargaban idan ba wani abin ya samu wani ba,

Madam sisi ma dake palon qasa tana wani aikin da gudu tayo saman tana rawar jikin jin ihun uwar dakinta.

AZIZ daya haye nasa saman da jannah a jikinsa ko jin ihun sosai beyiba bare ko yaji a yanzu daya saba da haukar kowa a gidan baya daga hankalinsa.

Madam sisi ce tabi Nicky dakin da sauri tana nufar toilet ta shiga jin irin yunqurin amai datake me karfi da nishi.

Kamata tayi cikin kulawa ta nufi ruwa da ita ta kunna mata tana wanke jikinta da fuskarta kafin ta daga idanuwanta da sukai jajir ta a wahalce tace

"Kiban towel kawai nayi wanka"

Da sauri sisi ta dauko mata ta bata tana juyawa ta fice.

Wanka tayi da ruwan dumi sossi sbd yanda taji zazzaɓi na rufeta sosai ga kuma ciwon rai da baqin cikin dayake lullube da ita.

Tana fitowa kaya masu kauri ta saka tana hayewa gado sbd zazzaɓi.

Firdausi da falaq dake bayanta lafe ne suka shigo dan dubata jin sisi tace ba lafiya ga mama me kulawa da ita babu wanda ya sake ganinta ta kuma dakatar da kowa shiga dakinta dan kuwa ko Ummah har yanzu basu haɗu sun fuskanci juna ba.

Tsabar baqin ciki da ciwo ko motsawa Nicky din bataiba bare tanka gaisuwansu haka suka gaji suka fice.

Amina Madam sisi ta aiko ta gyara toilet din ta wankesa tas ta qara gyara dakin ta kunna qamshi ta kashe mata wuta ta fice tana jan kofar dakin sbd baccin wuya na take daya dauke Nicky din.

Kowa dakinsa ya sake komawa fatma data kasa zaune ta kasa tsaye sbd tsoro da fargaban azo neman jannah da bata nan fitowa tayi tana kokarin waskewa cikin su Maheer ana dan fira sama sama.

Dad ne daya kalli fatma yace

"Ina jannah?
Ko har tayi bacci ne?

Murmushin karfin hali fatma tayi tana kallan kofar dakinsu tace

"Tana gurin Ummah amma yanzu ma nake cewa Bara naje na Kirita mu shige"

Numfashi me dumi ya sauke yana dan shiga nazari kafin yace

"Eh dare yayi kije ki kirata taxo ta kwanta tunda ba lafiya ne da itaba bai kamata tana kaiwa irin wannan lokacin can cikin gidan ba ki fada mata ta kiyaye daga yau."

Gyada Kai Fatma tayi tana cewa

"Insha Allah"

Barin gurin tayi nufi daki ta saka qaramar hijab akan doguwar rigar jikinta ta nufi hnyar da zata kaita can bangaren.

Tana fita Ammar da yayi shiru baice komaiba ajiyan zuciya ya sauke sbd zuciyarsa dake jin kaman ya rasa Jannah ko a wannan Karan sbd gabaki daya Soyayyar datake masa bata auratayyar dasuke fatan hadawa bane,

Soyayyar datai masa a baya kafin zuwan LIMBA rayuwarsu ko a idanuwanta da kuma yanda take muamalantarsa daban take da komai na Jannah din yanzu,

Yana tsananin son Jannah Wanda ya Sani itace jarabawarsa ta biyu Amma a yanzu Yana jin tamkar Soyayyar ta zama tamkar qunci a rayuwarsa da kodai ya hakura kokuma yayi gaggawar mallakanta ya samu cikar buri na biyu bayan na samun Uwar da rayuwarsa ke buqata.

Maheer ma baice komaiba sbd tinda tafiya zasuyi kuma suna tafiya zaa daura auren bama buqatan maimaita zance.

Fatma na isa dakin Ummah Jannah bata can dan haka ta wuce dakin su suma harsun kwanta bata Nan.

Kasa komawa tayi ta sauko ta zauna palon qasan su Falaq din tareda zaunawa ta rafka tagumi tana adduar Allah ya kawo ko Sayd ne ta dan sanar dashi Wadda aka aikota nema.

****Yana isa Sama da ita tin a palonsa ta Zame daga jikinsa tana sauka kan kafafunta ta dan dago batareda ta kalli idanuwansa ba ta bude baki a cikin sanyi tace

"Ba tsayawa zanyi ba su Dad zasu nemeni"

Hannunta ya kama Yana kallan bakinta da yayi maganar,

dumi jikinta yake dashi sosai sbd yanayin lafiyarta Dan haka dumin dayaji a tafin hannunta ya sakasa kai hannunsa a wuyanta ya Masa wata shafa yana gangarawa ahankali har bayan wuyanta dumin na ratsa tafin hannunsa zuwa jikinsa daya karban dumin a cikin sanyi yanajin kaman nutsuwarsa na ninkuwa.

Kashe mata jiki yake sake yi da dumama jikin da yanda yake shafa asalin fatar wuyanta zuwa bayanta Dan haka ahankali ta ta Dan yi baya kadan tana juya Masa baya ta bude baki zatai magana ya rungumeta ta baya ahankali yana bude bakinsa a kan fatar kunnenta cikin Wani irin sanyi da laushin sauti me nutsuwa yace

"Abinda nakeji a xuciyana yanada yawan da kaman xuciyan ma can't take it Jannah zad"

Bata iya cewa komaiba ta Dan fara zame jikinta.

Kasa barinta yai ya sake rungumeta da hannuwansa ta bayan da Kyau yana Dan sake ajiyan zuciya me dumi a fatan gefen fuskanta kafin ya sake taba jikinta yana jin dumin jikin ya yace

"Yaya jikin?
Ya kike ji?
Akwai inda yake da sauran damuwan ciwo ne?
Kinajin fever,pain or anything daya danganci rashin jin daidai?

Girgiza kai tayi tana bude baki tace

"No kawai dai inason komawa na huta ne"

Kasa sakinta yayi tsawon mintina yana shakar qamshinta da karban dumin jikinta cikin nasa a tsayen da suke rungume cikin jikinsa kafin ya sake ta yana kama hannunta yayi kissing ahankali kafin ya dauketa cak ya fito da ita tareda saukowa da ita har qasa ya nufi palonsu da ita tayi saurin zillewa ahankali ta sauka qasa tana dagowa ta Dan kallesa idanuwanta na Dan laushi ta murya mara karfi da hayaniya tace

"Dad or Maheer koma Ammar zasu iya dukana suka ganni a Hakan,
Just go back daga nan ya isa pls"

Yanda tayi maganar fargabanta na bayana ya sakasa zubawa fuskanta ido yana mamakin tsoronta,

Sbd itane yake da bayason sakawa tashin hankali da fadan family dinta ya saka yake biye mata yana mata yanda takeso tareda Bata time datace yayi alkwarin zai Bata harsai ta samu lokacinda ya kamata ta sanar dasu komai da kanta sbd idan ya fada da Kansa ko kawai sukaji daga sama ba qaramin tashin hankali zaayiba Dan bazasu yadda ba dauka zasuyi kawai ya fada ne Dan haka ne yake dannewa Dan yi mata yanda takeso din.

Ganin yanda ya ko motsawa beyiba ya zuba mata ido ne ya sakata kama hannunsa ahankali ta juya dashi tana jansa kaman karamin yaro shikuma yana binta.

Wani qaramin waiting area ne ya rabasu da palon can cikin dama Dan haka anan ta tsaya tareda sakin hannunsa ta kallesa idanuwanta na Dan yin kalan sanyi da laushi tace

"Pls AZIZ LIMBA"

Juyawa tayi zata wuce tabarsa a gurin ya riqo hannunta daya tareda dawowa da ita baya ta fado jikinsa ahankali ta baya ya juyo fuskanta cikin nutsuwa ya Kalli lips dinta ya hadiye wasu mayun yawun da tana Kallo suka wuce maqoshinsa ahankali sbd yanda Adams apple dinsa ya motsa ta moqoshin.

Idanuwanta ta dago cikin slow ta Kalli fuskansa sedai baima bari tace komaiba ya Dora bakinsa akan lips din nata ya lashesu cikin sanyi da nutsuwa ya sake hadiye yawun daya lashi lips din kafin ya zira harshensa me dumi da kamshi ahankali cikin bakinta ya fara tsotsa a natse yana zagaye qugunta da hannuwansa cikin salon kulawa da mannota jikinsa yana lumshe fararen idanuwansa ahankali.

Tsoro da fargaba ce ya fara shigarta sbd tina me zai iya faruwa idan ta bari yaci gaba da kuma tsoron inda suke tsayen Wani zai iya zuwa ya gansu.

Zamewa taso yi ahankali sedai motsawanta ya basa daman manne kirjinsa da nata yana sake lumshe ido yana zuqan bakinta cikin wata irin salon nutsuwa Dan wata irin deep kiss yake Bata.

Rawa kafafunta suka fara yi suna kasa daukanta ta sake a gurin ya qarasa tarota jikinsa gabaki daya yana dagata sama ya Dora kan console dake gurin yana bude kafafunta ya tsaya tsakiyarsu batareda ya sake bakinta ba har lokacin.

Ta qasan rigarta ya sako hannunsa daya yana shafa tin daga kafarta ahankali cikin Wani irin salon daya sakata qanqame kansa tana sauke numfashi me karfi daya kufce mata Wanda ya saka nutsuwarsa sake sauka yabi cinyarta da shafa yana yin sama da hannun har zuwa sama cikinta Wanda yayiwa mararta shafar data sakata yin baya ya samu damar sake sama da hannunsa yana shafa saman lace bra din datake jikinta.

Jin irin yanda komai yake Kara daukan zafi ya sakata Dan zamewa tana ciko idanuwanta da hawaye ta bude baki tace

"AZIZ"

yanda take ambatar sunansa a ko yaushe da Wani irin sanyi da nutsuwa yake sake kashesa amma sanin Batama warke ba kwata kwata ya sakasa rungumeta kawai ya kyaleta sukai mintina ahakan yana samun nutsuwarsa a jikinta kafin ya saukar da ita qasa ya gyara mata rigarta yana sake Rakata har kofar palon kafin ta shige shikuma ya juya.

Tana isa tsakiyar palon Maheer na fitowa yana waya zai kawowa Dad wayar.

Daga dad din har Maheer juyawa sukai suna kallan hanyar data shigo ahankali.

Garba sake zaune tareda Dad miqewa yayi yana kallan hanyar Shima sbd tinanin AZIZ LIMBA ne zai shigo.

Ganin yanda suke kallan bayanta ya saka gabanta Dan faduwa ta dakata tareda juyawa ahankali ta Kalli bayanta taga babu kowa.

Dawo da kallanta tayi kansu tana kasa qarasowa daf dasu ta bude baki tace

"Dad,Wani abu ya faru ne?

Kallanta Dad din yayi kafin yayi magana Maheer yace

"Qamshin AZIZ LIMBA ne yake biyowa bakiji bane ko me?

Ammar daya iso daidai maganar Maheer din Jannah din ya juya yana kalla wadda zuciyarta ke bugawa ta bude baki a cikin nutsuwa tana kokarin riqe nutsuwarta tace

"Banji ba kila kofan Dana bude ne na shigo"

Ammar Wanda kai tsaye qamshin yake shigar Masa hanci daga jikinta kuma yake jiyosa zuba mata idanuwansa yayi gabaki daya yana kalla itama juyowa tayi ta kallesa a sanyaye ta sauke kanta tana nufar daki sbd kada qamshin yaci gaba da tashi a jikinta.
#MAMUH
KUYI HKR YAU ASIBITI NAJE TIN SAFE WLH ACAN WAYANA TA MUTU BA CHARGE.
07019691719*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 48


Tana shiga daki rufo kofar tayi tareda jingina jikin kofar tana sauke ajiyan xuciya tareda rife ido tana jin jikinta na sanyi da damuwan yanda familynta zasuyi idan suka San AZIZ LIMBA haryanzu mijinta ne.

Fatma da har ta kwanta jin shigowan Jannah din ya sakata bude idanuwanta tana tashi zaune sanye da riga da wandon bacci masu santsi ta Kalleta tana cewa

"Su Dad sun ga shigowanki?

Gyada kai Jannah tayi tana kasa magana sbd damuwan dataji duk ta rufeta akan familynta da Bata taba iya boyewa komaiba.

Toilet ta wuce ta Dan yi abinda zatai ta fito tayi Shirin bacci itama kawai ta kwanta gefen Fatman tana Daukan remote ta Dan rage AC sbd zazzabin da har lokacin tana Dan jinsa a jikinta.

Rife idanuwanta tayi tana adduan bacci idanuwanta a rife sbd baccin datake son ya dauketa tinani yabar kanta.

Fatma ma komawa tayi ta kwanta tana shigewa lallausan bargo ta rife rabin jikinta tana rife idanuwanta itama.


Washe gari da safe koda Fatma ta tashi an sake kawo sabbin masu aiki an kawo musu sbd kula da komai nasu Dan haka ko data fito sayd yace ta koma sun dena kowane irin aiki.

Dawowa tayi ta sake komawa baccinta hankali kwance daman Jannah har lokacin Bata farka ba sbd Batama da cikakkiyar lafiyan cewa zatai Wani aiki.

Kusan dukkaninsu babu Wanda ya tashi da wuri sbd anriga anyi replacing nasu da maikata sabbi tini Dan haka ko sun tashi babu abinda sukeyi.

Karfe 10 Jannah ta farka Dan haka toilet ta nufa ta yi brush da toothpaste me tsadan gaske a cikin dukkanin siyayyar da akai mata da familynta.

Wanka tayi ta fito daure da towel ta zauna gaban mirror ta Dan shafa mai kadan da body spray masu sanyi da tsada ta miqe ta saka kaya.

Doguwar riga ta saka mara nauyi sosai purple daidai nan Amina ta kawo mata breakfast dinta dakin Wanda fiddausi ce ta bada umarnin abinda zaayi mata a breakfast din.

Zaunawa tayi taci abincin kadan tana gamawa Dr ta iso dubata.

Fiddausi ce taxo ta sanar mata da zuwan likitan Dan haka ta miqe suka fice can dakinsu fiddausin aka Dubata likitar ta tabbatarda ta samu sauki yanda ya kamata basai ta sake zuwa ba.

Dr na tafiya ta fito tai dakin Ummah.

Tana shiga Umman na zaune tayi Shiru ba komai ba kowa.

Da kulawa ta isa gurinta tana Kwantawa jikinta cikeda kauna da shaquwa tace

"Ummah ina kwana?

Murmushi me sanyi da farin cikin ganinta umman tayi tana cewa

"Lafiya kalau,Yaya jikin naki?
Kinji sauki?
Yaya su Ammar Shima dai ya warware ko?

Nauyin tambayar taji daga bakin umman duk da bawai umman tasan komai bane Dan haka cikin Sanyi ta amsa tana dorawa da cewa

"Ammar duka munyi kewanki ummah"

Murmushi umman ta sake yi tana cewa

"Kewa kuma bayan muna gida daya"

Shigowan falaq ne tana isowa da sauri itama ta kwanta jikin Jannah tana cewa

"Good morning my Jan"

"Morning Falaq Aziz,kin tashi lfy?

Amsawa Falaq tayi tana gaida ummah wadda tinda safe sun gaisa sakewa takeyi.

Fira suka fara saiga fiddausi itama tayi joining suka debewa ummah kewa sosai wadda mama dake dakinta tana jiyo hayaniyar fiddausi da Falaq din suna ambatar umman.

Ajiyan xuciya me zafi da karfi mama ta sake sakewa a karo na babu adadi tin shekaran jiya zuwa yau batareda lokaci yaja ba a cikin kwana hudu zuwa biyar abinda take ta yiwa fada da yaqi da tashin hankali ya faru ya tabbata,

Batareda anje koinaba Abinda take tsananin tsanar ya faru ya faru,

Bayyanar Fatima ga

Please Login or Register in order to submit comment