Reading KALBIM BOOK 2 BY MAMUHGEE Chapter 30 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

taba lafiyan nasa arzikin sedai bai samu Umman ba yayi nasarar samun Jannah din data qi barin ya ganta tinda suka dawo kaman tasan neman zarewa yake rashin sanin halinda take ciki.

Qarasowa yayi har inda take din ya tsaya akanta yana zubawa kyakkyawan fuskanta nasa fararen idanuwan yana kallanta kaman ya dauketa ya tafi duniyar dazai rayu da ita su reni babynsu.

Jin tsayuwan mutum a Kanta ya sakata bude idanuwanta ahankali tana saukesu akan fuskansa tana kallansa a kasalance sbd Dan zazzabi da rashin karfin dayake tattare da ita na Kukan datake yi tin jiya da Kuma damuwan data ciketa me tsananin rashin sanin wane hali da matakin familynta zasu dauka akanta da Kuma damuwan halinda ta saka Ammar Wanda kila qarasa rasa kansa zaiyi duk da ya kasa cewa komai ko kallanta bai sake ba.

Durkusawa yayi ahankali gabanta yana miqa hannunsa na dama ya shafi fuskanta cikin wata irin sanyayyan kulawa da kauna me tsafta.

Rufe idanuwanta ahankali tayi tana budewa akansa wasu hawaye masu dumi suna gangaro mata na tausayin Kanta da babynta da ubansa baima San dashi ba,

Idan su Dad sukace cire mata cikin zaayi batasan tayaya zata iya sake kallan AZIZ dinba duk da bai San dashi ba kaman yanda Kuma batajin zata musawa su Dad din sbd sanyaya zuciyarsu data kuntata,

Wasu zafafan hawayen ne suka sake sauko mata sbd tana kaunar cikinta har cikin ranta tana Kuma tausayin AZIZ da ita Kanta.

Hawayenta AZIZ din ya miqa hannunsa ya shafo yana kalla zuciyarsa na sanyaya da damuwa ya saka hannuwansa biyu ya tada ita Zaune ya dauketa yana komawa kan sofa da ita ya zauna ya zaunar da ita akan cinyarsa ya fara share mata hawayen da tissue daya dauka a gefen sofan dasuka zauna kan qaramin side table.

Hannunsa ta riqe da nata tana kallansa jikinta a sanyaye zuciyarta na ingixata akan ta fada Masa abinda take dauke dashi amma tana shakkar fushin su Dad idan suka San ta fada Masa Dan haka ta zuba Masa ido tana sake tsiyayan hawayen damuwa.
#MAMUH
07019691719*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 67

*_ZUZEAM VENTURES_*
Best kayan Mata
08144015291
*NEW ALERT*
*END OF DISCUSSION PACKAGE*
~25k~ promo 12k
Barka da Sallah promo pack
1. Tabajen kankana da fruit
(Mai saukar da niima nan take ta kara miki dadi na musamman keda oga sai kunyi kukan dadi ranar )
2. ⁠gumbar chakwala dadi
(Hmm yar uwa daga jin wannan kema kinsani basai anbaki labariba wannan hadin na zallar dadi ne da ciko da gaba)
3. Turare kyauta dole
(Wannan turaren na amsar kyauta ne ina masu fama da miji mai mako wanda ba a cin kudinshi Ga shi da abun amma ba a ci to yar uwa matsalarki tazo karshe da izin Allah Sai kinci abunshi ina yan kasuwa duk kina amfani da wannan turaren sai Kinga budi da izinin Allah)
4. Zumar bata gaban kishiya yar asali
( wannan zumar Ga mata wanda kishiya ta shiga gabansu mijinki baki gane kanshi ya fifita yar uwarki akanki baya son mu’a mala dake ko wadda mijinta ke biye biye yar uwa kukanki yazo karshe duk kikayi amfani da ita duk machen da yayi sex da ita zaijita salab kamar dusa don haka aji tsoron Allah banda wanda suke zaune lfy da kishiyoyinsu)
5. End of discussion powder
( wannan garin karshen zance kenan hajiya oga ya taba miki kukan agwagwa ko mussoshi 😁to ranar duk da kika sha wannan hadin garin hajiya sabbatu sai kin rufe mishi baki ihu da kururuwa ba sauki kuma garin wata 7 yake ajiki yana aiki )

Hajiya karki bari wannan promo ya wuceki 25k ne promo saboda sallah 12k kacal

TikTok: Zuzeam.ventures5
Instagram: Zuzeam_ventures
WhatsApp: 08144015291



***********
Fuskansa ya hade da tata yana goga hancinsa da nata yana kokarin rarrashinta ya bude Baki da wata irin sanyi yace

"Pls Jan bana iya ganin wannan hawayen naki"

Maganarta ta Santa kuka me sauti xuwar mata tana fadawa jikinsa gabaki daya tana Jin ita kamarma Rabasu zaayi.

Rungumeta yayi tsam jikinsa yana qanqameta yana Jin kaman ya tsaga jikinsa ya maidata ciki ya rife abarsa.

Kuka takeyi sosai tana fada Masa itace sanadin duka damuwa da quncin danginta..

Dago fuskanta yayi yana sake share mata hawaye yace

"Ba haka bane karki manta su kansu fada sukeyi kece farin ciki Kuma wadda suke alfaharin tsananin son dasuke Miki ne ya riqe ahalin zaadens har babu Wanda ya isa ya raba wannan kaunar,

Aurena da soyayyata akanki bazata taba raba tsakaninki da familynki ba sbd karfin kaunarku a tsakaninku ta wuce nan ni kaina na San Hakan,

Duk bacin Rai da abinda zai faru a tsakaninku bazasu taba tsana ko kyamatarkiba sbd kece zuciyarsu da suke jure komai na rayuwa da suka fuskanta akanta"

Zuba Masa ido tayi sbd Jin maganarsa na ratsata Dan ita Kanta kaunar datake musu ce ta saka take shakkar bayyanarda aurenta da AZIZ din haryanzu Wanda Shima sbd tsananin son dayake mata ne yabi umarnin yanda takeso na boye Hakan ya Bata lokacinda ta buqata isashe tinda dai bawai rabasa tayi da Kanta ba.

Ganin irin kallan datake Masa hawayenta na tsayawa ya sakasa saka tissue ya qarasa share mata hawayen yana kai bakinsa yayi kissing idonta ahankali kafin yayi na hancinta tukuna yayi na bakinta yana sake zagayeta da hannunsa daya.

Kallansa tayi tana kokarin bude bakinta tayi magana ya Dora yatsarsa a akan lips dinta yana girgiza Kai a natse yace

"Kin gaji pls ki huta karki sake wahalan da kanki"

Hannunta takai akan nasa tana janyewa ta ce

"Idanma Ammar ya fada musu meyake faruwa pls kamun alkwarin baza Kai interfering ba"

"No,i can't make a promise da bazan iya cikawa ba"

Kallansa tayi tana ciko idanuwanta da hawayen da tasan zasu iya sakasa yadda zatai magana ya Dora bakinsa a kan nata yayi kissing nata sosai kafin ya saketa yana kallan fuskanta hannuwansa tallafe da fuskanta yace

"Bazan taba iya Miki alkwarin tsayawa nayi Shiru ina kallan ana min wasa da Arzikina na duniya ba"

Hawayen ta sake tsiyayowa yana share mata yana kissing idanuwanta da hancinta yana kokarin hanata wannan hawayen da duk ya damesa.

Kokarin sake kissing lips dinta yakeyi aka bude kofar dakin da suka manta da inda suke kwata kwata.

Saurin janyewa Jannah din tayi jikinta na tsananin rawa ta miqe da mugun sauri daga jikinsa tana komawa bakin gado da gudun gaske har tana bigewa ya miqe tsaye yana kallanta da mamaki yace

"Kibi a hankali fa"

Ummah data shiga mummunan shock da firgita duk rikicewa tayi tana qarasowa tareda yi kaman bataga komaiba sbd ta kasa ma gane me idanuwanta suka ganar mata.

Rawa hannuwanta ke yi ta qaraso tana amsa gaisuwan AZIZ batareda ta iya kallansa ba hakama Jannah din Dan haka kai tsaye toilet ta wuce tana shigewa bayan tayi Masa Saida safe alaman batason fitowa ta samesa a dakin.

Tana shigewa ya qaraso ya durkusa yana duba kafan Jannah din data bige tayi saurin janyewa tana cewa

"Ka tafi kada Ummah ta sake fitowa ta ganka"

Kamo fuskanta yayi bayan ya miqe ya Dan rankwafo yai kissing goshinta yayi mata sai da safe ya fice.

Bai wani jima da fita ba Ummah dake bathroom tana faman sakawa da warwarewa cikin fargaba da tashin hankali ta fito tana qarasowa ta zauna har lokacin ta kasa kallan Jannah wadda ta kwanta ta lafe Shiru kaman tana bacci itama sbd kunya da tata fargaban data rufeta na tsoro da fatan Ummah Bata gansu ba.

Shirin bacci Ummah ta miqe tayi tana Jin kamar zazzabi na neman kamata sbd Bata fatar wani sabon tashin hankali a tsakanin AZIZ dinta da Zaadens da suke ahalinta a yanzu.

Gama komai tayi Tazo ta zauna bakin gado tana kallan Jannah wadda yanda take numfashi da motsi ahankali ya tabbatar mata da idanuwanta biyu ba bacci takeyi ba.

Cikin nutsuwa da sanyi Umman ta bude Baki ta ambaci sunanta tace

"Ummijan tashi magana zanyi dake"

Jannah na Jin Hakan gabanta yayi mugun faduwa tana Jin zufa na kokarin yanko mata amma ta riga tasan Ummah bazata taba fushi me muni da ita ba Dan haka ta juyo ahankali tana tashi zaune daga kwancen ta sauke Kanta qasa tana kasa hada Ido da Umman tayi Shiru.

Umman ma Shiru ya fara yi tana nazarin maganarta kafin ta fuskanci Jannan da Kyau ta bude Baki a cikin nutsuwan da zata fahimceta dakyau tace

"Jannah nice na haifi ABDULAZIZ Dan haka bazan taba goge a cikina ya fitito ba sedai Kuma a yanzu ba nice uwarsa ba ba shine 'dana ba,

A yanzu kece tawa,kece 'yata dan haka ke nakeson ji daga gareki idan har na isa na Kai matsayin uwa a gurin ki Jannah inason sanin meyake faruwa tsakaninki da AZIZ,
Yaya akai kike dauke a ciki a jikinki?
Kuma na waye?
Ni duka banason ma furta wanna maganganun a bakina sbd Daci da nauyi sukemin Dan haka ki sanar Dani komai bana buqatan sake tambaya."

Numfashi me sanyi da mutuwan jiki Jannah ta sake a boye sbd daga karshe dai zata samu rage damuwan ranta Kuma daman batada Wanda zata iya fadawa damuwa da abinda tayin bayan Ummah Dan haka a Sanyaye ta bude Baki tace

"Ummah bai sakeni ba tin farko...

Da sauri umman ta kalleta tana sake shiga rudani tace

"AZIZ din ne be sake ki ba tin acan baya har yanzu da mike magana?

Gyada kai Jannah tayi
Umman tace

"To tin farkon waye ne yace anyi sakin?

"Ummah takarda ya bani bayan munyi maganar rabuwar shiyasa ban bude ba na sanar dasu Dad mun riga mun rabu......

"Da kika fada Hakan baa duba takardar bane daman kokuwa Baki bawa ko dayansu takardar ba?
Innalillahi me nake ji haka ni Fatima
Jannah kinsan me kika aikata Kuwa?

"Ummah wlh tallahi bansaniba nima sai daya fadamun naje na duba naga ba sakin bane Kuma na kasa fada ne sbd ina tsoron su Dad amma wlh ummah nima bansaniba"

"Innalillahi yanzu kenan cikin nasa ne ko me?"

Gyada kai Jannah tayi hawayen kunyar duniya na gangaro mata.

"Kikace nasa ne?
Kenan kallan kitse saman ruwa kuke mana tintini ko??

Sauti kukan Jannah din ya fara ta girgiza Kai tana cewa

"Aa Ummah Dan Allah kuyi hkr wlh sharrin shedan da zuciya ne"

"Wane shedan da zuciya baya ba aljanu ne a kanku ba"
Shi AZIZ din ya biye Miki Shima ya boye aure kenan,
Sai yaushe ne kuke da niyar fada kokuwa se dai idan an haihu mun ganarwa idanuwanmu"

Kuka Jannah ke yi sosai tana rokon Umman tayi hkr karta fadawa su Dad yanzu.

Fada sosai Umman ke mata akan irin kuskuren datai na boyewa familynta sbd ko zasu kama da wuta ya kamata Susan komai da duk baa ma fara yiwa cikin zargin ta ina ya fito ba.

Yanda Jannah din ke kuka tana rokon da Bada hakuri ya saka Umman sassauta fadan nata tana komawa rarrashinta tareda Jin nutsuwa da farin cikin samuwan cikin tinda dai jininta ne batada yanda zatai kota wace hanya yazo ma haka zata so sa ta kaunacesa.

Hakanan ta rarrasheta tana sake mata nasihar kiyaye gaba ta Hanata kukan hadda Bata ruwa Tasha tace ta kwanta tayi baccinta.

Sanyi da sassauci a kirji Jannah tace sbd ta samu rage nauyin kirjinta da samun tattaunawa da ummanta Dan haka Bata jima a tinani da damuwan sauran su Dad na bacci ya dauketa.


Ummah tinani ta kwana na yanda zata sanar dasu Dad cikin fahimta zata bari sai sun dawo hankali ya kwanta tukuna tinda da komai yazo da mafi girman sauki akwai aure Kuma na gida ne.

Washe gari Tinda safe suka tafi asibiti har lokacin Ammar yana Nan a yanda yake na bangaren magana ko wata hayaniya duk ya ajiye ya koma musu sabon mutum.

Sallamo su akai suka dawo gida,

Kowa dakinsa ya nufa yayi wanka yahuta babu Wanda ya sake ganin Dan uwansa sai dare da suka fito gabaki dayansu cin abincin da suke jiran ya hadasu Dan magana.

Karfe goma kowa ya watse Dad ya saka Muhammad Kiran Jannah da fatma Wanda suke boyo a daki sun kasa fitowa.

Kaman munafukai haka suka fito kansu a qasa suka nemi guri suka zauna sai a lokacin Dad ya qarewa Jannah Kallo zuciyarsa na neman fitowa sbd bacin Rai da tsananin fushi yace

"Ki bude Baki yanzu kimun bayanin komai dallah dallah sbd wlh tallahi kikamun qarya zakiga abinda Baki taba gani ba,
Cikin waye a jikinki?
Daga ina ya fito.?

Ammar dake zaune kusa da Dad din lumshe idanuwansa yay ahankali yana ambaton sunan Allah cikin sanyi da nutsuwa.

Maheer jajir idanuwansa sukai yana Jin baima San me zaiyi ba ta ina ma zasu fara da wannan abin kunyar da baqin cikin.

Kuka Jannah ke kokarin farawa Maheer yace

"Kina fara kuka wlh tsinannan dukan da zakisha saiya barar da abinda yake cikinki"

Sunkuyar da Kai tayi tana rufe bakinta da hannuwanta biyu muryanta na rawa tace

"Dan Allah Dad kuyi hkr wlh bansan da cikin ba nima.....

Kanta Maheer yayo Muhammd ya riqesa sbd basason hayaniya sbd kada kowa ya jisu bare asan halinda suke ciki musamman Ummah da ita ce nauyinsu a yanzu basason tasan abinda suke Shirin aikatawa idan ma zarginsu ya tabbata kenan.

Fatma ce ta karbi zancen itama cikin tsananin fargaba da hawaye tace

"Wlh Yaya Maheer akwai aure a tsakaninsu bai saketa ba tin farko can baya."

Cak Maheer din ya tsaya yana kallan Fatma da tsananin mamaki da shakka yace

"Wane auren ne be mutu ba?

Dad daya kasa hakuri a bada amsar Shima cikin tsananin shock yace

"AZIZ dinne bai saketa ba kokuwa wani auren tayi a kauyen bamuda labari??

Murya na rawa Fatma tace

"AZIZ LIMBA dinne baiyi sakin aurensa ba tin farko Kuma shine baban cik.....

Mari Muhammad ya yankawa bakin Fatman yana Jin kaman ya rufeta da dukan gaske yace

"Uban waye yake Baki wannan labarin??

Da sauri jikinta na rawa ta dauko takardar ta kawo ta miqa musu Maheer na karantawa ya zube a kujera zufa na jiqasa tako ina idanuwansa Kafe akan Jannah data Dora su a zancen Banza tsawon shekaru.

Dad na ganin Maheer ya zube ya kasa karantawa muryansa na rawa yace

"Da akwai auren kenan???

Ammar daya kasa motsi bare iya cewa komai bude jajayen idanuwansa da sukai wani irin jajir yayi ya katse tashin hankalin da nasa maganar yace

"Dad gobe nima zan tafi bazan iya cigaba da zama anan ba"
#MAMUH
07019691719

*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 68

*_ZUZEAM VENTURES_*
Best kayan Mata
08144015291
*NEW ALERT*
*END OF DISCUSSION PACKAGE*
~25k~ promo 12k
Barka da Sallah promo pack
1. Tabajen kankana da fruit
  (Mai saukar da niima nan take ta kara miki dadi na musamman keda oga sai kunyi kukan dadi ranar )
2. ⁠gumbar chakwala dadi
(Hmm yar uwa daga jin wannan kema kinsani basai anbaki labariba wannan hadin na zallar dadi ne da ciko da gaba)
3. Turare kyauta dole
  (Wannan turaren na amsar kyauta ne ina masu fama da miji mai mako wanda ba a cin kudinshi Ga shi da abun amma ba a ci to yar uwa matsalarki tazo karshe da izin Allah Sai kinci abunshi ina yan kasuwa duk kina amfani da wannan turaren sai Kinga budi da izinin Allah)
4. Zumar bata gaban kishiya yar asali
( wannan zumar Ga mata wanda kishiya ta shiga gabansu mijinki baki gane kanshi ya fifita yar uwarki akanki baya son mu’a mala dake ko wadda mijinta ke biye biye yar uwa kukanki yazo karshe duk kikayi amfani da ita duk machen da yayi sex da ita zaijita salab kamar dusa don haka aji tsoron Allah banda wanda suke zaune lfy da kishiyoyinsu)
5. End of discussion powder
( wannan garin karshen zance kenan hajiya oga ya taba miki kukan agwagwa ko mussoshi 😁to ranar duk da kika sha wannan hadin garin hajiya sabbatu sai kin rufe mishi  baki ihu da kururuwa ba sauki kuma garin wata 7 yake ajiki yana aiki )

Hajiya karki bari wannan promo ya wuceki 25k ne promo saboda sallah 12k kacal

TikTok: Zuzeam.ventures5
Instagram: Zuzeam_ventures
WhatsApp: 08144015291

********
A rikice suka kallesa a tare Maheer na rintse idanuwansa dake radadi sbd yasan Hakan zata iya faruwa tinda ganin yanayin Ammar din ya sauya ba kaman Ammar dinsu na bayaba.

Dad kuwa kasa dauke idanuwansa yayi daga kan Ammar din yace

"Ka tafi ina?
Kanada gurin tafiyan ne batareda familynka duka ba?

Sunkuyar dakai yayi yana sake tabbatarwa da zuciyarsa abinda rayuwansa ke buqata kenan yace

"Dad bazan iya rayuwan bane anan,
Ina buqatan sabuwar rayuwan da ko babu komai na kyallin duniya zan samu nutsuwa,
Kuma Dad a duk inda kuke ko bama tare ku family na ne bazan taba sauya Hakan ba sbd Banda uwa Banda uba bayan ku din Kuma Jannah dinma ina rokon tinda Allah yasa akwai aure Hakan ta faru a barwa Allah komai a rungumi kaddarar a yanda tazo amma nidai gobe insha Allah zan tafi koda kauyen ne zan koma sbd zan samu nutsuwa acan"

Shiru suka Jannah na fasa kuka tareda rarrafowa gurin Ammar din tana rokonsa Dan Allah kada ya rabu dasu bazasu iya rayuwa babusa ba.

Dad da Maheer Shiru sukai sbd lamarin Kuma ya juye yana neman raba tsakaninsu Wanda daman Hakan suke gudu shiyasa sukeson hada auren koyaushe sbd kada Ammar yaji shi bare a cikinsu Dan Kuwa shi nasu ne har abada.

Ajiye maganar Jannah akai dukkaninsu suka fara kokarin sauya raayinsa na tafiyarsa yabar cikinsu amma Allah yariga ya cire Masa komai a ransa sabuwar rayuwa yakeso a inda ba Nan ba koma ina ne.

Wannan tsayayyen raayin na Ammar shine sabon lamarin daya riskesu Wanda ya sakasu yanke shawarar tafiya gabaki dayansu a taren washe gari batareda tinanin komaiba hakama maganar cikin Jannah sun rufeta a tsakaninsu babu me sanin tanada ciki zasu tafi suyi renansa ta haifesa kaman yanda Ammar ya roka ya Kuma bada shawara idan yaso daga baya ayi magana amma dai yanzu sbd Ammar din zasu tafi zasuyi Shiru suma kaman yanda AZIZ yasan basusan da maganar auren ba zasu fuske a Hakan sai sungama healing Ammar tukuna zuwa lokacin Jannah din ta haihu itama.

Ummah ma bazasu taba fada mata cikin AZIZ din bane a yanzu zasu rufeta sbd duka abar komai a rufe sai sun samu yanda suke son tukuna kome zai biyo ya biyo.

Da wannan suka kwana batareda bawa Jannah gargadi me karfin gaske na kada ta fadawa kowa komai har tafiyan.

Washe gari tin Asuba Ummah kaman ta sani ta Taho ta duba Jannah ta taddasu suna Shirin tafiya sai suka Dan boye mata sbd gargadin Dad da Maheer.

Kai tsaye Umman ta fahimci akwai abinda yake Shirin faruwa Dan haka ta nufi dakin Ammar Wanda yake kokarin kiranta a waya sbd bazai iya tafiya batareda yayi bankwana da ita ba.

A Palo suka hade yana ganinta sai a lokacin tinda abin ya faru yaji hawaye masu tsananin zafi sun ciko idanuwansa suna gangarowa tana qarasowa gabansa ya zube a kafafunta yana fasa wani irin kuka me tsananin karfi da wani irin tsananin ciwo da baqin cikin rayuwar dayayo a baya ayau gashi ya wayi gari baida kowa baida komai baida Wanda zai kalla yaji sanyi sai uwar daya kashewa 'ya da hannuwansa.

Wani irin kuka me ratsa xuciyan duk Mai sauraronsa yakeyi yana qanqame kafafun Umman wadda itama take kokarin hawayen tana Jin gabaki daya jikinta da zuciyarta na mutuwa akan Ammar din Wanda a yanzu ne lokacinda yake tsananin buqatan duk wani Mai kaunarsa Dan haka taji tana sake kaunarsa da tausayinsa.

Dad da dukkaninsu da suka fito sbd kukan Ammar din jikinsu tsananta sanyi yayi Maheer daya kasa riqe kansa sbd yanajin radadin da Ammar din yake ji har ransa kukan yakeyi Shima sbd jarabawan da Ammar yake ciki dole zasu runguma su bisa duk inda ta kama suyi rayuwan.

Dad ma Jin yayi yana hawayen gazawa a matsayinsa na uba daya kamata ya tsaya musu a komai ya Dora su akan hanyar data kamata gashi yanzu sun rasa alkiblarsu haryanzu basusan matsayin da rayuwa ta ajiyesu ba amma dai kaman yanda suka saba zasu runguma juna a kowane hali daman baya a kamata su tafi tin da dadewa Dan haka lokaci yayi na su tafin koda kauyen ne su koma sun Tara abinda zasu bawa Ammar da abinda Jannah zata Haifa rayuwa me Kyau.

Sun jima a wannan yanayin kafin Ammar din ya dago idanuwansa da sukai jajir ya Kalli ummah kallan bankwana ya bude Baki yace

"Ummah tafiya zanyi,
Zan tafi duk inda Allah ya nufa zan rayu Kuma,
Zan tafi Ummah,zan tafi.....

Kasa riqe Kanta Umman tayi itama kukan takeyi tana girgiza Masa Kai tana cewa

"Ammar kada ka tafi koina,
Babu inda zaka tafi Ammar."

Dad ne ya kalleta idanuwansa jajir Shima ya bude Baki yace

"Ba shi kadai ne zai tafi ba dukkanin mu ne zamu tafi"

Da sauri ta Kalli Dad din tana cewa

"Dukanku kaman Yaya?
Ina kuke maganar tafiya Dad??

Kallan yaran yayi Wanda sukai Shiru kowa zuciyarsa ba dadi.

Hannun Umman ya qaraso ya kama ya jata zuwa dakinsa a natse ya rufo kofar ya kalleta yana mata bayanin zasu sauya gurin rayuwa ne kawai sbd Ammar Wanda zai samu nutsuwa Dan haka idan tanada raayin cigaba da aurensa ta shirya zasu tafi tare idan Kuma batada raayi bazai taba mata dole ba.

Wani irin nauyi ne ya danne kirjinta data kasa cewa komai bayan Kafesa da ido tana Jin wani irin bacin Rai na taso mata amma Kuma bazata iya tsayawa fada dashi ba sbd kalamansa juyawa tayi ta fice daga dakin kawai.

Tana fitowa kai tsaye dakinta ta wuce ta dauki wayarta ta saka Kiran AZIZ Wanda baya gidan.

Wayarsa Bata shiga kwata kwata Dan haka ta saka Kiran sayd Wanda yana dauka ta sanar dashi Kai tsaye ya sanar da AZIZ din dake zaune yana wani meeting a laptop dinsa.

Katse meeting din yayi yana karban wayar ya miqe ya isa bakin window dinsa yana sauke ajiyan xuciya me sanyi yace

"Ummah ki barsu su tafi zasu tafi inda kowannensu zai samu nutsuwan da zasu samu damar tinani me Kyau harma a samu maslar komai,
Daman lokacin tafiyansu yai ko basu ce zasu tafi ba Mai tafiya dasu din yana gari ya sauka a jiyan,

Ummah Banda sauran damuwa ko wata gaba tsakanina da Zaadens sbd sune ahalin macen danakewa kallan itace rayuwata a yanzu Kuma ita da abinda yake cikinta sune arzikin da nake alfahari dasu Dan haka babu Komai ta bangarena Matiqar bazasu taba Matata da cikina ba Dan haka su tafi sbd itama Jannah din ta samu nutsuwan data rasa kwanakin nan a cikin familynta"

Ummah datake sauraronsa jikinta sanyi yayi sbd AZIZ din ya sake nuna mata zuciyarsa batada sauran tsatsar komai akan zaadens.

Ayau da Asuba yana dawowa masallaci ta gama tinkararsa da maganar Jannah da cikinta ta fahimta Kuma ta nutsu da yanda yake kaunar matarsa Dan haka itama tana bayan aurensa da Jannah.

Ajiyan xuciya Umman ta sauke tareda cewa

"AZIZ Allah yayi Maka albarka ya baka kariya da dukkanin abinda kakeso"

"Amin Ummah nagode"

Numfashi ta sake saukewa tace

"Bazan taba samun nutsuwan barin Jannah a cikin wannan halin da bacin Rai zai saka Dad da Maheer daukan matakin da bai kamata akanta ba sbd abinda yake cikinta Dan haka zan bisu har zuwa lokacinda zata haihu inshallah"

Murmushi me sautin nutsuwa AZIZ ya sake yace

"Ummah Jannah ai bazata haihu baa hannuna ba,
Na Bata daman daidaitawa ne da iyayen nata kafin karbanta,
Ummah bazan taba Baki zabi ba sbd inason kibi duk abinda zuciyarki take so idan har zaadens sune ahalin da zasu Baki nutsuwa ina Miki fatan alkhairi a cikinsu sbd nasan ko zuciyarsu ba Kyau ke suna Miki kaunar jininsu dake yawo a jikinsu Dan haka Ummah Allah ya Baki farin cikin da duk kike buqata a rayuwa ki bisu kawai sbd auren dayake tsakani"

Wasu hawayen tausayin dan nata ne suka cikowa idanuwanta sbd tana Jin karfin hali da tawakkali a muryansa dake fita cikin sanyin nutsuwa.

Dad ya Bata ranta sosai datake Jin Bata buqatan binsu amma kukan da Jannah ta ringa mata tana tsananin buqatanta ya sakata amincewa ta bisu sai Kuma Ammar datakeson tsayuwa a rayuwarsa taga bai sake nisa a duhu ba.

Gabaki daya gidan tashi hankalinsu yayi da tafiyan zaadens din Wanda babu Wanda yasan da ita Saida suka fito da komai nasu zasu wuce.

Falaq jikinta na tsananin rawa ta fito da gudu ta nufi Jannah ta rungume ta baya tana fasa kuka tareda qanqameta tana cewa zata bita.

Fiddausi da hawayen takeyi qarasowa tayi itama tana riqe Jannah din tana kokarin Kiran Sayd Dan ya sanar da AZIZ,

Mama ganin da Ummah zasu tafiyan tasu ya saka itama Hankalinta tashi batasan lokacinda ta isa gaban Dzad ba tafara rokonsa akan suyi hkr Dan Allah kada su tafi su bari AZIZ ya dawo.

Girgiza Kai dad yayi batareda ma ya iya Bata amsa ba.

Falaq gabaki daya ta daga hankalin duka Wanda yake gidan da kukanta ya riqe Jannah ta Hanata tafiya tana cewa a kira Daddynta cikin kuka.

Jannah data kasa kwacewa daga Falaq din

Please Login or Register in order to submit comment