Reading KALBIM BOOK 2 BY MAMUHGEE Chapter 29 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

zai kawo mafita da sauki tareda maslahan komai na damuwan da mike ciki"

Shiru Dad din yayi yana gyada kai kawai kafin ya dago ya kalleta yana Dan kokarin dawo da nutsuwansa yace

"Yaya Ammar din??

Maheer ne ya basa amsa da cewa

"Sun gama basa taimakon gaggawa dayake buqata Shima ana jiran farfadowansa ne kowane lokacin"

Ajiyan xuciya me Dan sanyi Dad din yayi yana sake bude Baki yace

"Ina Jannah?

Kai tsaye Muhammad dake kokarin gyarawa Dad din pillow din dayake kokarin jingina daya tashi zaune yace

"Sun koma gida ita da fatma"

Shiru ne ya sake ratsa gurin kafin Maheer da kama Dad din zuwa toilet Dan alwala Ummah Kuma sake gyara Masa shimfidar gadon me Dan wali sosai tayi tana cewa

"Muhammad ka tabbata sun koma gidan ai ko??

"Insha Allah Ummah suna gida"


******Acan sai da gari yayi haske Jannah ta farka lokacin daga ita sai AZIZ din a dakin yana hannunsa da nata yana sarqe cikin lafiyayyan bargon da aka rufeta dashi Wanda sayd ne yaje ya kawosa sabo fil daga gida tin tsakar Daren.

Zubawa juna idanuwa sukai tana kallansa a sanyaye sbd har yanzu tashin hankalin Soyayyansa a rayuwanta bai qare ba sbd a yanzu da akasan tana dauke da cikin da bazata iya fadan nasa bane sbd kada a zubar mata da cikin wani babban qalubale da tashin hankali ne a rayuwanta data babynta da tinda ya bayyana sun sani tsananin son abinta takeyi sbd AZIZ LIMBA dinta ne ubansa,shine yabata kyautarsa datafi komai a rayuwanta yanzu,
Zata so ta haife Dan AZIZ LIMBA dake cikinta sbd sake basa farin cikin dazaifi komai na rayuwansa.

Shi kansa AZIZ din bazata iya fada Masa tana dauke da cikinsa ba sbd tashin hankalin yawa zaiyi idan yasan akwai ciki a jikinta kuma yaga familynta na kokarin daukan mataki akan laifin datai bazai kyaleba fitinar ahalin biyu tashi zatai ayita yi bayan saukinta da son zama abu daya datake fatan musu tsakanin LIMBAS da ZAADENS Dan haka Sai tagama karban hukuncinta sun karbi cikinta tukuna zata iya sanar dasu mahaifin cikin nata Shima ta sanar dashi.
#MAMUH
07019691719*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 65

*_ZUZEAM VENTURES_*
Best kayan Mata
08144015291
*NEW ALERT*
*END OF DISCUSSION PACKAGE*
~25k~ promo 12k
Barka da Sallah promo pack
1. Tabajen kankana da fruit
  (Mai saukar da niima nan take ta kara miki dadi na musamman keda oga sai kunyi kukan dadi ranar )
2. ⁠gumbar chakwala dadi
(Hmm yar uwa daga jin wannan kema kinsani basai anbaki labariba wannan hadin na zallar dadi ne da ciko da gaba)
3. Turare kyauta dole
  (Wannan turaren na amsar kyauta ne ina masu fama da miji mai mako wanda ba a cin kudinshi Ga shi da abun amma ba a ci to yar uwa matsalarki tazo karshe da izin Allah Sai kinci abunshi ina yan kasuwa duk kina amfani da wannan turaren sai Kinga budi da izinin Allah)
4. Zumar bata gaban kishiya yar asali
( wannan zumar Ga mata wanda kishiya ta shiga gabansu mijinki baki gane kanshi ya fifita yar uwarki akanki baya son mu’a mala dake ko wadda mijinta ke biye biye yar uwa kukanki yazo karshe duk kikayi amfani da ita duk machen da yayi sex da ita zaijita salab kamar dusa don haka aji tsoron Allah banda wanda suke zaune lfy da kishiyoyinsu)
5. End of discussion powder
( wannan garin karshen zance kenan hajiya oga ya taba miki kukan agwagwa ko mussoshi 😁to ranar duk da kika sha wannan hadin garin hajiya sabbatu sai kin rufe mishi  baki ihu da kururuwa ba sauki kuma garin wata 7 yake ajiki yana aiki )

Hajiya karki bari wannan promo ya wuceki 25k ne promo saboda sallah 12k kacal

TikTok: Zuzeam.ventures5
Instagram: Zuzeam_ventures
WhatsApp: 08144015291

***********
"Hi Aslm alaikum Mrs LIMBA" shine abinda ya bude bakinsa cikin laushin murya da nutsuwa me sanyi ya furta can qasan maqoshinsa yana kallanta kafin yakai bakinsa yayi kissing hancinta yana Dan goga mata nasa hancin kan nata ya dago yana kallanta.

Bata iya cewa komaiba sai bakinta data bude kadan tace

"Meyasa kazo?
Su Dad zasu sake shiga fushi pls ka tafi banason kuyi wani damuwan fushi Kai da Dad"

Murmushi me sanyi ya sakar mata yana tayar da ita Zaune ahankali ya kama kafafunta ya sauko dasu qasa ya tayar da ita tsaye duka a natse kaman Wanda take cikin tsananin ciwo yace

"Muje ki fara tsarkake kanki da sallah tukuna"

Toile din dayake dakin kaman na tsadaddiyar hotel sbd tsari da kyansa ya shige da ita ya rufo kofar daidai nan Fatma da Sayd da fiddausi sai Falaq suka shigo dakin daga gida dauke da breakfast masu lafiya baske kusan uku da abubuwan buqatan Jannah din.

Da kansa ya taimaka mata tayi wankan tsarkin da bataiba tin jiyan sbd tashin hankalin da aka shiga tin acan ciki yace fiddausi ta kawo hand dryer da aka kawo da ita sbd yace a kawo da itan.

Da kansa ya busar mata da Kanta a toilet din kafin ta sauya kaya da kayan da Fatma tazo mata dashi tukuna ta fito tayi sallah shi Kuma Saida ya sauya nasa kayan Shima ya fito sbd wancan sun jiqe shikuma sayd daman baya wasa da komai na AZIZ a Shirye yake da kowane yanayin dazai kama Dan haka tin a cikin dare ya kawo kayan AZIZ din kusan kala uku sbd da safe koda babu abinda ya samu kayansa may b qamshin asibiti zaisa kayansa su ishesa ya buqaci sauya wasu.

Ko daya fito ta gama sallah da haka ya dago a sanyaye ta kallesa tana son cewa gurinsu Dad zata amma ganin duka wanda suke dakin basusan abinda yake faduwa ba yasata yin Shiru tana miqewa.

Breakfast akaso tayi ta kasa Sam gurin familynta take son zuwa dole ya hakura ya kyaleta.

Dukkaninsu suka isa dakin da Dad yake tana janyewa daga gefensa sosai ta koma gefe daya itada Fatma kaman tafiyarsu baa tare take ba musamman kallan da Maheer ke mata dad kuwa ko kallan inda take din baiyiba tukuna.

Ummah ce ta miqa mata hannu tana zaunar da ita gefenta Shima AZIZ din a dayan gefen Umman ya zauna yana kallan Dad bayan ya gaisa dasu Maheer kadaran kadaha ba sakewa ba Kuma basarwa.

Dad din ya yiwa ya jiki batareda yasan meya samesa ba amma dai kaman yanda sayd ma da baiji farkon draman data saka suman Dad dinba yace Masa shock ne na kasa dauka daukan halinda Ammar yake ciki ya sanyasa zubewa.

Ummah cikeda kulawa da kauna me sanyi take amsa gaisuwansa tana tambayarsa Mama.

Falaq ce ta amsa da cewa tana gida dayake tana zaune maqale da Jannah itama.

Dukkaninsu sunwa Dad fatan samun lafiya dashi da Ammar Kuma sun Dan jima kafin AZIZ da ahalinsa suka fice zuwa gida yana riqe da hannun yarsa dataso abarta gurin Jannah amma bazai iya Hakan ba sbd yasan suna cikin tashin hankali da damuwan Ammar ba zata gane kan Jannah dinba Sam ta bari kawai sai sun dawo gida.

Su AZIZ din na ficewa ummah ce tai karfin halin saka kowa yin breakfast akan dole na lafiyayyan abincin da aka kawo din Wanda daman dasu da Jannah da basuma San a asibiti ta kwana ba aka kawowa.

Sama sama kowa yaci abincin suka gama me gyara dakin ta shigo ta sake gyarawa tsaf ta daidaita ac ta sake cike dakin da kamshi ne sanyi ta fice tana sake musu fatan Allah ya karo lafiya.

Shiru dakin ya dauka kafin Dad ya dago ya kalli Jannah wadda ta rakube gefe Kanta a qasa ta kasa hada ido da Dad din bare Maheer.

Numfashi ya sauke me zafi yana bawa zafin kirjinsa damar ficewa ya bude Baki yana kallanta yace

"Jannah?"

Dagowa tayi ahankali ta kallesa cikin mutuwan jiki tace

"Naam Dad"

"Jannah me yake damunki?
Wane ciwo ne yake damunki kiketa sauyawa koyaushe?
Menene gaskiyan abinda nake ji sbd kwata kwata na kasa yadda da maganar da ni banason furtata da bakina"

Shiru Jannah tayi tana kasa cewa komai gabanta na faduwa zufa na keto mata tako ina sbd batasan tayaya zata iya bude Baki ta furtawa mahaifinta cikina a jikinta ba bayan sunsan batada auren kowa akanta.

Maheer ne ya dago jajayen idanuwansa da tin jiya yake Jin kaman zai makance sbd ja da radadin da suke Masa ya kalleta ya bude bakinsa Dan Shima so yake yaji ya tabbatarda gaskiyanta bai gama yadda da maganar wai ciki ne a jikintaba Dan bama abu bane me yiyuwaba yace

"Tambayarki akai kikai shiru"

Sake Dan ja baya tayi tana sake matsewa gefen Ummah hawaye masu zafi na cikowa idanuwanta suna fara gangarowa take ran Maheer daya matsu su fita wannan banzan tinani Da maganar cikin sbd tana kashesa yace

"Magana zakiyi ko kukan Banza ne anan an tambayeki abu kinayi kaman munafuka"

Ummah ce ta karbi zancen da cewa

"Ya isa Maheer abi a hankali mana ai zatai magana dole"

Dawo da kallanta kan Jannah dake kuka sosai qasa qasa tayi ta dafata tana kokarin kwantar da murya sbd kada ta sake daga hankalin Jannah din tace

"Ummijan,menene gaskiyan ciwon dayake damunki fada mun naji kinji sbd kowa hankalinsa ya kwanta,
Ki duba kiga halinda Ammar yake ciki sbd Hakan,ki Kalli Dad ma yanda ya kusa shiga mummunan hali duka sbd Hakan mu kanmu kwana mukai cikin zullimi da rudanin xuciya duka sbd Hakan Dan haka fada mana gaskia kowa ya samu nutsuwa,

Kinga ni bazan taba yadda da wannan zancen ba sbd ina shadan Ummijan Dina,
Dad ma Sam bai yadda ba sbd yasan wace yarsa,
Ko Maheer ma ransa yana sake baci ne sbd kin kasa cewa komai so muke ki bude Baki kice ba Hakan bane shikenan fa"

Wani sabon kuka Jannah ta sake Wanda ya saka tsikar jikin Dad da Maheer tashi,
Dad din ya hadiye wasu yawun wahala yana neman sarkewa sbd alamu na neman tabbata akwai abinda yake faruwa da Jannah din Dan haka ya bude Baki zaiyi magana Jannah din ta sake fasa kuka tana cewa

"Dad kayi hakuri ka yafemun Dan Allah......

Wani lafiyayyan mari Maheer ya dauketa dashi Wanda tinda take rayuwarta baa taba marinta ba Dan haka ta gigice tana riqe Ummah da karfi sbd jinsa cikin kunnuwanta da Kanta suna Wani dauke wuta ta fasa wani sabon kukan jikinta koina yana rawa ta sake bude Baki zatai magana Maheer yayo Kanta Ummah ta riqesa tana cewa

"Ka bari tayi magana tukuna"

"Ummah hakuri take hadawa ba tambayar da ake mata zata amsa ba" Maheer ya fada yana jin kaman zuciyarsa zata buga.

Fatma data miqe tsaye jikinta na tsananin rawa sbd tsoro kasa kallan Maheer din tayi yana yi bayan ummah itama sai a lokacin Maheer ma ya lura da yanayinta ya tsayar da kallansa kanta yace

"Fatma fito kizo nan"

Cikin sauri muryanta na rawa tana sake boyewa bayan ummah tace

"Yaya Maheer banyi komaiba bansan komaiba babu ma abinda yake damunta inji likita"

"Nace ki fito kizo Nan Fatma"

Hawaye itama ta fara masu gudu tana cewa

"Yaya Maheer dan Allah kayi hakuri sharrin shedan ne"

Da sauri dukkaninsu suka kalleta xuciyoyinsu na tsinkewa Dad ya sake hade wasu wahalallun yawu

Muhammad ma Matsowa yayi yana fizgo Fatman daga bayan Ummah da karfi ya turata gaban Maheer din zatai baya Muhammad ya riqeta yana daka mata tsawar data sakata tsayawa jikinta na Dan rawa tana kallan Maheer idanuwanta har lokacin suna hawaye.

Maheer da jikinsa ya fara mutuwa da maganar Fatman yace

"Fatma kikace sharrin shedan ne?
Ta ina shedan din ya biyo zaki mana bayani sbd kinsan komai"

Dad daya kasa hakuri da riqe tashin hankali bude Baki yayi yace

"Maheer ku kaita gurin likita yanzu Nan ya duba mana ita a gabanku kaida Fatima a kashe wannan zancen yayi nauyi"

Jannah na Jin Hakan ta sake sunkuyar dakai tana sabbin hawaye.

Gaba Maheer da Ummah suka sakata har scanning room dake asibitin Maheer ya samu yayi yanda zaiyi yayi payment me tsada aka shiga dasu scanning din sbd babu card nata na asibitin yana gida.

Karan farko ana farawa likitar tace

"Masha Allah babyn is healthy inshallah"

Rufe ido Jannah tai da sauri hawaye na gangaro mata gefen ido sbd ganin yanda Maheer yayi mutuwan tsaye yana jiri ya dibesa yayi baya zai fadi ya dafa bango da sauri yana Jin kansa na juyawa.

Ummah ma Shiru tayi tana zubawa Jannah din ido cikeda matsanancin mamaki harma batasan sanda tace

"Doctor cikin mutane ne Kuwa?
Kodai wani abin ne me kama da ciki kika gani?

Murmushi doctor din tayi tana cewa

"No,ciki ne lafiyayye wata uku a jikinta yanzu harda kwanaki ai kaman nai mata wani scanning din kwanakin baya data zo"

Shiru sukai babu Wanda ya sake cewa komai har aka gama suka fito takardar na hannun Maheer daya mata wata irin damqar da idan kaza ce data mutu.

Suna isa dakin Dad daga Dad din har Muhammad suna tsaye Fatma na zaune gefe zuru itama.

Rufe dakin Maheer yayi yana kasa kallan Dad sbd sanin zancen zai sake tabasa.

Ummah ma cikeda tausayi da kulawa take kallan Dad din Wanda tin a yanayin yanda suke kallansa ya sare ya miqawa Maheer hannu ya karbi scan din ya bude yana dubawa.

Jiri ne me karfi ya dibesa ya zaunar da karfi bakin gado sukayo kansa da sauri suna ambatar sunansa ya rintse idanuwansa jikinsa na rawa ya sauke kai yana cewa

"Innalillahi wainna ilayhirajiun,
Jamaa wannan masifar Kuma daga ina?

Ummah data kasa magana itama ajiyan xuciya ta sauke cikin sanyi da nutsuwa tace

"Ummijan daga ina?
Garin Yaya Hakan ta faru?

Fatma Maheer ya zubawa ido yace

"Kece me bakin bamu amsa yanxu saiki mana bayani"

Garba Kuwa cikin zafi yace

"Itama ai kaita yakamata ayi a dubata sbd tare suke komai"

Kuka Fatma tafashe dashi tana cewa

"Wlh tallahi Banda komai a jikina itama akwai aure ne a tsakaninsu"

Salati muhammd ya dauka yana cewa

"Kenan dai kinsan komai din Fatma?

Maheer Kuwa wani zufa ne ya fara jiqasa ya Kalli Dad Shima Dad din shi ya kalla suka Maida kallansu akan Jannah a tare tashin hankalinsu na tsananta Ummah da Bata gane inda zancen ya dosa ba sai ta karba zancen da cewa

"Indai akwai aure a tsakani Kuma su modibbo dake kauyen sun sani ai da sauki a lamarin" a tinaninta acan kauye akai wani auren.

Dad da Maheer Kuwa babu Wanda ya sake cewa komai sbd tsoron ma Jin abinda zai buga xuciyoyinsu Kuma ga Ummah a zaune basason fada ko nuna bacin ran da zai sosa ranta Dan haka sukai Shiru zufa na jiqa kowannensu amma tabbas suna buqatan zama na musamman da Jannah kafin suyi bikin kusan binneta da ranta.
#MAMUH
07019691719*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 66

*_ZUZEAM VENTURES_*
Best kayan Mata
08144015291
*NEW ALERT*
*END OF DISCUSSION PACKAGE*
~25k~ promo 12k
Barka da Sallah promo pack
1. Tabajen kankana da fruit
  (Mai saukar da niima nan take ta kara miki dadi na musamman keda oga sai kunyi kukan dadi ranar )
2. ⁠gumbar chakwala dadi
(Hmm yar uwa daga jin wannan kema kinsani basai anbaki labariba wannan hadin na zallar dadi ne da ciko da gaba)
3. Turare kyauta dole
  (Wannan turaren na amsar kyauta ne ina masu fama da miji mai mako wanda ba a cin kudinshi Ga shi da abun amma ba a ci to yar uwa matsalarki tazo karshe da izin Allah Sai kinci abunshi ina yan kasuwa duk kina amfani da wannan turaren sai Kinga budi da izinin Allah)
4. Zumar bata gaban kishiya yar asali
( wannan zumar Ga mata wanda kishiya ta shiga gabansu mijinki baki gane kanshi ya fifita yar uwarki akanki baya son mu’a mala dake ko wadda mijinta ke biye biye yar uwa kukanki yazo karshe duk kikayi amfani da ita duk machen da yayi sex da ita zaijita salab kamar dusa don haka aji tsoron Allah banda wanda suke zaune lfy da kishiyoyinsu)
5. End of discussion powder
( wannan garin karshen zance kenan hajiya oga ya taba miki kukan agwagwa ko mussoshi 😁to ranar duk da kika sha wannan hadin garin hajiya sabbatu sai kin rufe mishi  baki ihu da kururuwa ba sauki kuma garin wata 7 yake ajiki yana aiki )

Hajiya karki bari wannan promo ya wuceki 25k ne promo saboda sallah 12k kacal

TikTok: Zuzeam.ventures5
Instagram: Zuzeam_ventures
WhatsApp: 08144015291

*********
Nurse ce taxo ta sanar dasu Ammar ya farka Dan haka miqewa sukai dukkaninsu suka fice zuwa gurinsa har lokacin zufane ke jiqa rigarsa sosai yana Jin kaman jininsa na hawa yana qara hawa.

Maheer Kuwa rasa tinanin yi yayi sbd dai ta gama tabbata ciki ne a jikin Jannah yanzu Kuma tana sake Shirin tabbata cikin na AZIZ LIMBA ne ko me?

To tin sunada aure a baya aka samu cikin ya boye ya kwanta se yanzu yake bayyana ko me sbd baiga ta inda AZIZ din zai iya lalata musu 'ya ba harda ciki,
To yaushe ma akai Hakan?
Suna ina ne su harya samu kebewa da ita bayan sun kasa sun tsare sun Hana haduwansu bare alakarsu.

Idan cikinta wata uku ne ai a lokacin tana kauye kenan.....

Wani numfashi me zafin gaske ya sauke yana Jin yana buqatan karya kafafun Jannah da Fatma din kafin yaji komai Dan Kuwa wlh sai anfada Masa tayaya ma zaace AZIZ LIMBA ne uban 'dan cikin Jannah.

Dakin Ammar din suka iso Dad na tinanin da Maheer ke yi suna shiga suka watsar da tinaninsu suna qarasawa gurin Ammar din da sauri Wanda yake zaune Shiru ya zabge yayi fayau a Dare daya kaman ba Shiba,

Ummah ya zubawa idanuwansa wadda ta iso gurinsa tana zaunawa gefensa ya ciro hannunsa ahankali cikin rashin kuzari ya miqa mata ta kama cikeda kauna da kulawa tana Jin idanuwanta na cikowa da hawayen tausayinsa,

Shi kansa cikowa idanuwansa da sukai jajir sukai yana Jin inama kowa zai hakura ya bar Masa Umman ya tafi ya Gina sabuwar rayuwa daga shi sai ita sbd ya gaji da komai a yanzu Kam hutu da nutsuwan ruhi na kwanakin da suka rage Masa yake nema.

Dad da Maheer zuba Masa idanuwa sukai cikeda tsananin kulawa da kauna me karfi suna Jin jikinsu na sanyi da yanda ya kasa kallan ko daya daga cikinsu idanuwansa na bayyanar da gajiya da gazawa da rayuwan gabaki dayanta.

Dad ne ya qarasa yana zaunawa dayan gefen Ammar din ya dafasa a natse yana bude Baki yace

"Ammar Yaya jikin?
Ka bamu tsoro da halinda ka shiga,Allah ya karemu daga sake ganin irin wannan mummunan yanayin"

Cikin sanyin da ya saka jikin kowa sanyi da mutuwa Ammar din ya bude Baki a natse da qaramin sauti yace

"Amin" daga amin din bai sake cewa komai kaman yanda kowa ma yayi Shiru ya kasa cewa komai Saida Shirun yayi yawa Maheer Shima ya matso yana Masa sannu yana kallan fatma yace

"Hada Masa abinda zaici kafin yayi brush da sallah."

Miqewa Fatma tayi da sauri tana komawa dakin da Dad yake ta dauko basket na abincin da aka ajiye sbd Ammar din.

Maheer Kuwa shine ya kama Ammar din Wanda baida karfi sosai sbd karfin nasa bai dawo ba suka shige toilet.

Brush da wanka Ammar din yayi da ruwan zafi masu zafi jikinsa ya sake karfinsa ya Dan dawo ya goge jikinsa da towel din da aka kawo Masa tareda kaya tin daga gida ya saka riga da wando mara tsayi ya fito yayi sallah duka a natse ya koma bakin gadonsa ya zauna sai a lokacin ya dago ya zubawa Jannah idanuwansa yana kallanta batareda yace komaiba,

Jannah da tinda ta shigo ta kasa kallan Ammar din kunya da takaicin Kanta take ji data basa hope a karo na biyu bayan zuciyarta Bata cire Wanda shine yake cikeda ita ba gashi yanzu sun sake dawowa inda suka bari a baya ciwonsa zai iya tashin da zai sauya rayuwansa gabaki daya.

Dad da Maheer tsoronsu ciwon Ammar din dazai tashi daya sake tabbatarda da gaske cikin ne a jikin Jannah,

Abinda basu sani ba Ammar din ya riga yama San waye uban cikin sbd ya ga Hakan da idanuwansa da baya buqatan Jannah ta bude Baki ta fada waye me cikin,

Ajiyan xuciya me sanyi Ammar din ya sauke yana dauke idanuwansa daga kan Jannah din ya koma baya ahankali ya kwanta yana rufe idanuwansa Ummah ta rufe Masa jikinsa tana Hana kowa damunsa sbd babu abinda yakeso a yanzu kaman Shirun.

Haka sukai jigum jigum Shiru babu me abin fada zuciyoyi babu dadi Daci da ciwon Rai zalla tako ina.

Jannah ce ta zame tafice dakin ta koma waje ta zauna tana dafe goshinta sbd Kanta dake neman bugawa sbd a dakin Shiru kawai kowa yayi amma itace duka sanadin bacin Rai da quncin kowa tin farko haryanzu da ake cikin wannan halin.


Haka suka wuni a asibitin babu wani magana me Kyau dake shiga tsakanin junansu gabaki daya sbd Ammar kwata kwata bayason magana baya son rabar kowa bayason kallan kowa zuciyarsa tayi sakayau bayajin nauyin ko ciwon komai haka yake jinsa kaman sabon mutum din da aka Halitta ayau din,

Baya ganin laifi ko Jin zafin kowa kawai kansa ne yake gani Mai laifin daya kasa bawa zuciyarsa da rayuwansa damar samun sukuni da nutsuwan data kamacesa tin farko bayan rasa mahaifiyarsa,

Ya bari kunci ya mamayesa ya bawa duhu daman gauraye rayuwansa dayake ganin babu hasken dazai haskakesa saina Jannah da ahalinsa,
Ya rasa kowane irin hope na rayuwa da kwanciyan hankali da nutsuwansa ya kwallafasu akan macen da Bata taba Masa kallan masoyin daya sadaukar da kansa gaba daya akanta ba kallan Dan uwan da bazata taba iya zaman aure dashi ba take Masa gashi a karo na biyu ta sake zabar waninsa akansa Wanda a yanzu Kam komai ya qare yazo karshe take dukkanin abinda yake zuciyarsa yaji yana narkewa yana sauka daga kirjinsa Wanda a yanzu yake jinsa empty sbd Jannah ta riga ta zama macen AZIZ LIMBA Wanda ya gama mallakanta cikakkiyarta mace,

A yanzu Jannah Zad macen waninsa ce,
Jannah Zad a yanzu uwa zata zama wadda daga yanzu data dauki cikin wani ya gama samun iyakarsa da har abada ya tsaya anan bazai taba wucewaba sbd bawa rayuwansa daman samun sukuni da farin cikin daya rasa,

Ya sani haqqin Rai ne ke bibiyansa Wanda yake fatan zai samu nutsuwa ta hanyar yadda da Hakan sbd samun warwarewan damuwa da quncinsa daga ubangijinsa Dan haka Ayau shi Ammar Zad ya hakura da dukkanin rayuwansa ta baya ya shafeta ya rungumi kaddararsa zai bawa kansa damar Dora sabuwar rayuwan daya kamata ya Dora tin a baya.


Da yamma Ummah da fatma da Garba suka bar asibitin suka koma gida Wanda ummah dole tayiwa Jannah na zuwa gidan suna isa gidan Ummah Bata iya barin kowama yasan mugun tashin hankalin Da suke ciki ba na ciki a jikin Jannah sbd ganin sirrinsu ne da bai kamata kowama yaji ba ciki Kuwa hatta AZIZ dayake danta da Mama datake uwar AZIZ din Kuma aminiyarta sbd ita tama Fi Jin kunya da baqin cikin AZIZ da mama suji sbd mutuncin Jannah din dazai zube a idon tsohuwar sirikarta da shi AZIZ din tsohon mijinta suji cikin da baa San ina ya fito bane a jikinta Dan haka sukai Shiru babu Wanda yasan me yake faruwa a cikinsu.

AZIZ na gidan bai fita koina ba daman jiran dawowansu yake idan Bata dawoba yana niyar tafiya asibitin ya dawo da ita gida da kansa sbd ita tama Fi Ammar din da Dad buqatan hutu da nutsuwa suda suke kwance a gadon asibitin amma itace ya kamata a bawa dukkanin kulawa ba su ba.

A dakin Ummah tayi wanka tai sallan laasar tana idarwa fiddausi takawo mata fruits da abinci ta lallabata taci fatma taxo da maganin da AZIZ din ya Bata tin a asibitin Wanda na Jannah ne ta ringa tabbatarda Tasha akan lokaci.

Maganin Tasha tana gamawa ta kwanta a farkon gadon Ummah tana dan lumshe idanuwanta tareda Dan rage AC.

Ummah na kitchen tareda su fiddausi da Kanta takeson ayi aikin abincin da Ammar zaici sbd gabaki daya ya kasa cin komai baya iya cewa komai Shiru kawai yakeyi yana sauke ajiyan xuciya akai akai tace ya yawaita ambatar Allah zai samu nutsuwan xuciya Dan haka duk ya numfasa saiya ambaci Allah Dan haka yaji yana samun sukuni da nutsuwan xuciya ahankali ahankali Dan haka ya sake Jin baya buqatan yawan maganar Dan Hakan yana sakasa Jin yana sake dawowa daidai Wanda tin a shekarun baya ya kamata ace ya samu Hakan da kila baiyi batan da yayi ba a rayuwarsa.

Bude kofar dakin akai a hankali cikin nutsuwa tareda shigowa da sallamarsa me dadin sauraro ya rufe dakin qamshinta Dana AC daya gauraye dakin na shiga hancinsa take yasan tana dakin Umman Dan haka yakai idanuwansa bangaren lafiyayyan makeken gadon umman yana saukesu akanta.

Gurin Ummah yazo sanar da ita cikinsa dake jikin Jannah din sbd ta kula da ita a cikinsu Dad din da bacin Rai zai iya sakasu wani abinda zai

Please Login or Register in order to submit comment