Reading KALBIM BOOK 2 BY MAMUHGEE Chapter 20 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

na dan dawowa ahankali.

Cigaba yayi da shaqar numfashinta da ba karfin komai a cikinsa har tsawon mintina shiru a jikin juna kafin ya saketa ya miqe zaune ahankali Yana ziro kafafunsa qasa.

Bathroom ya nufa kafafunsa a sanyaye Shima jin yake baida karfi kwata kwata.

Ruwan sanyi ya sakarwa Kansa Yana lumshe idanuwa Yana sauke numfashi masu sanyi da samun nutsuwa a jere.

Ya dade a ciki kafin ya fito.

Ko daya fito yunqurin Amai takeyi Amma batada karfi ko kadan na yunqurin dan haka da sauri ya iso ya tallafota jikinsa Yana kunna hasken dakin me yawa idanuwansa suka sauka akan inda take kwance yaga jini.

Sarawa yaji kansa yayi da karfin gaske zuciyarsa na nauyi,

Da sauri ya dauketa cak ya nufi toilet Yana isa ya kunna ruwan zafi a bathtub ya sakata sbd bazata iya tsayuwa a shower ba.

Wani numfashi me karfi na azaba ta sake ruwan na ratsata ta qanqame hannunsa da dan karamin karfinta tana kasa bude idanuwanta.

Fitowa yayi zuciyarsa gabaki daya tana daukan zafi da halin daya sakata dan haka wayarsa ya nufa ya dauka ya saka Kiran Sayd.

Kiran farko Sayd ya dauka sbd ya farka tinda yaji qarar.

"Ina buqatan Doctors kaman biyu xuwa uku yanzu nan"

Tashi zaune Sayd yayi Yana sake kallan time kafin ya sauko gadonsa Yana cewa

"Ok Maza ko mata?

"Mata duka a yanzu nake buqatansu"

Kashe wayar yayi yana komawa toilet din gurinta yana isa ya bai damu da yanda ruwan datake cikin suka sauya ba ya shiga ruwan ahankali Yana rungumota jikinsa Yana ambatar sunanta cikeda tsananin kulawa Amma bata iya amsawa.

Ganin hakan da yanda take sake sakewa ya saka hankalinsa sake tashi ya fito yana sake daura towel ya dauki wayarsa ya kira Sayd Wanda tini ya fito tareda tada mota dace motar securities din gidan ta biyosa da wasu daga cikinsu.

Daukan wayar yayi cikin matsuwa AZIZ din yace

"Sayd am loosing my mind here me suke jira haryanxu ne??

Cikin sake qarawa motarsa gudu Sayd yace

"Ina hanyar dauko sun sbd zuwansu zai dauki time Amma kafin su iso ko akwai taimakon da fiddausi zata iya bayarwa?"

Da sauri AZIZ din yace yes.

Sayd da sauri ya kira fiddausi wadda take bacci tana ganin Kiran ta tashi zaune tana daukan wayar cikin mamaki.

Bai tsaya cewa komaiba cikin sauri yace

"Fi kije Jannah na buqatanki yanzu"

Kashe wayar yayi Yana sake bankawa motarsa wuta.

Fiddausi take bacci ya saketa ta miqe tana saka hijab akan riga da wandon baccinta masu santsi da tsada ta nufi kofa ta fito dakin ta sauka qasa tana nufar palon da zai kaita saman AZIZ.

Ko data isa harya bude kofar palon Yana zaune palon idanuwansa jajir.

Kasa kallansa fiddausi tayi kaman yanda bai kalletaba yace tayi saurin taimaka mata.

Ko data shiga ya sauya beddings duk da bai wani iya sakawa yanda ya kamata ba ya dai sauya hakama ya sakawa Jannah shirt mara nauyi.

Toilet fiddausi ta shiga ta isa gurin Jannah din da sauri tana kallanta yanda koina jikinta da fuskanta yayi jajir bata iya ko zaunawa tana cikin ruwa kwance.

Ruwa fiddausi ta sauya mata masu zafin gaske tana sake zaunar da ita cikinsu Jannah ta fasa kuka mara sauti amma duk da hakan ya shiga kunnensa dan haka ya dawo toilet din da taimakonsa yana riqe da hannuwanta cikin kulawa kaman zai zare ransa ya bata aka sake sauya mata ruwa yabi duk ya rufe ruwan da towels kusan Guda uku sbd kada ko cinyoyinta fiddausi ta gani.

A haka ya fahimci ruwan zafin Jannan ke buqata dan haka ya sallami fiddausin ya dinga sauya mata ruwa kamar zararre Yana sakata har saida Sayd ya iso da likitoci mata biyu Wanda suka hawo har sama suka dubata da kyau yanda ya kamata babu buqtaan stitches kawai dai girman da yayi mata da karfin daya bata tareda gurzuwa datai ne ya saka ta goge sosai ta dan jin rauni Amma ba dinki.

Magani da allura sukai mata take ta samu wani wahalallen bacci.

A cikin duhun Daren ana gap da Kiran asuba Sayd ya sake maida doctors din fiddausi kuma taje itama a cikin Daren ta sake dafo madara me zafi da zuma ta sako a gurinda zai aje zafin ta kawo palon ta ajiye ta koma dakinta.

Rufe Jannah din yayi a da abin rufa Yana rage mata ac ya miqe ya nufi toilet sai alokacin yayi wankan tsafta da tsarki da ruwan zafi sosai ya fito ya saka dogon wandan kayan bacci kawai da jallabiya yayi sallar asuba da akai yana idarwa yayi adduoinsa na godia ga Allah daya basa mutane biyu dayafi so akan tasa rayuwar wato mahaifiyarsa da Jannah da ayau ta zama cikakkiyar macensa.

Yana gamawa zare jallabiyarsa yayi ya hau gadon ya shige jikinta ya kwanta Yana shakar kamshin dayake fita a jikinta na rigarsa dake jikinta daya hadu da qamshin jikinta.

Baccin ne ya daukesa a jikinta Shima sedai bai dade sosai Yana baccin ba dumin numfashinta dake sauka a kirjinsa yana tada tsikar jikinsa tareda laushin jikinta da fatarsu dake ta sake mannuwa da juna babu kayan kirji ya saka hankalinsa gabaki daya ya tashi yaji Yana shiga wani dumin jiki da sabuwar buqatarta me karfi da zafi.

Bude idanuwansa yayi Yana zuba mata tana bacci cikin nutsuwa da rashin karfi,

Lips dinta ya zubawa idanuwa Yana kallan yanda sukai ja ya hadiyi wasu yawu masu dumi Yana saka fuskansa wuyanta Yana sauke mata numfashinsa me dumi daya sake dumama jikinta cikin bacci ta motsa ahankali tana dan sake shigewa jikinsa numfashinta ya sake sauka da dan karfi akan fatar tsakiyar kirjinsa take ya zagoyota da hannuwansa Yana mannata sosai da jikinsa Yana Shafa wuyanta zuwa kirjinta ahankali kafin ya gangara zuwa cikinta da Mararta Yana kasa riqe Kansa sbd jin kaman ya hadiyeta gabaki dayanta.

Yanda yake shafarta ne ya sakata bude idanuwanta jajir ahankali cikin sanyi da rashin kuzari ko karfi ko kadan ta kallesa da idanuwanta da sukai wani irin laushi....

Cikin wata irin kasala da zarewan da yaji notikan hakuri da control dinsa na yi ya bude baki da kyar ya iya cewa

"Da kin Sani baki bude idanuwanki akaina ba sbd your eyes sun....kasa qarasawa ma yayi Ya Dora bakinsa kan lips dinta da suka bushe jajir Yana tsotsansu ahankali Yana sake shigewa jikinta Yana zare rigar jikinta kai tsaye.
#MAMUH
#LIMZAD
#BEST LOVE
#ROMANCE
#NICKY
#GARBA

07019691719*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 44
07019691719


Rawa jikinta ya dauka cikin rashin karfi ta fara girgiza kai tana ambatar sunanta can qasan maqoshinta daqyar sedai kwata kwata ba alamar zata samu ya saurara sbd hakuri kawai yake bata Yana cigaba da dumama jikinta da zafafan romance kafin ya rabata da komai yana shiga tsakiyanta tareda bude kafufunta a natse ya fara fama mata raunikan da batama San yaushe zata warkesu ba.

Azabar data sake sha ce ta saka ta jin tsoro na kamata ta ringa kuka mara sauti ahankali jikinta na tsananta zafi sosai tana rungume a jikinsa Yana jera mata kalman sorry da I love you a kunnenta cikin sanyi da tsananin tausayinta.

Yana jin gamsuwa iya gamsuwa a tattare dashi,

Madaran da fiddausi ta kawo mata yaje ya dauko mata ya kawo mata ya bata Tasha daqyar jikinta zazzabi sosai.

Dr ya sake kira tace ba komai bane idan ta samu isashen bacci da hutu tareda abinci me kyau zata warware Amma ya daga mata kafa.

Kashe wayar yayi ya kira fiddausi kai tsaye yace ta hadawa Jannah breakfast dinta daban a kawo mata.

Sake taimaka mata yayi ta shiga ruwa sosai tayi wanka ta fito da taimakonsa tayi sallah kafin ya kwantar da ita ya shige toilet Shima.

Yana shigewa ta sauko gadon tana dafa bango sbd jiri tana tafiya ahankali ta dauki hijabinta ta saka ta fice bata gani sosai.

Da bin bango da durqusawa take saukowa stairs jikinta na rawa sosai sbd karfin da zazzabinta yake qarawa.

Bata hadu da kowa ba sai Fatma Wadda take gyare palon da sauri ta kalleta tana jefarta mopper ta iso gurinta ta kamata zatai magana take ta fahimci meya samu Jannah din da tashin hankalin gaske ta kalleta tana qasa da muryan tace

"Su Dad kaman sun tashi suna palo fa?"

Duk da halin da Jannah ke ciki gabanta mummunan faduwa yayi ta qanqame Fatma hannuwanta n rawa ta kasa magana.

Kamata Fatma tayi itama tsoron cikeda cikinta jikinta har rawa yakeyi sbd tsoron kada wanda ya fahimci wani abu.

Cikin saa koda suka isa palon babu kowa dan haka da sauri Fatma ta Isa da ita daki ta kwantar da sauri tareda rifeta da bargo tana rage ac sbd yanda jikin Jannah din ke rawar ciwo sosai.

Tana kwantawa babu jimawa baccin azaba ya dauketa me karfi.

Sai a lokacin fatma ta sake ajiyan zuciya me karfi har lokacin tsoronta bai sauka ba sbd balain dazai iya biyowa baya idan su Dad suka San akwai auren AZIZ da Jannah din bare kuma ace suna cikin gidan suna bacci AZIZ LIMBA ya maida Jannah macensa da suke jin gwara ta samu ciki da Ammar ba aure dadai wani abu ya shiga tsakaninta da AZIZ LIMBA.
To yanzu ko ita data Sani mummunan hukunci zata karba a hannun su Dad bare kila jannar,

Ita yanzu gabaki daya jin tayi tana son tafiya kauyen su bar nan din sbd gudun bacin rana.

AZIZ na fitowa bai ganta ba kai tsaye yasan abinda yasa ta koma cikin karfin hali dan haka bazai tirsasa ta Musamman yanzu da batada Lfy dan haka yana gama shiryawa sake Kiran likita yayi yace zuwa 10 na safe su sake zuwa dubata.

Fiddausi ma 10 din nayi takai abinci dakinsu Jannah din lafiyayyu ta jere.

Angama musu komai na shirin tafiya akace Fatma ta kira Jannah din sai alokacin fatma da zuciyarta ke tsinkewa ta sanar dasu Jannah ba lafiya sosai sosai ko bacci basuyi ba Daren gabaki daya.

Cikin mamaki da tashin hankali suka dunguma zuwa dakin.

A yanda suka ganta gabaki daya tayi fayau idanuwanta a kumbure alaman kuka da azabar ciwo ya saka jikinsu sanyi tareda shiga damuwa.

Ammar ne dayake likita ya dubata yaji ba ciwon zuciyarta bane dan haka bai tinani ko nazarin Komaiba saiga likita taxo tareda fiddausi da Falaq wadda duk ta daga hankalinta jin Jannah na rashin lafiya sosai.

Ganin fiddausi da Falaq ne suka kawo likita ya saka basu damu ba sbd sunsan Falaq ko zasu kasheta saita je gurin Jannah din dan haka suka fice.

Dr kadai ce ta shiga ta dubata ta bawa fatma sabbin magani da yanda Jannah din zata kula da kanta ta fice.

Fatma boye maganin tayi sbd Ammar zai iya Sanin na menene idan ya gani kila.

Mai gidan bai sauko ba sai karfe 11 na rana kuma kuma kai tsaye gurin Jannah din ya fara zuwa ya dubata har lokacin bacci takeyi dan haka kai tsaye ya sake wucewa gurin Ummah Wadda yana shiga dakin ya taddata Zaune Daram akan gadon datake idanuwanta jajir alaman kuka me tsananin gaske tasha.

Mutuwar tsaye yayi daga bakin kofar Yana kallanta jikinsa na mutuwa gabaki daya idanuwansa kafe akanta suna sauyawa.

Dagowa tayi itama ta kafesa da idanuwanta jajir a kyaftawa hannuwanta na rawa ahankali tana kasa bude baki tayi magana.

Dad dasu Maheer ne suka iso dakin ganinsa tsaye bakin kofar dakin ya sakasu isowa da sauri cikin tsinkewan zuciya.

Ganinta zaune ya saka dukkaninsu tsayawa cak kaman AZIZ LIMBA zuciyarsu na harbawa da matsanancin tashin hankalin wa zata tina ko ambata a cikin su ko AZIZ LIMBA.

Mama ma a daidai lokacin ta iso sbd tin ranar d abin ya faru bata sake saka AZIZ a idanuwanta ba hakama batasan yaya Fatiman ba ta tashi kuma waye ta tina a tsakanin AZIZ ko Zaadens.

Itama tsayawa tayi cak a kofar dukkaninsu kallanta sukeyi kowa zuciyarsa na tsinkewa.

Sayd dake bayan AZIZ Shima zufa ne ya tsinke masa Yana fatan baqin ciki da quncin uban gidansa ya qare daga yau har abada idan har mahaifiyarsa ta Tina sa.

Ummah tsurawa kowannensu idanuwanta tayi babu Wanda tinnainsa ko memorynsa ya fita daga kanta ko daya idanuwanta suka sake cikowa da hawaye masu zafin gaske suna saukowa kan fuskanta ta bude baki ahankali da muryan da babu wnada ya Santa da ita sbd sanyi da nutsuwanta tareda wani irin kewan da har abada bazata cike daga zuciyarta ba Musamman yanzu da babu Ummitah tace

"ABDULAZIZZZ" Cikin wani irin sauti me sanyin daya saka kafafunsa sarewa Yana zubewa qasa a bakin kofar wani irin kuka me karfin gaske Yana kubuce masa ya kai goshinsa qasa Yana sujjada cikin kukan daya tada tsikar jikin Sayd dasu Fatma dake palo duka a tsaye suna sauraron komai.

Yana dagowa daga sujjadan ya isa gurinta da wani irin karfin gaske ya fixgota jikinsa ya rungume da tsananin karfi Yana wata irin tsima zuciyarsa na neman fashewa da farin cikin duniya gabaki dayanta.

Baya mama tafara yi kafafunta na kakkarwa idanuwanta na cikowa da hawayen baqin cikin duniya gabaki daya tana jin rabin jikinta na neman shenyewa sbd riqewan dayake.

Zaadens ma kusan mutuwar tsayen sukai idanuwansu duka akan Umman wadda take qanqame jikin danta idanuwanta kafe akan Dzad da Shima nasa ke kafe akanta.
#MAMUH
07019691719*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 45

Sayd ma baisan lokacinda ya zube qasa yayi sujjada ba Yana jin wani nauyi na sauka daga kirjinsa sbd ciwon dake danne da rayuwar AZIZ na rashin mahaifiyarsa na shekaru shima jinsa yakeyi sbd yafi kowa Sanin irin hali da quncin da zuciyarsa ke lullube cikinsa,

Falaq ma da sauri ta qaraso tana rungume daddyn nata ta baya tana tayasa murna sbd ita farin cikinta akan daddynta y samu abinda yakeso ne tinda ba Sani datai Daddynta nada wata asalin uwar ba bayan Mama se yanzu da abubuwa suka bayyana.

Cikin wani irin farin cikin da bai taba shiga ba a rayuwarsa tin rasuwar mahaifinsa Yana qanqani ya dago Yana kallan fuskan Umman ya kama hannuwanta duka biyun yayi kissing nasu ya rungumesu a kirjinsa Yana rufe idanuwansa kirjinsa kaman zai fashe da farin ciki.

Falaq dake bayansa ya janyo ya rungumeta yana jin itama kaman zai maidata ciki ya dagota yana kallan Umman ya Dora hannun Falaq akan nata ya hada ya riqe a cikin hannunsa ya bude baki yace

"Ummah ga wata Fatimanki,
Little Ummitanki ce,
Jinin Ummitah c..... Kasa qarasawa yayi sbd wani irin sanyi da jikinsa yayi Yana kallan yanda hawaye ke gangarowa daga idanuwan Umman ta zubawa Falaq ido Yana kallan kamanninta da bata Sani ba na Ummitah sbd tin daga ranar data haihu ta tasa hankalinta hakama ko data rabu da yayanta suna Yara Ummitah na qanqanuwa sosai.

Falaq zubawa Umman ido tayi itama tana kallan matar data haifi mahaifiyarta sbd daman can Mama a matsayin mahaifiyar daddynta take kallanta mantawa takeyi Sam da itace uwar tata mahaifiyar sai a yanzu ne take jin ta hadu da mahaifiyar data haifi mahaifiyarta.

Ahankali Umman ta sake dago idanuwanta ta sauke akansu Dad dake tsaye jiki a tsananin mace Musamman Ammar daya iso yana ganin halinda ake ciki idanuwansa da suke jajir a kumbure suka ciko da wasu irin hawaye masu tsananin zafin gaske sbd a Karo na uku ya sake rasa Uwa dayake tsananin buqata a rayuwarsa dan mummunan rayuwarsa dake cikin tsananin duhu hasken uwa ne kadai yake buqata ya yaye masa shi,

A rayuwarsa Yana tsananin so da kaunar uwa a tattaredashi wadda tin yana qarami Allah ya karbe masa wannan rahamar ta samun Uwa.

Ya rasa mahaifiyarsa,ya rasa Mimi a yanzu daya hango hasken samun wata uwar Ashe baida rabon fita duhun rayuwarsa.

AZIZ ne ya kasa juyawa ya kalli su Zaadens din da dukkaninsu kansu yayi qasa suna kasa kallan Umman da kuma jin tsananin nauyi da kunyar kallan datake musu sbd ta tabbata ita dasu kauna ta yanke sbd sune makasan 'yarta bata tabama taba samun damar saninta a matsayin Yarta ba sbd ta haifeta ta rasa hankalin ganeta hakama ta rabu da ita batareda hankali ba ayau data samu hankalinta babu Ummitah a duniya sedai zuciyarta dake bugawa a duniyar.

Ammar a Karo na farko a rayuwarsa ya samu Kansa cikin matsanancin kunya me girman gaske ta wani dan Adam,

A Karan farko yaji wani irin dana Sanin abinda yayi me tsananin gaske,

A Karan farko yaji ya tsani kansa da tinaninsa da iliminsa na likitanci tareda tsanar daular daya taso a cikinta Wadda ta sakasa bacewa a cikin batan da yayi,

A Karan farko dayaji Soyayyar Jannah na sanyi a zuciyarsa sbd itace sanadin batansa da gurbacewan zuciyarsa ya zama makashin Matar da ayau yakewa tsananin so na uwa kuma yake tsananin buqata,

Ciwo da quncin dayake hangowa a idanuwan Umman na rashin Ummitah tana kallansa ya saka dukkanin duniyar fita Kansa dan kuwa se yanzu ya gane kaddarar da suke ciki a yanzu ta haqqin Rai ce da rayukan da suka dauka da hannuwansu,

Babu ran da suka dauka wanda jininda bai bata hannuwansu ba wanda quncin da ahalinsu suke ciki kila bazai wanke ba har abada.

Wasu hawaye masu tsananin zafi da quncin zuciya ne ya ciko idanuwansa dukkanin jikinsa da jininsa suna wani mummunan sanyi.

Dukkaninsu idanuwansu jajir sukai suna jin zuciyarsu na fidda radadin samun kansu a matsayin hannun Riga da Umma Fatima sbd idan har da gaske suna sonta da kaunarta zasu barta da Wanda hankalinta ya zabar mata wato danta sedai kuma babu maganar sakin aurenta ga Dad har abada sbd abu ne da bazai taba iyawa sedai idan yabar duniy.

Daga kafa Ammar yayi idanuwansa na lumshewa hannuwansa na wani irin fara rawa ahankali Kansa na daukan yanayinsa gadan gadan sbd wannan Karan shi Kansa baya fatan ya warke daga haukarsa idan ta tashi yana fatan ya dawwama cikinta har mutuwarsa sbd ya huta daga quncin dayake ciki.

Juyawa yayi Yana barin gurin...

"AMMAR" shine kalman daya fito daga bakin ummah cikin wata irin sanyi da nutsuwa tareda tsananin kaunar data sakawa zuciyarta bayan tayi yaqi da zuciyarta akan korar duk wani ciwo da baqin cikin daya gabata Wanda yake mummunan kaddara da dukkaninsu.

Dukkaninsu idanuwansu dagowa sukai suna sauka akan Umman wadda idanuwanta suke jajir wani azababben ciwo takeji a kirjinta datake dannewa sbd tanason karban kaddarar Allah da hannu bibbiyu akan dukkanin abinda ya tsaro musu na hadesu guri daya duk da muguwar kaddarar daya kamata ta tarwatsasu har abada Amma Allah bai rabasu ba.

AZIZ dago idanuwansa yayi ahankali ya sauke akan Umman cikeda mamaki da wani irin sanyi Yana kallanta kafin ya gangara da idanuwansa ya tsayar akan hannunta daya data zare daga nasa tabar dayan cikin nasa ta miqawa Ammar data ambata Wanda ya tsaya cak tareda kasa juyowa sai data sake ambatar sunansa ahankali muryanta na rawa cikin karfin hali.

Juyowa yayi ahankali idanuwansa na sauka akan hannun data miqo masa cikeda kulawa da kauna irin ta Uwa....

Kasa motsawa yayi ya durqushe a gurin tareda fasa wani irin kuka me tsananin tsima zuciya jikinsa na rawa Yana fidda kukan dayake maqale a zuciyarsa na shekara da shekaru sbd mahaifiyarsa data haifesa a ranar da zata barsa duniya haka ta ambace ta miqa masa hannun dabai kama ba kenan dan kafin ya iso ranta ya fice hannunta ya sake.

Kuka yakeyi sosai Yana jin tsanar rayuwarsa gabaki daya sbd bazai iya dagowa ya kalli Ummah ba Wadda take miqa masa hannu a matsayin 'da.

Irin kukan dayake ne ya saka gabaki daya gidan yin tsit gashin jikin Zaadens gabaki daya Yana miqewa sbd kuka ne da Ammar bai taba yi ba,
Kukane yakeyi na tsananin kadaicin dayake jin rayuwarsa a ciki ba uwa ba uba ba madafa ba jannar daya qwallafawa rayuwarsa harya zama mugun Abu akanta.

Ahankali Ummah da hannunta yayi sanyi ta sake hannunta Wanda Maheer yayi saurin isowa ya tallafe idanuwansa jajir ya bude bakinsa dake rawa ya ambaci sunan Ammar Wanda yake wata irin jijjiga jikinsa na rawa Yana kuka.

AZIZ da yayi mutuwar xaune kasa dauke idanuwansa yayi daga kan mahaifiyarsa dake amsar Wanda ya bude kirjin yarta ya rabata da rayuwar a matsayin 'da da hannunta...

Wani irin ja idanuwansa sukai tsananin kaunar mahaifiyarsa na yagalgala zuciyarsa data kasa yafe komai Amma ita batareda ma tasan waye Ammar Zad ba take amsarsa,

Baisan ciwo da tsananin radadin da zataji ba idan ta san waye Ammar din,
Yaya zata karbesa?
Yaya zuciyarta zata iya daukan hakan?
Zai iya kallanta ya fada mata?
Zai iya bari ta dandani quncin da har abada bazai wanke daga zuciyarta ba,

Tsakiyar idanuwanta ya kalla ya hango kauna da shakuwa datakewa Ammar din Wanda take kalla idanuwanta na sake ja da hawaye a cikinsu take yaji wani irin nauyi akansa kaman Yana sauka sbd ranar farko daya hadu da mahaifiyarsa Yana karban tarbiyan da ya kasa samu ko bawa kansa akan rama sharri da alkhairi.

Juyawa yayi ya kalli Zaadens din dukkaninsu idanuwansa jajir kafin ya dawo da kallansa kan Umman Yana tattara maganar Kisan Ummitah da dukkanin Wanda yake cikinta ya rufeta a ransa har abada sbd bazai taba dandanawa mahaifiyarsa baqin ciki da quncin daya rayu a cikinsa ba,

Bazai iya dandana mata radadin da Zaadens suka dandana masa,

Bazai dandana mata radadi akan mutanen datakewa kallan ahalinta na biyu ba sbd irin kulawa da kaunar da suka nuna mata duk da baisan tayaya suka hadu ba hakama tayaya suka kula da ita Amma dai yasan sun kula sun kaunaceta a lokacinda batada kowa batada hankali bakuma tareda sunsan ita wacece ba.

Miqewa yayi ahankali tsaye Yana juyawa ummansa ta kama hannunsa tareda hanasa tafiya tana kallan Ammar har lokacin.

Da rarrafe kaman almajirin dayake tsananin hali Ammar ya iso har gaban Umman yana kasa miqa hannu ya kama na Umman ya kasa dagowa ya kalleta ya daga kai ya kalli AZIZ LIMBA Wanda ya idanuwansa sukai jajir sedai babu kiyayya ko daya a cikinsu sbd ayau ya zabi nutsuwar zuciyan mahaifiyarsa akan komai,

Daga yau a gurinsa maganar Kisan Ummitah ta tafi har abada a bakinsa insha Allah sbd dukansu masu laifi ne me tsananin girma a gareta,

Idan su sun raba Ummitah da duniya dan raya 'yarsu shi kuma ya kamu da tsananin son wadda aka kashe Yar uwarsa dan rayata da har yake jin zai iya sake bata tasa rayuwar dan ta rayu dan haka shima lefinsa me girma ne a gurin Umman.

Kallansa Ammar yakeyi da dukkaninsu suna jiran ya sanarwa Umma sune suka rabata da Ummitah,
Sune suka kashe Ummitah,
Sune suka raba Ummitah da duniya dan raya tasu Yar dake raye a yanzu Amma ya kasa juyowa ya kallesu bare Umman sbd dukkaninsu sun kasa kallanta.

Dagowa Ammar yayi ya bude baki cikin mummunan yanayin quncin dayake cin rayuwarsa Yana neman sassauci da sautin daya saka kowa sake kasa motsi yace

"Ni me laifin da babu yafiya ne a gareki da bazan taba zama 'dan ki ba sbd na riga na zama makashin daya rabaki abinda kikafi so a duniya,

Ni makashin Ummitah ne da har abada bazan taba goge hakan ba a tarihinki da nawa ba,

Yau itace rana mafi baqin cikin danai Dana Sanin gani,

Ummah bazan taba zamowa 'da a gurinki ba,
Nayiwa kaina mummunan tabon da zai bini hr abada,

Ciwo da radadin rashin uwa n Sani bansan ciwo da radadin rasa 'da ba sai a yanzu danake ganinki a cikin ciwon rashin 'yar da nine na rabata da.....

Kasa qarasawa yayi Yana wani irin kukan da yake fitowa daga kirjinsa Yana dafe kirjinsa.

Duk yanda Umman taso riqe kanta kasawa tayi sbd dalla dalla Ammar ya fara bayyana mata girman laifinsa Danasani da quncinsa me tsanani a bayyane take ta fasa wani irin kuka me tsananin tsima zuciya tana qanqame AZIZ LIMBA da Shima sai ayanzu yake jin yanda Ummitansa ta rabu da ranta idanuwansa sukai jajir Yana qanqame mahaifiyarsa dake kuka kaman ranta zai fita jikinta na mutuwa.

Dzad da kafafunsa suka kasa daukansa durkushewa qasa yayi ahankali Yana zamewa zaune bakin kofar dakin cikin tsananin kunyar Kansa da tarbiyan daya Dora zuriarsa akai na tsananin son zuciya da tsananin son kai idan ba kansu ba basusan kowa ba hakama balain da masifa idan ya wuce kansu basu damu yahau kan kowaba.
#MAMUH
#LIMZAD
07019691719*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 46

Basuda kunya da baqin cikin tareda magirmamiyar Dana Sani akan abinda zuriarsu ta aikata sai gurin ubangiji da suketa neman yafiya a gurinsa sai ayau da suka samu kansu a cikinta akan Ummah Wadda Allah ya dasa kaunarta me girma da tsafta a zuciyarsu gabaki daya sbd ta shigo rayuwarsu a daidai lokacinda basuda kowa,kowa gudunsu yakeyi yana tir dasu,
A lokacin da suke cikin tsananin buqatar uwa a cikinsu hakama ta kaunace su tamkar jininta duk da batada cikakkiyar hankali kaunar datai musu me tsafta da girma ce dan haka ita din itace ta zama mutum ta farko da suka saukewa kansu qasa cikeda kunya da sarewa ga dukkanin hukuncin

Please Login or Register in order to submit comment