Reading KALBIM BOOK 2 BY MAMUHGEE Chapter 18 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

bata gane Umman bane??

Jannah ma daya hanata motsowa kusa dashi Sam jikin Dad dinta ta lafe tana tsiyayar hawaye zuciyarta cike fal da tsoron sabuwar kaddarar data bullo musu a yanzu na kasancewan Ummansu mahaifiyar AZIZ LIMBA Wanda tasan wlh komai AZIZ zai iya basu Amma bazai taba barinsu da mahaifiyarsa ba,

Zai durkusawa Zaadens qasa ya basu damar takasa Amma bazai taba basu Ummansa ba kaman yanda tasan Dad dinta zai rasa ransa da shi kadai ne ya rage masa Amma bazai rabu da Umman ba.

Hawaye masu tsananin zafi ne suka gangaro mata tanajin tsananin tausayin AZIZ din ganin yanda yake cikin rashin nutsuwansa da hankalinsa kwata kwata sbd ganin macen daya rasa tin Yana qanqaninsa,

Ya rasa kaunarta,ya rasa duminta,ya rasa kulawanta,ya rasa nutsuwar mahaifiyar,ya rasa walwala duk sbd rashin uwa mahaifiya,

Mama sunan uwa kawai take amsawa a garesa Amma babu shaquwa da kauna me zurfi da kusancin dayake tsananin buqata daga uwa shiyasa rayuwarsa take gabaki daya a baibai.

Maida idanuwanta tayi akan fuskan Umman ta kafeta da ido kaman bata taba ganinta ba kamanninta na bayyanar mata tanajin zuciyarta na narkewa sbd kaunar datake jin tanawa ummah me tsananin da babu sirki ta zuciyar Ummitah ce dake kirjinta da kuma kasancewarta uwar data haifi love of her life,
Uwar data haifi AZIZ LIMBA mutumin da bazata taba iya dena so ha har qarshen numfashinta.

Isowan likitoci ne ya saka AZIZ din miqewa tsaye Yana basu guri yana cewa kada su bari komai ya sameta zai basu komai na rayuwarsa.

Lafiyayyan bedroom din a cikin na palon aka maidata doctors din suka shiga.

Ana rufe dakin ya juyo idanuwansa jajir hannuwansa na rawa ya dago idanuwansa ya fara kallan Zaadens din daya bayan daya hawaye na ciko idanuwansa kafin ya tsayar da idanuwansa akan Jannah wadda take kallansa cikeda tsananin kauna tanajin kaman ta rage masa abinda yake ji a zuciyarsa na tsananin halinda baimasan yaya yakeji ba.

Shima kallanta yakeyi da dukkanin tsananin sonta da buqatanta hawayen idanuwansa na saukowa kan fuskansa...

Kasa riqe Kansa yayi ya iso inda take idanuwansa na rufewa ya janyota jikinsa ya rungume yana fasa kuka mara sauti Yana cewa

"Ummanah ta dawo gareni"

Hawayenta ne suka gangaro tana Manta kowa da komai ta rungumesa tana kokarin basa sassauci.

Dad da Maheer mutuwar tsaye sukai suna kallansu zuciyoyinsu na rawa da jijjiga,

Ammar da daman baya cikakken hayyacinsa bin bango yayi Yana fita waje sbd numfashinsa dayake sarkewa Yana neman rasa ransa yana fita waje y zube qasa wani irin kuka na zuwar masa Amma kirjinsa ya kasa dauka dan haka ya zube qasa yana dafe kirjinsa.

Mama dake tsaye itama mutuwar tsayen tayi sbd ganin sabon tashin hankali a gabanta AZIZ a jikin Jannah Yana kuka.
#MAMUH
#JAZIZ 2025
#LIMZAD 2025

07019691719*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 39

*_SHOP WITH ME BY RANO_*
08030811300
Kina neman in da zaki samun kayan yara classy kaya na yan gayu at a very affordable price? Ko kina son fara kasuwancin kayan yara amma baki da jarin da zaki saro kayan? Nesa ta zo kusa, kiyi joining community din nan muna saka kaya masu kyau available da inganci a farashi me sauki da zaki dauka ki tallata har ki samu naki kema.
Burinmu shine kowacce mace ta samu sanaar da zata dogara da kanta.

***********
Qanqameta yakeyi kaman zai shige jikinta tamkar yaro qanqanin da baisan abinda zeyiba da neman sassauci a jikin wanda yake samun nutsuwa,

Sassaucin take kokarin basa ta hanyar sake basa daman rungumeta da kyau tana shafa bayansa duk da yafita tsayi sosai tana kokarin hana nata tashin hankalin kere nasa sbd duk yanda suke cikin tsananin shock da tashin hankalin me yake shirin tabbatar musu na cewan Ummansu itace Umman AZIZ LIMBA amma tasan nasa tashin hankalin da mummunan shock din ganin Matar daya shafe shekaru tin Yana yaro yana nema dole ya kere nasu.

Dad da tashin hankalin dayake ciki da kuma abinda idanuwansa ke gane masa zuciyarsa ta kasa dauka yana kokarin isa gurin Jannah ya fizgota Maheer da tasa zuciyan take radadi da bacin rai ya rigasa isa tareda kamo hannun Jannah ya janyota daga jikin AZIZ din da karfi Yana jefata gaban Dad dinsu daya dago ya kalleta da idanuwansa jajir zuciyarsa na sake shiga wani halin tsananin tsoro akan tashin hankalin d suke ciki.

Me AZIZ yake kokarin yi masa akan 'ya?
Shin bai gaji da wasa da zuciya da rayuwarta bane bayan duk abinda yayi mata ya kuma dankara mata saki?
Menene kuma sukai masa yanzu da zai sake lalata rayuwar Jannah ta hanyar kokarin dawo mata da sonsa,

Numfashi ya sauke me zafin gaske Yana kallan Jannah da fuskanta ke kallan qasa cikin tsananin tsoro da baqin cikin kasa riqe zuciyarta datai ta bari ta sakawa ahalinta shakku akan zuciyarta da zata iya sake jefasu wani masifar kaman farko data jefasu masifa akan son datake wa AZIZ LIMBA Wanda shine ya lalata komai.

Cikin sanyin jiki sbd damuwar dataci karfinsa Dad yace

"Kinsan me kikeyi Jannah?
Kinsan haramcin abinda kikeyi kuwa?
Karki manta ba aure tsakaninku a yanzu kuma babushi har abada sbd ba abu ne me yiyuwaba ba dan tamkar ma ya haramta ne dan mun haramta so yafi Miki kiyi gaggawar dawowa hayyacinki kafin ki saka raina mummunan baci"

Shiru tayi tana qasa da kanta tareda hadiye hawayenta da suka ciko idanuwanta tana janyewa gefe inda Maheer ke mata kallan mamaki dan kuwa kaman yanda Dad ya fada menene zai sake sakasu barin tabi raayinta akan duk Wanda takeso bayanma maganar aurenta da Ammar ta riga ta gama tsayuwa ba fashi har abada.

AZIZ da baya hayyacinsa cikakke baisan me suke yi ba bare fada sbd ya zube zaune a kujera dafe da kansa.

Tsit palon ya sake dauka kowa a tsaye da fargaba da tashin hankalin dake tsananta sbd farfadowan Ummah dake tattare da tabbatarda abubuwa da dama wanda zasu kawo sabon rikicewa a rayuwar kowa,

Shin da gaske mahaifiyar AZIZ LIMBA ce Ummansu shine tashin hankalin da Zaadens suke ciki Wanda idan hakan ta tabbata basajin zasu sake nasu matsayin a kanta tinda ta riga ta zama  mata kuma a uwa a Zaadens tsawon lokaci dan haka ba abu ne me yiyiwa ba kai tsaye su sake barin AZIZ LIMBA ya rabasu da abu me mahimmaci dan haka suke tsaye cikin rikici da tinani suna fatar ba hakan bane ya zamto sabanin tinani kawai aka samu da kamanni.

AZIZ LIMBA kuwa babban buri da tsananin buqatansa daya a yanzu kada wani abin ya samu Umman tukuna ta farfado ta kallesa ya samu kallan rahama daga idanuwan da sukafi kowane daraja a rayuwarsa,

Ummansa ko ya girma zata ganesa sbd kamanninsa da basu sauya ba,
Zata gane 'danta,jininta kuma hamma AbdulAziz dinta itada Ummitah koda kuwa tana cikin yanayi na gushewan hankali haryanxu.

Falaq ce data kasa isowa garesa tin dazu sbd tsoro ta daure ta iso ta zaune gefensa ahankali tareda kama hannunsa daya da duka hannuwanta biyu ta qanqame tana kwantawa jikinsa tace

"Daddy Ummansu Jan zata ji sauki ka kwantar da hankalinka dan Allah kaji"

Lumshe idanuwansa yayi ahankali Yana zagaye Falaq din da hannunsa daya ya rungumeta Yana sauke ajiyan zuciya ahankali batareda ya iya cewa komaiba.

Mama da kiris zuciyarta ke jira ta buga hakama jikinta gabaki daya kaman zai kama da wuta sbd zafin tashin hankalin daya gama kameta,

Tsoro da tashin hankalinta daya ne tak wato AZIZ,
AZIZ ne iya tashin hankalin datake tsoron rasawa ko shakkar fita a ransa datake fiyeda kowa,

Zaadens takejin sabuwar tsanarsu na cike koinanta sbd abinda tai gudun shine suka hadasa mata tareda qarin zasu iya fadawa AZIZ komai akan Fatima data kasa fda musu gaskiar wace ita,

Idan har suka bude baki suka fadawa AZIZ ko kalma daya akan yanda komai yake tsakaninta dasu sun gama lalata mata rayuwa sbd AZIZ zai cireta ne daga ransa Wanda tafi kaunar kowa ya mutu kafin a samu maganar fahimta a tsakaninsu harma a fada abinda tayi,

Bare bazata taba iya gani ko barin AZIZ ya samu shiri da Zaadens ba kaman yanda tasan zafin tsana da fushinsu na Nan fil a ransu saita dawowa da AZIZ tasa akansu ta yanda bama aure tsakaninsa da Jannah zai dawo ba dan kuwa irin son da Fatima kewa Jannah AZIZ zai qare ne gabaki daya akan Jannah da Fatima,

Duka batama fatan hakan ta faru adduarta da fatanta Fatiman ma kada ta tashi kwata kwata idanma ta tashi bata fatar ta dawo hankalinta shine lamarin zaiyi saukin sauki.

Nicky kuwa tana dayan palon t kasa qarasa shigowa sbd yanda kanta ke rawan rashin lafiyanta tana jin kaman ta Dora hannu akai ta kurma ihu kokuma ta sakawa 4&4 din wuta kowama ya mutu ta huta da wutar datake jin tana cin kirjinta tana tafasa jininta sbd batajin zata iya daukan ace mahaifiyar data AZIZ LIMBA itace a hannun Jannah tana riqo tamkar uwar data haifeta,

Kenan ko anan Jannah ta sake shan gabanta sbd zata sake samun AZIZ ko akan hakan ne,
Ita kuma fa?
Wa ta kama? Uwar da bata haifesaba Ashe ta kama wadda ta gama lalata mata komaiba itama a yanzu ta kanta takeyi.

Fitowan doctors ce ta saka kowa miqewa tsaye suna kallansu da dukkanin hankalinsu da nutsuwarsu,

"Bata cikin kowane irin mummunan hali yanzu zata farfado kowane lokaci inshallah so sai ta farfado zamu iya qarasa dubata da wasu aune aunen"

Shiru dukkaninsu sukai kafin Dad cikin damuwa yace

"Hope dai ba konuwa a jikinta koina"

Numfashi Dr ya sauke Yana kallan Dad din yace

"Eh babu a iya dai inda muka duba so banajin akwai konuwa koina inshallah"

Ajiyan zuciya suka sauke dukkaninsu palon Banda Mama data bar palon idanuwanta na cikowa da hawayen tsananin baqin ciki.

Dad ne da Jannah kai tsaye suka nufi dakin da Umman take sedai kafin su isa AZIZ ne yafara isa cikin dakin Yana zubawa fuskanta idanuwansa da har lokacin suke kasa gasgata itace a gabansa har cikin gidansa.

Zaunawa yayi gefenta tareda Dora hannunsa ahankali kan nata zaiyi magana su Ammar da Maheer suka shigo Dad kuma ahankali ya janye hannunta daga na AZIZ din Yana riqewa cikeda kulawa ya riqe cikin nasa Yana qin dagowa ya kalli AZIZ din sbd ko fuskansa baya son kalla kaman yanda su Maheer ma babu wanda ya kallesa.

Jannah ce ta saci kallansa cikeda fargaba taga ya dago jajayen idanuwansa ya zubawa Dad cikeda mamaki da wani irin dacin daya taso masa ya maida kallansa kan su Ammar yaga sun dauke kai suna sake tsananta hade fuska cikeda baqin cikin kasancewansu guri daya dashi suna shaqar iskan daki daya.

Hadiye radadi da bacin ransa yayi Yana kokarin kallansu da fuskan rahama ya miqe tsaye kai tsaye y zare hannun mahaifiyarsa daga cikin na dad din ya kallesa cikin ajiye komai yace

"Bansan tayaya mahaifiyar AZIZ LIMBA ta zama Ummah a zuriar Zaadens ba,
Bansan meyake faruwa ba anan Amma dai nasan duk duniya mahaifiyar data haifeni daya ce kuma itace Nan a gabana Wanda babu Wanda zai iya sauya hakan kaman yanda duk duniya babu Wanda ya isa ya sake rabani da ita idan ba Allah ba dan haka inaga abinda kaima kakeyi din haramun ne ga mahaifiyata sbd.......

Ammar ne cikin tsananin quncin dake cin zuciyarsa y katsesa da cewa

"Kana tinanin kai tsaye zamu yadda da ka Santa ne kafin ma a yadda da ita din mahaifiya ce a gareka??

Ba kaine ka fara ikirarin ka santa ba mahaifiyarka ce ta fara yi mana barazana da dukiya harma da rayuwar dan uwanmu akan mu bata ita tasan Yan uwant, ohh nama manta kudi tace mu fada zata siye mana Umman ta rabamu da qaya hkaa ta fada,
Kai kuma yanzu sai ka fada mana nawa ne naka farashin da zaka bayar akan siyanta kokuma kaima rayuwar Saleem din zaka dauka sbd ka qarasa gamawa damu??

AZIZ da idanuwansa sukai mummunan ja yana sanqarewa a tsaye da jin mummunan abinda Kansa yake kasa dauka bare fahimta.

Maheer ne ya karbe zancen da cewa

"Koma menene abu daya ne da zaka fara Sani anan shine Ummah tamu ce halak malak sbd matar mahaifinmu ce kuma uwa a Zaadens dan haka kasan abinda zai fito bakinka....

Cikin wata irin mahaukaciyar Muryan da baitaba Sanin Yana da ita ba ya daga hannu dukkanin jikinsa na rawa zai saukewa Maheer wani lafiyayyan Mari Dad ya riqe hannunsa tareda tsayawa gabansa ya kallesa yace

"AZIZ LIMBA ka koyi riqe fushinka sbd kada mu bayyana maka namu fushin abin zeyi muni dan haka gwara mu tsya a iya qiyayyar datake cikin kowannenmu a yanzu.....

Da wani irin tsananin fushin maganganun Ammar na farko dake kashesa yake jin saukan maganganunsu da bama yanda ko daya zai yiyu sbd Mama bazata taba gani ko sanin fatima na kusa dashi ba ta kasa fada dan abune da har abada bazai yiyuba,

Sai kuma maganar aure da akeyi na cewan Ummansa Matar wani ce ba waninma Dzad Wanda a tasa zuciyan be San matsayinsu ba a nasu Bangaren kuma ya San tsana ce zallah mara sirki,

Wayene ma ya isa yace masa ya auri mahaifiyarsa a cikin yanayi na ciwon rashin hankali?

Me suke nufi da wai Ummansa Matar Zaadens ce?
Tayaya ma hakan zata faru?
Bama abu ne me yiyuwaba dan kuwa yasan ba saukowa zasuyiba kaman yanda shima a yanzu baima karba aurenba bare se yaji Wanda ya bada ikon yin hakan.
#MAMUH
#LIMZADS

07019691719*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 40

*_SHOP WITH ME BY RANO_*
08030811300
Kina neman in da zaki samun kayan yara classy kaya na yan gayu at a very affordable price? Ko kina son fara kasuwancin kayan yara amma baki da jarin da zaki saro kayan? Nesa ta zo kusa, kiyi joining community din nan muna saka kaya masu kyau available da inganci a farashi me sauki da zaki dauka ki tallata har ki samu naki kema.
Burinmu shine kowacce mace ta samu sanaar da zata dogara da kanta.


************
Jajayen idanuwansa ya dago ya saukesu akan Dzad Yana masa wani irin kallan fushi Yana kasa riqe dukkanin abinda yake ransa dayake riqewa sbd Jannah akansu Amma sun wuce limit na yanda zai iya riqe kansa sbd Ummah Fatima ta kere kowace irin darajar rayuwarsa ya bude baki Yana kallansu daya bayan daya da tsananin fushi kafin ya tsaida idonsa akan Dzad da yake ganin shine ma kadai yakai ya iya magana dashi yace

"Anan,a gabana, a cikin gidana a cikin kunnuwana da gaban idanuwana Mahaifiyar LIMBA ce ko Fatima sbd maganar Aure da tarkacen da yake cikinsa babu Wanda ya isa duk duniya ya tsaya gaban idanuwana yace mun kai tsaye shi mijin mahaifiyata ne Wadda batada lafiya hankali batareda na masa mummunan daurin da seya rasa nasa hankalin ba sbd girman laifin hakan,

Kallan Maheer yayi yace

"Kuna tinanin kunada mahaukata ne?
Mahaukacin ku yanada license na zama cikakken mahaukacin gasken?
Idan akwai cikakken daya isa ya rabani da mahaifiyata zan gansa ko shi waye"

Shan gabansa Maheer yayi Shima cikin tsananin fushin da bacin rai a bayyane yace

"Wannan kuma ba kaine zakai deciding ba Umman ce da kanta idan ta farka zata tabbatarda ita waye a gurin kowa daga Nan ne zakasan kai din ba kowa bane face AZIZ LIMBA dan kuwa ba Umman kadai ba ko Jannah ka saka kalla wlh nayi maka alkawarin ganin cikakkiyar haukar da kake ambatar Zaadens din nada sbd har abada Jannah ta gama dakai babu abinda zata sake yi da Wanda yayi sanadin rasuwar mahaifiyarta da baqin cikin ahalinta tareda salwantar da dan uwanta.."

Lumshe idanuwa AZIZ yayi ahankali Yana controlling da hadiye tsananin fushi da masifar dake quna cikin jininsa ya bude idanuwansa akan Jannah ahankali Wadda idanuwanta sukai jajir wani irin daci da ciwo ke cin kirjinta akan tashin hankalin AZIZ LIMBA da familynta da batasan yaya zataiwa kowannensu ba.

Magana yaso fada musu wadda har abada bazasu dena jin zafinta ba sbd idan ana maganar wani yayi sanadin rasuwar wani sunkai karshen marasa kunya da har bakinsu yake iya furta hakan sbd abu daya dashi kansa daya Sani shine bai dauki fansar daya kamata akansu ba sbd Mummunan son 'yarsu daya shiga gabansa ya dakatar da komai ya hanasa ganin sun karbi hukuncin daya kamata Wanda shine hukuncin kisa dan koda kowa bai karba hukuncin kisa ba Wanda shine asalin hukuncinsu to Ammar da Dzad zasu karba Amma ya hana barin hakan ta hanyar zabar musu hukuncin dayafi kowane sauki dan kawai kada ya dawwamar mata da baqin cikin rashinsu a rayuwarta,

A yanda sukaiwa Ummitah kisan gilla ko me gadin gidansu akaiwa wannan kisan ya tabbatarda wani labarin ne daban bare ace daya daga cikinsu ne Amma sunada bakin fada masa magana.

Numfashi ya sauke me zafin gaske kafin ya juya ya fice daga dakin dan zai iya kasa riqe zafi da tsanarsu shima daya danne yana kokarin gogewa tsawon shekarun nan da kuma bayyanar mahaifiyarsa a hannunsu Wadda zai iya musu komai akan hakan sbd sun basa sabuwar rayuwar da bai taba tsammani ba Amma kuma yaga alamar bama zasu taba samun fuskantar juna bada wannan fushin da qiyayyar ba sbd Shima a nasa bangaren abinda suke kokarin zuwa dashi bazai taba yadda ba dan Yama fisu jin duk abinda suke ji dannewa yakeyi Amma akan mahaifiyarsa gwara suyi fito na fiton.

Yana ficewa daga dakin Dzad ma ya fito haka dukkaninsu aka bar Jannah kawai Wadda ta rasa tinanin yi sbd kanta dayake toshewa.

Yana fitowa kai tsaye palon su Mama ya nufa Falaq da fiddausi na bayansa koda ya isa Nicky na tsaye tana bubbuga kanta dake neman bugawa,

Mama dake zaune idanuwanta jajir tana ganinsa ta miqe tsaye ahankali zuciyarta na neman fadowa sbd bugawa ta zubawa fuskansa da babu rahama ko kadan tana kallansa lokacin Sayd y shigo palon shima fuskansa jajir sbd tashin hankalin dayake qin qarewa a gidan.

Wani mugun 'daci da zafi tamkar na wuta AZIZ ya hadiye a maqoshinsa daya bushe ahankali kafin ya bude idanuwansa yaqi kallan Mama sbd maganganun Ammar Zad akan Maman dake yawo cikin Kansa suna neman haukatasa da bakinta yakeson ji ta fada.

Rawa hannuwansa ke yi ya bude baki a Karan farko daya hadesu gabaki daya gidan har Mama dayake banbanta girmanta akan kowa,

"Waye da waye ya San da Ummah Fatima na gidan nan?
Waye da waye ya taba ganinta?
Waye kuma ya taba magana da ita?

Shiru dukkaninsu sukai tsit kowa jikinsa na daukar rawan fargaba sbd yanda yake din d yanda yayi tambayar kai tsaye kowannensu yasan ba AZIZ LIMBA din bane wannan tsananin fushi da bacin ransa a bayyane yake da zai iya aikata komai akan duk wani me laifi lokacin.

Falaq ce da duk take cikin tsananin rudanin kasa gane gaskiar waye Mama waye Fatima a gurin Daddynta da Ummitah ta matso gaba ahankali tana kallansa tace

"Daddy ina ganinta duk naje gurin Jan Amma kafin na fara zuwa gurin Jan ban taba ganinta ba kuma haryanxu bantaba jin maganarta ba ni"

Fiddausi ma cikin sanyi daga inda take tsaye bayan Sayd ta bude baki tace

"Ina ganinta idan naje gurin Jan Amma na fara ganinta ne a lokacinda ta fara bugawa Mama kai.....

Qafewa yawu da numfashin Mama yayi ta rintse idanuwanta tana jin jikinta na mutuwa gefe daya tana kallan AZIZ da sauri wanda rufe idanuwansa ahankali ya budesu akan Nicky.

Nicky da gabaki daya ta rude da tashin hankali sbd bata taba ganin AZIZ a cikin wannan yanayin nasa ba a rikice tace

"Mama ce tafara zuwa gurinta acan nasan Ummansu Jannah ce"

Bai juyo ya kalli Maman ba saida ya tattare duka fushinsa ya saka a maqoshi kafin ya ambaceta Yana qin kallanta har lokacin sbd gudun yanda zuciyarsa zata karbi zancen da zai fito bakinta akan idanuwansa sbd zuciyarsa ta kasa yadda da har abada Mama zata ga fatimanta ta kasa bayyana masa bayan yasan yanda suke kaunar junansu.

Shiru Mama tayi tana kasa magana idanuwanta sunyi jajir sun kafe da tashin hankalin da bata taba saka ran zai risketa ba sbd tin a yanzu tana hango wata irin zazzafar tsanar da AZIZ zai mata Wanda bazata taba iya daukan hakan ba sbd ta San bazai taba iya cigaba da zama da ita ba zai raba kansa da ita ne a lokacinda take ganin babu wanda ya isa yaci amfaninsa idan ba ita ba sbd itace tai dawainiya dashi ta shanye baqin cikin da duk ya shiga da qunci.

Shirun mama ya saka jikinsa tsananta rawar daya saka kowa ja da baya suna sauke kai ya juyo ya kalli Maman da idanuwansa da babu kyan gani ya bude baki yana kokarin riqe girmanta dake idonsa har lokacin da da'a yace

"Mama kinsan da Fatima na Nan gidan tareda Zaadens?

Kinsan da Ummanah na 4&4 tin lokacinda kika dawo tsawon watannnin Nan?

Kinje gurinta?
Kinyi magana da ita?
Kinyi magana da Zaadens akanta?

Mama ban yadda da maganarsu data kowa ba taki kawai nakeson ji sbd kece kika San girma da mahimmacin Umma Fatima a rayuwata,
Kece kadai kikasan waye Fatima a duka fadin duniyar AZIZ LIMBA"

Bakinta na wata irin rawa hakama hannuwanta da kafafunta ta bude baki tana kallansa idanuwanta jajir tana kasa musawa sbd tsanarta da zata wuce misali da gyara a zuciyarsa tace

"Eh AZIZ nasan tana Nan Amma wallahi inason......

Wata dafar data saka console mirror din dake gefensa yayi Wanda ta sakasa fashewa da karfin gaske Yana yanka hannunsa sosai yayiwa mirron jikinsa na wata irin jijjigar data saka Sayd da Falaq matsowa da sauri zasu riqesa ya daga musu hannu jikinsa na tsananta rawa koina.

Mama na ganin hakan ta matsosa kafafunta na sake rawa idanuwanta n sake rinewa da rikicewa tace

"AZIZ walh da farko bangane ba inason tabbatarwa ne kafin na sanar maka sai ga....

Sarewa kafafunsa sukai Yana zubewa cikin glass din gurin da gwiwansu idanuwansa na rintsewa hawaye masu tsananin zafi na cikowa idanuwansa sbd bayan mahaifiyarsa data haifesa Mama itace uwarsa daya san haihuwansa ne kadai bataiba Amma zata iya bda ranta dan nemo masa duk abinda tasan shine rayuwarsa wato mahaifiyarsa,

Amma a Karan farko Mama ta basa shock din dayafi na Zaadens sbd su daman yasan zasu iya komai akan son kai da zuciya... itace ta farko data fara boye masa ganin Fatima....

Dafe kirjinsa yayi sbd wani irin azabar dayake jin Yana kasa dauka ya rintse idanuwansa Yana kasa magana sbd bazai iya yanke hukuncin Mama cikin fushi ba.

Falaq da sauri ta qarasa gurinsa tana fadawa jikinsa tana fasa kuka tana kokarin tadasa sbd hannunsa dake jini sosai tana Kiran sunansa da karfi.

Nicky ma gabaki daya tsoro ya rufeta jikinta wani irin rawa yakeyi tayi baya ta kasa matsowa sbd tsoron AZIZ din.

Maman ma hawayen baqin ciki da dacin zuciya ne suka fara gangaro mata tana son matsawa Amma fushin dake tattaredashi ya hanata hakan sbd kada ta tinzirasa aikata abinda baiyi niya ba akanta.

Sayd ne ya isa garesa Shima zai kamasa AZIZ din ya miqe Yana sake dafe kirjinsa yabar gurin baya ganin gabansa ya nufi stairs yana dakatar da kowa daga binsa.

Kallansa sukeyi cikeda kulawa da faduwan gaban kada ya fado sbd yanda baya gani harya haye saman ya shige palonsa ya rufe kofar.

Yana shiga suka fara jin qarar fashewan kaya da karfin gaske tareda glasses.

Da sauri Falaq ta yunqura zata bisa saman Sayd ya riqeta yana rungumeta ta fasa kuka tana cewa

"Daddy na zai sake illata Kansa,
Yana cikin qunci da damuwa,
Banason inga Daddyna a cikin irin wannan yanayin Ya Allah ka basa lafiya ka kawo nutsuwa da kwanciyar hankali a rayuwarsa"

Mama zubewa tayi qasa tana dafe kanta cikin hawaye da baqin ciki halin data saka AZIZ din da kuma tsananin tsanar Zaadens da Nicky dama duk Wanda yake rayuwar AZIZ din bayan ita.

Zaadens da duk abinda yake faruwa suna ji shiru sukai suma zuciyoyinsu a tafashe sbd tana sake tabbata dai Umma Fatima mahaifiyar AZIZ LIMBA ce,

Babu Wanda yayi farin ciki ko misqala zarratin da hakan,
Basa kaunar abinda duk zai sake hadasu da LIMBA,
Basa kaunarsa basa kaunar zuriarsa basa kaunar duk wani ma me kaunarsa tayaya yanzu kwatsam zaa ce Ummah itace uwar data haifesa?

Babu ruwansu da hakan tinda dai watsi yayi da ita suka samu suka tattala suka kaunata suka bata sunansu dan haka ba gudu ba ja da baya bazasu taba basa ita ba karshenta ma tana tashi tattarawa zasuyi su tafiyarsu da ita idan ma Yana ikirarin mahaifiyarsa ce to ai mijinta a yanzu yafisa iko da ita zasu nuna masa power da igiyoyin aure yake dashi ya gani ganin idonsa.
#MAMUH
#ZAADENS
#LIMBAS

07019691719*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 41

Jannah da sautin komai itama yake sauka a kunnenta rufe idanuwanta tayi tana jin zuciyarta kaman zata dena bugawa sbd tausayin AZIZ da jin ciwonsa cikin ranta,

Yana tsananin buqatanta ayanzu dayake cikin mummunan halin ciwonsa da duk saiya raunana Kansa rauni me Muni ma kila batareda kowa

Please Login or Register in order to submit comment