Reading KALBIM BOOK 2 BY MAMUHGEE Chapter 17 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

me karfi da kudirin daukan fansar abinda ya sameta ta warke dan haka kai tsaye bayan warkewanta ta kalli Mama tace

"Mama Zaadens sun yiwa rayuwata illan da bazan taba iya yafe musu ba,
Mama wallahi wannan Karan sai Zaadens sun biya abinda sukayi?
Sai na tabbatarda Zaadens ko da kafafunsu koda gawarsu sai sun bar rayuwar gidan nan kafin dawowan AZIZ sbd zan rasa kaina idan na sake ganin Zaadens da AZIZ,
Mama ki....

Cikin gajiya da nata baqin cikin dayake cin ranta da rayuwar da gabaki daya ta juye ta koma batada nutsuwa duk ta haukace akan Zaadens da AZIZ dan haka itama ta gaji amma kuma tafi gajiya da masifun da koyaushe tsarin Nicky yake janyo musu dan ta kusa rasa sashen jikinta akan Nicky tace

"Aisha na gaji da tsarinki da haryanzu babu abinda yake bani sai ciwon zuciya da neman rasa kaina a gaban AZIZ,
Tin yaushe zamu zauna ace mutanen Nan sun gagaremu?
Ni na gaji,abu daya na sani ko a rayen ko a macen nidai su bar gidan nan kafin dawowan AZIZ,

Idan zaki iya mun hakan ta kowace hanya na Miki alkawarin wlh Yana dawowa bazai kwana ba sai an daura aurenki dashi koda a cikin dare ne.

Da sauri Nicky ta juyo idanuwanta jajir sbd kanta dake wata irin rawa tanajin wuta na ci a cikinsa tace

"Mama wlh tallahi sai sun bar duniyama gabaki daya ba 4&4 ba"

Mama da idonta ya rufe tace

"Indai zasu bar AZIZ koma lahirar ne su tafi."

Nicky da maganar aurenta da AZIZ ta birkitata gabaki daya ficewa tayi tana buga kanta da juyasa sbd yanda yake wani Kara Yana mata motsi.

Numfashi me zafi Mama ta sauke tana bin bayan Nicky din da jajayen idanuwanta sbd Nicky zata kawar mata da matsalar rayuwarta a yanzu datafi komai zamar mata babbar masifar rayuwa wato Haduwan AZIZ da Fatima.

*****Falaq ako yaushe yanzu tana gurin Jannah bacci ne kadai se wani abin ke maidata ita da fiddausi sun tare acan duk da basa samun fuska ko kadan a gurin Zaadens sbd tsanar da kiyyyar a bayyane take sosai.

Itama Falaq bata damu dasu din ba Jannah kawai takeso a cikinsu dan haka ita kadai tadamu da ita.

Ammar neman zarewa yakeyi sbd dawowan Falaq rayuwar Jannah zai iya lalata masa komai kamar a baya dan haka ya tsananta fidda tsanar LIMBAs a fili wadda ta qar bayyanarda tsanar da kowa kewa juna a tsakaninsu.

Ayau tin safe kowannensu ke parking a bisa umarnin Dad dan haka zaune take a dakinsu ta kasa hada kayanta data fidda gabaki daya daga wardrobe.

Fatma bata dakin ita kadaice shiru zuciyarta tayi wani irin nauyi da sanyi.

Ummah ce ta shigo dakin ahankali cikin tsananin sanyi itama ta qaraso gurin Jannah din ta zaune gefenta a sanyaye idanuwanta jajir.

Qurawa Jannah idanuwa tayi tsawon mintina kafin ta ciro hannuwanta dake tsananin rawa zata dafa Jannah din sai kuma ta fasa ta rintse idanuwanta ta bude ahankali ta bude baki da wani sautin daya saka Jannah kallanta da nata jajayen idanuwan.

"ABDULAZIZ AYOUBA LIMBA?

Rintse idanuwa Jannah tayi ta budesu akan Umman cikin tsananin mamaki da shock din cikakken sunansa a bakinta sedai tinanin komai baizo kanta sbd mutuwar da jikinta yayi da tsananin ciwon abinda ake shirin aikatawa na rabasa da abinda yakeso idan aka tafi da ita.

Hawayene suka ciko idanuwan Umman ya sake maimaita sunan Wanda ya saka Jannah rungumeta tana gangaro da hawaye masu tsananin zafi da wani irin raunin zuciya tace

"Ummah AZIZ LIMBA shine rayuwata,
Bazan iya rayuwa babu sa ba,
Bazan iya dena sonsa ba har abada,
Zan dena numfashi idan na rasasa,
Zuciyar Ummitah zata mutu kaman yanda ta Jannah ta mutu da dadewa idan aka rabata da AZIZ,

AZIZ yana tsananin buqata,
Baida kowa,
Ya rasa mahaifiyarsa Fatima tin yana qaraminsa shi da Ummitah,

AZIZ yana cikin quncin rayuwar da warakarsa mahaifiyarsa ce,

Babu mahaifiyarsa babu Ummitah tayaya zan barsa nima?

Zamewa tayi ta kwanta jikin Umman ciwon kirjinta na tsananta da quncin dayake ciketa ta rintse idanuwanta hawaye masu dumi suna sake gangarowa muryanta tayi sanyi tace

"Ummah kaddara ta saka ahalina da AZIZ LIMBA zama maqiyan juna tin kafin mu hadu sbd kaddarar zuciyar Ummitah dake cikin nawa kirjin,

Rasuwar Ummitah ta sauya duniyar AZIZ LIMBA da Zaadens gabaki dayanmu sbd haryanxu muna cikin tsananin Dana Sani da baqin cikin abinda ya faru,

Bantaba Sanin an daukan ran wani dan rayani ba dana dade da karban kaddarata na zabi mutuwata da AZIZ bai shiga qunci da ciwon rasa Ummitansa ba,

Da ayau bamu shiga quncin daukan ran da ahalina sukai ba,

Sun tuba sun nema yafiyar,sunata qara tubarwa Allah,
Ran mahaifiyata ya tafi a gurin girban abinda ya faru,
Ran daddy Mahmoud ma ya tafi,
Mun rasa Saleem,
Mun rasa Anny,
Mun rasa mummy duka akan wannan mummunan kaddarar data hadamu Amma haryanxu gabar tana qin qarewa,

Ummah inason AZIZ LIMBA inason Ahalina dan haka bansan yaya zanyiba..

Kuka takeson fasawa yaqi zuwa sbd ciwon komai dayake dawo mata ta ringa fayyace komai da irin rayuwar datai a hannun AZIZ da rayuwar da suka fada da ahalinta tareda halinda suka shiga na tozarci da rasa komai hatta suna da mutuncinsu ayau sun qare a zero Amma quncin ya kasa qarewa.


Ummah da jikinta ke wata irin jijjiga idanuwanta jajir wani irin gunjin kukan daya girgiza Jannah ta fasa me karfin gaske tana dafe kirjinta dayake mata wani ciwon data ke jin kaman ranta zai fita sbd azabar radadi.

Tashi Jannah tayi jikinta da sauri tareda kallanta Amma ganin yanda jikinta ke tsananin rawa tana kukan Wanda yake daga ja na ciwon rashi ne da baqin cikin.

Rungumeta Jannah tayi da sauri tana fasa kukan tausayinta da kaunarta tana cewa

"Ummah ki dena kuka irin wannan bazamu iya ganinki a wannan halin ba shiyasa zamu tafi dan neman lafiyarki,
Nima Ummah na zabi tafiya nabar AZIZ din sbd neman lafiyarki indai zaki dena jin quncin dayake tokare da kirjinki...

Kuka takeyi sosai wanda Umman ma kukan takeyi.

Fatma ce data shigo taga mugun halinda suke ciki taje ta sanar dasu Dad.

Su Dad na zuwa kowannensu idanuwansa sukai jajir Dad ya kamo Umman tareda rungumeta a jikinsa Yana kasa cewa komai sedai tsananin damuwarsa da dacin dayake ransa a bayyane yake.

Shiru sukai dukkaninsu cikin dacin zuciya suna sauraron kukan Umman wanda ta jima tana yinsa kafin ta dena ta kasa dagowa ta kalli kowannensu.

Jannah ce takaita toilet tayo wanka Maheer ya bata magani Ammar ya bata ruwa tasha ta kwanta Dad ya rufeta kafin dukkaninsu suka fice.

Wunin sukuku sukai cikeda damuwa da dacin zuciya sbd yanayin Umman wadda duk ta kasa cewa komai sedai binsu da ido a duk hidimar da sukeyi da ita.
#MAMUH
07019691719*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 37

*_SHOP WITH ME BY RANO_*
08030811300
Kina neman in da zaki samun kayan yara classy kaya na yan gayu at a very affordable price? Ko kina son fara kasuwancin kayan yara amma baki da jarin da zaki saro kayan? Nesa ta zo kusa, kiyi joining community din nan muna saka kaya masu kyau available da inganci a farashi me sauki da zaki dauka ki tallata har ki samu naki kema.
Burinmu shine kowacce mace ta samu sanaar da zata dogara da kanta.


**********
Washe gari Dad ya samu Mama yayi magana da ita akan koma yayane suna son tafiya subar gidan.

Da farin cikin zancen ta kallesa tace su shirya tayi alkawarin komai tsurin tsaron AZIZ zasu tafi a gobe sa sassafe kafin kowa ya tashi.

Koda ya taho kai tsaye ya sanar da kowa dan haka suka qarasa shiryawa.

Mama shugaban securities na gidan gabaki daya ta kira da daddare har palon qasa ta sauko tareda kallansa bata son batawa kanta lokaci ta kallesa ta sanar dashi Zaadens kawai takeso ya bari su tafiyarsu kafin dawowan AZIZ,idan ya dawo ztsan abinda zata fada masa Wanda bazaiga laifinsa ba.

Kudi ta ciro bundle goma na Yan 1k ta ajiye masa tana kallansa.

numfashi ya sauke me nauyi shima bai tsaya bata lokaci ba yace gate zai zama a bude goben idan suka tashi tafiya.


Murmushi da ajiyan zuciya me karfi Mama ta sake tana cewa ya tafi zataji da sauran.

Yana fita Nicky dake labe tanajinsu ta sauke numfashi zuciyarta na tafarfasa sbd bata dauka Mama zata bata Mata shiri ba,
Ita Sam batason Zaadens su tafi dan su rayu sbd Jannah zata iya dawowa rayuwar AZIZ hakama Garba har abada zaici gaba da Tina yanda ya sameta dan haka ita sam batada niyar subar gidan a raye dan haka bama kowa ze kai gobenba bare kai labari.

Da daddare karfe 9 na dare Mama ta iso bangaren Zaadens din gabaki dayansu suna zaune.

Abinci Dad ke kokarin ganin ummah taci ko kadan ne Amma kwata kwata ta kasa zazzabi ne sosai a tattare da ita kuma har lokacin taqi cewa komai.

Ammar dake gefen Umman daya Yana mata fita ahankali ko dagowa beyiba ya kalli Maman sabanin kowa daya dago ya kalleta hadda ummah data dago jajayen idanuwanta ahankali ta kafeta dasu.


Mama bata batawa kanta lokaci ba ta jefa musu kudin dayake hannunta a gabansu ta kalli Fatima cikin idanuwa kafin tace

"Gobe karfe 7 na safe kubar 4&4 zaa bude muku gate wannan kudin kuma ku tabbatarda kunyi nisan da AZIZ bazai taba ganinku ba har abada"

Tana fadar hakan ta juya tabar gurin babu Wanda ya kalli kudinta bare tankawa

Harta bace ummah bata iya dauke idanuwanta akanta ba kafin ta rufe tana sunkuyar da kanta.

Har karfe 10 suna waje kafin suka tattara kowa ya shige.

Ummah Dad ne ya kama hannunta har dakinsa suka shige.

Itama Jannah suna shigewa wanka ta fada tayi da brush tana fitowa ta zauna ta shafa turare kadan kafin ya saka doguwar rigar bacci me tsantsi ta nufi gadonta ta hau.

Cikin bacci taji fatma na tada ita batareda tayi nisa sosai a baccin ba.

Bude idanuwanta tayi ahankali ta kalli Fatman.

Janyewa Fatma tayi tana kasa cewa komai dan Jannah taga waye a bakin kofar shigowa dakin daga waje.

Kaman a mafarki ta gansa tsaye sanye da ash Armanis da waya da jacket a hannunsa da alamar daga mota nan ya wuto direct.

Farin cikin daya cike zuciyarta ne ya sakata saukowa gadon da sauri ta nufesa da wani irin gudu tana isa ya dauketa sama Yana rungumeta itama tana qanqamesa farin ciki fal zuciyarta.

Fatma ma farin cikine ya ciketa ta sunkuyar da kai.

Kallan fatma yayi batareda ya sauke Jannan ba ya furta "thank you" ahankali cikin kasala yana juyawa da ita ko takarmi ko wani abin rufe jikin babu a tareda ita.

Suna barin gurin baifi da minta biyar ba Ummah ta dawo dakin ta kwanta a gadon Jannah tana duqunqunewa.

Suna isa bai ajiyeta ba sai tsakiyar bedroom dinsa Yana kallan fuskanta ya kama bakinta ya sakar mata wani zafafan kiss kafin ya rungumeta yana cewa

"Alhmdlh ya Allah"

Murmushi takeyi tana sake qanqamesa itama kafin ta dago ta kallesa tace

"Daman yau zaka dawo?
Amma kowa besan yau zaka dawo ba?

Fuskansa ya saka a wuyanta ya shaqi qamshinta yana gangarowa har kirjinta Yana shakarta kafin ya bude baki yace

"Yes sedai sa safe su ganni bayan kin gama Dani"

Murmushi tayi tana kokarin janyewa sbd yanda shinshinarsa ke kashe mata jiki hannuwansa na yawo jikinta kaman cakulkuli ta bude baki cikin son kwacewa da dariya tace

"AZIZ"

Tana rufe baki ya sake maida bakinsa cikin nata ya tsotseta da kyau kafin ya saketa Yana binta da kallo idanuwansa a kasalance.

Daqyar ya saketa ya wuce toilet ita kuma ta sauka kaman barauniya taje kitchen ta hado masa tea me karfi da short bread biscuits na shan tea tareda fruits ta dawo.

Taba barin kitchen karfe daya tana bugawa daidai lokacin Nicky ita kuma ta fito dauke da abinda yake hannunta tabi ta kitchen din ta fice zuwa bangarensu.

Motarta ta nufa ta bude ta dauko qaton galon na diesel da ashana ta rufe motar ta nufi bangaren Zaadens.

Ita kuma Jannah tana dawowan ya fito wanka kenan.

Ajiye tray din hannunta tayi kafin ta motsa yayi Sama da ita tace

"AZI....bata qarasa ba suka fada gadon taba jikinsa ya zagayeta da hannuwansa sbd shine a qasa itace a samansa.

Zubawa juna ido sukai Yana zagaye bayanta da hannuwansa Yana Shafa lafiyayyun cinyoyinta da suka bayyana dan rigarta data janye.

Ahankali ta bude baki zata kira sunansa cikin kasala yace

"Pls don't,youre killing me slowly da yanda kika fadan"

Murmushi tayi tana yin qasa da kanta ya dago fuskanta da hannunsa daya yai kissing hancinta Yana sake shakar qamshinta kafin ya saka kansa wuyanta yai kissing fatar wuyan.

Saukan lips dinsa a fatar wuyan nata ya sakata sake numfashi me dumi ya sauka akan fuskansa ya lumshe idanuwansa tsigar jikinsa na tashi gabaki daya.

Ayau sosai yake jinta ta yanda bazai iya tsallake yau bai mallekta gabaki dayanta ta zama cikakkiyar macen AZIZ LIMBA dan haka juyar da ita yayi ta dawo qasan ya koma samanta Yana zare rigar jikinta gabaki daya daga jikinta Yana zubawa farar lafiyayyan fatar cikinta ido zuwa kirjinta.


A daidai wannan lokacin ne karfe daya da hamshi da biyar ta buga,

Sama sama kunnuwan Jannah suka fara jiyo mata ihun Madam Sisi da hayaniyar iska kaman na hadari.

Dakatar dashi tayi tana ambatar sunansa ahankali cikin mutuwar jikin halin da suke ciki.

Idanuwansa ne suka sauka akan hasken dayake tashi saka ta balcony dinsa kaman na wuta.

Da mamaki ya miqe Yana saukowa gadon kafin ya isa window wutar tayi wani irin karfin gaske.

Hayaniyar mutanen dake gidan da securities ne yake tashi ahankali wanda sakasa qarasawa balcony din idanuwansa suka sauka akan wuta dake cin Bangaren masu aiki sosai.

Jannah wani irin mummunan mutuwar tsaye tayi idanuwanta na neman makancewa

Shikuwa da sauri ya saka kaya jikinsa ya dauko kayansa ya saka mata suka fito bata ko ganin gabanta wani irin gudun tashin hankali takeyi tana ambatar sunan Dad dinta da Ummah.

Ko da suka isa Dad dasu Maheer na fitowa cikin wutar a tsananin hali suna tarin azaba.

Kowa ya fito hankali tashe da tsoro,

Mama Nicky ta kalla wadda kai tsaye ta gane itace tayi aikin

Bata damuba kawai dai fatarta aikin kada ya zama na banza a garesu,

Falaq da fiddausi ma saurin taresu Sayd yayi duka masu aiki kowa ya fito hankali tashe.

Cikin tsananin hali Dad ya kalli Jannah dake tsananin rawar jiki yace

"Ina ummanku?

Shi ta kalla da sauri tana girgiza kai a rikice,

Maheer daya shiga firgici cikin daga mury yace

"Ina Umman take?

Ammar ne yahau ture kowa da sauri Yana dubata bai ganta a wajen ba baisan lokacinda yayi cikin wutar ba da karfi Yana kwala Kiran sunan Umman.

Securities ne sukai saurin riqesa

Jannah ta miqe da gudu tana dosar dakinsu tana kwala sunan Umman cikin tsananin kukan gaske da tashin hankali.

Riqeta AZIZ yayi yana cewa a riqe Maheer da Dad da sukai cikin wutar suma.

Damben gaske aka ringa yi dasu suna kwacewa amma anki sakinsu

Mama kuwa jin takeyi kaman ta qarawa wutar karfi da gudu takeji kowama ya huta.

Ammar ne ya sakarwa security daya mugun noshi ya kwace ya fada cikin wutar Dad na bin bayansa.

Nan Jannah ta sake haukacewa tana Kiran sunan Dad dinta da Umman kaman ranta zai fita.

Buga kofar su Dad suka hau yi da karfi Wadda ta bude da qyar bayan duk sun kona hannuwansu.

Suna shiga ummah da idanuwanta suka kusa rufewa akan idonta Dad ya sako kai yana nufota da sauri Ammar kuwa daukanta yayi gabaki dayanta suna kokarin fitowa garba ya fado ya dauki fatma Shima.

Suna fitowa Maheer ya kwace da karfe Yana nufosu ya karbi Umman sbd Ammar da dad din dake neman xubewa a qasa.

Yana karbanta Jannah dake ihun Kiran sunanta ya nufa ta fizgo da gudu itama tana zubewa gaban Ummar da Maheer ya kwantar a qasa gaban ABDULAZIZ AY LIMBA Wanda yayi mutuwar tsaye idanuwansa kafe akan fuskar dake gabansa kwance.
#MAMUH
07019691719*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 38

*_SHOP WITH ME BY RANO_*
08030811300
Kina neman in da zaki samun kayan yara classy kaya na yan gayu at a very affordable price? Ko kina son fara kasuwancin kayan yara amma baki da jarin da zaki saro kayan? Nesa ta zo kusa, kiyi joining community din nan muna saka kaya masu kyau available da inganci a farashi me sauki da zaki dauka ki tallata har ki samu naki kema.
Burinmu shine kowacce mace ta samu sanaar da zata dogara da kanta.

*************
Wani irin haske idanuwansa suka cike dashi jinsa na daukewa daga sautin komai saina ihun Kiran sunan da Jannah da ahalinta ke yi,

Dumm kansa yayi Yana kasa motsa ko yatsa daya daga jikinsa ya bude bakinsa ahankali cikin wani irin sauti da slow yace

"UMMAH"

Falaq ce datake isowa gurinsa da gudu tana kokarin riqesa cikeda tsoron wutar ya tureta da karfi Yana ficewa hayyacinsa gabaki daya komai na jikinsa na tsananin daukan rawa ya isa gabanta da karfin gaske yana ture Maheer tareda kowannensu ya cakumota da karfi yana kallan fuskanta cikin karfin gaske yace

"UMMAH, UMMAH FATIMA.....

Mama da gabaki daya imaninta yake akan wutar batareda tasan nafito da Umman ba jin saukar muryansa a kunnuwanta ya amabaci Fatiman ya sakata juyowa da karfin gaske a rikice gabanta na mummunan faduwan data saka jikinta daukan rawa idanuwanta na sauyawa gabaki daya.

Ture Nicky da Madam Sisi tayi da karfi daga gabanta tana nufar inda AZIZ din yake kafafunta na hardewa ta kife qasa da karfi,

Da rarrafe jikinta na rawa ta iso gurin tana zubawa fuskanta Fatima idanuwanta dake cikowa da tsananin hawaye zuciyarta na cewa

"Fatima sai da kikai nasara akaina,
Fatima saida kika bayyana gaban AZIZ,
Fatima kin kasa tafiya ki barni da AZIZ sbd nice na cancanci zama uwarsa Ni danake da cikakken hankali,
Fatima bazaki iya rabani da AZIZ ba sbd na riga na zama uwar da bazai taba iya sauyawaba...
Fatima kin lalata komai."

Nicky ce ta iso da sauri gurin Maman ta kamota Zata tayar Maman da babu karfin komai a jikinta tanajin kaman taje da gudu ta fada wutar ta kone ta huta akan yanda zata iya fuskantar AZIZ akan bayyanar Fatima gidan.

AZIZ kuwa sake dago Umman yayi gabaki dayanta da karfi yana sake ture duk Wanda ya kusantota ya sake ambatar sunanta da karfin gasken daya saka idanuwanta budewa a wahalce suka koma suka rufe tana qarasa somewa gabaki daya.

Dad ne da babu karfi sosai a jikinsa sbd zafi da hayaqin wutar daya dakesu,

Ganin irin girgiza da riqon da AZIZ yayi mata Yana tare kowa da isa gareta ya sakasa tahowa ya ture AZIZ din da karfi dan ya saketa sedai ko gezau sbd ba qaramin riqo yayi mata ba gabaki daya ya fice hayyacinsa.

Ammar ma turesa ya hau yi jin Yana kiranta da Umman da suke kiranta Wanda duk a tininsu sbd Jannah ne yake kiranta hakan,

Maheer ma banbareta daga hannunsa suka hau kokarin yi suna kasawa,

Su uku suka tarar masa suna kokarin cireta Amma hakan ya gagara,

Wasu hawaye masu tsananin zafi da gudu ne suka fara gangarowa daga idanuwansa ya dagota da karfi ya rungumeta a kirjinsa qamqam Yana fasa kuka a gaban kowa me karfi da tsananin tsima zuciya sbd kukane da duk duniya babu Wanda ya taba ji yayi,

Cikin kukan ya sake ambatar sunanta da "FATIMAN ABDULAZIZ DA UMMITAH......
UMMAH FATIMA...

Cak Jannah da duka Zaadens suka tsaya daga kokuwar da sukeyi dashi dan basu hakura ba sai ya saketa,

Fatiman daya ambata ne ta AZIZ da Ummitah ya sakasu kallan Umman da wani irin sauri da tashin hankali me tsananin gaske wadda sukasan sunanta Fatima a bakin Mama,

Dad ne da Ammar a lokaci daya suka juya gurin Mama suka kalleta wadda ta rintse idanuwanta da sukai jajir hawaye na cikowa a cikinsu.

Maheer kuwa kai tsaye fuskan Umman tasu ya zubawa idanuwa jikinsa na daukan tsananin rawa sai kawai a take kamannin AZIZ LIMBA suka ringa bayyanar masa akan fuskan Umman da basu taba tsayawa suka lura da hakan ba sbd abune da ko a mafarkin sun haukace basu taba kawosa ba.

Jannah kuwa qanqancewa idanuwanta sukai cikeda yanayin da batasan ma ya zata fassaraba ta rarrafa gurinsa da sauri ta kamo fuskansa dake cikin wuyan Umman Yana kuka sosai..

Qwace fuskansa yayi da karfi yana sake maidawa wuyan mahaifiyarsa yana jin kaman yana motsi ba daidaiba zata bace daga gabansa.

Sake riqo fuskansa Jannah tayi da sauri hawaye na bin fuskanta muryanta na rawar tashin hankali tace

"Ummanah ce....

Girgiza kai yayi da karfin gaske kaman qaramin yaro jikinsa na sake daukan rawa yanayinsa na tsananta ya sake qanqame Umman yace

"Umman AZIZ ce,
Umman data haifi ABDULAZIZ ce,
Umman data haifawa AZIZ Ummitah ce,
Ummanah ce,
Rayuwata ce ita ba Umman kowa bace bazata....

Rungume Kansa Jannah tayi tana fasa kukan ganin yanda haukansa gabaki daya ta bayyana a gaban kowa hakama Umman na tsananin buqtaan taimakon gaggawa tace

"Umman AZIZ ce,Fatiman AZIZ ce,
Ummanka ce babu Wanda zai sauya hakan amma tana buqatan taimakon gaggawa ka bari a tafi da ita AZIZ"

Yana jin hakan ya dago da sauri Yana sakin Umman daga jikinsa ya miqe jikinsa na rawa ya dauketa sukutum gabaki dayanta yana barin gurin da ita da gudun gaske Yana qwala Kiran Sayd Wanda tini ya kira likitoci kusan uku duk suna hanya gashi basuda nisa.

Gabaki daya duk Wanda yake gurin mutuwar tsaye ce ta kamasu Musamman Nicky datake jijjiga sbd a gban idonta ko yanzu aikinta ya lalace lalacewan da kila dama irin wannan zatai wuyan samu,

Bata yadda da AZIZ nada wata uwar ba bayan Mama sbd tasan dai koma wacece wannan din Mama dai itace ta haifesa dan haka kallan Maman tayi jikinta na sake rawa da jijjiga ta bude baki zatai magana Mama datake jin jininta na qonewa batasan lokacinda ta daga hannu ta sauke mata wani lafiyayyan mari ba tana mata kallan tsananin baqin cikin shigowanta rayuwarta ma gabaki daya.

A rikice Nicky da rabin hayyacinta yabar jikinta sbd kanta daya motsa ta kalli Maman zatai magana Maman ta katseta cikin mugun yanayin na tafarfasa da cewa

"D farko bansan wace kaddarar takaini karbanki ba Sedai a yanzu na San mummunan kaddara ce sbd babu alkhairi ko daya a tattare dake,
Duk abinda kika sakawa hannu saiya lalace ya zama mugun Abu,

Kinsan ayau me kikayi?
Kinsan me kika janyo da wannan aikin da kika lalata mana?
A tinaninki zaki kashe matsalolinki ne a cikin wutar da kika Cinna?
To ki Sani dukkanin manyan matsalolin da suke kwance ne kika tayar mana Wanda wutar zata cinyemu,
Babbar matsalar dataci uwar tasu Zaadens ce kika tado mana wadda a yanzu sedai kowa yayi ta Kansa dan kuwa a yanzu babu sauki ko kalilan a lamarinmu sai kuka da baqin ciki."

Nicky data kasa yadda da faduwa cikin tafasar zuciya tace

"Mama bazan taba yadda da faduwa ba akan Zaadens,
Bazan taba barin.....

A tsananin fusace da tashin hankali Mama tace

"Kin San waye Fatima?
Kinsan waye mahaukaciyar Zaadens da kike fada koyaushe?
Kina ganin yanda suke tsananin sonta take sonsu??
To itace Asalin mahaifiyar data dauki cikin AZIZ LIMBA ta kawosa duniya,
Itace macen datafi kowace mace a duniyarsa da babu kamarta kuka babu Wanda zai iya cika gurinta a ransa har abada,
Akan Fatima AZIZ zai iya fito na fito da kowa,
Akanta ne idan ba mafita muka samo ba AZIZ LIMBA ya gama zama bawan Zaadens har abada sbd Fatiman da kanta ta zama Zaadens sbd auren Dzad ne a kanta....

Baya Nicky tayi tana faduwa qasa jikinta na tsananin rawa da shiga mummunan tashin hankalin da bata saka masa rana ba.

Mama ma datake jin tana neman haukacewa juyawa tayi ko gabanta bata gani tabi bayan AZIZ da Zaadens da sukai ciki tin dazu acikin tashin hankali.

Palo AZIZ ya nufa da Umman ko gabansa baya gani kaman zai kife suna biye dashi dukkansu suma kaman zasu kife din sbd basuda wata niya ko qarama ta daga masa kafa akan Fatiman dan haka wutarsu a riqe take.

Jannah ce take kwashe pillows din kujera Ammar da baida hakuri ya fizgosu gabaki daya ya watsar dasu qasa AZIZ ya kwantar da ita Yana kasa dauke idanuwansa akanta har lokacin jikinsa rawa yakeyi sosai kansa kaman zai buga hakama ya hana kowa tabata a cikin rashin hayyacinsa dayake ciki sbd gabaki daya duk Wanda yake gurin yasan ba AZIZ LIMBA bane a gurin wani AZIZ LIMBA dinne da basu sani ba dan haka Sayd daya san meyake faruwa yace subi komai a sannu idan ba hakan ba komai zai lalace dan AZIZ din yanzu baya Kansa.

Falaq da gabaki daya hankalinta yayi mummunan tashin da tsoro ya ciketa sbd ayau Daddynta ya tureta sa karfi har sai dataji rauni,
Kuka takeyi sosai a jikin fiddausi da itama ta dade da Sanin Mama ba itace asalin mahaifiyar AZIZ LIMBA ba to Amma shock dinta shine babu Wanda ya santa daga AZIZ din sai Mama kuma Mama ta dade da Sanin Umman na gidan duka lokacin nan tayi shiru Harma suke kiranta mahaukciya
To kadai Maman

Please Login or Register in order to submit comment