Reading KALBIM BOOK 2 BY MAMUHGEE Chapter 2 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ne tinda sunyi lokacinda babu ranar da a labarai baa fadar irin tarin nasarorinsu da arzikinsu hakama kusan kowa daya sansu yasan labarin kaddarar data samesu,
Wasu sun tausaya musu wasu kuma sunyi Allah wadai dasu,wasu kuma sunyi Allah ya qara musu azaba da kunci dan haka a cikin mutane yanzu basusan da wace fuska kowa ke kallansuba.

Numfashi ya sauke yana nuna musu gurin zama a hankali tareda karban folders din hannuwansu Yana cewa

"Kun dade kuna jira ko? Baqin ne da yawa hakama ayyukan"

A natse Maheer yace

"Ba damuwa ai munsan yanayin ayyukan"

Bude takardun yayi Yana dubawa ahankali
Akan sunayensu ya tsayar da idanuwansa tsawon mintina kafin ya dago ya kallesu a natse tukuna ya sake maida idanuwansa akan takardun Yana dubawa.

Abinda ya ganine a ciki game da irin girman ilimi da tsagwaron karatu da experience da suke dashi ya sakasa jin ganganci ma ne a gurinsa daukansu aiki a gurinsa sbd ba bata lokaci yake ganin zasu dokesa su zarcesa sedai ya koma kallo.

Dan haka ajiyar zuciya ya sauke yana rufe takardun ya kallesu da dukkanin nutsuwarsa yace

"Well gaskia a yanzu ba kowace irin damar dauka aiki tako ina
Mun riga mun cike slots namu Wanda ko zaa samu wata damar ba yanxu kusa kusa ba so ina me baku hakuri sbd Kunyo tafiya me tsayi"

Numfashi me dumi suka sauke ahankali idanuwan Ammar na sauyawa ahankali zuwa ja sbd baqin ciki da damuwa da wani irin sanyin jiki

Maheer ma cikin karfin hali da juriya tareda hadiye damuwarsa ya bude baki yace

"Ba damuwa,thank you so much"

Miqewa sukai suka nufi kofa Ya bisu da kallan tausayi kafin ya bude baki yace

"Kunga ku dawo na fada muku wata damar idan kunaso"

Dakatawa sukai a tare tareda juyowa a natse suka sake zauna suna jiran bayaninsa.

Ajiyan zuciya ya sake saukewa Yana fuskewa kai tsaye yace

"Akwai securities na gate da masu aikin cikin gida da masu aiki da ake nema a wani kamfani Zaa kai gidan wani baturen Alh da baa qasar nan yake ba,
Masu aiki da securities da ake nema wainda sukeda ilimi me zurfin gaske akeso sbd yanayin familynsa da turancin suka fi ji,
So a taqaice dai masu ilimi irinku ake nema idan zaku iya
Slots din na nan amma sai anyi muku interview so if zaku iya yayi muku zan iya gabatar daku a kamfanin da ake neman"

Zuba masa idanuwa Maheer da Ammar sukai idanuwan na jajir sbd wani irin baqin ciki da qunci daya cike kirjinsu da zuciyarsu da maganganunsa wai securities masu gadi fa kenan kuma har sai an musu interview a gidan wani Wanda bayama kasar gadin gidansa zasuyi abanxa kafin ya dawo din.

Ganin yanda idanuwansu sukai jajir na Ammar hadda wasu zafafan hawayen qunci da dacin zuciya ne suka cikasu
Bude baki yayi sbd ya sake fahimtar dasu yace

"Karku damu aikin ba wani aikine me wahala ko yawa ba
Zakuji dadinsa na tabbatar sbd a bayanin gidan mansion ne sabo da aka kammala a watan nan hakama kwata kwata fa basa qasar,
Matarsa da zai aura ce baturiya shiyasa dole se masu zurfin ilimin irin naku,
Hakama a cikin mansion din akwai bangaren masu aiki da da zaku zauna acikin kwanciyar hankali da wadata tareda jin dadin gaske,
And idan kunada mata ko kanne mata kuma sunada ilimi irin naku duka sauku cike slots din sbd ku samu zaunawa dukanku a cikin mansion din bangarenku na masu aiki sbd samun nutsuwa
Daga karshe kuma albishirin da zanmuku albashin nada tsananin tsoka da girman gaske Wanda duk aikin da zaku samu na kamfani bazaku samu albashi me Kyansa ba"

Ammar kasa cewa komai yayi ya miqe hawayen idanuwansa na gangarowa yafice kirjinsa na masa wani irin nauyi,

Hannuwansa yasaka Yana share hawayensa da suka gangaro Yana jin zancen na sake yankar zuciyar ta yanda bama akansu zancen ya tsaya ba ace wai idan sunada kanne ko mata suzo suyi aikatau dasu,

Tayaya zai iya kallan Jannah a matsayin maid tana aikin aikatau a karkashin wata macen?

Tayaya zasu bari Ummah tayi aikatau a qarqashin wata bayan yanayin lafiyarta ma dasuke lallabawa dan su samu su farfado su nema mata lafiya da duk abinda zasu tara.

Maheer ma dago idanuwansa da sukai jajir yayi ya kalli mutuman ya bude baki ahankali yace

"Mun gode bama buqtaan hakan zamu ci gaba da neman aikin a wani gurin"

Miqewa yayi shima ya fice yana danne radadin da zuciyarsa ke masa.

Modibbo na ganinsu hankalinsa ya tashi jikinsa yayi sanyi sedai kafin ya juya ya bisu secretary din office din yazo yace ana kiransa.

Modibbo na shiga office din ya zube qasa yana gaidasa cikeda girmamawa.

Amsawa yayi kafin ya sake korowa modibbo zancen dallah dallah da irin tarin kudin da zasu ringa samu a aikin kafin ya ciro katinsa ya bawa modibbon yace

"Ga numbern wayata nan idan kunje gida sun sake shawara akan zasuyi saiku nemeni"

Karba modibbo yayi da sauri yana rudewa akan jin kudi da alkhairin da zaa iya samu a aikin idan sunyi.

Kudi ya ciro dubu goma ya bawa modibbon yace

"Gashi ku hau mota sai naji daga gareku,idan kuma kunja lokaci zasu iya rasa damar sbd aikine da duk me wayo ya samu zaiyi gaggawan karba"

Godiya modibbo ya hau yi Yana rawan jiki kafin ya fito yana jin idan badan masu zurfin ilimi da akace ana nemaba da babu abinda zai hanasa tattaro su Garba dasu isiya suzo su karba aikin amma ko su Ammar din wlh ba barinsu zaiyiba sai sun karbi aikin nan koda asiri ne.

Yana fita tini su Maheer sun fice daga kamfanin zuciyoyinsu cikeda daci da radadi me zafi.

Acaba suka tara su uku sukai overload suka wuce masaukinsu kowa zuciyarsa cikeda tinani me nauyi Musamman modibbo daya matsu daya koma ya fayyacewa su isiya wannan samu da rashin dasu Maheer ke kokarin janyo musu dan rashin tinaninsu,
To wlh tsaf zai gama zugasu da takurasu saiya tabbatarda sun karba aikin dukansu har Jannah tinda itama tanada ilimin da akeson gwara suje suyi aikin ai yafi zaman banza.
#MAMUH
#BEST LOVE
#STEEZ
#ROMANCE
#LIMBAS
#ZAADENS


ZAFAFA BIYAR

KALBIM 500
Mamuhgee

KIRJIN ME HANKALI 500
Miss Xoxo

ADUNIYATA 500
Huguma

AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul

09033181070
09032345899*_KALBIM_*

Book 2
Chapter 4

Suna isa gida Maheer jin yayi gabaki daya garin ya fita ransa kauye ma kawai yake son komawa sbd zuciyarsa ta huce daga radadin datake masa,

Ammar ma jin yayi kamar ya hakura da neman aikin gwara su fara wata sanaar su fara Gino kansu daga nan sbd baa taba cin fuska da mutuncinsu kamar yau din ba da zaa kalli girman takardunsu da babu inda ko a ido zaa samu ganin irinsu ba ace wai zaa basu aikin securities a matsayin masu gadi Jannah da suke gwagwarmayar neman komai dan inganta rayuwarta data Ummah ace suma a matsayin masu aiki,wace irin cin mutunci da tozartawa ce wannan?

Modibbo ganin yanayin da suka shiga ya saka ya dakata daga musu magana ya bari sai sun koma gida tukuna amma kam wannan aikin shi a gurinsa kamar anyi an gama ne Banda rashin godiyan Allah irin nasu tayaya zaka samu aiki irin wannan ka tsaya wani duba darajar kai da duba girman iliminka,

Banda sun samesu masu zuciyar tausayi da duba zumunci uban me zai saka su karbesu su basu gurin zama Harma da abubuwa da yawa harda gurin nema da basu damar sanaa tinda su a lokacin da suke cikin daularsu basu taba tinawa ma da akwai dangin kakarsu kakarsu a kauye ba saida suka hadu da qwallon shegen da baya barwa Allah ya fisu zama dan ta'adda ya ruguxasu tukuna suka nemesu.

Har dare babu me walwala a cikinsu sunyi sanyi sosai haka suka kwana bama tareda sun nema wani abincin kirki sunciba.

Washe gari suka so komawa amma Maheer ya daure ya dangana suka sake fita neman aikin Wanda kamar hadin baki babu inda suka samu komai sai wulaqancin dayafi na farkon dan akwai inda aka daukesu amma wai shi Maheer din driver shi kuma Ammar security a kamfani.

Modibbo ganin hakan yasa suka aje maganar aiki suka bisa sabgar kasuwancinsa data kawosa suka koma yawon kasuwannin hatsi da dabbobi a haka suka cike kwanakinsu suka tattaro suka dawo.

Dan abinda ya rage musu na canjin da suka samu a kasuwa tareda modibbo suka siyowa Jannah da Ummah sabin takarmi da dogayen riguna masu dan kyau da turare da sabulun wanka me kyau da toothbrush da sabon brushes na dukkaninsu su biyar sbd iya kokarinsu basa son Jannah ta rasa kyan sigarta ko yayane bazasu iya bari ta koma abar tausayi ba tinda sun fito zasu nema komai su kuma qarar da koman akanta da Ummah.

Jannah ce ta fara samun labarin isowansu a bakin yaran gidan daketa ihun modibbo ya dawo dan haka ta wanke hannunta ahankali daga gama gyara daure dogon gashinta da fatma ta gama mata kitso me kyau.

Kofar shigowa bangarensu ta kalla daidai lokacinda Ammar ya fara sako kai da sallama ta sake murmushi me kyau da nutsuwa na farin cikin ganinsu zuciyarta na sanyi me dadi ta karbi babbar jakar hannunsa tana cewa

"Welcome Ammar Zad"

Sanyi daya mamaye zuciyarsa ne na saukan muryanta kunnensa da yanda haryanxu take kiransa yake kashesa akanta take quncinsa ya narke yabar kirjinsa murmushinsa me kyau shima ya bayyana yana qarasawa ya zauna a kujeran data tashi Yana cewa

"Thank you Jan,
Yaya kauyen nan?
Ina Ummah ne ta shiga?

Hannu ta miqawa Maheer suka gaisa Ya jata zuwa shimfida suna kokarin zama Ummah ta fito dgaa daki tareda Dad da zai fita suna ganinsu Ummah ta sake fuska sosai tana kallan Ammar da shima ita yake kalla Yana nuna mata gefensa taxo ta zauna ya fidda Apple Guda biyu daya siyo mata ya miqa mata Yana cewa

"Ci wannan kiji yafi wancan mangwaron nasu garba me shegen tsami da saka ciwon ciki"

Cikin farin ciki me tsanani Umman tace

"Da gaske kake?
Wannan yafi wancan dadi kace??

Gyada kai yayi yana dariya

Juyawa tayi ta kalli dad ddaa farin ciki sosai a fuskanta alamar hakane

Yana dariya cikeda kulawa da wani irin sanyin kaunarta dake cikeda zuciyar Dad din ya gyada mata kai yace

"Yes kici zakiji"

Maheer ta maida kallanta akansa har lokacin farin cikinta a bayyane yake

Dariya shima yayi Yana gyada mata kai alamar eh

Zata kalli Jannah
Jannah din Tai saurin karbewa tana cewa

"Bara na wanke muji ko Ummahna"

Da sauri Umman ta miqa mata dayan tana cewa

"Wanke duka mu cinye"

Maheer dake kusa da ruwa ne ya miqo musu Yana cewa

"Ba kudine ai da ansiyo da yawa tinda nasan Ummah zata so shi sosai dan nima bana son suna shan mangwaron nan kwata kwata"

Jannah cikin kulawa ta bawa Ummah tana cewa taci.

Dad ne ya kalli Maheer Wanda shima shi din ya kalla kafin suka kalli Ammar suka miqe dukkaninsu suka fice zuwa waje.

Suna fita Jannah ta bisu da kallo sbd tin shigowansu taga damuwa boye a tattare dasu.

Suna fita masallaci suka fara nufa sukayo sallar laasar kafin suka dawo a hanya Maheer yakewa Dad bayanin abinda ya faru.

Shiru Dad yayi zuciyarsa na sanyi da damuwa kafin yace

"To Allah yasa hakan shine mafi alkhairin ya kuma kawo mana wata mafitar"

Amin" suka amsa dashi suna qarasawa gida.

Abinci suka ci da daddaren kafin suka fidda siyayyr da sukayo musu,

Fira suka hau yi hankalinsu kwance cikeda kulawa da juna har dare sosai kafin kowa ya shige.

Da sassafe Garba ya shigo bangaren yayi sallama ya sanarda Dad su Modibbo na son magana dashi.

Fitowa Dad din yayi daga daki Yana saka hular sanyi a Kansa sbd akwai sanyi ya fice Maheer na bayansa Ammar be tashi ba hakama Jannah da Ummah.

Tin daga nesa Maheer ganin irin kallan dasu kawu ke jeho musu da irin yanda suka zauna babu me faraa a fuska ya san akwai inda aka samu matsala.

Dad a natse ya qaraso yai musu sallama ya nema guri ya zauna suna gaisawa.

Maheer ma gaidasu yayi cikeda girmamawa kafin ya zauna dga gefe kan dutse.

Shiru gurin yayi tsit kafin Kawu Jibo ya bude baki yace

"Dzad kasan da labarin su Mahe sun samu aiki me kyau da asirinka da nasu harma da namu zai rufu sunqi karba sbd girman kai da ganin sunfi karfin hakan?

Kai tsaye Dad yace

"Wane aikin ne wannan??

Modibbo ya karbe da cewa

"Aikin securities me kyau da albashi me tsokar gaske"

Numfashi Dad ya sauke yace

"Ni bana takura yarana akan abinda basaso ko basuyi niya ba sbd kawai ina cikin talauci,
Idan har tin acan since bazasu iyaba to shikenan din bazasu iyaba"

Wani kallo kawu isiya yayiwa Dad din cikeda mamaki da siqewa tareda takaici yace

"Kenan dai sun fada maka kuma ka goya musu baya?
Harkar samu?
Harkar ci gaba sbd kada mu lasa arziki shine kuka taru kuka yanke shawarar bazasuyiba"

Kawu Jibo daya gama cika shima da baqin ciki kai tsaye yace

"To Ni kawai aban kudina dana bayar bazan iya wannan kayan baqin cikin ba tin yanzu anfara kafin ayi nisa,
Dubu sittin cif a miqomin abuna yanxun nan inada abin yi dasu"

Kawu isiya ma cewa yayi

"Eh gaskia indai bazaa karba aikin da aka gani a kasa ba nima aban kudina bazan iya jira ba dan ba ranar samun wani aikin gwara aban na fara wata sanaar dasu kawai"

Modibbo daya rasa abin fada kallan dad yayi ya gyara zama Yana tattaro nutsuwarsa yace

"Dzad ka nutsu ka duba lamarin rayuwar dake gudana a yanzu,
Kai din baya ba kai bane a yanzu
Hakama yayan naka da sunan da mutuncin da matsayin duka basu bane a yanzu,
A baya idan akace Zaadens magana ake ta masu qasa da wajen qasar ma amma ka duba a yanzu a ina kake?
A ina rayuwa ta dawo da kai.

Maheer ya kalla yace

"Kai Mahe inace cewa kukai zaku sake farowa daga farko ku sake gino Zaadens da guminku da gwagwarmayar da duk ya kamata,
Idan da gaske hakan ne to banga dalilin qin karban aiki kowane irri bane indai bana haram bane ko sabon Allah,
Aikin nan fa bana dindindin bane ku karba ayi na dan lokaci ana samun abin Gina kai saiku ajiye ku fara duk kasuwanci ko aikin da kukeso,
Dan haka xabi dai anan biyu ne kodai ku karba aikin nan ku samu damar fara kafa kanku kokuma ku tabbata anan kauye cikin wannan rayuwar da bakwason ku mutu a cikinta,
Hakama dukanmu idan lamarin bazai yiyuba muna buqtaan kudinmu a cif cif ba bata lokaci"

Shiru Dad da Maheer sukai jikinsu a mace zuciyoyinsu a jagule da maganganun su Kawun.

Ajiyan zuciya Dad ya sauke kafin ya kalli su Kawun yace

"Ba damuwa inshallah zamuyi shawara muga abinda zai yiyu gameda biyan kudin"

"Ah ah bawai shawara ba muji shiru,
Aikin nan dai modibbo yace kada a wuce dan lokaci Idan ba hakan ba zaa rasa dan haka ayi me yiyuwa asan nayi"

Kawu Jibo ya fada hakan Yana sake matse fuska.

"Inshallah zaa kokarta kafin lokacin" Dad yace Yana miqewa yabar gurin Maheer na bin bayansa.

Suna isa ciki babu Wanda yayi magana saima shiri da sukai suka fice bayan sun karya da madara da zafi da waina

Se yamma sosai suka dawo,
Dare nayi suka ci abinci gabaki dayansu a tare kafin Dad da Maheer suka sanar da Ammar abinda yake faruwa da kuma tafiyar da zasuyi goben hadda Dad su sake bazama neman aiki koda bana office ba koda na manyan shaguna ne haka ko supermarket ganin sukeyi gwara shi akan aikin gadin.

Washe gari tinda sassafe suka sake Aron kudi a gurinsu modibbo suka wuce.

Tinda suka tafi Jannah ta maida hankalinta ta duqufa a gurin adduar Allah ya zabar musu abinda yafi zaman alkhairi koda aikin gadin ne sbd ta jima da ajiye matsayinta na princess Jannah Zad koina ne indai zata zauna ta rayu da familynta cikin kwanciyar hankali batada damuwar komai.


Kwanansu Dad goma sha shida suka dawo babu Hasken komai a tafiyar sbd duk inda suke saka ran samun wata mafitar babu,

Aiki harna tsaron shaguna da wasu guraren sun nema basu samuba gashi duk bashin da suka laftawa kansu ya qare ba aikin.

Bayan dawowansu su kawu suka sake bude wuta akan a basu kudinsu har abin yakai anfara samun matsala da damuwa sbd tini abin ya koma hadda gori da fade.

Dad ne ya samu su Kawun a Karo na ba adadi cikin nutsuwa ya sake rokonsu akan su qara musu lokaci.

Budar bakin Garba dake tsaye cewa yayi

"Baba ni idan zaka yadda inason Jannah a bani aurenta na bada dukiyar aure se abiya bashin da dukiyar Harma ayi canji"

Wani Amai ne me karfin gaske ya kubcewa Ammar dayake bayan Dad tsaya jin maganar Garba kamar saukar Mummunan qarnin kifin daya kwana cikin ruwan jini.

Maheer ma dagowa yayi yana yiwa Garban wani mummunan kallan baqin ciki me tsananin gaske.

Dad su kawun ya kalla yaga babu Wanda ya shiga mamakin zancen da alamar sun dan da maganar dan haka take yaji gabaki daya kauyen ya fita ransa fit sbd gwara mai aikin gadi daya nakasta rayuwar Hasken idaniyarsa.

Bude baki modibbo yayi yace

"Daman ta isa harta wuce aure kuma kila sbd itane basason aikin gadin sbd bazasu iya barinta ba hakama bazasu iya barin taje aikatau ba dan haka gwara AUREN nima na amince dashi"

Kawu Jibo ma kai tsaye yace ya amince shima.

Dad kuwa idanuwansa ne sukai jajir ya saukesu akan su Kawun sbd ya gama fahimtar toxartasu kawai suke son yi sbd suna rabe a gurinsu dan haka gwara ma su tattara din su qara gaban,
Bude baki yayi zaiyi magana Ammar da idanuwansa sukai jajir hannuwansa na rawa sbd wani irin azababben kishin dayaji Yana neman kashesa take ya riga Dad cewa

"Dad pls mubar nan koda a aikin gadin ne zan iya mutuwa idan naci gaba da zama anan"

Maheer ma kai tsaye ya amince da hakan Wanda shima Dad ya gwammace su tattara su tafi gurin aikin tinda zasu zauna gabaki dayansu guri daya cikin aminci.
#MAMUH
#BEST LOVE STORY
#AZIZ AY LIMBA
#ZAADENS
#JANNAH LIMBA

ZAFAFA BIYAR

KALBIM 500
Mamuhgee

KIRJIN ME HANKALI 500
Miss Xoxo

ADUNIYATA 500
Huguma

AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul

09033181070
09032345899*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 5

Da mamaki dukkaninsu kawu suka kallesu kawu isiya Yana cewa

"Au dukiyar aurence bazaku iya biyan bashi da ita ba kokuwa aurar da ita dinne baku tashi ba?"

Kawu Jibo ne ya qarasa dora masa zancen da cewa

"Kokuma Garba dinne bazasu iya bawa Yar gwal din ba kuma ba"

Da mamaki kawu isiya ya kalli Dad yace

"Aa wane su su fada hakan tinda a yanzu babu binda akafi karfin Garba dashi tinda shine yake da abinda basada shi a yanzu"

Daqyar Ammar yaji bugun zuciyarsa na dawowa daidai ya juya gefen Garba zai kallesa ya fasa sbd zuciyarsa zata iya bugawa kokuma zai iya shaqesa ya rabasa da duniya gabaki daya dan haka su kawun ya kalla yana kokarin dedeta numfashinsa yace

"Kawu kwata kwata fadar auren ne ma a tsakaninsu tamkar mugun sabo me zunubi ne sbd ko mun rasa komai a duniya Jannah tana nan a matsayinta na na sarauniyar Zaadens kuma darajarta ta wuce rayukanmu duka,

Duka wannan gwagwarmayar da aikin da muke nema sbd ita da Ummah ne kadai,
Duka abinda zamu nema mu samu harma mike son sake gina kanmu sbd mu basu rayuwar jin dadi d kwanciyar hankali ne kawai bawai munayi ne dan kanmu ba,

Hakama Jannah tamkar matar aure ce sbd ni Ammar Zad nine mijinta dan haka sunan matata ma ya fita a jerin hada sunanta da sunan wasu"

Maheer da Dad dake cewa yayi shiru baiyiba saida yakar karshe jikinsu mutuwa yayi da jin haryanxu Ammar Yana kan bakarsa ta auren Jannah wanda a yanzu kam zasu iya fuskantar komai dan aura masa ita ta yanda zasu rayu a guri daya dukkaninsu a duk inda rayuwa zata kaisu suna tare.

Afusace kawu isiya yace

"Dzad kana kallan danka Yana mana rashin kunya Yana nuna mana kunfi karfin hada zuria damu ko?
Waton Kun rayu a cikin arzikinmu idanuwanku sun bude yanzu kunada maganganun fada,

Ita Jannah din Banda farar fata da turancin banza sai sanyin jiki mara amfani kullum mace kamar amaryar Aljanu itace zaace tafi karfin auren danmu?

Maganar ta sosa zuciyar Dad da duka Zaadens din sosai sbd har abada Jannah a zuciyar Dad babu wani abu daya kaita daraja a gurinsa kaf kuwa a duniyarsa wanda yasan hakan shine babbar jarabawarsa sbd ko a yanzu da baida komai idan ya kalli Allah bai rabasa da abinda yafi so a duniyarsa fiyeda komaiba saiyaji shi baima shiga jarabawar komaiba,
Sai kuma Ummah a yanzu da haka kawai yake jinta itama a tsakiyar ransa saima yanajin kamar auren kuruciya ne yayi sbd a baya dukiya da daula tareda yawan yawon kasashe dayake bai samu time sosai ya bawa Mimi ba dukda irin son da itama yake mata me karfi Musamman da ciwon Jannah ya bayyana suka fara gwagwarmayar neman lafiyarta gabaki daya bai sake samun nutsuwan rayuwa data sukunin zama da Mimin ba yanda ya kamata har saida Jannah ta samu zuciyarsa Ummitah Limba,

dan haka a yanzu da Ummah take rayuwar aure dashi tamkar yarinya karama sbd yanayinta yasaka rana tsaka Allah ya sakata a tsakiyar zuciyarsa itama dan haka a rayuwa yanzu bayan Jannah Ummah ce mutum ta biyu da zai jure komai munin kaddara akansu sbd haka kuma bazai iya daukan kowane cin mutunci akansu ba.

Kawu Jibo bazai iya doguwar hayaniya ba sbd baqin ciki da bacon rai daya gama rufesa yace

"Kai isiya kanada karfin batawa ne akan wannan lamarin ne ai amma ga abu a bayyane kai tsaye idan bazaa bawa Garba auren Jannah ba a bamu kudinmu a yanzu a take idan yaso su aura mata sarkin larabawa mugani dan babu ubanda talauci baya sakawa ciwon hauka tinda ai suna da ma me haukar ai"

Miqewa tsaye Dad yayi batareda yace komaiba ya juya yabar gurin sbd yanda zuciyarsa tayi mugun daukan zafi hakama bayajin yanada energy din batawa gurin magana dasu kawun sbd kwata kwata yaji ya tsani cigaba da zama da iyalinsa a cikinsu.

Maheer ne ya kallesu tareda tattaro gabaki daya kudin dayake jikinsa ya ajiye gabansu ya bude baki cikin danne daci da baqin cikin dayake ransa yace

"Sauran kudinku din inshallah bazaa a kwanaki biyu zamu hada muku"

Kawu Jibo ne ya rufe ido yace

"Wlh tallahi kwandala kai ko sisi idan babu a kudina ni bazan karba ba"

Kawu isiya kuwa daukan kudin yayi ya kirga a nasa dubu Tara ne babu dan haka ya dunqule kudin ya saka aljihunsa yana cewa

"Na biyo dubu tara kuma nima wlh kwana biyu na bayar a hadomim dubuta Tara cif a ban idan ba hakan ba har birnin tarayyar zan samu mutum ba abinda ya damen"

Maheer bai iya cewa komaiba ya juya yabi bayan su Dad da suka wuce.

Koda Dad ya shiga gidan kai tsaye Jannah da Ummah dake zaune suna nade kayansu na wanki da Maheer ya wanke musu ya kalla fuskokinsu cikeda kwanciyar hankali da farin cikin kasancewa tareda ahalinsu.

Ajiyan zuciya ya sauke me zafi Yana rintse idanuwansa yana rokon Allah yayi masa arzikinda zai dawwamanar da farin ciki da kwanciyar hankali a wainnan fuskoki da zuciyar tasu.

Jannah ce tafara dagowa da fararen idanuwanta ta kalli Dad din kafin ta kalli Ammar daya shige dakinsu Yana dafe da kirjinsa dake masa wani irin nauyi sbd ambatar auren Jannah din kadai ya dawo masa da tinanin da ko a lahira yana fatar kada Allah ya hadasa da LIMBA,

LIMBA shine sunan da har abada harya bar duniy baya fatan ya sake ji bare tinawa,
Yana kullum yanda yake rokon Allah kada ya sake hadasu da ko me sunan AZIZ bare Limba baya rokon Allah yayi musu mafita kamar hakan,

Bazai iya sake rasa Jannah ba akowane hali dan hakama kawai a yanzu yake jin zuciyarsa ta bushe qamas gwara yaje aikin security din suje inda zasuyi rayuwa a natse ba barazana ko gori bare kauyanci da dabbancin da akeson kawo masa wai jannarsa da auren wani.

Tasowa Jannah tayi ta nufo Dad dinta ta kama hannunsa ahankali cikin kulawa tace

"Dad,akwai damuwa ne?

Kallanta yayi ahankali tareda sake damke hannunta ahankali cikin nasa yana jin kamar ya maidata cikinsa ta dena fuskantar kowace irin matsala,

Wai yau Princess dinsa ce a cikin wannan rayuwar bayan wani qaton banza ya mayar masa ita bazawara.

Rufe idanuwansa yayi ya bude yanajin radadin tinawa da Wanda ya maidata bazawarar kirjinsa na nauyin da haryanzu bai manta yanda azabarsa take ba sbd a rubuce a kaddarance AZIZ LIMBA shine kaddarar ZAADENS da har abadan abada komai nisa da yawan da zuriar Zaadens zasuyi bazasu manta ko goge wannan tarihin daya riga ya kafu ba.

Ahankali Dad din ya sake sauke idanuwansa da sukai sanyi akan fuskan Jannah Wanda fuskanta take bayyanarda a kowane hali zata iya rayuwa indai dasu ne duk da akwai ciwo da kunci me zurfin gaske a zuciyarta datake rufewa zata kuma cigaba da rufesa

Please Login or Register in order to submit comment