ki ci gaba da gasawa Amina magana, yaron nan ba zai fasa kirɓarki ba. Shashasha."
Nan yaran suka shiga ba ta hakuri gami da nunamata kuskuren Aliyu cikin sanyi. Aliyu ya ba Amarya hakuri aka ce ya ci gaba da zama anan gidan Abulle. Bayan watsewar surukan da jikoki, Abulle ta nemi shawarar ta yanda za'a inganta rayuwar yaron tunda ya ƙi boko. Nan take Justice ya kawo shawarar a dorashi kan kasuwanci. Ba musu kowa ya yi na'am. Justice da kansa ya dauki nauyin budewa Aliyu shago da komai. Nan kuwa Abulle ta yi ta sanyamasa albarka daga nan aka tattauna batun auren yanmatan da suka isa aure a zuri'ar da zarar sun kammala Sakandire don a sannan suna ajin karshe. Budar bakin Abulle ta ce.
"Banda Muhibbat, na yi mata miji."
Kalamanta sai da yasa kirjin Justice bugawa, tsoransa kar ya zamana abinda yake gudu ne zai afku. Duk yanda suka so jin waye mijin Muhibbat ta ƙi basu fuska. Asalima goronta ta hau tauna ta ce su mike su bata wuri ta sallame su. Jiki ba kwari dai Justice ya tafi.
Ita kuwa Abulle tun wani dare da ta kama Muhibbat na kallon hoton Aliyu tana kuka ta ci alwashin sai ta auramata shi. Ba ta bari ta ganta ba ta juya ta ci gaba da baccinta cike da farin ciki da tausayin yarinyar.
Cikin luɗufin Allah zaman kasuwa ya karɓi Aliyu, dakyar yake ajiye wasu kudaden don shi da za'a bar shi ya yi facaka zai fi son hakan. Bai fasa shaye-shayensa ba sai dai ya fi yi da dare wanda daga ya sha ya ɗan yi tamɓelansa zai ɓige da bacci. Taba kuwa ko a kasuwa zuƙarta yake don zuwa lokacin bai dauketa abar tashin hankali ba. A wannan lokacin ne kuma Inna ta tashi lafiya kalau, daga baccin rana ta gamu da ajalinta, ta rasu. Mutuwarta ta girgiza jama'ar gidan musamman kishiyoyinta wadanda suka cika da dana sanin zaman gaba da hassadar da suka yi da ita. Batun mijinta kuwa ba'a magana, Abdussalam ya shiga tashin hankali marar misaltawa. A gefen Aliyu da yaran Innar mata suma ba'a magana.
"Ka ji tsoron Allah." Shi ne abinda Innar ta fi yawan fadamasa a kalamanta masu tsawo, sai a sannan ya san yana son mahaifiyarsa halinta na banzatar da lamuransa kawai ya tsana. Yan uwanta daga Gombe duk sun zo. Mutuwar Inna ya karawa Abulle da Muhibbat tausayi da son Aliyu.
Suna kammala Sakandire magabata suka yiwa Muhibbat caa akan ta fiddo da miji, ita kuwa ta kasa zaɓen ko ɗaya saboda Aliyu.
Aka yi sa'a koda Abulle ta tari Aliyu da zancen Muhibbat don jin ta bakinsa sai ta ga ya hau murmushi, nan take ya nuna ya amince don dama ya jima da sanin yarinyar na sonsa. A cewarsa ko ba komai zai ƙara martaba a idon duniya kasancewar mahaifinta wani ne kuma ɗan uwan mahaifinsa.
Tashi ɗaya kowa ya ce bai yarda da auren ba, Justice dai ya yi alkunya ya yi shiru, daidai da mahaifin Aliyu bai amince a ba Aliyu auren Muhibbat ba. Ita kuwa Abulle ta rantse ko bayan ranta aka ƙi aurawa Aliyu Muhibbat ba ta yafewa yaranta ba. Kuma bakinta sai ya bi su, wannan ya tashi hankulansu, a dole suka amince.
Justice ya yi mamakin murnar da Muhibbat ta nuna. A gefe guda Mamarta Saudatu na cika da batsewa.
"Dama kina sonsa?" Ta riga Justice jefamata tambaya, ta kara sunkuyar da kai tana murmushi kafin ta mike a guje ta nufi daki. Saudatu ta dubi Justice dake hamdala da alama abin ya mishi dadi.
"Kana nufin ka amince da auren yaron da ya fitini kowa a dangi da ɗiyarka kamila?"
Yayi murmushi.
"Allah Ke shiryawa, kuma Ya shirya Aliyu sai dai a ci gaba da yi mishi addu'a. Farin cikin Muhibbat ya fiyemin komai, fargabana kar ya kasance ba ta sonsa. Tunda har tana sonsa shikenan, Allah Ya tabbatar da alheri. Ba zan ƙi bin umarnin Mahaifiyata ba."
"Tabɗijam!"
Abinda Mama ta furta kenan. Rigima sosai ta tayar akan lallai sai dai a fasa auren, karshe Justice ya zuciya ya fita harkarta, har yaji ta yi da ta gaji ta dawo ɗakinta. Abulle ta rantse ba don darajar ta haifomata sanyin idaniyarta Muhibbat da sauran jikoki ba da sai ta saka an saketa. A dole ta dangana aka yi auren Aliyu da Muhibbat wanda alokacin ya yi nisa da son Ramlat.
Muhibbat ta sauke ajiyar zuciya, ta kara maimaita sunan Ramlat da mijinta yake yawan kiranta da shi a shimfiɗa. Hannu ta sanya ta dauke hawayenta. Kauna da son Aliyu abu ne da ta fara tun ba ta mallaki hankalin kanta ba. Ba kuma ta jin za ta daina. Addu'a za ta dage da yi har Allah Ya fidda Ramlat daga ran mijinta. Ba ta santa ba ko a hoto, ta dai santa a bakin mijinta. Takan yi mamakin yanda Ramla ke aminta su yi waya da mijin aure har cikin dare. Ta rasa gane SON ZUCIYA ne ko kuwa a'a?
Fatanta Allah Ya karkato hankalinsa gareta su ci gaba da rayuwa kamar yanda suka fara a farko.
***
*DAWOWA 🕯️ *ƘARFEN ƘAFA*🕯️
_*Rufaida Umar*_
Bismillahir Rahmaanir Raheem.
08)
_*Dawowa Labari*_
A kofar gidan Amrah ɗan sahu ya ajiye Ramlat. Ta biyashi tana mai kama hannun Affan wanda duk ya ɓata kayansa da cakulet suka fara knocking. Aka bude, harararta Amrah ta yi.
"Sai yanzu ko? Yinin kenan?"
Ramlat na dariya ta juya.
"Shikenan, bari mu juya daga nan." Da sauri ta kama hannunta ta maidota baya suna dariya.
"Ni ban ce ba, yi hakuri."
Suka shiga ciki suka zauna, nan take sanarmata sai da ta biya gidan Muhibbat.
"Allah Sarki Muhibbat, matarnan akwai kirki wallahi. Ba ruwanta, kinsan babu ranar da ba za ta turomin gaisuwar juma'a ba."
Murmushi Ramlat ta yi.
"Ai wannan daban take cikin mutane ma. Allah dai Ya bamu ikon yin zumuncin mu ma."
Amrah ta amsa da Amin. Ramlat ta shiga waige-waige.
"Ke ina ƴata wai? Tun da kika ce min kun dawo ita nake son ganin yanda ta girma."
"Tana wurin Mama na kai mata yaye. Abinda ya ban mamaki ko ciwon nono ban yi ba."
Ramlat ta dara.
"Kika sani ko wani cikin ya shiga? Tsarabar Lagos?"
"Allah Yasa. Ai nikam ina so wallahi."
Ba ta yi mamakin kalaman Aminiyarta ba don tun bayan aurenta sai da ta shekara biyar ba ta samu ciki ba sai yanzun. Mijinta Ɗahiru ya ce ba ita babu planning sai ta yi biyu.
"Allah Ya kawo mai albarka toh. Nidai yanzu yunwa nake ji."
Miƙewa suka yi a tare zuwa kicin Amrah na fadin.
"Mutuminki ɗan wake nayi niyyar yi kuwa, na haɗa komai ki dora ruwa idan ya tafasa ki yi sakin bari na yanka mahaɗin."
"To da ban zo ba fa?"
Amrah ta yi dariya.
"Ai kuma tunda kin zo din magana ta kare. Yi hakuri ki taimaka ban jin dadin jikin."
Haka ta soma sakin ɗan waken tana yi suna hira.
"Ni kuwa ina Hilal?"
Tambayar Amrah ta tunasar da ita yanda suka yi a kwanakin baya, text ya yi mata akan ta sanyamishi rana da lokaci ya zo su tattauna abu mai muhimmanci sai dai ba ta yi karambanin ba shi amsa ba, daga ranar kuma bai ƙara nemanta ba.
"Kamar ban kyauta masa ba, amma a wurina hakan ne daidai."
"Me kika yi mishi?" Jin abinda Amrah ta ce yasa ta fahimci zancen zucin ya fito fili, nan ta bata labarin yanda suka yi. Ajiye wuƙar hannunta ta yi ta juyo da mamaki ƙarara saman fuskarta tana dubanta.
"Meyasa kike yiwa kanki irin wannan gangancin?"
Cikin rashin fahimta ta ɗan dubeta.
"Wane gangancin kuma?"
Haushi da takaici ya kusan kashe Amrah anan tsaye.
"Tambaya kike Ramsy? Ko kin manta na tunamaki waye Hilal? For all abinda ya faru bai sa ya juyamaki baya ba, bai kuma sa ya bar sonki ba, don me yanzu kin samu damar gyara laifukanki kike kokarin juyamasa baya? Allah Kike son yiwa butulci?"
Murmushi mai ciwo Ramlat ta yi, ba ta ce komai ba ta juya ta ci gaba da sakin ɗan wake, sanin hali na idan ta ga dama ba za ta ce uffan ba yasa Amrah itama ta ci gaba da aiki sai dai ta kumbura kiris ya rage ta fashe. Dama sun saba irin haka tun yarinta.
Ita kuwa sai da ta kammala ta wanke hannu ta jira ya dahu ta kwashe ba ta ko tsaya tambayar inda filas yake ba ta dauko. Sai da za ta zuba ne Amrah ta dakatar da ita.
"Wannan na Daddy ne." Tana nufin mijinta, murmushi Ramlat ta yi don tasan ƙawarta ta shaƙa, ta fice daga kicin rike da plastic din da Amrah ta yanka kayan cin dan waken. Sai da ta soyamusu manja sannan ta fito itama. A falon suna zaune sannan ne Ramlat ta dubeta a nutse.
"Tsaya don Allah ki saurareni."
Amrah ta dakatar da zuba ɗan waken da take kokarin zubamusu bayan ta ɗibarwa Affan nashi ya ja gefe. Harararta ta yi.
"Me kuma za ki cemin bayan kin maidani wata banza don kawai ina nunamaki abinda ya dace."
Hannunta ta riko tana dubanta.
"Kiyi hakuri, wallahi duk ba haka bane. Amrah yanzu ke a tunaninki da wane ido zan kalli Hilal na ba shi dama a karo na biyu bayan ni ce ummul aba'isin duk wani abu da ya faru a baya? Ko kin manta ba da Hilal kadai zan zauna ba? Akwai matarsa kuma akwai danginsa da babu ranar da zan goge bakin fentin da na yiwa kaina a idanunsu? So kike na bar wa ƴaƴan da zan haifa da shi abin gori? Yanzun ma wadannan din da ya na ƙare? Kin fi kowa sanin abinda ya faru, kuma kin fi kowa sanina Amrah. Da ace zan iya auren Hilal, da tuni yanzun wani labarin ake banda wannan. Amma bakin alƙalami ya bushe, zan iya yin aure ga kowane mutum a doron ƙasa banda Hilal. To balle ma auren babu shi a gabana yanzu, na gwammace na zauna na kula da yarana. Hakan zai fiyemin komai dadi."
Tausayinta sosai ya kama Amrah, har ba ta san sadda hawaye ya zubomata ba, ita kanta uwar gayyar sai jin ɗuminsa ta yi saman kuncinta. Ta kuwa shiga yi ba kakkautawa.
"Na cuci rayuwata Amrah, na cutar da mutane da dama wanda har gobe ban bar dana saninsa ba. Amrah har gobe ina tunanin bakin cikina ne sanadin mutuwar Abbana duk kuwa da irin rabuwa ta salama da amincin da muka yi. Ƴan uwana ba sa fahimtana, har gobe suna min kallon mai laifi a idanunsu. Ya zan yi ne wai?"
Nan fa suka shiga kukan har Affan wanda ganin Mominsa na kuka shima ya shiga yi. Dakyar suka rarrashi kansu sakamakon ƙarar da Affan yake da kuka yana rirriƙe Ramlat. Komai da komai ya shiga dawowa kwanyarta, daga lokacin da ta saki jiki suka soma gudanar da soyayya mai karfi tsakaninta da Aliyu, daga lokacin ne komai ya faro asali wanda har gobe ta kasa goge *BAƘIN FENTIn* a zuƙatan masoyanta.
***
*BAƘIN FENTI*
_*Komai yana da sila, komai da mafarinsa. Duk abinda bawa bai ɗora kan turba mai kyau da tsari ba, mafi yawan lokuta ƙarshensa nadama ne! Koda ace a haka kaddarar ta zo masa.*_
"Wai Ramsy me kike ne? Ki fito kina ɓata lokaci."
Muryar Amrah kenan sa'ilin da ta ke kokarin shigowa dakin. Zuwa yanzu ta kai matakin da ba ta jin za ta ɓoyewa kowa a duniya sonta ga Aliyu. Wannan tasa ko bayan shigowar Amrah ba ta fasa amsa wayar a nutse ba ba ta ko damu da kallo da murmushin Amrah ba.
"Kai wannan Hilal, shi ba ya jin kudinsa ko? Daga Malaysia mutum ya kira a yi ta wayar fin sa'i biyu? To nidai don Allah ya kyalemin ke ai daya, idan ba haka ba wallahi zamu yi lattin."
Ba ta da niyyar ba ta amsa, ta fahimci ba ta gane wanda suke wayar ba, ko ma ta ce ba ta sanshi ba.
Daga dayan gefen Aliyu wanda ke zaune a falon Muhibbat yayinda ita kuwa ke kicin tana shiryamusu abincin rana ya ɗan hade fuska kamar tana kallonsa.
"Baby waye Hilal? Baby ashe ban Kai darajar da har yanzu za ki iya sanar da mutane ni din kike so ba ba wani banza ba? Watanni goma da soyayyarmu wanda ya fi karfin na wadanda suka kwashe shekaru goma suna yi shine har yanzu ban samu karɓuwa ba? Sai anjima."
Ya katse wayar gaba daya yana fitar da huci. Fitowarta kenan daga kicin, ta ji dukkan abinda yake fadi, sai dai ta yi kamar ba ta ji ba. Ranta na ƙuna kamar koyaushe, ta haɗiye kwallar dake barazanar tona abinda ke ranta. Ganin ya ɗan kalleta ya kauda kai ya ja tsaki ya sanya ta kakalo murmushi ta nufi inda yake zaune a darare.
"Yaya na kammala girkin."
Ya yi mata kallon sakara. Ta sauke kwayar idanunta, a duniya idan da abinda ta tsana ya biyo bayan kallon wulakancin da Aliyu ke mata a lokuta da dama.
"Sai aka ce miki yunwa nake ji? Ga jaki kin ajiye? Mtsww!"
Ya ja dogon kafin ya mike tsaye ya sa kafa ya ture Centre Table a zuciye har yana kifewa, ɗan flower vase din dake kanta na ado shine ya fashe. Bai ko waiwaya ba ya sa kai ya fice daga gidan. Ta zubawa ɓarnar da ya yi mata ido, ko ba komai kudi aka sa aka siyamata. Ba abinda ta nema ta rasa na ƙawata gida wanda iyayenta basu yi mata ba, yayyunta maza kuwa ba wanda bai ba ta gudummuwarsa ba duk kuwa da irin tsanar da suka yiwa Aliyu. Kuka sosai ta shiga yi tana tattarawa, Aliyu bai damu da ita ba. Ta hakikance ba ya sonta, ba kuma ya tausayinta. Ita kullum ke kwana da tashi da bakin cikinsa, ga so da tausayinsa wanda ke sanyawa ta ɓoye aibunsa a idon danginsu har a gaban Abulle wacce koyaushe cikin sanyamusu albarka take. Burin Abulle ta ga ɗa ko ƴarsu sai dai har a sannan Allah bai ba ta ciki ba. Ba kuma ta zargin Aliyu da komai.
"Allah ga mijina, Allah Kai ke shiryawa, Allah Ka shiryamin shi. Ka karkato da hankalinsa gareni." Ta furta a fili tana mai daga hannu gami da kuka, sannan ta shafe fuskarta ta ci gaba da tsince ɓarnar da ya yi.
A gefen Ramlat hankalinta idan ya yi dubu to ya tashi, hawaye take tana kara dialing lambarsa sai dai amsa daya ce, a kashe. Wannan ya tashi hankalin Amrah. Ta dubeta a gigice gami da dafa kafaɗarta.
"Ke, meyafaru da Hilal din? Me yace maki? Mun shiga uku."
Ambaton Hilal da ta ƙara ya farkar da Ramlat. Ta buge hannunta a saman kafaɗarta ta hau masifa.
"Hilal Hilal! To hell with him! Haba! Sai kiramin Hilal kike, a sanadinsa kin sa Aliyu ya yi fushi da ni! Ya kashe wayarsa bansan kuma me zai aikata ba! Dole ne zuwa walimar?! Ba zan je ba! Nace ba zan je ba ko za ki kaini dole?! Wallahi zuwanki bai min rana ba! Ni ki tafi kawai ki rabu da ni!"
Yanda take rufe ido tana zuba masifa iyakar gaskiyarta shi ya fi komai ba Amrah mamaki.
"Aliyu kuma? Waye hakan? Yanzu akan wani banza Aliyu kike min masifa?"
Ai kiran Aliyu da banza shi ya kara tunzura Ramlat. Ta nuna ta da yatsa.
"Kin yi na farko ya zama na karshe Amrah don wallahi ba don ina ganin mutuncinki ba sai na gasamaki abinda zai miki zafi a rai! Aliyu ya fi karfin ki kiramin shi da banza! Kika kara kuma Allah Ya isa! Ba zan je walimar ba ki tafi ki kyaleni! Aliyu shi nake so kuma da iznin Allah shi kadai ne mijina anan duniya!"
Daga nan ta juya a fusace ta soma cire kayanta tana tsaki. Amrah ranta ya dinga suya har bata san sadda ta shiga hawaye ba.
"Akan wani Aliyu kikemin Allah Ya isa? Idan kin kara ganina a gidanku kimin abinda ya fi haka."
Daga haka ta juya ta fice. Allah Ya taimaka Hajiya na wurin Abba, A'isha kuwa kallon cartoon da take a tashar Spacetoon ya dauke hankalinta.
Ita kuwa Ramlat ko a kanta, tashin hankalinta fushin Aliyu. Ta kwanta lamo tana fitar da hawaye, text ta shiga aikamasa kashi kashi.
_*Sweet na tuba don Allah Ka yafemin. Sweet fushinka barazana ne ga lafiyata. Wallahi sweet kai kadai nake so, Kar ka manta na san da zaman Hilal din amma nake sonka."
_*Wallahi Sweet Aliy zuciyata za ta buga. Wallahi har fada muka yi da Amrah a kanka. Ka yafemin. Wallahi don ba ka yanda na ci mutuncinta ba.*_
_*Sweet Aliy har walimar ban je ba saboda kai. Na kasa samun nutsuwa. Sweet Aliy ka yafemin ka bude wayata. Na maka alkawarin fadawa kowa kai nake so. Ka ji? Kuka fa nake. Kaina ma ciwo yake*_
Haka ta yi ta rubuta malamai kashi-kashi tana aikawa sai dai duk ba ya tafiya adalilin wayarsa a kashe. Ta kuwa ci gaba da rusa kuka, dakyar ta samu ta mike ta yi alwalar la'asar ta shiga sallah. Tun tana cikin sallar ta ji wayarta na kara, sallamewa kawai ta yi ba ta ko ida ba ta nufi wayar a guje. Ganin mai kiran ya sa ta ɗagawa da sauri ba tare da ta jira ya ce ba, ta ce.
"Sweet Aliy ka yafemin don Allah, na tuba wallahi ba zan ƙara ba."
"Zan yafemaki Baby amma sai kin fito na ganki. Ina nan bayan layinku. Ba zan iya bacci ba idan ban sanyaki a ido ba."
Wani dadi ta ji a ranta,
"Yanzu zan zo Sweet, ban minti biyar."
Sallar da ba ta yi ba kenan ta bar shi a sai ta dawo, nan da nan ta shafa hoda ta sanya lip gloss, kayan zuwa walimar da ta cire su ta mayar. Ta ja mayafinta, sai da ta kama kofa za ta fice daga dakin ta ji faduwar gaba, me Amrah ta ce ga su Hajiya kafin ta fita?
'Ko me ta faɗa ita ta sani, ke dai kar ki ƙara laifi wurin Aliyu.'
Wani bangare na zuciyarta ya ba ta shawarar da nan take ta dauka. A hankali ta fito tana ɗaga labulen da ya raba dakunansu da falon, babu kowa sai A'isha da ta gaji da kallonta tana bacci. Hamdala ta yi ta fice da sauri.
Tun kafin ta karasa a hangoshi tsaye gaban mashin ɗinsa. Ya haɗe cikin shadda kalar sararin samaniya, babu hula a kansa sai dai ya yi kyau kwarai a idanunta. Kirjinta har wani bugu yake tsabar so da kaunarsa. Shima ya zubamata ido yana ji kamar ya saceta su gudu.
"Ba ki kyautamin ba."
Ya furta yana dubanta da shanyayyun idanunsa. Ta yi narai-narai da idanunta.
"Ka yi hakuri don Allah."
"Banda wannan, na hakura ai tun kallon farko da na miki na mance dukkan damuwata. Sai dai ba ki kyautamin da kika yiwa Aminiyarmu wulakancin da kika faɗa ba."
Sai a sannan ta tuna da ta yi laifi, ta jinjina kai.
"Haushi ta bani, banza fa ta kiraka." Ta fadi cike da wauta.
Ya ji ciwon kalmar sai dai ya yi murmushi. Har a ransa ya ji haushin Amrah na kiransa da banza.
"Kiyi hakuri, a kanki komai zan dauka zan kuma shanye muddin za ki zama rabona. Idan dai kina don farin cikina ku shirya a yau ba gobe ba."
Ta shiga gyada kai.
"Zamu shirya, zan je har gidansu na ba ta hakuri amma yau ba ta nan ta tafi walimar da na fadamaka zamu je dazun. Idan muka hadu a makaranta gobe zan bata hakuri ka ji? Ka yi hakuri don Allah Sweet Aliy."
Ya dan lumshe idanunsa yana murmushi, murmushin da ke ƙara tafiya da imaninta.
"Ya isa, shikenan ya wuce. Allah Ya kaimu goben. Da ban ganki ba, ba zan iya bacci ba."
Wani sanyi da dadi suka lulluɓe zuciyarta. Nan da nan kuma suka shantake da hirar soyayya kamar kar su rabu. Sai dab da karfe shida suka rabu, ba ta iya tafiya ba sai da ta ga tafiyarsa sannan ta juya cike da annashuwa ta koma gida.
"Sai yanzu ku ka dawo? Kun so ku yi dare." Abinda Hajiya ta fadi kenan, sai ta ji kaunar Amrah a ranta, wato dai ba ta sanarmata rigimarsu ba.
"Eh Hajiya, ki yi hakuri."
Hajiyar ta gyada kai tana kallon yanda ƴar ke zuba uban fara'a kamar wacce aka yiwa albishir da aljannah. Gudun kada Hajiyar ta watsamata tambayar da za ta kasa amsawa game da walimar, ya sanya ta saurin shigewa daki gami da faɗawa kam gado tana murmushi, Aliyu shi ne komai nata a yanzu, ba kuma ta jin har abada za ta bar shi ko me za'a yi, kuma ko me zai faru. Tunawa ta yi da sallar la'asar, da sauri ta mike ta faɗa banɗaki ta kara dauro alwala sannan ta tayar da sallar kusan ma a sallar banda murmushi da addu'ar Allah Ya sa ta zama matar Aliyu ba abinda take.
***
Muhibbat tun tana zuba idon ganinsa ya dawo gidan har ta gaji, ragowar abinci ranar ta juye ta miƙawa wasu makwaftansu marayu suka yi ta godiya. Tasan ko ta bar shi Aliyu ba zai taɓa ci ba don a cewarsa ba ya son kwantai. Ba ta gaji ba ta ɗora sanwar dare, tuwon semo ta yi da miyar danyen kuɓewa, a gefe kuma ta yi farfesun kifi sai kunun aya. Komai ta jera inda ya kamata ta faɗa wanka, tana fitowa ta haɗe cikin doguwar riga ƴar kanti mai ɗankwali. Ko ba ado ita din kyakkyawa ce, hakan dai bai hanata daukar kwalliyar ba. Ta fesa turare ta fito falon tana addu'a cike da tsoron yanda zai shigo gidan. Fatanta kar ya shigo a maake kamar yanda ya saba. Jin karar mashin dinsa ya kara kaɗa hanjin cikinta. Ta miƙe da sauri ta bude kofa, a kan idonta ya yi parking ya shigo. Ta yi mamakin ganinsa cike da walwala. Itama sai ta saki fuska.
"Sannu da zuwa." Ya riko ƙugunta yana murmushi kafin ya kai mata sumba a kumatu.
"Yauwa Matar."
Ta rufe kofar suka karasa falon zuciyarta kamar ta fito ta taka rawa tsabar farin ciki duk kuwa da tasan silar farin ciki nasa. Ramlat ce! Ganinta ya je ya yi hakan yasa shi sakarmata fuska sai dai hakan bai dakusar da nata jin dadin ba. Murmushin Aliyu da dariyarsa ma kadai abin so ne a wurinta.
Ta taimaka ya yi wanka, ga mamakinta sosai ya ci abinci har suna hirar abinda ya shafi danginsu. Ga duk wanda ya ga Muhibbat ya san tana cike da farin ciki. A karshe ma ya ja hannunta suka shige ɗaka.
Tun da ya soma sarrafata yake kiranta da suna Baby, wani sa'in ya ce Ramlat sai kuma ya ce oh i an sorry na manta. Har ya yi ya gama ba ta fasa fitar da hawaye na baƙin ciki, ta waiga ta dubeshi yana baccinsa hankali kwance, miƙewa ta yi ta tsarkake jikinta ta fito zuwa ɗakinta. Nafila ta yi ta zauna tana addu'a tana kuka. Sau da dama takan ji kishin Ramlat, sau da dama kuma takan ji ko ma mene Aliyu ne ya ba da fuskar da komai ke faruwa. Sai ta dinga kallon wasu abubuwan ba laifin ita Ramlat din bace. Ta gaji da kukan ta dau Kur'ani ta karanta sannan ta haye gadon ɗakinta sai bacci.
Da asuba koda ta mike ta yi alwala ta shiga tashinsa. Wayar da yake ta tsaida ta.
"Baby ki tashi mana ki sallah, ban san wannan baccin fa. Uhum? Ina magana kina min magagin bacci ko?"
Kasa ƙarasawa ciki ta yi da sauri ta maida kofar ta rufe ta koma ɗakinta cikin hawaye. Mutumin da sai ya ga dama yake tashi salla idan ta tashe shi, shi ne har ya iya tayar da wata yin ibadar. Abinda bai taɓa yi gareta ba kenan, koda dai lokuta da dama ita keda kokarin tashi salla ta tayar da shi.
Wannan karon kasa zubda hawayen ma ta yi ta haɗiye abinta.
***
_*Alhamdulillah, your future husband is back. I can't wait to see you. Love you.*_
Saƙon da ya shigo wayarta misalin bakwai na safe kenan, sa'ilin da take shirin fita makaranta, saƙon da ta tabbatar na Hilal ne. Wani makokon bakin ciki ya turnuƙe zuciyarta har ba ta san sadda ta ja tsaki ba. Sai me idan ya dawo? Ba dai za'a
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 6 Chapter of 58