daga bisani ya yi musu sallama.
Washegari da misalin karfe uku na yammaci ƴanmatan su biyar, Usaina, Maryam, Jidda, Nafisa sai Ramla. Suka shirya suka fita zuwa gidan babban ɗan Hajja Zulai, Kawu Kabiru don ziyara.
Tun kafin su fita titi Ramla ke mitar ita kam ba wacce za ta dauka saman cinyarta sai dai su yi abin hawa biyu.
"Kai Mrs Hilal, don ɓarnar kuɗin mota?" Fadin Jidda tana auna abinda zasu kashe daga Yakasai zuwa Zoo road.
"Aa fa, da gaskiyar ƙawalli, ba zan yarda nima na ɗora kowaccenku a cinya ba, ke kuma Jidda idan har za ki iya hawa bayan kujera shikenan."Faɗin Usaina.
Ta ƙasashe suna dariya don ita kanta ta faɗa ne, a ƙiba kam duk Jidda ta fi su.
"Allah Ya kiyaye." Cewar Jidda.
Aikuwa dai sai rabawa suka yi, kusan a tare suka samu abin hawa, Ramla da Usaina su biyu kacal a adaidaita sai Jidda, Maryam da Nafisa wuri guda.
Sai da suka kusa Zoo road ya samu fasinja. Sallama ya yi ya shigo, kusan da sauri ta dubeshi. Shi ne, shima yana zama ya kai duba gareta. Duk da yanda ta yi saurin kauda kwayar idanunta gefen Usaina wannan bai hanashi ganeta ba. Ta ƙara matsawa jikin Usainar ganin yanda jikinsu ke ɗan gogar juna. Murmushi ya yi ya matsa ta yanda ya san za ta fi sakewa.
Bai ce uffan ba banda murmushin da yake faman dokawa, abin mamakin shima Zoo road ya nufa. A hankali ta kai duba gareshi ta cikin karamin gilashin ɗan sahu. Kwayar idanunsu ya sarƙe da juna ta yi azamar janyewa. Ba ta ƙara gangancin kallonsa ba, mutumin da take kwana da tashi da tunaninsa. Kirjinta bai bar bugu ba, ba ta fahimtar zantukan da Usaina ke yi.
"Sauka mana." Ta ji muryar Usaina karo na biyu, sai sannan ta dawo nutsuwarta ta dubi gefenta, tsaye ta hangoshi a waje yana sallamar mai adaidaita. Ta kauda ido ta fito, Usaina na bayanta.
"Ɗauka har da nasu." Ya furta ga ɗan sahun.
Nan suka ce a'a, ya rantse shi zai biya, Ramla na shirin jan musu ta ji Usaina ta ɗan bugi kafaɗarta alamar ta yi shiru. Godiya suka yi mishi, hango su Jidda sun tsaya ya sanya Usaina nufarsu.
"Ramlat."
Ta tsaya cak gami da juyowa ta dubeshi, ba ta yi mamakin jin ya ambaci sunanta ba don Usaina ta kira sunan ya fi a ƙirga cikin adaidaita. Ya ɗan matso kaɗan.
"Karo na biyu Allah Ya yi haɗuwarmu. Tun sadda na sanyaki a idanuna har yau bani da sauran sukuni. Wallahi ina sonki!"
Ya furta fuskarsa na nuna alamar gajiyawa da kuma gaskiyar abinda ke ransa.
Ta matse yatsun hannunta jin yanda kirjinta ke bugu, ta ɗan kuramasa idanunta da suka cicciko da kwalla. Shima kallonnata yake da nashi mayun idanun wadanda tuni sun dulmiya cikin tafkin kauna da shauki.
"Ayya ka yi hakuri Malam, wallahi an sakamata rana. Nan da shekaru uku ba kaɗan bikinta."
Kalaman Usaina ya maidota hayyacinta, ta tsinci bakinta da maimaita abinda aka ankarar da ita.
"Eh, an sanyamin rana. Ka yi hakuri."
Ya yi murmushin yaƙe. Ya dubi Usaina.
"Kaicon wanda zai yi wasa da damarsa. Akwai kuskure a jan lokaci har haka. Watakila kuma rabon Aliyu ce. Ina muku fatan alheri."
Ya dubi Ramla da fuskarsa wacce ta yi narai-narai.
"Matar mutum Ramla, matar mutum.."
Daga haka ya juya ya bar wurin. Ramla ta tsaya kamar wata mutum-mutumi. Kafaɗarta aka jijjiga.
"Ke dillah can! Mene hakan? Waye shi? Ko kin manta da sanya ranar da ke kanki? Ke Usaina waye shi?"
Duk Nafisa ke wannan kalamin daidai sadda suka ƙaraso, zantukan ƙarshe sun sauka saman kunnuwansu.
Tuni ta soma tafiya kanta a ƙasa, tana ji Usaina na basu labarin abinda ya faru suna jan tsaki da kiran kwalelansa. Can kuma ta ji suna koɗa iya ɗaukar wanka da kuma kyan da Allah Ya mishi daidai gwargwado. Ta shiga tariyowa.
Milk shadda ya sanya da aka yiwa aiki daidai da zamanin, ya dora hula brown da ratsin milk din. Dogo ne don har ya fi ta da kaɗan, yana da hasken fata. Tafiyarsa ma kadai za ta burge mutum. Yana da ɗan duhun lebba, gashin kansa a cike luf-luf wanda ya taho har gefen fuskarsa ya haɗe da ɗan ƙaramin gemunsa. Lafuzzan Aliyu ma kadai abin burgewa ne.
Murmushi ta yi wanda ya taho tare da hawaye, ta yi azamar sharewa lokacin da Maryam ta dafa kafaɗarta. Ta kai duba gareta.
"Ina za ki?" Sai sannan ta waiga ta gansu tsaye a ƙofar gidan yayinda ita kuwa ta ɗan yi gaba. Tabbas tunanin Aliyu ba zai kasheta ba. Ta yarda matar mutum kabarinsa don haka ta haramtawa rai da gangar jikinta tunaninsa tunda har shima ya fahimci Hilal ne zaɓin Allah a rayuwarta, kamar yanda shima ya samu daidai shi.
'Allah Yasa hakan kake nufi.'
Ta furta a ƙasan ranta.
Sun wuni cur a gidan Kawu Kabiru tare da iyalinsa, tun Ramla na ƙin magana da faɗawa tunani har dai ta yi watsi da komai sai dai ta kasa yakice kalmar Ina sonki da Aliyu ya furta. Da zarar ta tuno a karon kanta sai ta saki murmushi.
Sai yamma suka bar gidan.
Haka ta ci gaba da rayuwa gidan kakanninta tare da su Jidda, duk kuwa hakan bai tafiyar da tunanin Aliyu ba. Abinda ke tsorata ta bai wuce yanda so da kaunarsa ke neman rinjayar zuciyarta ba. Har yakan maida tunanin Hilal gefe guda ya ajiye.
Sai da ya rage sauran kwanaki uku su koma makaranta sannan duk aka watse kowannensu ya koma gidansu, nan ma ji suke kamar kar a rabu.
***
"Wai ke ba za ki buɗe kofar ba? Me kenan hakan? Ba'a isa a faɗamaki ki ji ba?"
Muryar Maman twins ta bugi kunnuwanta, ta share hawayenta ta tattara hotunan ta maida mazauninsu sannan ta bude kofar fuska a haɗe.
Shigowa ciki Maman Twins ta yi tana fadin
"Allah Ya shiryamana ke Ramla, bansan sadda za ki rabu da wannan bakin ran naki ba. Haba jama'a! To sai ki fito Hajiya na nemanki."
Ta miƙe ta bi bayanta zuwa falon. Hajiya sosai ta buɗe mata wuta kan ba ta son irin haka, dole ta ba Hajiyar hakuri itama Rafee'ah ta bata.
Kafin su bar gidan sai da ya kasance komai ya wuce kamar ba su yi ba.
***
Kwanci tashi asarar mai rai, cikin ikon Mai Duka bikin A'isha ya taho gadan gadan, ana saura sati ƴan Daura suka dinga cika gidan. Wasu a can Yakasai wasu kuwa anan wurin Hajiya.
Ana saura sati a sanya A'isha a lalle Ramla ta ɗauki katukan daurin aure da na wuni ta kai ofishinsu. Ranar da ta kama Asabar kuwa, takanas ta shirya yara sai gidan Muhibbat wanda daga nan zasu wuce gidan Ramla rabon kati. Mutane biyu masu muhimmanci a 🕯️ *ƘARFEN ƘAFA*🕯️
_*Rufaida Umar*_
Bismillahir Rahmaanir Raheem
07)
Daga ita sai Affan suka fita. Unguwar Gwammaja nan suka soma nufa gidan Muhibbat don ta tabbatar idan ta shiga gidan Amrah za ta ɓata lokaci, ko ba komai an dade ba'a hadu ba dalilin tafiyar da Amrah ta yi zuwa Lagos tare da Maigidanta wanda rabin aikinsa a can ne.
"Don Allah ina iya ɗaukar fasinja?"
Muryar ɗan sahun ta katse tunaninta, ta kai duba ga wanda ke tsaye shima yana kallonta yana jiran amsa, abubuwa da dama hakan ya tunamata, ta daure ta dubi mai adaidaita fuska a haɗe.
"Ba haka muka yi da kai ba. Ko ka mance shata na ɗauka?"
Kafin mai adaidaita ya ce wani abu mutumin ya kauce gami da bata hakuri. Wannan tasa ɗan sahun fisgar abin hawar da alama ransa bai mishi dadi ba. Ta ƙara riƙe Affan kar ya tuntsira ba ta ko damu da yanda ɗan sahun ke shirga uban gudu ba. Hankalinta ya tafi ga tunani. Meyasa abubuwa da dama suke ƙin ɓacewa daga kwanyarta? Ba ta jin har ta mutu za ta mance da Aliyu.
***
_*ABIN ƁOYE*_
Tafiya na kara yin nisa, makonni na shuɗewa zuwa watanni, har ta kai lokacin da Ramla suka kammala aji na hudu a Sakandire suka wuce SS2 kai tsaye. A wannan lokacin idan ta ce ta huta daga tunanin Aliyu tasan ƙarya ne. Motsinta da komai ya zama shi, ramarta na tada hankalin Hajiya.
"Na tsammaci ko kujiba-kujibar bikin Rafee'ah ne ke ramar da ke yanzu kam na tsorata. Ki fadamin mene damuwarki? Ko ba ki ga yanda kika bi kika lalace bane? Idan ma tunanin aure kike ki tattara ki ajiye a gefe tunda sanin kanki ne Abbanki ba zai aurar da ke ba sai kin kammala Sakandire. Wannan ai shirme ne. Kalli yanda ko abin kirki ba ki yi ba a jarrabawa, ni ban ga amfanin wayar da Abbanki ya siyamaki yanzu ba, na tabbata kuma zai kara dauke hankalinki ne kurum daga karatu!"
Duk wannan bambamin da Hajiyar ke yi, Ramla na zaune tana fidda hawaye ga wayar da Abba ya damƙamata Nokia mai tocila rike a hannunta, ƙala Hajiya ba ta ce ba sadda aka yi budurin ba ta wayar sai bayan fitar Abban ta ke fitar da abinda ke ranta. To itama ta gaji! Ta gaji da tunanin mutumin da ba ta san inda za ta ƙara ganinsa ba. Tunaninsa na taɓa walwalarta, ya kasance ba ta murna da kiran Hilal, ba ta murna idan ya yi mata aike ta hannun Yaya Munir. Yakan tambayeta ko lafiya ta ce ba komai. Duk a rashin sanin cewa yanzun ba shi take da muradi ba, soyayyar wani can da ba ta san inda za ta ganshi ba, ya fi komai dagula lissafinta.
"Shikenan, kin yi shiru ina magana kin rabu da ni! Tunda haka kika zaɓa ki yi ta zama da kuncinnaki, sai dai wallahi kin ji na rantse muddin wannan shekarar a zangon karatunki na farko (1st term) naga ba ki tsinana abin a zo a gani ba, da kaina ba Muniru ba, zan kwace wayar na kuma hanaki fita. Shashasha kawai!"
Ta dawo nutsuwarta sa'ilin da Hajiyar ta miƙe za ta fice daga falon. Da sauri ta ƙarasa ta sha gabanta, kallon da Hajiyar ta mata sai jikinta ya yi sanyi, ta sunkuyar da kai tana ci gaba da kuka a hankali. Tsakanin ɗa da uwa sai Allah, ba ta san sadda ta ja hannunta ba suka zauna saman kujera.
"Menene Ramlatu? Kun samu matsala da yaron ne?"
Ta na nufin Hilal, ta tsinci kanta da gyaɗa kai.
"Amma mun shirya, don Allah kiyi hakuri Hajiya. Na miki alƙawarin chanjawa, wannan karon ba zan ƙara ba ku kunya ba a karatuna."
Jikin Hajiya ya yi sanyi, nan ta shiga yi mata nasiha akan kar ta sake ta sabarwa da kanta haka.
"Don kin yi faɗa da mutum bai zama dalilin da za ki sauya rayuwarki ba. Kenan ko kun yi aure haka za ki dinga yi? To kul! Shi rashin jituwa idan an yi nan take ake yiwa juna sulhu kuma a nemi gafarar juna. Idan ba mai fahimta bane sai ki bari idan ya huce daga baya ki nemi gafararsa. Wannan damuwar bana so, kar ki ƙara."
Ta amsa da to gami da godiya. A ranar ta yi kokarin sauyawa kuwa, ta rage kulle kanta a ɗaka tana tunane-tunane, gidan yanzu daga ita sai Auta A'isha tun bayan bikin Rafee'ah. Hakan da ta yi sai ya kwantar da hankalin Hajiya. Ita kuwa duk abinda take daurewa take gudun matakin da Hajiya za ta dauka a kanta.
Yau wunin gidan Rafee'ah zasu yi tare da Auta A'isha. Tun safe suka shirya Abba ya ragemusu hanya ya basu kudin mota. Sai da direbansa ya taremusu abin hawa drop har gidan Rafee'ah sannan suka rabu. A hanya suna tafe tana yin game na snake a waya, kusan a lokacin kaga budurwa da irin wayarta ba karamar babbar yarinya bace. Wannan ta sa take latsawa cike da jin ta isa.
A daidai junction suka tsaya, ba ta ankara ba ta ji an zare wayar daga hannunta. Cikin razana ta juyo har tana shirin fasa ƙara, yana kan mashin yake dubanta yana dariya. Kirjinta ya buga da ƙarfi, ta kasa gaskata cewa shi ɗin ne. Hakan ya sa ta lumshe ido ta kara budewa. Ya sauya, ya yi wani fresh, wannan karon ƙananan kaya ne cikinsa. Bakin jeans da riga green wanda ya karɓeshi sosai.
"Barkanki."
Ta yi kasa da kai gami da amsawa murya na rawa.
"Yauwa."
Ta ɗago ta mika hannu.
"Bani wayata."
Ta ƙarashe a kasalance, sai dai wani irin annashuwa take ji can ƙasan ranta, ta kasa daina murmushi. Kullum adduarta Allah Yasa ta ƙara ganinsa.
"Allah Ya karɓi addu'ata, ba zan bari ki tafi ban da lambarki ba."
Maganarsa ta katse tunaninta, ta saci kallonsa ya shiga latsa wayarta. Daidai nan aka basu hannu ya ce ma ɗan sahun su tsallaka sai su yi parking. Ba musu akai hakan. Ya danna kira wayarsa ta dauki ƙara, ta saci kallon wayar, wata ƴar ƙaramar waya ce Lg flip mai murfi ya fiddo. Wayarta ya miƙamata gami da kasheta da kallo.
"Nagode, Allah Ya kaiku lafiya."
Daga nan ya ja mashin ɗinsa sabo fil ya yi gaba, suma suka wuce. Ranar wuni ta yi cikin annashuwa, ji take kamar an mata albishir da aljanna.
Tun daga wannan ranar suka yi wani irin ɗinkewa da Aliyu. So da kauna mai karfi ya shiga tsakaninsu, duk kuwa a sannan ta ji cewar ya yi aure har tsawon sati hudu. Kishi mai tsanani take yiwa matarsa kuma ƴar uwarsa MUHIBBAT.
Duk yanda ta kai ga ɓoye alaƙarta da Aliyu abin ya ci tura don tuni Abin Ɓoye ya fito fili.
***
"Gwammaja daidai ina?"
Muryar ɗan sahun a zafafe ya katsemata tunanin baya da ta faɗa. Ta sauke ajiyar zuciya tana mai gyara Affan da ya fara bacci ta hau yin kwatance har suka isa kofar gidan Muhibbat. Ta sallami ɗan sahun ta tashi Affan, ya kuwa farka suka kama hanya.
Gidan Muhibbat take karewa kallo, gani ta yi kamar koyaushe ƙara ƙawatashi ake da sabbin furanni da kuma abubuwan ɗaukar ido. Da sallama suka sanya kai falon.
Matar gidan ba ta nan sai masu yi mata hidima su biyu sun shantake suna kallon fim na AfricanMagic Hausa. Sai kuwa yaran Muhibbat su biyu a saman kujera wasa. Babban zai yi sa'ar Ansar yayinda ƙaramin ya girmi Affan da kadan. Fuskarta ba baƙuwa ce garesu ba, aka gaisa, Mujahid da Ammar suka gaidata. Fuska a sake ta amsa kafin ta dubi Affan.
"Ba gaisuwa?"
Ganin haka ya sunne kai yana wangale baki.
"Bari a kirata." Cewar ɗaya cikin masu aikin tana nufar sama, yayinda ɗayar ta mike ta nufi kicin. Toh kawai Ramla ta ce tana mai ƙarewa gidan kallo lokaci guda tana kara jinjina arzikin mijin Muhibbat.
'Kin manta itama daidai gwargwado suna da rufin asiri?' Wani ɓangare na zuciyarta ta tunatar da ita wacece Muhibbat.
_*Mahaifinta Justice AbdulRazak Buba, tsohon alƙali ne a wata babbar kotu ta ƙasa. Ƴan asalin garin Kano ne gaba da bayansu, duk a zuriar Marigayi Malam Buba shi ne fitaccen mai arziki wanda sunansa ya shahara har wasu a zuri'ar kan ara su yafa. Babban family house ne wanda kusan duk ana tare wuri guda. Muhibbat ita kadai ce ɗiyarsa mace wacce yake so kuma yake matukar ji da ita. Ita ce kuma wacce kaddarar aure ya faɗa mata wanda a yanzun ya zama tarihi.*_
Ƙamshin turaren da ya mamaye falon ne ya ankarar da ita zuwan Muhibbat. Ta ɗago kai tana dubanta lokaci guda suka sakarwa juna murmushi mai nuni da tsantsar kauna da farin cikin ganin juna. A gefe guda kuwa kamanninta da ALIYU take ƙara gani zahiran wanda har Muhibbat kan rikiɗemata zuwa kamannin Affan wanda ke matukar kama da mahaifinnasa.
Fara ce mai matsakaicin tsawo, tana da siririn jiki sai dai ba mai muni ba. Gashinta luf-luf ya kwanta har saman goshinta. Mace ce mai hakuri kuma mai yawan fara'a. Ba ta daukar lamura da zafi. Cikar kamala dai Muhibbat ta kai, jaruma ce har gobe a idanun Ramlat, yayinda bata fasa yiwa kanta kallon zalamammiya kuma mai laifi a idanun Muhibbat ba.
"Kai Madam, kinga yanda kike ƙara mulmulewa kuwa? Anya nan gaba za ki nuna kin san mu?"
Muhibbat ke wannan kalamin sa'ilin da take zama da kamo hannun Affan, lokaci guda tana ƙarewa Ramlat kallo cikin dariya.
Harararta ta yi da wasa gami da jan guntun tsaki.
"Kin ji wata magana, ina hutu a wurina nida koyaushe ina hanyar Ofis? Hutu ai sai ku Hajiyoyi."
Suka dara.
"Ba ki kyauta ba, shi ne kika bar Ummina da Ansar a gida? Wannan autan na ƙagu ki yi aure a mishi ƙanwa ko ƙani mu ga ta autantaka."
Taɓe baki Ramlat ta yi sa'ilin da take kurɓar ruwan da aka ajiyemata.
"Ke kika san wannan, ni kam ai na rufe babin aure har abada."
Jiki a sanyaye Muhibbat take dubanta.
"Kar ma ki fara wannan tunanin, shi aure lokaci ne. Idan ya zo ko bakya so sai mun wanke ki mun kaiki. Kuma da yardar Allah ma kina so za'a yi shi. Duka-duka ashirin da nawa kike?"
Murmushi mai ciwo Ramlat ta yi, ta basar da zancen ta hanyar janyo jakarta.
"Kar ki dameni da wannan zancen, ni karɓi wannan."
Ta miƙa mata envelope da ta ciro, ɗaya na kamu da yini ne da za'a yi a Meena Event Centre yayinda ɗaya na dinner party ne da ango ya shirya a Marhaba.
"Allah Sarki mai sunan Mamana za'a fada kwaryar manya, toh Allah Yasa zamu gani. Ya kawo na ƴan baya. Ko Affan?"
Ta ƙarashe gami da rungume Affan wanda tuni ya sake yana dariya. Murmushi Ramla ta yi, zuwa yanzu masu neman ta yi aure dariya ma suke ba ta wasu lokutan.
"Akwai fa taro da za'a yi na family, har jikoki gaba daya. Ba ki da labari?"
Ta girgiza kai.
"Ba wanda ya fadamin, to wa zai fada?"
Harararta Muhibbat ta yi,
"Ai dole a fada ko don yarannan. Ina jin nan da sati biyu zasu gudanar. Zan biyo mu tafi tare da yarana."
"Toh." Shine kawai abinda Ramlat ta ce, ba ta wani jima sosai ba ta mike. Duk yanda Muhibbat ta so ta tsaya ta ci abinci ta nuna akwai wuraren da za ta je kan ta koma gida. Dole Muhibbat ta cika Affan da kayan zaƙi kala-kala ta takomata har farfajiyar gidan suka rabu. A hanya tana tafe tana tunaninta. So da kauna tsantsa idan an ajiye na ƴan uwantaka a gefe, Muhibbat ta nunawa Aliyu. A yanzun sai soyayyar ta koma kan yaransa. Har ta tsayar da adaidaita suka yi cinikin unguwar Gaida ba ta bar tuna tarin laifuffukan da ta aikata ga Muhibbat din ba.
***
*Son Zuciya*
Zaune take ta zuba uban tagumi ta yi shiru, kai ta ɗaga tana kallon ƙaton enlargement na hotonta da Aliyu. A ƙasa an rubuta sunansu. Aliyu Abdussalam Buba da Muhibbat Abdulrazak Buba. Za ta iya cewa ita ke son shi, son da take mishi ya hanata ganin aibunsa.
Tun suna yara suke shakkar haɗa inuwa da shi, don ko kusa ba ya wasa da su. Mutum ne wanda ya fita zakka a zuri'arsu, don kuwa a iya saninsu Aliyu giya ce da kwaya kawai za'a ce yana sha su ƙaryata. Ya soma shaye-shaye a ɓoye ba tare da sanin mutan gida ba. Hakan ya samo asali ne daga manyan ɓatattun yaran masu kuɗi da yake abota da su a sakandire, Innarsa Amina bafulatanar Gombe, mace mai hakuri wacce ba'a taɓa yin kace nace da ita ba duk kuwa da tarin facaloli da kuma kishiyoyinta biyu da take tare da su. Aliyu ɗa na fari a wurinta hakan yasa koda wasa ba ta sakewa da shi. Kusan rayuwarsa ya yi ta ne a hannun kakarsa Abulle matar Marigayi Malam Buba. Da wuya ka ganshi cikin gidan Mahaifinsa Abdussalam sai dai sashin Abulle wacce ta dauki son duniya ta ɗora akan Aliyu. Wannan tasa a duka yaran Malam Abdussalam, Aliyu ne kadai ke makarantar manyan masu kuɗi irin na yaran Justice bisa jajircewarsa akan shi ba zai yi makarantar da za'a rainashi ba. A sannan sai da Mahaifinsa ya ji kamar ya mishi duka don shi mutum ne mai zuciyar nema da kuma son kyautata iyalinsa da daidai karfinsa. Yana aiki a ma'aikatar ilimi ta gwamnati. Mahaifiyar Aliyu ita ce matarsa ta biyu. Yana sonta da kuma tausayamata ganin ita kadai ce ya auro daga nesa.
Abulle ce ta dage Justice ya mayar da Aliyu makarantar yaransa, wannan abu ba ƙaramin bakin jini ya janyo wa Aliyu wurin iyalan Justice ba idan ka cire Muhibbat da ke jin kamar ta zuba ruwa a ƙasa ta sha don dadi.
A hankali bayan sun tasa, ta tattara ta koma gidan Abulle da zama itama kawai don ta dinga sanya Aliyu a idanunta. Ranar farko da ta soma ganinsa a makaranta yana shaye shaye da abokansa, ranar ta gigita. Za ta gudu ya kamata ya fallamata mari dama da hagu akan yanda ta gani ta binne a nan kar ta sake ta fadawa wani ko wata a gida. Wannan ta sa ta kama bakin dole. Abin mamaki soyayyar da take mishi bata ragu ba sai ma tausayi da yake ba ta. Kewarta da yayyunta suka yi har ma da iyayenta ta sa Justice da kansa ya zo ya lallaɓa Abulle dakyar ya tafi da ita. Abulle ta rantse kaf a jikokinta Aliyu da Muhibbat ne ƴan gaban goshinta.
Aliyu na aji na biyu a jami'a kowa ya fahimci mummunan ɗabi'ar da ya faɗa na shaye-shaye, karatun ma ba ya bar maida hankali, kullum yana daki yana bacci. Taro kuwa na family an yi akan Aliyu ya fi a kirga, Innarsa kan shiga daki ta yi kuka son ranta. Shi kadai namiji da Allah Ya bata sai kannensa mata uku, sai dai ya zamemata wani tambari wanda ake faƙewa da shi a ci mutuncinta. Mahaifinsa kuwa ya ce sam ba zai yarda ba sai dai yaronsa ya koma gabansa. Wannan ne silar komawarsa gidansu.
Duk wannan bai sa Muhibbat ta fasa so da tausayin Aliyu ba, takan rufe kanta a daki ta ci kuka ta kuma bishi da kyakkyawar addu'a akan Allah Ya shiryeshi.
Rayuwa ta yiwa Aliyu zafi yakan ji kamar ya yi hauka duk ranar da Babansa ya kulleshi a ɗaka ya hanashi fita ko nan da can. Makaranta dama ba labarinta don tun ranar da aka rabashi da gidan Abulle ya zuciya ya ce ya fasa karatun gaba daya. Ranar da ya ɓalle ya fice daga gidan, bai koma ba sai da ya yi mankas. A ranar Innarsa ta yanke jiki ta fadi. Tun daga wannan rana ba ta ƙara lafiya ba. Ciwon Innarsa ya sanyaya jikinsa kadan, duk da a ganinsa matar sam ba ta damu da shi ba hakan bai mantar da shi matsayinta wurinsa ba.
Bayan farfadowarta ya daukar mata alkawarin ya dainawa, ba ta ce mishi uffan ba har ya fice. A hankali kuma ya dinga ɓoye munanan halayyarsa, ya maida turare abin fesawarsa, ba ya taba yarda ya zauna na awanni da yan uwansa gudun kar a ga sauyawar leɓɓansa adalilin shan taba. Sai dai ya zama masifaffen karfi da yaji, ya daina ragawa duk wata mace da za ta gasawa Innarsa magana. Akwai ranar da ya kusan yiwa Amaryar babansa duka duk don ta zagi Inna a fakaice. Wannan ya fusata Baban ya ce ya bar mishi gidansa. Zuciya irin ta Aliyu ya sanyashi haɗa komai nasa ya koma gidan Abulle. Ba abinda ya boyemata har da karin gishiri, nan kuwa ta tara meeting ta gargadi kowa akan takurawa Aliyu da ake.
"Duk wanda ba zai bi shi da Addu'a ba kar ya zageshi ya kara bin duniya. Kai kuma Abdussalamu ba ka isa ka rabashi da gidan ubansa ba. Ko yau yaro ya ga dama zai je. Don kunga an samu ya soma gyaruwa shikenan kuma sai ku kara sanyashi ya bi duniya? Ke kuma Amarya ki ci gaba, idan dai za
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 5 Chapter of 58