ga ƴarsa bai sa ya ɗauki zafi irin na yau ba. Duk cikin yarannata ta fi su sanya da kuma yanke hukunci cikin sanyin zuciya ba da hargagi ba, ta san Alƙali magana daya yake, idan kuwa ya yi to fa shikenan ta zauna. Yana da wahala ya yi ja in ka da ita, yau kam ko daga yanayin fuskarsa za ka fuskanci ransa dagaske a ɓacen yake don har wani ja-ja yake yi.
"To ai shikenan, zan aika kauye wurin Shehu,(mijin mai tayata aiki Ladidi da ta damƙa mishi amanar kiwo) ko bijimina ne sai a siyar na ba shi. Amma ka yi hakuri ka tambayeshi wanda ke binsa bashi ka biyamishi. Ka yimin wannan alfarmar domin Allah da Annabi s.a.w. Yaronnan maraya ne, babansa bai da karfi. Ni ce komai nashi, hannunka ai ba zai ruɓe ka yanke ka yar ba."
Ta yi maganar cikin karaya har da sharar kwalla, yasan har yanzu dai ana jika. Abulle ba za ta taɓa bari Aliyu ya san zafin nema ba da kansa, kowane gata burinta ta yi mishi. Ganin hawayenta ya sa shi saurin magana.
"Shikenan, bashi ko? Zan biyamishi, zan tura da kaina wurin Alhaji Yusha'un da ya ce yana binsa. Na san mutumin a yanzu shi ne shugaban ƴan kasuwar kwarin, da kaina zan biya. Wannan ya miki?"
Sai ta hau dariya da sanya albarka. Haka ya fita yana kara jinjina kaunar jika da kaka dake tsakanin bayin Allahn.
***
*Bayan Watanni Biyu*
Allah Madaukakin Sarki Mai sauya dukkan lamura, Shi ke da ikon mayar da talaka Sarki, ya kuma maida Sarki talaka. Kamar haka, Ya kawo sauyuka masu dama a rayuwar auren masoyan.
***
Handout ne a hannunta tana haskawa da fitilar waya. Ta bararraje a kan gado daga ita sai karamin vest da gajeran wando. Mace ce mai gashin jiki, ga zufa. Duk da kasancewar ta bude winduna ta daga labulayen dakin, hakan bai hanata jin zafi ba, karatun ma ba shiga yake ba. Aliyu kuwa tunda ya sa ƙafa ya fita da maraice, har yanzun karfe takwas na dare ba shi da niyyar dawowa.
Ta miƙe tana jan tsaki ta hau rage kaya ta faɗa wanka. Wankanta na biyu kenan daga Magriba zuwa lokacin. Ta goge jiki, wannan karon bata bi ta kan undies ba, ta zura karamar rigar bacci mai jikin cotton, duka-duka tsawonsa iyaka guiwarta ne. Ta tufke gashinta wanda rabonsa da relaxer tun na aure. Hakan yasa ya kakkarye, kitso kawai take buƙata yanzun.
"Haka za'a rayu babu wuta? Nepa ma ba samu ake ba? Tab."
Ta furta a fili, za ta iya cewa tun tasowarta ba ta san matsalar wuta sosai ba a gidansu. Koda zasu rasa wuta, na ƴan kwanaki ne. Yanzun kuwa a gidan Aliyu ta haura wata bata ga kyallin wuta ba. Ƴan Nepa sun musu zagaye ya fi kirga akan su biya kudi sai dai Aliyu ya ce bai da halin biya, suka gaji suka yanke jonin direct din da suka yi.
Banda wannan ma lamura da dama sun sauya, idan ta ga Aliyu ya yi cefanen kaza toh fa wata ribar mai tsoka ya ci a kasuwa. Naman miya na neman kakare musu. Duk wata cima ta jin dadi ya ja baya. Ta miƙe a hankali ta fito zuwa falo ta na kallon farfajiyar gidan. Motar Aliyu na nan kamar yanda ta zata don a yanzu sai ya shafe kwanaki biyu na bai fita da mota ba sai mashin da ya siya, duk a dalilin jarinsa ya karye.
Jingina ta yi jikin window ta kurawa hasken farin wata idanu tana tunani. Tunanin gidansu take, tunanin yanda aka yi watsi da lamuranta. Abba ya hanata taka gidansa, duk sadda ta ce za ta je sai ya ce mata duka-duka yaushe ma aka yi auren. Karshe ya rantse idan ya ga kafarta a gidan yanzu zai saɓamata.
*"Kewarku nake Abba, kewa sosai, babu wanda ke zuwa gidana, daga dangin Aliyu har ku, ya kuke so nayi da rayuwata? Har yanzu ba ku bar fushi da ni ba?"*
*Tana jin sadda ya yi murmushi mai sauti.*
*"Kiyi hakuri Ramlatu, muna sonki ne, da ba ma sonki ba zamu tayaki son abinda kike so ba kinji ko? Ki shekara tukunna, ki shekara. In sha Allah a sannan ko ba ki fadamin ba, ki taki da iznin mijinki ki zo mu gaisa. Hakan ya miki?"*
*Ba haka ta so ba, sai dai kuma babu yanda ta iya, ta amsa da toh yayinda kwalla suka cikamata idanu. Ba za ta iya fadawa Abba cewa Aliyu na shan taba ba har a gidan kuma a gabanta, tasan dariya zai yi mata. Don haka suka yi sallama bayan ta bada saƙon ya gaida Hajiya domin ba ta daukar wayarta.*
Ramlat ta sauke ajiyar zuciya, ɗumin da ta ji a saman fuskarta ya tabbatarmata da zubar hawayenta, ta sa hannu ta share. A yau ta tsinci zuciyarta da kewar ƙawa kuma aminiyarta Amrah. Gashinan dai makarantarsu ɗaya, abinda suke karanta ma ɗaya, sai dai koda wasa Amrah ba ta taɓa bata fuskar da za su gaisa ba balle magana ta haɗasu. Ranar da ta taɓa kuskuren yi mata magana, nan take Amrah ta yi mata Allah Ya isa idan ta kara nunawa ta santa. Wannan ne ya bata haushi har ta kasa ɓoyewa ta sanar da Aliyu, sai da ta yi danasanin fadamasa da ta yi don zagin Amrah ya yi, irin ashar din da idan wani zai ce mata Aliyun ya iya, za ta musanta.
*"Babu ke babu ita! Babu ke ba ita! Kika kara ma kulata nima ban yafe ba!"*
Kalamansa sun mata tsauri, ta yi danasanin furtawar da ta yi, kusan ma ba ya ganin mutuncin kowa nata yanzu, daga ta soma batun kewar gida zai ce ai basu damu da ita ba.
Tunaninta ya katse sadda ta ji ana ƙoƙarin bude ƙyauren gidan. Ta sa hannu ta share hawayenta gami da goge gumin da ya tsastsafo a goshinta. Maimakon ta ganshi da mashin, sai ta ganshi shi ɗaya, abinda ya daure mata kai bai tsaya rufe kofar ba ya soma kokarin nufo cikin gidan. Tabbas dai Aliyun ne kamar yanda farin wata ya haskamata fuskarsa da kuma t-shirt fa jeans din jikinsa.
A gaggauce ta koma daki ta sanya dogon hijabin sallarta kuma na zuwa makaranta har ƙasa ta fito rike da fitilar wayarta. A barandar kofar falon suka yi kiciɓus.
"Oops! Baby sorry. Ina mangareki ko?"
Ta hau murza idanunta, kirjinta ya shiga bugun tara-tara. Ga abu dai a gabanta amma ta kasa gaskatawa, hakan yasa hannu na rawa ta dago ta haske fuskarsa ido a waje.
"Aliyu?" Ta furta cikin tabbatarwa da kuma alamar tambaya lokaci guda, kafafunta ta ji sun hau wani irin mazari, kwakwalwarta ta kasa daukar abinda ta gani a fuska da yanayin gangar jikin Aliyun.
"Bani hanya Malama." Ya kara fadi cikin muryar ƴan maye. Ba ta da niyyar kaucewa ya kuwa bangajeta ta fadi ƙasa ya shige yana kundumar ashar. Ta kama leɓɓanta biyu da hannunta na hagu kamar mai karɓar punishment a makaranta, kukan take yi amma gani take kamar idan ta bude bakin ihu ne zai fito madadinsa. Tunawa da ta yi kofar gidan a bude yake ya sanya ta miƙewa ta je ta rufe. A hanzarce ta koma ciki, a falon ta sameshi ya zube anan kasan tiles yana maganganu barkatai marasa ma'ana da tsari.
"Aliyu? Innalillahi wa inna ilaihir raajiun! Aliyu me zan gani? Me..me...me?"
Ta kasa ƙarasawa tana sheshshekar kuka, ta zube a gabansa.
"Aliyu ka ce mafarki nake, don Allah ka daina yimin irin wannan wasan. Na yarda na sani taba kawai kake sha, ka bar yimin wasan maye, wallahi ba zan iya dauka ba. Na shiga uku ni Ramlat."
Ta ƙarashe tana mai riko hannunsa. Cikin wani irin dariya na shaƙiyanci ya kamo tufkar da ta yiwa gashinta da iyakar karfinsa har ta saki ƙarar azaba.
"Keee, au baby...don uwarki da kika aureni ba ki...san...ina..hawa...sama...ba? Baby...kin cinyemin kuɗina...na talauce...amma na tsira da hawa gajimare..."
Ta yi nasarar ƙwatar gashinta, da wani karfin zuciya don kuwa yanzun ba ta jin kowane karfi a jikinta ta mike za ta gudu daki, ba zato ta ji ya riƙe kafar sai ga ta yiff! Ta fadi saman tiles, baki da goshinta suka ƙumu a ƙasa. Kan ka ce me sun yi suntum! Kuka sosai ta soma.
"Ka kyaleni Aliyu! Don Allah ka rabu da ni karka kasheni!"
Ta firta jikinta na mugun rawa, za ta iya rantsewa ba ta taɓa yin ido hudu da mutum yana maye ba sai a ranar. Ta fi gani a akwatin talabijin.
Jikinta na rawa bai fasa rabata da hijabi ba kuma ya ketamata t-shirt din dake jikinnata ba, ya shiga sarrafata ya dora dukkan karfinsa a kanta. Fadi yake.
"Shege G-Baba...ya ce na yi son raina dake na huce....Baby farar ƙafa gareki...ubanki bai ban komai ba....Hahaha..uban Muhibbat har gida ya ba..."
Bai karasa ba sakamakon hankaɗashi da ta yi ya bugu jikin kujera, ta mike a guje ta shige ɗaki ta rufe da muƙulli. Anan cikin duhun ta zube ta shiga rera uban kuka, innalillahi wa inna ilaihir raajiun kuwa, ta ambata ya fi dubu. Aliyu mashayi?
Wani irin dunkulewa ta yi a wurin ta shiga risgar kuka. KEWA, yau kewar iyayenta da ƴan uwanta take ji. A yau ta yi dakacen biyewa zaɓin ranta. Tausayin kanta ne ya lulluɓeta. Ta yi kukan mai isarta, tana jin yanda yake surfamata ashariya ta uwa da uba mara kyawun sauraro, ya gaji da bugu ya kife anan, tana jin fita da saukar munsharinsa. Miƙewa ta yi kanta na wani irin bala'in sarawa ta zura doguwar riga, ta tattare takardun ta kwanta saman gado,yanda ta runtse idanu haka ta budesu. Baccin ya tafi, damuwa da bakin ciki sun tararmata sun tsaya a ƙahon zuciyarta. Nan da nan zazzaɓi ya sauka a jikinta, haka ta kwana tana rawar ɗari.
***
Sanyin asuba da kuma iskar dake kaɗawa ce, ta tasheshi daga baccin da ya shimfiɗe yana yi, ya bude ido gami da tallafe kansa da ya yi mishi wani gingirigim. A hankali hasken wayar Ramlat ta taimaka mishi wurin gane inda yake kwancen. Zumbur ya mike tsaye, komai ya dawo mishi tiryan-tiryan. Bai mance yanda ya sha magungunan mura na saka maye a tare da su Sa'ad ba a club. Ya je musu da ɓacin ran yanda a yanzun kasuwancinsa ya ja baya babu wani albarka, har ta kai ya rage facaka yanda ya dace, suka duramasa abin maye, ya yi ta sha babu kakkautawa duk domin ya ji sanyi. Bai kuma mance yanda suka kawoshi gidan ba, yana da tabbacin mashin dinsa ma can ya bari.
Wani wawan tsaki ya ja, ya gaji da wani ɓoye-ɓoyen banza. Shi da gidansa? Ai dole ma wataran ta san halinsa. Maimakon ya kwankwasamata, sai ya wuce dakinsa ya kara shimfidewa saman gado, babu tunanin tashi sallar Asuba.
A gefen Ramlat kuwa, dakyar ta iya lallaɓawa ta yi alwala ta yi sallah, jiri sosai ke kwasarta, ta mike ta koma saman gado, kwanciyarta ba jimawa ta ji amai na yunkurin tasomata. A guje ta faɗa banɗaki ta shiga yunkurin sai dai banda ruwa ba abinda ke fita. Ta gaji da yunkurawar ta wanke baki ta fito. Kifewa saman gadon ta yi ta shiga rera sabon kuka, tunaninta kawai mutuwa za ta yi. Babu wani mai sanyaya zuciyarta a yanzun, Aliyu tana fushi da shi, fushi mai tsanani. Gani take ta tsaneshi, ba kuma za ta iya ci gaba da zama da mutum mashayi ba.
***
Motsin bude ƙyauren gidan ne ya farkar da ita daga azababben baccin da ya kwasheta ba tare da ta shirya ba. Rana tarr a saman kanta, Allah Ya taimaketa ma babu makaranta, Asabar ce. Ba laifi jikin da sauki sai dai ciwon kan bai sauka ba, bakinta babu ɗanɗanon komai. Wanka ta faɗa. Doguwar riga jallabiya kawai ta zura ta daure kanta da ɗankwalinsa.
Cikin faduwar gaba ta bude kofar falon, don bata da tabbacin fita ya yi ko shigowa. Ganin ba kowa sai wayarta da kaya a yashe saman kujera ya bata tabbacin shi ne ya maido su wurin. A hankali ta taka ta dauka ta kai daki, gaban madubi ta kara tsayawa tana kallon yanda goshi da bakinta suka kumbura suntum. Hawaye ta shiga fitarwa, ba ta isa ta je wa Abbanta da wani zancen ba akan Aliyu. Sai dai kuma shi kadai ne ke sauraron ta, banda shi ko waya ta kira su Zulaihat sama-sama suke amsawa.
Kicin ta koma ta dafa ruwan shayi da kayan kamshi kamar yanda Hajiyarta ke yi, ta zauna tana sha. Ba ta jin cin komai don haka ko kulolin tuwon da ta yi ba ta kalla ba balle ta iya ɗumamawa.
Babu abinda ta iya gyarawa a gidan, nan falon ta naɗe tana rawar sanyi, ciwon kai ya fi na baya. Ruwan shayin da ta sha shima haka ta amayar da shi. Bacci wahalalle ya kara daukarta, ba ta ji ƙarar shigowar mashin dinsa ba, sai jin hannunsa ta yi saman goshinta. A firgice ta farka, ganinsa ya sanya ta zabura za ta ruga ɗaki. Ya riketa gam a jikinsa, kawai sai ta fashe da kuka jiki na rawa.
"Don Allah ka yi hakuri ka rabu da ni, na tsaneka Aliyu, meyasa ka ɓoyemin munanan halinka? Wallahi ba zan iya ci gaba da rayuwa da kai ba."
Ya ɗago fuskarta yana mai riko haɓar.
"Baby wannan shi ne so? Don kin ganni a halin da ƙaddara ta jefani shi ne za ki gujeni? Baby maimakon ki ji tausayina ki tayani addu'a? Meyasa kika zo kusa da ni? Kalli yanda na ji miki ciwo? Baby baki da lafiya, jikinki zafi, muje ki sanya hijabi na kaiki asibiti. Kinji?"
Cikin karfin hali ta fincike jikinta ta faɗa saman kujera tana sheshsheka.
"Kar ka kara kirana da Baby. Wannan kuma ba ƙaddara ba ce, son zuciyarka ne! Kana saɓawa Allah kana kiran hakan kuma da suna ƙaddara? Wallahi sam ban yarda ba!"
Kalamanta sun soma yi mishi zafi sai kuma ya danne, lallaɓata kawai yake don ba ta jin dadi, don kuma wani abu da ya ƙudurta a ransa game da itan. Wannan tasa ya gane faɗa da zafi ba nashi bane. Ɗakinta kawai ya shiga ya fito da dogon hijabi ya taho da wayarta.
"Haba, ashe wayarki ba chaji shiyasa na yi ta kira bana samunki. Muje idan mun fita na bada chaji. Ki tayani addu'a, akwai wani ciniki da zan yi yau, idan ya faɗa har kaza zan siyomana, na kunna mana inji. Rashin wutar ya isheni."
Maimakon ta ji sanyin kalamansa, sai ta kasa jin hakan. Asalima baƙaƙen maganganun da ya jefeta da su a daren jiya har da zagin iyayenta sun fi komai tsayuwa a ƙahon zuciyarta. Ta haɗiye komai ta danne, ita kanta yanzun tana bukatar a duba lafiyarta, tana jin jikinta kamar babu jini balle ruwa, kamar ma a yau ɗin za ta mutu.
***
"Congratulations, kina da ciki wata biyu."
Kalaman da ke fitowa daga bakin likitiyar suka sanyata jin hanjin cikinta kamar zasu tarwatse.
"Ciki kuma? Dama haka ake cikin?"
Abinda ta fadi ya sanya daga Aliyun har Likitar dubanta, shi Aliyu ko fuskarsa kadai ka kalla za ka san yana murna da hakan duk da cewa yana auna yanda nauyi zai ƙara hawa kansa.
"Yes ciki, haka report ya nuna. Yaushe rabon da ki ga al'adarki?"
Tsabar rudewa ma ta mance da wani batun al'ada, ita tun zuwanta gidan Aliyu ba ta taɓa ganin jini ba. Shima Aliyun sai a sannan ya ankara da hakan. Maimakon ta yi murna, maimakon a ga tana dariya sai ta rike cikin tana kuka kamar wacce aka fadawa ranar da za ta mutu.
"Bana so, wallahi bana so! Dr ki zubar da shi."
Wani wawan mari Aliyu ya dauketa da shi. Ta rike ƙuncin a zabure ta mike tana dubansa cike da dumbin mamaki.
"Haba Malam, matarka ta sunnah? Ita za ka mara? Wane rashin hankali kenan? Koda ta yi kuskure ba ka ganin yarinya ce, bai kyautu ka lallaɓata ba? A ina aka taɓa marin mace, matar ma ta sunnah?"
Bai ko kalli Likitar ba wacce haushi da takaicinsa ya kamata. Ta zagayo ta kama hannun Ramlat da gaba daya ta gigice kukan ma ya tsaya cak. Ashe dai akwai marin da ya fi karfin kuka.
"Please get out. Ka bamu wuri."
Yana huci ya yi kwafa gami da hadata ita da Ramlat din ya watsamusu wani banzan kallo, har ya kai ƙofar ya juyo ya hau magana.
"Kika kuskura kika yi gangancin zubarmata da ciki, daga ke har ita sai na yi shari'a da ku!" Daga haka ya fice gami da banko ƙofar da ƙarfi har iskar na bugunsu. Dr Sadiya ta zauna kujerar da Aliyu ya mike, sannan ta maida Ramlat din mazauninta suna fuskantar juna.
'Ga ta a haka yarinya mai hankali da nutsuwa, sai dai da alama ba ta yi dacen miji ba.' Cewar Dr Sadiya a ƙasan ranta. Tausayin Ramlat ya kamata,ta danne ta soma yi mata nasiha.
"Ramlat ke fa musulma ce, cikinki koda shege ne ya haramta ki zubar balle kuma cikin sunnah. Ba ki yi kama da mutuniyar banza ba, ba kuma ki yi kama da mata ballagazazzu ba wadanda basu je makaranta ba. Ko mene ya yi zafi a rayuwarki, ki dinga tunawa da Allah. Shi ne Mai yaye dukkan wani azaba. Ki kwantar da hankalinki, idan ma haihuwa kike tsoro ki miƙa lamuranki ga Ubangiji, In sha Allah sai kiga kin haihu lafiya. Mutum nawa ne za ki ga su na neman haihuwar ba su samu ba? Wata ma da kudi za ki ga ta zo nan tana neman maganin da za ta sha ta samu ciki. Wata kuwa har kuka take yi tana faɗin yanda miji da danginsa ke wulaƙanta ta duk akan ba ta haihu ba. Ke kuma da Allah Ya ba wa cikin ma na sunnah ki ce bakya so? Kenan kina nunawa Ubangiji ba ki yi murna da kyautarSa ba?"
Ta girgiza kai tana share hawayen da sai a sannan suka zubo, so ta ke ta ce ba haka bane, so ta ke ta ce yaron ko yarinyar da ke cikinta, ba ta so su dauki ɗabi'un mahaifinsu, sai dai kuma ba za ta iyaba. Ko ba komai wannan sirrinsu ne.
Dr Sadiya ga ci gaba da lallaɓata da ba ta shawarwari har sai da Aliyu ya gaji ya dawo ofishin.
"Wai me ake yi? Ni fa zan iya barinki ki kwana anan idan ba ku kammala ba."
Ya yi maganar a fusace, Ramlat ta mike ta yiwa Dr Sadiya godiya, ita kuwa ta miƙa wa Aliyu file din suka fita. Tun a asibitin tana jinsa yana jan tsaki har dai suka siya magani suka fito yana mitar kudinsa sun kare.
"Wallahi injin ma na fasa kunnawa, kudin sun ƙare. Zan dai siyamaki kazar tunda na sakamaki rai."
Gyada kai ta yi kamar kadangaruwa, fuskarta duk ta kumbura saboda kuka. Bini bini sai ta shafi cikinta. Iskar mashin na neman yi mata yawa don haka sai ta dukunkule ta kwantar da kai kadan a gadon bayansa. Hakan da ta yi dukkansu sai suka ji wani sanyi da kaunar junansu yana kara ɗarsuwa a zuƙatansu.
"Ina sonka Sweet Aliyu, ba zan iya rabuwa da kai ba."
Ta furta a hankali, kalaman sun ratsashi. Ya yi murmushi gami da ɗan rage gudu.
"Baby wa ya ce miki zan iya rabuwa da ke? Ai mai rabamu sai mutuwa Baby. Don ina shaye-shaye addu'a za ki yimin har na daina, kin ji?"
Ya ji sadda ta gyada kai a jikinsa, kusan a tare suka yi murmushi. Murmushin tana yi hawaye na zuba, zuciyarta ta kasa tsanar Aliyun. Soyayyarsa da na abinda ke cikinta suka haɗarmata. Ta kuma daura ɗamarar faɗa wa Allah matsalarta akan Ya shiryamata mijinta.
Sai gashinan Gen din da yake cewa ba zai tayar ba, sai da ya siya mai rabin galan ya kunna suka ga haske. Ranar tattalinta ya dinga yi gami da fadamata karya da gaskiya duk don ta ji tausayinsa ta kuma yarda ba'a son ransa ya soma shaye-shaye ba. Ya kuwa ci galabar hakan.
***🕯️ *ƘARFEN ƘAFA*🕯️
*_Rufaida Umar_*
Bismillahir Rahmaanir Raheem.
_Assalamu alsikum ƴan uwana. Na gode sosai da addu'oinku. Allah Ya bar zumunci. Ameeen ameeen._
17)
Tun fitowarsu take bin bayanta, har suka bar wurin jama'a sosai. Tsayawa ta yi cak gami da juyowa a fusace.
"Wai Malama bibiyar ta menene? Me kike nufi? Kin san ni ne?"
Maganar ko kadan ba ta fusata Ramlat ba. Asalima hawaye ta soma ƙoƙarin zubarwa. Amrah da sauri ta kauda kai gefe, ba ta son ko kusa ta karya zuciyarta, ita kanta ta yi kewar aminiyarta sai dai kuma tunda har hakan ta zaɓamusu zai fi.
"Kiyi hakuri, don Allah ki yi hakuri ki yafemin Amrah. Kowa yan guduna, idan kema kin gujeni wa nake da shi? Da ke kadai na saba shawara, ki yi hakuri ki yafemin kuskuren da na maki."
A ɗan sace Amrah ta kalleta.
'Ta rame.' Ta ayyana a ranta. A fili kuwa ƙara tamke fuska ta yi gudun kada ta nuna rauninta a fili.
"Ai ba ki yimin laifin da na riƙe ki da komai ba. Mutum duk abinda ya zaɓarwa kansa, sai a zuba ido a bar shi da zaɓinsa. Ba ma miki mummunan fata ko kadan."
Ta juyo don ta san idan ta ci gaba da tsayuwar tsaf Ramlat za ta kalamance ta. Yanzun sai ta sauya dukkan ra'ayinta.
"I am pregnant."
Ta furta a hankali bayan ta kara matsawa gaba kadan. Cak kuwa Amrah ta tsaya, ta juyo tana dubanta. Gyada kai ta shiga yi tana share fuska.
"Eh Amrah."
Har ga Allah jin cewa tana da ciki ya sanyayawa Amrah jiki.
'To ko wannan shi ake kira rabo? Wannan auren kaddarar Ramlat ce.'
Ta yi maganar a zuciya, ganin jama'a na kallonsu ya sanya Amrah magana.
"Allah Ya raba lafiya. Na miki murna sosai. Kinga ana kallonmu, ki wuce gida kawai, gobe ma hadu a makaranta. Na yafemaki."
Ta ƙarashe da dan murmushi. Ramlat ta ɗan rungume kafaɗarta tana ƴar dariya. Ko ba komai za ta maido amintarsu.
Tare suka jera suka fita waje, abin hawa ne ya rabasu. Hatta Amrah sai sannan zuciyarta ta yi sanyi.
***
Kofar falon a bude, wannan ya kara tabbatar mata da zargin maigidan na nan, tun a bakin ƙyauren ta ga motar da a yanzun ta shaida na abokinsa G Baba ne. A gajiye take lis amman murnar shirinta da Amrah ya mantar da ita hakan.
Tun kafin ta saka ƙafa a falon, ƙaurin sigari da kuma hayaƙinsa ya baƙunci hanci da idanunta. Hira suke suna haɗawa da ashariya. Ji ta yi zuciyarta na tashi. Ta daure ta karasa shigowa falon da sallama. Suka dubeta. Aliyu ya saki murmushi.
"Baby, kin dawo?"
Gyada kai ta yi, don takaici ko kallon G Baba ba ta tsaya yi ba balle su gaisa ta yi ɗakinta. Zama ta yi bakin gado ranta na wani irin zafi. Kallon agogon bangon ta yi, shida na dab da yi. Kwafa ta yi ta rage kayan jikinta fa faɗa wanka.
A falon kuwa, G Baba ya zuƙi sigari ya fesar.
"Madam dinka fa ba ta yi murnar ganina ba. Hala ba ta son wannan hayaƙe-hayaƙen?"
Wani tsaki Aliyu ya ja, ɓacin rai sosai Ramlat ta jazamishi.
"Don uwarta an fadamata ni ban isa da gidana bane? Ko an fadamata shashashan miji ne? Zan je na sameta ai! Sa'arta ɗaya tana dauke da Baby."
Wani mugun kwarewa G Baba ya yi, Aliyu ya tsaya cak yana kallonsa.
"Lafiya? Ka zuƙa over Malam."
Sai da G Baba ya kora ruwa sannan ya samu nutsuwa. Ya ɗan dubi kofar dakin sannan ya juyo ya kalleshi.
"Ciki? Kai murna kake Madam dinka ta haihu yanzu? Kasan irin nauyin da zai ƙara hawa kanka kuwa? Wani fita eh yane, wani hawa gajimare duk raino zai sa ka daina. Kai Zaki! Yawane wallahi! Nawa kake ma yanzu? Gaskiya ku san abin yi game da cikin."
Aliyu
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 14 Chapter of 58