kalli ƙafar benen ta tabbatar babu mai saukowa sannan ta amsa a fusace.
"Ina jinka."
"Ya ake ciki?"
Ta safe goshi gami da runtse ido cikin soma gundira da tunani.
"Ni kaina na gaji da tambayar kaina. Abinda ya fi shi ne zan nemi Halima har gidansu na bincika."
"Ga dukkan alamu lamura sun ɓaci."
"Ina tsoron hakan ta kasance."
Ba ta jira cewar Kawu ba ta kashe kiran.
"Zeenat."
Da wani irin ruɗewa ta juyo tana dubansa, yana dafe da goshi a hankali kuma ya shiga saukowa daga matattakalar. Ta yi kokarin saita kanta ta karasa gareshi da murmushin yaƙe.
"Sannu, ka sha bacci."
Hussein ya gifta ya karasa ya zauna saman kujera kansa na ci gaba da sarawa.
"Me ki ka ban na sha?"
Ya tambaya ba tafe da ya kalleta ba. Ta zauna gefensa.
"Ba ka samun bacci yanda ya kamata, ga gargadin likita da ya ce ka dinga samun hutu, shiyasa na sanyamaka maganin bacci a lemu na kashe wayoyinka."
Ya dubeta da idanunsa da har sannan ba ya jin baccin ya sakeshi.
"Haba Zeenat, shi ne dalilin sanyamin maganin bacci? Meyasa haka? Wane irin hutu ne ba na samu? Cuta ba ta Allah ba ce?"
"Hakane, to ka yi hakuri." Ya mike rai a ɓace ya ɗauki wayoyinsa ya haye sama. Ta bishi da kallon munafuki karon farko a rayuwarta.
"Ka ci darajar son da nake maka Husseini, da yau sai ka gane shayi ruwa ne."
Ta furta a hankali yanda ta san ba zai ji ba. Har hango hotonsa da Ramlat ta ke yi a kwayar idanunta. Takaicinta, meyasa ba ta nemi kwararrun ƴan daba sun aiwatar mata da komai ba? Meyasa sai Halima?
Ta ja tsaki tana sharce gumin da fargabar ko Hussein ya ji wayar da ta yi ya haifarmata.
***
"Ita kuma wace ce wannan?" Hisham ya tambaya yana karewa Halima da ke faman sharɓar kuka a bayan cell kallo.
"Sharrin shaiɗan ne wallahi, don Allah don Annabi s.a.w ku yafemin wallahi nayi alƙawari ba zan ƙara ba. Nima san..."
_*"Halima, ki tabbata koda wasa aka samu matsala, kar bakinki ya yi kuskuren ambaton sunan ɗaya daga cikinmu. Ki ce kawai dai kina kishin Ramlatun za ta auri Chairman dinku ne. Ki ka kuskura ki ka yi gangancin tonamana asiri, ki sani rayuwarki ce za ta ƙare a doron ƙasa saboda za mu bar ki ki rayu kuma ki mutu a gidan yari ba tare da mun ɗauki matakin fiddoki ba. Idan kuwa ki ka bar komai a cikinki ki ka faɗi yanda na ce, toh shakka babu ina mai tabbatarmaki ko kwana uku ba za ki yi a hannun ƴan sanda ba za mu sanya a fiddo ki kuma ki bar garin. Idan kunne ya ji....jiki ya tsira."*_
"Kin yi shiru? Me ki ke son ki ce?!"
Tana kuka sosai ta dubi Sajan da ke mata tsawa, a gefensa Hisham ke tsaye yana jiran ji daga bakinta. Girgiza kai ta yi.
"Nima sharrin shaidan ne."
"Ƙarya ki ke! Ba haka ki ka so ki ce ba!Ki fito ki faɗi wanda ya sanya ki!"
Cewar Hisham a ruɗe. Ya ja, itama ta ja. Gwaska tuni an yi asibiti da shi.
Dole haka Hisham ya hakura ya bar case hannunsu sannan ya wuce gida, lokacin sha biyu ta wuce.
***
WASHEGARI...
Da sassafe Hajiya Zeenat ta shirya. Motsinta ne ya tashi Hussein dake bacci. Ya dube ta sadda ta ke kokarin ficewa daga ɗakin.
"Lafiya? Ina zuwa haka da sassafe?"
A firgice ta juyo tana dubansa,ta wayance da yaƙe.
"Am..am..dama Hajiya Batool ta kirani ba lafiya har an kai ta asibiti ma. Shi ne zan je dubiya." Ya gyada kai kawai ya juya ya kara jan bargo, ta sauke ajiyar zuciya ta fice. Ta bar Hussein da tunanin irin nasu auren, wannan wane irin aure ne da mace ke da ikon fita ba tare da iznin miji ba? Anya kuwa hakan zai haifarmusu da ɗa mai ido?
Ya sauke ajiyar zuciya gami da lumshe idanu cikin tunanin laifinsa ne tunda tun farko haka su ke yi. Bai kuma san ya hakan ta faru ba.
Wayarsa ce ta yi ƙara, sunan Hisham ya gani yana murmushi ya ɗaga.
"Kira da safiyar Allah, bashin me na ci?"
"Haba Malam, ina ka shiga ne wai? Jiya na kira duka wayoyinka amma a kashe, lafiya dai ko?"
Hussein ya lumshe ido ya ja guntun tsaki tuno da shirmen Zeenatu.
"Share kawai, lafiya lau ne. Ya aka yi?"
"Ba ka da labarin an kai wa Ramlatu hari?"
Wani irin miƙewa Hussein ya yi gaba ɗayansa har santsin bargon na ƙoƙarin kifar da shi ƙas.
"What?"
Labarin komai Hisham ya ba shi.
"Tana wane asibitin?"
Ya sanarmasa.
"Yanzu zan zo."
Daga nan ya katse kiran bai jira komai ba.
***
MISALIN ƘARFE TAKWAS NA SAFE...
Hawaye ta ke fitarwa yayinda ta ke tariyo komai a kwanyarta. A yanzun da Hajja ke salati da tambayar wa zai aikatamata hakan? Itama a sannan kwakwalwarta ta shiga aikin tunani. Kasancewar ta juyamusu baya ya sa ba wanda ya lura da tashinta. Cikin dare dai ta farka sannan ta ƙara komawa bacci.
"Abin dai da ɗaure kai." Hajiya ta furta tana ƙara riƙe carbin hannunta da ta ke ja.
"Nifa ina zargin matar Hussein wallahi. Tunda..."
"Yi shiru kawai Rafee'ah, zato dai zunubi. Irin haka ne sai ki ga ana zaton wuta a maƙera sai aka same ta a masaƙa."
Rafee'ah ta yi shiru amma dai kam zuciyarta cike take da zarginta. Kwankwasa ƙofar da aka yi ne suka bada iznin shigowa. Hisham ne da AlHassan, suka karasa aka gaisa.
"Kada dai ace har yanzu ba ta farfaɗo ba?" Cewar Hisham.
"Aa, ta farfaɗo cikin dare, har na taimaka ta ɗan zagaya. Sannan ta yi salla da Asuba ma. Baccin ne dai ya ƙara kwasarta."
Ramlat da ke jin bayanin Hajiya sai ta runtse idanu, wani radadi kafaɗarta ke mata, sai dai idan har za ta iya jure wannan adalilin Hussein, idan har zaa iya yaudararta a kafamata tarko a kansa, toh ba karamin so ta ke yi mishi ba. Ta ƙara aminta da hakan.
"Au dama idanunki biyu?" Cewar Rafee'ah wacce ta zagayo domin gyaramata ɗankwalin kanta da ya zame.
Ta dube ta, ganin tana hawaye ta sa hannu ta shiga sharemata.
"Haba Ramlat, meye kuma na kukan tunda Allah Ya riga da ya tsare? Yi shiru don Allah. Ko za ki tashi zaune?"
Ta gyada kai. Da taimakon Rafee'ah ta miƙe zaune ta jingina da filo. Ta gaida Hajja da su Alhassan.
Wayar Hisham ta yi ƙara ya duba, shi kansa AlHassan tunda ya ji batun zuwan ɗan uwansa ya rasa sukuni. Burinsa kawai ya gan shi don ya tabbatar da komai. Aikuwa shi ɗin ne.
"Kana waje? Ok gani nan zuwa."
Yanda Hisham ya miƙe hakanan shima AlHassan ya mara mishi baya. Rike hannunsa ya yi.
"Ka yi hakuri, nan zai shigo, ka jira ya karaso ciki ka ganshi."
Ramlat da kirjinta ya tsananta bugu ta dubi Hisham a hargitse. Nan da nan wasu hawayen suka kwaranyo. Baki na rawa ta ce.
"Hussein..Hussein ne?"
Hisham ya dubeta.
"Shi ne, ku kwantar da hankalinku yanzu zan kawo shi."
AlHassan a dole ya dakata sai dai ya kasa tsayuwa wuri guda, safa da marwa ya shiga yi yana kallon ƙofa. Koda aka tura ƙofar aka shigo. Hisham din ne a gaba, a bayansa kuma Hussein. Kamar wani gunki haka AlHassan ya ja burki yana kallonsa ƙurr.
"Hussein...?" Ya furta, furucin da ya ja hankalin Hussein dake sanye da Maroon shadda da hula, ya dubeshi.
I think you'd like this story: "Ƙarfen Ƙafa" by Rufaida-Umar on Wattpad https://my.w.tt/IRx4QB4kMcb
🕯️ *ƘARFEN ƘAFA*🕯️
_*Rufaida Umar*_
Bismillahir Rahmaanir Raheem.
48)
Kallonsa yake yi sosai kirjinsa na bugawa da sauri. Ramlat ta runtse idanu tana mai addu'ar komai ya tafi daidai.
Da wani irin sassarfa AlHassan ya tako ya rungume Hussein kawai sai ya soma kuka.
"Hussein." Ya ƙara kiran sunansa karo na biyu, Hussein ya yi ɗif sai hawaye da ke zuba saman fuskarsa. Ji ya yi kamar ana saramasa guduma a tsakiyar kansa, a hankali ya soma ganin dishi-dishi, lokaci guda idanunsa suka juye yayinda baƙin kwayar idanun ta ɓace ɓat. Hisham da ke tsaye a baya shi ya lura da sauri ya karasa ya rike Hussein. Jikinsa wani irin kakkarwa ya ke yi.
"Innalillahi wa inna ilaihir raajiun!"
Cewa Hisham yana rike hannun Hussein, jin haka AlHassan ya ɗago wanda saura kiris Hussein din ya zube don kuwa da jikinsa ya samu madafa.
"Riƙe shi sosai." Cewar Hisham, suka taimaka suka fitar da shi sai wurin likita. Ramlat tuni ta miƙe tsaye. Su kansu su Hajiya sun rude. Ganin tana kokarin ficewa yasa Rafee'ah riƙo ta.
"Ina za ki je? Ba ki ganin halin da ki ke ciki? Idan kin je lafiya za ki ba shi?"
Ta girgiza kai tana hawaye, ta bude baki sai dai ta rasa me za ta ce don haka ta koma ta zauna. Hajiya ce ya fidda waya don ta kira Malam ta sanarmasa halin da ake ciki. Nan take ya ce maza ta aiko a karɓi ruwan da ya haɗa da ganyen magarya ya yi addu'o'in karyewar sihiri. Ba shiri ta yiwa direbanta waya ta ce ya biya Yakasai ya karɓo mata saƙo.
***
Duk iyakar awon da likitocin su ka yi ba su gano komai game da ciwon Hussein ba. Don haka koda suka samu ya bar jijjigar, idanun suka dawo daidai sai Likitan da ya karɓi Hussein ya fito wurin su AlHassan. Suka tarbe shi da gaggawa.
"Ku yi hakuri.."
"Mutuwa ya yi?" Faɗin AlHassan a gigice, girgiza kai Likitan ya yi yana mai riƙe hannunsa.
"Ko kusa ba haka ba ne, asalima yanzu mun samu komai ya daidaita. Sai dai hakikanin gaskiya ba za mu ce ga abinda ya jawomasa hakan ba, yanzu dai halin da ake ciki, dole zamu yi mishi tests don mu gano ainahin inda matsalar take."
Suka jinjina kai.
"Ba damuwa Dakta. Allah Ya ba shi lafiya." Cewar Hisham da hankalinsa ya ɗan kwanta.
Bayan wucewar Dakta ya dafa kafaɗar AlHassan wanda ya cire hular kansa tsabar gumin da fargaba ta haifarmasa.
"Kada ka damu ɗan uwa, na fadamaka dama duk sadda maganar dangi ko ƴan uwa ta haɗa mu da Hussein ya kan shiga wani irin hali, ina kuma ga yau ya yi ido huɗu da ɗan uwansa?"
"Hakane, sai nake ganin kamar ba na asibiti ba ne."
AlHassan ya faɗi bayan kai karshen nazarinsa.
"Hisham, ya jikinnasa?"
Suka juya, Rafee'ah ce. Ta karaso suka yi mata bayani.
"Allah Ya ba shi lafiya. Kada ku damu, Hajiya ta aika a karɓo ruwan ganyen magarya mai addu'o'in karya sihiri, da yardar Allah komai zai daidaita."
AlHassan ya sauke ajiyar zuciya yana ɗan murmushin jin dadi da wani irin kaunar zuri'ar da ke kara mamaye zuciyarsa.
"Na gode kwarai, Allah Ya sakamaku da alheri. Allah Ya bar zumunci."
Ta yi dariya kadan.
"Ameen. Ai yiwa kai ne. Bari na koma, dama Hajiya ce ta ce na sanarmaku sannan na gano halin da yake ciki don marar lafiyarmu ta tashi hankalinta sai kuka ta ke yi."
Murmushi AlHassan ya yi yana mai hasashen wani abu da tun a jiya ya yi zaman dirshan a kwakwalwarsa.
***
TA FARU TA ƘARE...
"Innalillahi wa inna ilaihir raaji'un! Halimar aka kama?!"
Hajiya Zeenatu ta faɗi tana tsaye a bakin ƙofar gidan Kakar Halima wacce ke rike da ita. Ƙanin Halima uwa daya uba ɗaya wanda daga ita sai shi, su uku iyayensu suka haifa kafin rasuwarsu, dayayar Halima, Halima sai Yusufa. Kakarsu ta karɓi riƙo. Yusufan ya share hawaye yana duban Hajiya Zeenatu.
"Wallahi ranki ya daɗe, ɗazu aka yi mana waya, naje har ofishin ƴan sandan na sami Aunty Halima, wai dumu-dumu aka kama ta da bindiga za ta yi kisa. Wannan abu ne da ko a mafarki ba mu zaci faruwarsa ba. Su biyu aka kama, shi ɗayan ko Gwaska ko wa? Yana asibiti. Yanzu Kaka na kwance ba lafiya tun da ta ji halin da ake ciki."
Hajiya Zeenatu wacce ta yi mutuwar tsaye, ta yi sauri ta dawo hayyacinta. Baki na rawa ta ce.
"Ta..ta..faɗi wadanda suka sanya ta?"
Kallon da Yusufa ya yi mata na nazari sai da ya sa ta sakin ƙaramar tusa mai haɗe da fitsari ba shiri. Ya girgiza kai.
"Abin kunya ne ace saboda ɗa namiji za ta aikata hakan. Kishi ne kawai don uban gidansu na aiki zai auri abokiyar aikinta Ramlat. Haka ta sanarmin."
Ya karashe da wani irin jin kunya. Ajiyar zuciya Hajiya Zeenatu ta sauke ta juya za ta shige mota.
"Amm..Hajiya, na ce sai dai ban sanki ba. Kema wurin aikinta ki ke ne?"
Ta juyo.
"Eh, tare muke aiki." Tana kaiwa nan ta juya da sauri ta faɗa mota, ta ja. Kiyayewar Ubangiji ce kawai ta isar da ita gidan Hajiya Batool. Itama nan ta iske ta su na dambe da surukarta. Dakyar ta raba su. Ɗan Hajiya Batool ba ya nan ya yi tafiya Dubai, shi ne surikar ta zo gidan kwana.
"Haba Hajiya, me ya yi maki zafi za ki tsaya dambe da suruka? Ke kuma don ba ki da kunya wannan ba uwar mijinki ba ce?"
Fareeda wacce ke tsaye tana huci ta narkawa Hajiya Zeenatu uwar harara kafin ta saki dariya gami da tafa hannu.
"Ahayye! Ai fa da yake daga ke har ita jirgi ɗaya ya kwaso ku dole ne ki ga laifina! Tsoffin banza da ba su riƙe girmansu ba ai ba zan ji kunyar taka su son rai ba. Kin tauye hakkin yaro kin danne kina zaune da shi! Ko an fadamaki bani da labarin mijinki? Kina kai min uwar miji yawon bin bokaye don mijina ya ƙara aure ko? To wallahi karyar ku domin tun kan a haifi uwar mai sabulu balbela ke da farin kai. Don haka idan ku na son na lulluɓe dukkan sirrikanku to ku tabbatar an fasa batun auren Mijina da kowace shegiyar kucaka. Idan kunne ya ji..." Ta ƙarashe da rike kunne kafin ta wuce tana dariya ta bar su baki galala. Bayan shigewarta ɗaki Batool ta yi gaba ta haye sama, Hajiya Zeenatu ta bi ta a baya. Su na shiga ɗaki suka sa mukulli.
"Batool akwai matsala!"
Hajiya Batool da ta zauna rike da ƙugu tana ambaton wash sakamakon cizon da ta sha a wurin Fareeda. Ta amsa wa Hajiya Zeenatu kamar za ta yi kuka.
"Matsala nima cikinsa kika tarar da ni Zeenatu. Kamar Gora yaudararmu ya ke yi yana cin dukiya a ɓagas. Ni na rasa kan wadannan lamuran."
Hajiya Zeenatu ta yarfar da jaka da mayafi, da sauri ta faɗa banɗaki. Can kuma ta fito ta zauna tana sharce gumi. Ta kora dukkan bayani ga Hajiya Batool gaba dayanta a rude.
"Ya zan yi ne Batool? Ga Visa ta yi wuya an ce mu kara hakuri zuwa sati na sama, ga wannan lamari na neman kwaɓemin? Ba mu ga ta zama ba Batool, ta inda aka hau dai ta nan ake sauka idan ba haka ba mai afkuwa za ta afku. Ba ni da tabbacin Halima ba za ta tonamana asiri ba. Ban san iyakar lokacin da za ta riƙe sirrinmu matsayin sirri ba. Wannan fa barazana ce garemu. Tashi za ki yi mu kama ƙafa muje mu ga Gora tun kafin komai ya lalace."
Hajiya Batool ta share hawayen takaici, yau ita suruka ke dambe da ita, ta rantse sai ta ga bayanta tunda dama ba ta haifarmata ko ƴartsana ba sai afkin ci da kasayarwa.
"Muje. Bari na lallaɓa."
Ta miƙe dakyar ta dauki gyalenta. Suka fice. Fareeda na leƙensu ta window ta yi dariya ta saki labule. A fili ta ce.
"Munafukan banza, da alama an tafi yawon abinda aka saba. Zama daram ni Fareeda!"
Ta furta tana mai zama kan gado tana dariya.
***
Tunda Hajiya Zeenatu ta sanarmasa da batun kama Halima ya gaza samun nutsuwa. Don haka ya kira Dada a waya karon farko. Hakan ba karamin mamaki ya ba ta ba don har sai da ta ce.
"Yaya lafiya dai ko?"
"Ah lafiya kalau mana Amina, ba damar na kira ki kenan sai idan babu ita? Mtsw. Ina yaran nan kuwa? Husseini? Yana gari?"
Dada ta amsa a sanyaye.
"Aa, ya shigo nan Kano wani uzuri na ma'aikatarsu, bai ƙaraso nan ba?"
Wani zufa ya karyowa Kawu a goshi, ya samu wuri ya zauna ɗabas! Sai ya ɓige da faɗan borin kunya.
"Ina na isa dama ya zo wurina? Ai ban isa ba! Kin koyawa yara tsanata da tsanar iyalina. Sai ki yi idan hakan zai haifarmaki da ɗa mai ido! Mu din dai mu ne nasu."
Daga haka ya katse wayar bai saurari ban haƙurin Dada ba. Miƙewa tsaye ya yi yana sunturi, ba zai yiwu ba. Babu abinda zai ruguza dukkan sirrinsa. Idan ya tabbata lamarin Hussein ne ya kawo AlHassan garin Kano kamar yanda Bokansa ya buga ƙasa ya bincikamasa, toh shakka babu komai ya rushe. Tonuwar asirinsa kamar jin kunyarsa ne a cikin dangi, ya san duk tsanar da sauran yan uwansa suka yiwa jinin Aminu da Amina (Dada), bai kai tsanar da ya yiwa HUSSEIN ba.
Ya dau waya ya dannawa Hajiya Zeenatu kira, haka ya yi ta ringing ba'a ɗaga ba, wannan yasa shi kasa zama ya fice daga gidan don ƙara tuntuɓar Bokansa karo na ba adadi.
***
Ya mike zaune dakyar daga saman gadon da yake kwance. A hankali ya dafe kai yana salati.
"Sannu Hussein, ka tashi?" Ya dubi mai maganar da sauri, shi dai wanda ya gani a ɗazun ne mai kama da shi. Ɗan uwansa da ya daina sanyawa a idanu shekara da shekaru. Ƙuri ya yi mishi da idanu, daidai nan Hisham ya miƙamasa kofin ruwan tofi.
"Shanye duka please." Ba musu ya karɓa ya shanye tas. Kamar yanda jini ke zagaye a cikin jiki, haka ya dinga jin ruwan na zaga dukkan wata gaɓɓa ta jikinsa, a hankali hawayen da suka sauya kalar kwayoyin idanunsa suka samu damar kwaranyowa saman kuncinsa. AlHassan ya taso ya zauna a gefe gami da sanya hannu cikin nasa.
"Hussein, ka gane ni?"
Gyada kai kawai yake yi bakin na rawa amma kalmar A ta kasa fita daga bakinsa. Kawai sai ya ɗora hannunsa haɗe da na AlHassan saman goshi ya shiga kuka kamar ransa zai fita. Hisham a hankali ya juya ya fita daga ɗakin yana share kwallar dake kokarin zubowa a kokarinsa na katse ta yana mai hamdala ga Mahaliccin Sammai da kuma Ƙassai.
"Na gane ka. AlHassan Aminu Gidado."
Hussein ya furta da kakkarwar murya, jin haka AlHassan ya ƙara jan sa a jiki shima yana kukan. Zai so ace Dada na zaune a dakinnan, matar da idanunta ba su taɓa kafewa da zubar hawayen rashin Hussein ba. Kullum kiranta, amanar Allah ne su din a hannunta, koyaushe ɗorawa kanta laifin ɓatan Hussein ta ke yi.
"Ina Daa...da, Baba Naziru.?"
Hussein ya tambaya, AlHassan ya ɗago fuskarsa da wani irin murmushi mai haɗe da dariya-dariya.
"Dada tana nan, tana nan kullum cikin kuka da addu'ar Allah Ya nunamata kai. Babban burinta ta samu wani ko wata da zai kawomata kai koda labarin mutuwarka ne, ita dai ta san cewa ka mutu cikin musulunci kuma an maka kyakkyawan sutura. Da yawa ya faru bayan gushewarka Hussein, abubuda da dama sun faru garemu da baki bai isa ya buɗamaka su ba."
Hussein ya jinjina kai yana jan hanci.
"Eh, da yawa ya faru. Irin yawan da ban taɓa kawo wa kaina a rayuwa ba. Ban sani ba ko ni na jazawa kaina ko kuwa dai.."
Rufemasa baki AlHassan ya yi yana girgiza kai.
"Kar ka ce komai ɗan uwana, ka yi shiru mu ƙara godewa Allah da ganin wannan ranar da muka kwashe shekaru muna jira. Haɗuwa da Ramlatu alheri ne garemu baki ɗaya. Ina zan manta da ita da zuri'arta?"
Hussein ya ci gaba da dubansa da idanunsa da suka kaɗa. A idanun AlHassan ya gano karin bayani ɗan uwannasa ke nema. Murmushi ya yi.
"Mai hali ba ya fasa halinsa, ashe ba ka sauya ba?"
Suka yi dariya gami da ƙara rungume hannun juna gam! Kamar ance ga wani abu zai ƙara raba su. Tirya -tiryan ya ba shi labari tun daga haɗuwarsa da Ramlat har zuwa yanzu da aka harbe ta sanadinsa. Hussein ya yi shiru, ya rasa me zai ce. Ya kuma rasa wane yanayi ya ke ciki, tunani sosai ke neman shigarsa don haka ya gaggauta yanke tunanin.
"Mu je na ganta don Allah."
Ba musu suka mike, ya zura takalmansa, bini-bini za su kalli juna shi da ɗan uwansa su yi murmushi, haka suka jera idanun jama'a a kansu don ba karamin burge su suka yi ba musamman masu juna biyu, nan suka fara addu'ar su ma Allah Ya basu ƴan biyu masu bala'in kama irinsu, su gan su sun girma haka tare.
***
Gora ya duba, ya ƙara buga ƙasa ya duba, ya ɗago kai ya kalli Hajiya Zeenatu da Hajiya Batool da ke zaune gabansa cike da wani fargaba da tsoro.
"Lafiya dai?" Zeenatu ta nemi sani.
Ya girgiza kai ya ƙara maida hankali ya yi buge-buge da rubuce-rubucensa. Can ya ɗago ya dubesu yana sharce gumi.
"Bana jin akwai sauran duhu da yanzu haske bai mamayeshi ba a rayuwar mijinki. Yanzu haka maganar da nake maki yana tare da ɗan uwansa. Gaskiyar magana babu sauran asiri a jikin yaronnan. Da alama akwai wanda ya tsayamasa." (Allah Ya raba mu da aikin jahilci da jahilai. Ya kiyayemana imaninmu. Ameen).
"Na shiga uku na lalace ni Zeenatu!" Ta dora hannu a kai ta kurma ihu da kuka.
"Na fadamaki ai! Duk ranar da ya yi tozali da abokin haihuwarsa aikinki ya rushe. Ko kin manta wannan gargadin? Toh bari ki ji, akwai wani babban bala'i da ke tunkaroki daga ke har Batulu, ina mai gargaɗinku akan ku gaggauta barin garinnan kafin komai ya ida lalacewa. Wallahi kun ji na rantsemaku, taku ta kare domim ruwa ya ƙarewa ɗan kada!"
Gora ya na kaiwa nan ya mike ya gyara zaman malun-malun hadi da ɓantalar goro ya hau tauna. Da wani irin tsalle Hajiya Zeenatu ta miƙe ta shaƙe wuyansa ya hau kakari.
"Karya ka ke wallahi! Karya ka ke! Nawa na kashe?! Har kabari na tona! Hatta da jariri nayi amfani da shi duk akan Husseini! Karya kake ka ce duka wannan aikin ya tashi a banza Gora! Dole ne ka nemomin mafita idan kuwa ba haka ba wallahi sai na kashe ka!"
Gora wanda ya ji shaƙa dakyar ya iya ɓanɓare hannun Hajiya Zeenatu daga wuyansa. Bai yi wata-wata ba ya kwaɗamata lafiyayyen mari da rawar hannu ya hau nunata da yatsa.
"Ni ki ke kokarin kashewa? Yau sakamakon da za ki yimin kenan? Shegiya ƴar zina! To ki sani kin taɓowa kanki tsuliyar dodo, yanzu kika soma ganin bala'i da masifa! Babu ke ba jin dadi a rayuwa wallahi. Ni na miki wannan alƙawarin."
Jin haka ta ƙara daka tsalle ta shaƙe wuyansa ta hau bori, ga hawaye caɓe-caɓe ga zani na neman kuncewa sanadin jijjigar da ta ke yi. Tana faman ikrarin ko mutuwa ta yi kaɗan ta raba ta da Hussein. Hajiya Batool ta yi iyakar yinta amma ta kasa kwatar Gora don haka ta bazama rumfar da matan aure da karuwai har ma da ƴanmatan ke bin layin ganin Gora, ta nemi ɗoki. Nan da nan suka bazama aka shigo dakyar suka kwaci Gora wanda tuni ya galabaita har ya suma. Ruwa aka watsamasa ya farfaɗo. Idanun na kyarma ya shiga nuna Hajiya Zeenatu.
"Za ki yi dana sanin wannan yunƙuri da ki ka yi na kashe ni Zeenatu. Sai na nunamaki waye ni! Na fi karfin wulakancinki!"
"Hoo! Shege tsinanne wanda ba ya kallon gabas! Ni Zeenatu baƙar ashana ce! Ka san tarihina ka kuma san asalina! Babu uwar da ban gani ba don haka ka shirya! Sai na ga bayanka da karyar bokancinka. Ba wanda ya isa ya raba ni da Hussein! Wallahi sai na kashe ko waye!!"
Da haka Hajiya Batool ta janye ta suka bar wurin zuwa mota. Hankali a tashe Hajiya Batool ke tuƙi, Allah Ya taimakesu gilashin mai duhu ne sosai ba'a ganin haukar da Hajiya Zeenatu ke yi. Ita Hajiya Batool ma ta fi ta kwanciyar hankali. Ita dai Hajiya Zeenatu kira ta ke sai ta kashe AlHassan da ma Ramlatu idan hakan ne kadai hanyar da za ta rayu da Husseininta!
***
Tana zaune daga ita sai Rafee'ah da Amrah, Hunainah da Zulaihat sai Muniru. Hajiya ta wuce gida wanka da ɗan runtsawa. Hira suke yi amma ita kam tana zaune ko abincin da aka zubamata ta kasa ci, hankalinta na kan Hussein. Kwankwasa ƙofar da aka yi ce ta sa da sauri ta dubi ƙofar. Amrah ce ta mike tana gyara
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 41 Chapter of 58