hamma ta saki tana mai rufe baki, a gajiye liƙis take jin ta. Kakkaɓe gefen da za ta kwanta ta yi, hankalinta ya kai ga wayarta, shaf ta mance da ita a chaji, ta cika tun awanni biyu ma da suka wuce.
Zareta ta yi ta shiga cikin whatsapp ganin saƙonnin da suka faɗo daga kunna Data.
Saƙon Hussein ya sanyata dariya ba kaɗan ba, ta maidamishi amsa.
"Ba fa celebrity ba ce."
Daga haka ta yi zaman jiran amsa har gyangyaɗi ya soma fisgarta, can dai ta hakura ganin ba ya kusa ta kashe wayar ta yi addu'a ta kwanta.
***
Ruwan da ake kamar da bakin ƙwarya ya sa ta barin yara a gida don sun kammala jarrabawa kusan wasa kawai ake a makarantar yanzun, itama ba don fitar ta zama dole ba da babu inda za ta je. Amrah ce ba lafiya, abin tsoron kuma lokacin haihuwarta da saura don duka-duka cikin bai kai wata shida ba.
"Ki je zuwa anjima ma leƙa. Kar dai ki manta da kiran Kawunnaki. Ki karasa Yakasan idan ruwan ya tsagaita."
Wani ɗaci Ramlat ta ji da bayanin karshe na Hajiyarta, tasan kiran da Kawun ke mata bai wuce akan aure ba. Ita shikenan yanzu kowa idanunsa a kanta, an takura akan sai ta yi aure. Dama tun da Hajiyar ta soma batun kai yara dangin Babansu don su ci hutunsu a can, ta soma jin ba dadi. Babban takaicinta yanda tun rasuwar Abulle babu wanda ya kara nemansu banda Malam da ke kira lokaci zuwa lokaci su gaisa ko kuma ita ta kira. Hakanan Justice duk sadda zai yiwa yaran ƴan uwansa kayan sallah toh zai haɗa da su. Kannen Aliyu ta yi musu uzurin aure, amma a ganinta hakan bai kai dalilin da zasu dauke ƙafa da hankalinsu daga kan yaransa ba. Ko ƙafarsu ba ta tako ba ai akwai waya.
"Kin yimin shiru kina wani ƙunƙuni, idan ba za ki je ba sai ki kira ki faɗamasa."
Hajiya na kaiwa nan ta mike a fusace ta yi ɗakinta. Sauke ajiyar zuciya Ramlat ta yi, ranta har sannan babu dadi haka ta gyara zaman mayafin abayarta maroon ta fita rike da kwandon abinci. Idan ka ganta ba za ka ce ta haifi yara har uku ba, Allah Ya yi mata baiwar jiki mai kyau kuma wanda ya samu kulawar da ta dace.
Har ta iso asibitin da Amrah suke ba ta cikin walwalarta. Ɗahiru ta soma kiciɓus da shi a barandar emergency, suka gaisa ya fadamata lambar dakin sannan ya fita. Ta karasa, Amrah na kwance tana bacci sai Umma a gefe. Ta karasa suka gaisa da Umma.
"Wai, gaskiya kin yi kokari, ana wannan ruwan kika fito?"
Murmushi ta yi.
"Umma ai dole ne, ƴar uwata guda ba lafiya fa."
Ƴar dariya Umma ta yi.
"Kinga da sauki ma, likitan ya ce wai Malaria ce kuma kinsan ba'a son Mai ciki da ita, amma yanzu Alhamdulillah. Ba ta jima da samun baccin ba ma."
Jinjina kai Ramlat ta yi tana maida dubanta saman fuskar Amrah, duk ta ajiye wani kumatu.
"Allah Ya bata lafiya."
Daga nan ta ajiyewa Umma kwandon suka shiga hira kadan-kadan. Sun kai kusan mintuna sha biyar kafin Amrah ta farka.
"Ya jikin?"
Umma ta furta tana dubanta. Gyada kai ta yi tana kokarin miƙewa zaune.
"Alhamdulillah, kan ya sauka ma."
Yanda ta furta ma ka san ba lafiyar. Suka yi mata sannu. Da taimakon Ramlat, ta shiga banɗaki ta yi alwala ta wanko baki. Suka dawo ta zauna, Ramlat da kanta ta zubamata farfesun naman ragon da ta kawo wanda ya ji karas da ɗankali. Ta haɗamata shayi sannan ta haɗa na Umma, itama ta zubamata farfesun.
Suna ci su na taɓa hira. Ruwa na tsagaitawa Umma ta wuce gida da zummar za ta turo kanwarta (ita Ummar), Magajiya ta zo ta zauna da ita.
"Ya na ganki wani iri?"
Amrah ta watsowa Ramlat tambaya tana dubanta. Murmushin yaƙe ta yi.
"Ba komai."
Girgiza kai Amrah ta yi.
"Karya ne wallahi. Dama shiru nayi don Umma na wurin amma tun da na dora idanu a kanki na gane akwai matsala."
Shiru Ramlat ta yi kafin kuma ta soma fitar hawaye, a yau dai zuciyarta ta motsa da kewa mai yawa na Aliyunta. Da ace za ta rasa duk abinda ta mallaka don kawai Allah Ya ba ta damar ganinsa su yi magana ko sau daya ne, da tuni ta aikata hakan. Sai dai kuma ita mutuwar gaskiya ce, barin duniya ce ta har abada da babu dawowa sai dai ka je ka tarar.
"Lafiya kuwa?"
Cewar Amrah kusan hankali a tashe, ganin tana neman jefa mai juna biyu cikin matsala ta yi saurin dauke hawayenta ta hau murmushin yaƙe.
"Ke ba fa wani abun tada hankali bane."
Nan ta kromata dukkan abinda ke faruwa, murmushi Amrah ta yi. Ta lura ba maganar kai yaran gidan kakanninsu ne tashin hankalin ƙawarta ba sai maganar auren da ake budemata wuta a kai.
"Yanzu don Allah Ramlat kin fi kaunar ki yi ta zama haka ba aure? Kina zaton hatta Abba idan ace yau yana doron ƙasa zai yi murna da zamanki haka? Ko a tunaninki Aliyu zai yi farin ciki da zamanki haka babu aure? Wallahi kin ji na rantsemaki cikinsu babu wanda zai so ki ƙare rayuwarki a haka. Kema fa mace ce, a karon kanki sai dai ki ɓoye, kinsan cewa kina bukatar auren. Kina son wanda zai kula da ke da rayuwarki."
Amrah ta ci gaba da kwantarwa Ramlat hankali ta hanyar nasiha da rarrashi. Tun Ramlat na jin haushin maganganun har ta soma gane dagaske duk abinda ta fadi babu ƙarya ko sharri a ciki.
"Batun yara kuwa kema kinsan ba ki isa hanasu zumunci da dangin mahaifinsu ba koda su din ba sa ta su."
Murmushi kawai Ramlat ta yi a nan.
"Ke ni ina Muhibbat ne? Kwana biyu na ji ta shiru a WhatsApp."
"Tana nan, ko juma'ar da ta wuce mun gaisa. Ta yi rashin lafiya kwana biyunnan wai."
"Allah Ya bata lafiya." Cewar Amrah.
Zuwan Baba Magajiya kanwar Umma ne ya ba Ramlat damar yi musu sallama ta tafi. Yayyafi-yayyafi ake yi garin ya yi luf-luf da sanyi mai sanya nutsuwar zuci.
Tana tafe tana tauna zantukan Amrah har ta isa ga motarta.
***
YAKASAI..
Kanta kamar ya tsage biyu, bakinta ya yi mata nauyi yayinda ta ƙurawa Kawu Bello idanu don ji take kamar babu sauran laka a jikinta. Ta rasa ma me za ta ce, ta kasa fahimtar idan bayanan suka dosa. Batun dai zai bayar da ita ga CHAIRMAN ALIYU DIKKO ya fi komai ba ta mamaki da kuma dariya.
"Kin yi shiru kin tsuramin idanu kamar wani sa'anki?! Sarai kin ji ai abinda na ce! Mun gaji da zubamaki idanu, ke ba ki kawo wani kin ce kina sonsa ba, kuma ke ba ki ba masu sonki dama ba! Toh na bayar da ke ga Chairman, zai soma zuwa hira wurinki ku fahimci juna. Nan da sati uku ma zan dauramaku aure."
Ya ƙarashe yana fitar da wani huci har da muzurai, bakin ciki ya sa hawayen ma kasa zubowa. Wato Chairman shigo-shigo ba zurfi ya yi mata kenan? Ta ya akai ma ya san gidan kakanninta?
"Ki je ki saurari zuwansa cikin satinnan, saura kuma wannan karon kamar yanda kika nunamana a baya, yanzun ma ki nuna ba mu isa da ke ba. Dama ai mai hali ba ya fasa halinsa. To mu zuba da ke."
Wasu zafafan hawaye suka zubomata, ta kasa duban Kawun har ya mike ya bar mata dakin. Jiki a sanyaye ta share hawayenta, ta mike ta koma sashen Dada. Nan ne ta samu Dada ta shiga kwantar da hankalinta da hanyar nasiha da nunamata muhimmancin auren a gareta. Ita dai ji ta yi gidan duk ya isheta, sallar la'asar kawai ta gabatar kafin ta yiwa Dada sallama ta yi ficewarta.
A zauren suka yi kiciɓus da Kamal.
"Ashe Ramlat arzikina kika raina ban sani ba, kin nunamin ba za ki iya aurena ba saboda a gidanmu ba'a sonki, yanzu ai gashinan da wannan maigidannaki ya fito kin kawoshi har ya ga Kawu. Ki dai bi a hankali duniya ce, ta fi bagaruwa iya jima!"
Yana kaiwa nan ya gifta ta ya wuce, ta bishi da kallo sannan ta fice, a hanyar tana tafe tana hawaye sosai. Komai ba ya mata dadi, wannan ne yasa ta zaɓi kaɗaicewa ita ɗaya ba tare da kowa a kusa da ita ba. Wani Rainbow Park ta je, wuri ne mai karancin hayaniya, mutanen da ke a wurin tsilli-tsilli, ba ruwansu da harkar kowa. Wannan ne yasa ta zaɓi can wurin da za ta je ta samu nutsuwar zuciya.
Cikin wata rumfar kara ta nufa inda aka jera kujeru, iska mai dadi wurin ke bayarwa. Akwai ƙarancin jama'a a Park din adalilin ruwan da aka yi.
Tunani kawai take tana fitar da hawaye masu ɗumi. Duniyar da abinda ke cikinta take ji sun ishe ta, an ce bazawara nada ƴancin zaɓin wanda ta ke so, amma tana ji kamar ba ta da wannan damar.
***
Tafe yake a hanyarsa ta zuwa wurin Gym. Tafiyarsa yake cikin nutsuwa yana sauraron yabon Ya Habibal Qolbi na Sabyan Gambus. Waƙar sosai yake jin dadinta, murmushi yake. Hankalinsa ya kai ga motar da ko a mafarki, lambarta ba za ta ɓacemasa ba. Ɗan tattara gira ya yi don son tabbatar da abinda idanunsa suka gani, ya nemi wuri ya yi parking.
"Me ta ke yi anan?" Ya samu kansa da furtawa a fili alhalin ya san babu mai amsawar.
Fitowa ya yi ya kara kallon lambar don tabbatarwa. Can kuma ya fito ya shiga Park din don son tabbatarwa kansa.
Sanye yake da wando da riga na kamfanin Adidas, farare da layi-layin navy blue a gefen hannu da wandon. Ƙafafun cikin farin canvas.
Gashin kansa ya kwanta luf-luf har a ƙeya, baza dara-daran idanunsa ya shiga yi wanda gashin ido ke kokarin rufewa duk sadda ya kyafta.
Har ya juya cikin fidda ran ganinta a wurin, idanunsa ya kai gareta cikin rumfa. Tana zaune ta ɗora gwuiwar hannunta saman kujera ta kama dage kanta da tafin hannu.
Kamar tunani take yi mai zurfi, kamar kuma hawaye ne saman fuskarta. Don so ya tantance, sai ya ƙarasa. Sallama ya yi amma ga mamakinsa ba'a san ya yi ba. Jan kujera ya yi da ke fuskantarta ya zauna. Wannan ƙarar ce ta maidota hayyacinta, ta dubeshi da idanunta da suka ƙanƙance suka yi ja. Shima zubamata nasa kwayar idanun ya yi fuskarsa da wata kwantacciyar damuwa.
Ta yi saurin share fuskarta, sosai ta kaɗu da ganinsa a wurin, ta kuma yi mamaki.
"Assalamu alaikum."
Ya kara maimaitawa, ta amsa a ciki-ciki. Miƙewa ta yi da niyyar barin wajen, ya yi saurin riƙe gefen dankwalin abayarta wanda ba shiri ta koma ta zauna.
"Lafiya?" Ta fadi murya a ƙasan maƙoshi. Murmushi ya yi.
"Ke zan tambaya, daga ganina sai ki gudu. Zauna ki ci gaba da hawayen ni tayaki kawai na zo yi."
Ta kauda kai daga barin kallonsa, ba ta ce uffan ba, zuciyarta ba ta cikin nutsuwar da za ta yi wani murmushi har ta kai ga darawa. Yau an motsa mata dukkan damuwarta. Yau ta tuna da mutane biyu masu ƙima da daraja a wurinta kuma mafi soyuwa a zuciyarta da ta rasa.
"Kiyi hakuri, komai na duniya mai ƙarewa ne. Wannan hawayen faɗuwa ce a wurinki ba nasara ba. Babu abinda zai yayemaki. Kema fa kin sani. Wani abin muna ji muna gani amma yake gagararmu tankwarawa saboda ba mu isa ba, sai yanda aka ce da mu, sai yanda akai da mu."
Ya fadi hankalinsa na kanta. Ta dubeshi, lokacin da ta ji saukar wasu sabbin hawayen, ba kanta kawai ta tausayawa ba, kalamansa na karshe kamar dan tsakure ne daga tasa matsalar a iyakar fahintarta domin kuwa ba shi da masaniya akan nata.
"Ka san damuwata ne? Ya akai ka san ina nan?" Ta furta kanta tsaye a sadda ta ke kokarin share hawayenta. Ya yi murmushi.
"Gashinan rubuce saman fuskarki."
Ta kara tsuke fuska ganin ya share tambayarta ta biyu.
"Kinsan me?"
Ta dubeshi gami da girgiza kai. Ya maida hankali kan wayarsa dake ringing, ganin sunan Hisham na yawo saman screen ya ɗaga.
"Ba zan samu shigowa ba." Abinda ya ce kenan bayan sun gaisa. Ramlat ta saci kallonsa, ba shiri ta kauda nata idanun ganin irin duban da yakemata.
Tana jin muryar Hisham na tambayar dalili.
Murmushi ya yi mai sauti.
"Ina tare da Heart."
Daga nan ya katse kiran. Kalmar Heart da ya furta ta sanya gabanta faɗuwa, ta dubeshi, ganin ya ɗagamata kira ta kauda kai. Ya ajiye wayar saman teburin.
"Tambayarki ta biyu ce ni kaina amsarta nake nema. Nasan dai a wautana motarki na gani, na haddace lambarta fiye da zatonki. Sai dai na rasa ya akai jikina ya bani ke ɗin ce ke jan ta, kuma har na zaɓi shigowa nan na ga wanda kika zo gani. Sai kuma na ganki ke ɗaya kina hawaye. Nan take tunanina ya bani cewar watakila faɗa ku ka yi ya tashi ya bar ki ko kuma bai zo ba. Ma'ana, ya yi disappointing dinki."
Murmushin takaici ta yi.
"Babu ko daya cikin hasashenka, asalima a karon kaina na zaɓi nan matsayin wajen da zan samarwa zuciya da kwakwalwata nutsuwa."
"Kina zuwa kenan?"
Ta ɗan taɓe ƙaramin bakinta gami da girgiza kai. Ya bi bakin da kallo ya kauda fuska yana murmushi.
"Heart." Ya furta a hankali, sai dai ta ji shi sarai. Miƙewa ta ƙara niyyar yi ya hanata ta hanyar rike mayafin karo na biyu. Dole ta zauna.
"Tafiya zan yi."
Yanda ta furta kusan a fusace sai ta ba shi dariya.
"Ba ki isa ba ai, uzuri ne fa da ni kika dakatar da ni."
Ta saki baki da mamaki.
"Yaushe?"
"Yanzu mana."
"Ni na faɗa?"
Ya girgiza kai.
"Abar maganar, kawai dai shawara zan ba ki. No matter what, ko meke damunki kar ki bari hakan ya sa ki zo irin wuraren nan. Ki yi hakuri, babu matsalar da wani ko wata zai magancemaki. Ki miƙa wa Allah lamuranki. Ki dage da kai kukanki gareShi. Wannan shi ne babban kuskurena a baya wanda a yanzun ya ke farautana."
Ya ƙarashe cike da tsantsar damuwa, ta dubeshi da kulawa.
"Ban yi zaton kana da damuwa ba, Allah Ya maka dukkan ni'ima. Kuma.."
"Ke Allah bai miki dukkan ni'ima ba?"
Ta kauda fuskarta daga kallonta.
"Ni kuwa Allah Ya yiwa ni'ima. Ya bani lafiya, Ya ban iyaye da ƴan uwa masu sona, Ya ban ƴaƴa. Alhamdulillah."
Tana kaiwa nan ta saci kallonsa. Kamar ta so karantar damuwarsa da yanda ya sauya lokaci guda. Can kuma ta ga ya ɓige da jinjina kai.
"Yes, you are right. Alhamdulillah."
Yanda ya yi maganar a sanyaye sai ya bata tausayi.
"Gwara ki tafi, yamma ta yi."
"Kana da ƴan uwa a garinnan?"
Abinda ta ce kenan. Wani banzan kallo ya watsamata da ya razanata.
"Ba ki damar shiga rayuwata hakan ba yana nufin har da lasisin da za ki tambayi abinda ya shafi rayuwata bane. Ya kamata ki san wannan."
Yana kaiwa nan ya mike a fusace ya yi gaba.
Ta bishi da kallo duk sai ta ji hankalinta ya tashi, bata taɓa ganinsa a yanayi makamancin wannan ba. Labarin da Hisham ya ba ta sadda magana makamanciyar haka ta haɗa su shi ya fado ranta. Da sauri ta mike ta dauki jakarta da zummar mara mishi baya. Wayarsa ta gani ajiye, ta dauka ta bi bayansa. Sai dai har ya kai ƙarar fita. Kafin ta karasa har ya shige mota ya tayar. Zagayawa ta yi da sauri ta bude mazaunin gefe ta shiga.
Ya buga sitayari murya a kausashe ya ce
"Fita!"
Girgiza kai ta yi hawaye na zuba.
"Ka yi hakuri don Allah, wal..."
"I said get out!!"
Ya faɗi cikin tsawa hadi da buga sitayari iyakar karfinsa har sai da ta razana. Idanunsa kamar an watsa barkono. Yanda jikinsa ke rawa itama haka nata jikin ke yi. Ta bude murfin motar ba shiri ta fita. Bai bari ta karasa rufewa ba ya fisgi motar har yana kokarin buge wani mota. Mai motar ya dakata da sauri yana duramasa ashar. Hussein bai ma san yana yi ba. Ita dai Ramlat kirjinta je dukan tara-tara da irin gudun gangancin da ta hangoshi yana yi, hawaye kamar famfo take fitarwa ba ta ko damu da kallon da jama'ar wurin ke bin ta da shi ba. Ta shiga motarta ta bar wurin cike da jin haushi kanta, me ya kai ta wannan gangancin?
***
MAFARIN KENAN.....
I just published "BABI NA TALATIN DA TARA" of my story "Ƙarfen Ƙafa". https://my.w.tt/dCw5vESQqbb
🕯️ *ƘARFEN ƘAFA*🕯️
*_Rufaida Umar_*
Bismillahir Rahmaanir Raheem.
39)
Jikin Hajiya ya yi sanyi bayan gama sauraron Ramlat. Sam ba ta tsammaci hakan ce za ta faru ba. Ta dauka dai faɗa akan fiddo mijin kawai za'a yi mata. Ta sauke ajiyar zuciya tana kallon yanda Ramlat ke kuka kamar ranta zai fita.
"Ke fa na yarinya ba ce, kin kuma sani dama can ba'a yi miki dole ballantana a kwata wannan karon. Da ace wani ne ba shi Maigidannaki ba, toh ba lallai ya dameni ba. Amma sam bana son wannan haɗi na Yaya Bello. Duk ke kika jaza wa kanki ai Ramlatu, tun yaushe ake biyamaki karatun fidda miji kin ƙi haddacewa balle ki yi aiki da shi? Yanzu gashinan an miki shigo-shigo ba zurfi."
Ramlat ta dubeta tana sharce hawaye.
"Nima Hajiya ba wai ba zan bi umarninsa ba ne, sai dai nasan waye Chairman tunda ni ke aiki karkashinsa. Ya sha nunamin zai zo gidanmu ina ƙin ba shi dama don na riga na san waye shi. Ban ɓoyemaki komai dangane da alaƙarmu ba. Yanzu kam an zo gaɓar da zan bar ma'aikatar Revenue, ba zan iya ci gaba da zamansa ba. Ya kamata ace dama tun a baya na yanke wannan hukuncin. Amma yanzun ma lokaci bai ƙuremin ba."
Kai Hajiya ta jinjina.
"Ina bayanki, ya dace yanzu kuma ki bar masa ma'aikatar duk da ba tasa bace ta gwamnati ce, kinga kenan ba shi da wata ƙafar da zai yi amfani da ita wajen cin zarafinki ko yi miki bita da kulli. Ni ai tunda ki ka ce ya san waccan matar hankalina bai kwanta ba."
Nan da nan Hussein ya fado ranta, ta dubi Hajiya. Ta ji tana son zayyanemata komai.
"Hajiya kin tuna baƙinmu na Adamawa?"
"Ta ya zan mance su, mutane masu karamci haka Ramlatu? Meyafaru?"
Hajiya ta tambaya cike da ƙaguwa. A zatonta, abinda ƴan uwan Ramlat din ke zargi ne zai tabbata, wato soyayya tsakanin Alhassan da ita. Abinda ba za ta yarda ba kenan ko don mutunci da girmamawar da Kausar ke mata.
"Kinsan kuwa suna da alaƙa da Hussein da nake ba ki labari mijin Hajiya Zeenatu?"
Ido waje Hajiya ke dubanta.
"Alaƙa wace iri?"
Tiryan-tiryan ta ba ta labarin duk abinda ta sani. Sai ga Hajiya na salati har da hawayen tausayi.
"Kai duniya! Mata me muka dauketa ne? Matattarar da za'a dauwama ko me? Zunuban kanmu kaɗai bai isa ba sai mun zalunci wasunmu? Kaico da wannan rayuwa. Allah Ya sakawa wannan yaro, Allah Ya karya ƙadarin wannan mata."
Hawayen Ramlat suka ci gaba da ambaliya, sam ba ta faɗa wa Hajiya abinda ya faru tsakaninsu a yau ba, hankalinta ya yi kansa sosai, tana son ta ji muryarsa ko don tabbatar da lafiyarsa.
"Amma wannan fa ba karamin aiki ba ne na wasa, addu'a ce sosai zamu dukufa ga yi masa. Zuwa anjima zan kira Kawunki Malam Yakubu. Na tabbatar shima zai taimaka. Ba a banza matarnan ta bar shi ba."
Zantukan Hajiya masu dadin sauraro suka katsemata tunani. Wani sanyin dadi ta ji, har ta mance kaso mai yawa na damuwarta, ta yi murmushi gami da godiya. Daga wannan ta mike ta bar mata dakin zuwanata.
Nan ta iske yaran sun yi baja-baja saman gadonta ana game a waya. Dubansu ta yi gami da murmushi, haka kawai ta ji har ta soma kewarsu. Maimakon ta korasu kamar yanda ta saba, kawai sai ta zauna ta biyemusu tare da alƙalanci.
Sai da wani tunani ya faɗomata sannan ta karɓi wayarta ta basu umarnin zuwa falo. Agogo ta duba, ƙarfe shida da rabi na dare, so ta ke ta kirashi amma ba ta kaunar abinda zai je ya dawo don haka ta zaɓi aikamasa saƙo.
***
LAMIƊO CRESCENT...
Yana zaune kamar kurma yana sauraron Hajiya Zeenatu da ke buɗewa John wuta akan ya yi girkin da mijinta ya kasa ci. Ɗora laifi kacokan ta yi akansa, shi dai ƙara russunar da kai ya yi yana ambaton "Sorry Ma." Hussein da abin ya ishe shi, miƙewa tsaye ya yi gami da daukar wayarsa.
"Please ya isa haka, na fadamaki yunwar ce kawai ba na ji, ba wai girkin ba ne."
Yana kaiwa nan ya nufi matattakala. Ta bishi da kallo kafin ta maido dubanta ga John, harara ta watsamasa gami da ba shi umarnin tafiya. Hankalinta ya koma ga tunanin abinda ta shirya yi. Wato shan maganin da Gora ya ba ta wanda ya tabbatar da zarar Hussein ya kusanceta za ta samu ciki. Samun cikinta ne zai mantar da Hussein tunanin kowa da komai face tattalin da zai koma ba ta.
Wannan ta sa da sauri ta jawo kofin ruwa ta daga riga ta ciro ƙullin maganin ta zuba gami da gaurayawa ta kafa baki, ba ta ɗago ba sai da ta shanye tas tana wani murmushi.
Shi kuwa Hussein, zube wayoyin saman gado ya yi ya shiga rage kayan jikinsa, wanda ya ke da niyyar shiga, ƙarar shigowar saƙo ya ɗauki hankalinsa. Duban wayar ya yi, kamar kada ya buɗe sai kuma ya tuna da saƙon da za'a aikomasa na abinda ya shafi aikinsa. Madadin hakan ya ci karo da sunan da hannunsa ya rubuta saman lambar da ya ɗauketa da wani irin muhimmancin da bai san dalili ba.
_*Heart*_
Ya furta tamkar baya so kafin ya kai ga buɗewa.
*_"Dukkanmu ajizai ne, mukan yi kuskure da saninmu ko kuma akasinsa. Bana fatan na yi abinda zai jefaka cikin ɓacin rai da damuwa. Shakka babu, Ramlat mai laifi ce, na yarda na shiga personal life dinka, na zaƙe da yawa. Ka yi hakuri, ka yi hakuri. Hakan ba za ta ƙara faruwa ba. Ka ji?"*_
Murmushi ya yi, ya kara karantawa ya fi sau uku, ya so ya gogeshi daga wayar amma ya ji ba zai iyaba. Wani nauyi hakan ya yi mishi don haka sai ya fasa, ya sanyawa wayar muƙulli ya jefa saman gado. Har ya shiga banɗaki bai bar murmushi ba.
Fitowarsa ba jimawa ya sanya kayan bacci, shigowar Hajiya Zeenatu ne ya sa shi dubanta. Saura kaɗan wata dariya ta kufcemasa. Rigar bacci ce a jikinta shara-shara kuma marar tsawo don duka tsawon iyakarsa gwuiwa. Ƙaton tumbinta da ruguza-ruguzan mamanta wadanda suka zube sun kwanta luf sun bayyana cikin rigar. Damtsenta kuwa a cike sosai sai dai ba ka misalta shi da na karfafan maza ba. Akwai bambanci.
Duba sosai ya ke mata, riga dai gatanan mai ɗan karen kyau da daukar ido. Lumshe idanunsa ya yi yayinda wani tunani ya bijiromasa.
'Za ta yi kyau sosai.' Ya furta ƙasa ransa, ankara da kuskuren kalaminsa ne yasa shi jan istigfari. Sai kuma lokacin ya tuna da bai yi sallar Isha'i ba ya ke shirin kwanciya. Abin yana damunsa, ya rasa me ke shagaltar da shi daga bautar UbangijinSa, ma'ana gabatar da sallah akan lokaci. Abin yana mishi ciwo, sai dai mafi yawan lokaci ji yake kamar wanda aka mantar. Sau tari ma wani bacci ke zuwa ya rufe idanunsa da zarar an soma kiraye-kirayen sallah.
Ganin ya mike yasa Hajiya Zeenatu tunkaroshi, hannayenta biyu ta sanya saman kugunsa.
Ya yi mata murmushi mai kama da yaƙe. Duk yanda ya so nunamata tsana ko wani abun, sai ya ji ya kasa.
"My Zeenat, kin yi kyau sosai."
Wani sanyin dadi ya mamayeta, ta sumbaci leɓɓansa.
"Nagode Sweetheart."
Ganin tana kokarin wuce gona da iri yasa shi janye jiki.
"Bari nayi sallah."
"Sallah, wace sallar?"
Yanda ta fadi a mamakince shima sai ta jefashi cikin mamakin kalamanta. Ya zubamata idanunsa mai
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 33 Chapter of 58