hanata daukar matakin da zuciyarta ta rayamata, wato ta tureta ta faɗi. Dole ta kakalo murmushi suka kara gaisawa. Itama Zahra haka ta yi mata, Hilal dai na gefe yana kallonta yana kara wassafa yanda so ya koma ƙi.
Abba ya yi mata murmushi, a kallo daya ya karanci abubuwa da dama a cikin kwayar idanunta, ya kauda kai sadda ta karasa ta gaidashi.
"Allah Ya muku albarka." Aka amsa da Amin. Nan kuma aka ɗauki hotuna, bayan wucewar Abba da su Yaya Munir har iyayen Amrah. Jidda dake rike da karamar Camera na Hilal ta ce.
"Yayana matso na muku hoto da Aunty."
Ya saci kallon Ramlat dake tsaye gefen Zahra, ba musu ya matso yayinda Zahra ta ja baya.
"Ina wuni." Ya gaidata, gaisuwar da ya ankarar da ita ashe fa ko kallon inda yake ma ba ta yi ba balle ta gaidashi. Ciki ciki ta amsa.
"Lafiya kalau."
"Oh, don Allah ku daina magana, ku kallo nan."
Maganar Jidda ya sanya su dubanta lokaci guda, aikuwa ta shiga hotuna ba kakkautawa. Don kanta Ramlat din ta ja baya. Hakan yasa Hilal kallon Jidda.
"Ya ishemu haka, ke idan kin soma ba ki san ki daina ba."
Ta yi dariya, jiki a sanyaye ta ke duban gefen Ramlat din, tuni ta soma tafiya da nufin barin wajen.
"Lah, Aunty ina za ki? Dawo ku yi hirarku bari mu ɗan zagaya. Dama akwai wata old schoolmate dita a nan, bari naga ko zan ganta."
Da wayo ta ja hannun Zahra suka tafi suka bar su, abinda tunaninta ya bata da sauyin Ramlat shine sun samu saɓani da yayannasu ne shiyasa ta sauya, barinsu su kadai zai sa ta sauko daga dokin fushin.
"Idan ba damuwa mu ɗan fita daga hayaniyarnan please."
Ta kalleshi, idanunsa sun kaɗa, ko menene yau Hilal ta kai shi bango. Yanayinsa ya sanya ta kasa yin musu, suka soma tafiyar kamar ba sa so har suka fice daga Hall din. Can parking space suka isa kasan wata itaciya saman kujeru suka zauna.
Duk kalaman da Hilal ke zubamata na ban hakuri da rokon ta dawo da soyayyarshi a ranta, ba ta san ya na yi ba, hankalinta na ga ta hanyar da zasu tattauna da Aliyu. Wannan ta sanya ta dubansa.
"Za ka yimin wata alfarma?"
Ya ƙuramata idanu, sai ya murmusa
"Ba abinda za ki nema wurina ban miki ba."
Ajiyar zuciya ta saki, ba kuma ta ji a ranta ya burgeta ba, duk kuwa da cewa tana danne wani tausayi dake tasomata yana son mamaye zuciyar, ganinta hakan ne daidai.
"Ka sanya Yaya Munir ya ban wayata, ka nunamusu yanzu komai ya wuce. Don Allah ka yimin wannan alfarmar."
Kamar ya ce mata sadda aka kwace bai san dalili ba, bai kuma kamata ya shiga tsakani ba, sai dai ya share.
"Zan san dabarar da zan yi a ba ki wayarki."
Ga mamakinsa sai lokacin ya ga murmushinta.
"Nagode sosai."
Wata ajiyar zuciya ya sauke gami da miƙewa tsaye tun kan kishi ya ci gaba da nuƙurƙusarsa.
"Ki jirani ina zuwa."
Bai jira amsa ba ya wuce. Ta bishi da kallo. Handsome da shi, zai burge kowace mace, amma banda ita. Tana son tuna wani mugun abu da Hilal ya taɓa yi mata sai dai babu ko daya banda tarin alkhairai.
"To ya zan yi? Banda iko da zuciyata."
Ta furta a fili sa'ilin da idanun suka cika da kwalla. Ba ta ji takunsa ba sai wani kwali mai kyalli da ta gani, ta dubeshi. Murmushi yake mai kama da yaƙe.
"Karɓa, kyauta ne gareki. Ina kara tayaki murna."
Ta murmusa itama gami da karɓa.
"Nagode sosai."
"Muje ko? Ina son zuwa wani wuri ne."
Ta amsa da toh, daga nan suka koma ciki ya hada kan su Jidda suka tafi. Jidda ta ji dadi ganin sauyi a saman fuskar Ramlat, wannan yasa ta fahimci abinda take zargi a farko hakanne. Wato dai saɓani suka samu.
***
"Wai nikam Rabi'atu, ina yiwa yarannan daidai? Hukuncin da na yanke akan auren Ramlatu da yaronnan ban mata gata ba?"
Yanda yake maganar murya a karye ya ɗarsa tausayinsa ba kaɗan ba a zuciyar Hajiya.
"Babu wani hukunci mai tsauri da ka taɓa yankewa Abban Yara. Kowane uba burinsa ɗiyarsa ta auri kamilallan yaro mai kyakkyawar nasaba. Kuma Alhamdulillah, Yaronnan ya kai yanda ake so. Don Allah ka bar sanyawa ranka tunani na daban har ya taɓa lafiyarka."
Ya yi murmushi gami da kara rungume matarsa.
"Aliyu da Ramlatu ke so, yaro ne mai kyakkyawar nasaba sai dai a iyaka bincikena yana shaye-shaye. An sanar da ni goyon kaka ne, ba wanda ya isa ya fadamasa ya ji. Uwa uba bai yi wani zurfi a karatun boko ba balle kuma na addininsa, koda ace na yi niyyar bai wa Ramlatu zaɓinta, ba zan iya daukarta na kai inda za ta yi baƙin jini ba. Ina son yarana. Ina son su samu wanda zai kularmin da su ko bayan ranmu. Meyasa Ramlatu ba za ta yiwa kanta faɗa ba?"
Tashin hankalin Hajiya dai ganin Abba ta yi yana hawaye, itama ba ta san sadda ta fara ba.
"Yaran ne muke haifarsu bamu isa mu haifo da halinsu ba. Addu'a kawai ya kamata mu ci gaba da yi musu. Allah Ya shiryamana su, Ya bamu ikon kula da amanarsu da Ya damƙamana. Sai dai hakkinsu ne su bi mu, hakkinsu ne su so abinda muke so. Mun tayasu son abinda suke so, meyasa su ba zasu hakura da son ransu su yi mana biyayya ba? Gani suke muna yin wani abin ba don muna sonsu ba. To ya zamu yi? Addu'ar ce dai. Ina tabbatar maka sai ta fi mu alfahari da wannan zaɓin in sha Allah."
Ta ƙarashe tana ci gaba da daukemishi hawayen, ba tare da ta damu da natan dake kwarara ba. Shima ya sharemata yana murmushi gami da sumbatar goshinta.
"Allah Ya yi maki albarka. Ina alfahari da dukkan yaran da muka haifa. Ramlatu ma tausayi take ban, sau tari ne idan ta aikata wani abun sai na cika da mamaki, kamar ba jininmu ba."
"Kar mu yi saɓo, addu'ar ta fi duk wannan."
Suka ƙara murmusawa cike da jin wani ɗaci a kasan ransu kafin kuma su hau tuna yanda a lokacin iyayensu ake auren ɗiya ba ta ko samu damar ganin mijin ba kuma ta yi biyayya ta zauna.
Karshe suka tattara komai suka ajiye gefe suka fuskanci rayuwarsu.
***
A satin biki aka kawo lefe da komai da ya kamata.
Gyaran jiki sosai aka shiga yiwa Ramlat, mutanen Daura sun soma zuwa gidan. Yau ma tana zaune wata gwaggonta, ƴar dan uwan mahaifinta daga Daura, ta tasata a gaba da wani hadin magani ta shanye. Dole ta kwankwaɗe ta mike ta bar wurin suna zolayarta. Kai tsaye wayarta ta ciro wanda tuni Hilal ya sanya an damƙamata. Aliyu ta hau kokarin nema a waya, ba zato ta ji an zare wayar a hannunta. Amrah ce tsaye fuska ba fara'a.
"Kar ki cemin har yanzu kina kiransa? Kwana uku ya yi sauran a sanyaki a lalle Ramlat, ki ji tsoron Allah. Kar ya kasance har bayan aurenki za ki ci gaba da kula wannan mutumin."
Tun soma maganar take watsamata banzan kallo kafin ta ja tsaki ta kwace wayarta.
"Ai an so hakan ta faru shiyasa aka yi gangancin haɗani aure da Hilal. Ba zan fasa ba, nace yanzu na fara Amrah. Idan kin ga dama ki yi shiru idan ma ba ki ga dama ba ki yimin terere a dangi. Mtsw."
Ta gifta ta wuce cikin banɗaki ta rufe. Ta san nan ne kaɗai wurin da za ta yi wayar sirrin da Aliyu. Amrah ta saba da wannan cin fuska na Ramlat akan Aliyu, wannan ta sanya ta girgiza kai da fadin Allah Ya kyauta. Daga nan kuma ta dauki kyallen anko don abinda ya maidota dakin kenan, zasu fita kasuwa siyowa wasu mutan Daura anko. Su Naja'atu ne zasu yi mata rakiya. Saboda biki nan gidan duk suke kwana.
***
Tana fitowa daga banɗakin ta ga Bilkisu zaune a gefen gado tana shayar da ɗiyarta. Fuskar Bilkin a daure take dubanta, ta kauda kai itama. Maganar duniya ba ta ɓuya, tuni Bilkisu ta gane komai ta sanar da su Fareeda, har ma can dangin Hilal sun soma ƙananan magana. Babansa ne ya tsawatar da abin ya kuma ce kar ya ƙara ji.
Mamar Hilal da kannensa kuwa sun soma jin tsanar Ramlat, banda Hilal na gyara wasu lamuran da kalamai, da wutar da Bilkisu ta kunnamishi a gidan ta janyo mishi fasa aure da Ramlat. Sai dai mahaifinsa mutum ne mai magana ɗaya, yanda ya dage akan ba wanda ya isa ya hanashi aurawa Hilal abinda yake so, hakan ya kashe bakin kowa sai ƙananun magana da ba'a rasawa wurin mata.
"Ina wuni Anti Bilki."
Ta gaisheta ciki-ciki don yanzu ba wani mutunci suke ba.
"Lafiya kalau Laila ta Majnun."
Sanin cewa magana ta yaɓamata ne yasa ba ta ce komai ba.
"Ni na rasa abinda Hilal ya gani ya maƙale maki alhalin yanzu ba kya ta ta shi. Wallahi mata hudu ya so zai iya aura a lokaci guda. Amma da yardar Allah ko ya aureki sai mun mishi aure."
Cewar Anti Bilki tana mai kwantar da Yasmin a saman tana jijjigata don ta yi bacci. Ramlat dake shirin tayar da sallah ta dubeta rai a ɓace.
"To ko hakan za'a yi? Ki tambayeshi wanda ya nacewa wani tsakanin ni da shi. Nace bana so, bana yi, wai dole ne?"
Ta ja tsaki ta fice daga dakin zuwa can bayan gidan wurin ciyayi ta zauna tana aikin kuka.
Ita kuwa Bilkisu ranar wuni ma ba ta yi ba a gidan yanda ta yi niyya, ta goye diyarta ta fice ba da sanin mijin ba.
Duk borin da ta je ta tayar a gidan su Hilal game da kalaman Ramlat din, iyakar su matan kawai ta tsaya don su Jidda har da kukan takaici da tausayin yayansu. Ji suke kamar a fasa gaba daya sai dai ba su da ta cewa tunda iyaye maza sun tsawatar.
***
Duk wani hidima da za'a yi Abba ya ce ayi kafin a daure aure, don a cewarsa ana daura auren to fa dakinta za'a miƙa ta.
Shagulgulan koda sun yi armashi, basu yiwa Ramlat ba. Baƙin komai take gani. Dinnerparty Hilal yace ya fasa ganin irin shirin da ƴan uwansa ke yi na gasawa Ramlat magana a ranar.
"Shirun Ramlat na nufin abubuwa da dama."
Fadin Hajiya bayan daurin aure, a sadda Zulaihat ta bi ta sashin Abba don amsar laffayar da Ramlat din za ta sanya.
"Nima nayi mamakin yanda ta kwantar da kai ake bikin lafiya ba kamar yanda na zata ba. Amma ko ma mene ita ta sani. Mijinta ne yanzu, idan ma ta wulakantashi ita za ta kai kanta wuta."
Cewar Zulaihat cikin halin ko in kula.
"Uwani kenan, ku dai dinga zagayawa kuna yi mata faɗa. Ta dauki duniya da zafi, ta sauke."
Ba ta son ma zancen, don haka ta sungumi karamin akwatin da aka zuba kayan da duk Ramlat din za ta yi amfani da shi a ranar farko bayan kai ta gidan kafin a kawomata sauran akwatin, ta fice daga falon.
Hajiya sai ta tsinci kanta da kasa fita wurin yan uwanta, ta zauna ta yi shiru cikin tunanin meke tafiya a zuciyar yarinyarnata.
"Allah Yasa dagaske kike Ramlatu."
Ta furta cikin faduwar gaba kafin ta yunkura ta mike ta fita.
***
Dogon hijabi ta sanya a saman leshin da ke jikinta. Ga kunshi da kitso an mata. Kwalliyar fuskar ta kara fiddo kyawunta sosai.
"Ina zuwa?" Cewar wata Hannatu ƴar Gwaggonsu Sa'adu ta Daura.
Murmushi ta ɗan yi.
"Yanzu zan dawo."
"Ki sauri don Allah, yanzu za'a zo nemanki tunda an yi magriba."
Ta ja guntun tsaki ta fice. Allah Ya taimaketa har ta fice ba ta hadu da su Zulaihat ba.
"Malam Hassan. Malam Hassan."
Ya fito daga dakin gugar. (Daki karami a gidan inda Malam Hassan ke musu gugan kaya)
"Na'am."
Ta ɗan waiga sai kuma ta yi shiru sanadin wasu da suka zo wucewa. Ta kauda fuska har suka fita. Cikin sauri ta dubeshi.
"Ya ake ciki?"
Cikin rashin gaskiya ya kalli jama'a kafin ya ba ta amsa.
"Bayan gidan na ajiye, na tabbatarmaki ba wanda zai kawo komai don kusa da inji ne."
Ta yi murmushi.
"Nagode." Daga nan ta daga zani ta fiddo kudi masu yawa kulle a leda ta mikamasa.
"Abinda kake zargi ba shi zai faru ba kamar yanda na rantsemaka. Barazana ce kawai."
Ya yi murmushi ya gyada kai. Shi ko mene ba damuwarsa ba ce tunda ya ji dumus. Hankali kwance ta koma ciki, suka yi kiciɓus da Zulaihat.
"Ina kika je?"
Ta yi murmushi.
"Shikenan kuma ba damar na yawata a cikin gidanmu?"
"Nan da awa kadan za ki bar gidan zuwa gidanki kema."
Fadin wata abokiyar wasansu Asabe. Aka yi dariya, ita kuwa ta shige don kaucewa kaifafan idanun Zulaihat din dake kanta, kallon rashin yarda tsantsa take mata.
***
Aka kammala shirin kai ta gidan miji, Abba ya ce aje zai je har gidan washegari ya yi nashi fadan. Hajiya kuwa ta ce wanda yayyunta da gwaggonni suka yi ya wadatar.
"Saura ku yafemata."
Cewar Dije abokiyar zaman Hajja. Daga Abba har Hajiya suka ce sun yafemata duniya da lahira.
Tana kuka aka tafi da ita gidan Hilal. Gidan da ta ke mishi kallon wuta.
Aka watse aka bar ta, jikin Amrah a sanyaye, ta kara juyowa ta dubeta da lulluɓin har lokacin. Dawowa baya ta yi tana hawaye ta lalubo hannunta ta rike.
"Na sanki Ramlat, ba ki fiye cire abu a ranki da wuri ba. Na sanki kamar yunwar cikina. Kiji tsoron Allah. Ki ji tsoron Allah."
A hankali ta ji Ramlat ta zare hannunta daga nata.
"Amrah muje, suna jiranmu."
Fadin Maryam da ta leƙo. Amrah ta mike tana kallon Ramlat, kafin kuma a sanyaye ta juya ta fita bisa gargadin Abba da ya ce ba ya son abar mutum ko daya da zummar wani siyan baki.
Kamar jira ta ke sahu ya dauke, kamar jira ta ke ta bar jin motsin kowa a gidan. Ta bude lulluɓin laffaya gaba daya ta fito. Babu kowa kamar yanda ta zata, ba ta damu da dukiyar da aka zuba a gidan ba, bai isheta kallo ba hakan yasa a gaggauce ta fita. Komai da sauri take yi tana kara waigen kofa har ta zagaya bayan gidan. Nan ta iske baƙar ledar da ta tabbatar shi ne saƙonta. Ta dauka ta jijjiga sannan ta murmusa. Ledar ta cire ta dauki sakon zuwa ciki. Ta adana a karkashin gadon ta zauna.
"Komai zai zo karshe a yau, daga yanzun ba wanda zai kara tadamin hankali akan Hilal. Babu shi!"
Ta furta a fili, ƙarar bude gate da ta ji ne ya sanya ta warware ɗankwali da yin wurgi da ribbons dinta a gefe. Idanunta kuwa dama kallo ɗaya za ka yi mata ka gane irin kukan da ta ci.
"Yau ko ni! Ko kai Hilal!"
Ta ƙara fadi.I think you'd like this story: "Ƙarfen Ƙafa" by Rufaida-Umar on Wattpad https://my.w.tt/iRW2CA35T9
🕯️ *ƘARFEN ƘAFA*🕯️
_*Rufaida Umar*_
Bismillahir Rahmaanir Raheem.
14)
Kallo ɗaya za ka yi mishi ka hango annashuwa a zuciyarsa. A jikinsa yake ji komai ya zo karshe, a jikinsa yake jin ya samu soyayyar Ramlat da yardar Allah. Sai dai bai san meyasa kirjinsa ya hau bugu bayan daka motarsa da fitowarsa ba. Ya ɗan yi shiru yana kallon kofar gidan, bai jima da rabuwa da babban amininsa Ma'aruf ba. Sosai ya ba shi shawarwarin da suka dace game da zamansa da Ramlat. Ya dauka dari bisa dari.
Ya kalli sama, walkiya ake yi sosai ga hadari. A hankali ya sauke ajiyar zuciya sannan ya yi kari cikin gidan.
Ya rufe kofar falon sannan ya ƙaraso ciki da sallama, falon ya tsaya ƙarewa kallo. Ɗakin Amarya kam ya yi kyau iyakar kyau, abu daya idan ya tuno yakan dakushe farin cikinsa sai dai kuma karfin gwuiwar da ya samu daga Amininnasa shi ya rinjayi komai har ya sa shi nufar hanyar ɗakinta da sallama. Bai son gayyar abokai da sunan rakiyar Ango.
Ya cika da mamakin rashin ganinta zaune a saman gadon kamar yanda ya zama al'adar aure.
"Ramlat." Ya kira da tattausan murya yana karasa shigowa dakin.
"Tooh." Ya kara ambata ganin farin laffaya da ɗankwalinta yashe saman gadon, hanyar banɗaki ya kalla, kai tsaye ya shiga bayan ya ajiye babbar riga da hula saman gadon. Nan ma wayam, sai tashin kamshin turaren wutan da aka sanya da kyallin fararen tiles da ya kashemishi ido.
"Gani nan!"
Sautin muryarta a sama, wannan ne ya sa shi juyowa da sauri yana kallonta baki sake. Ya kai duba ga jarkar da ke hannunta na hagu da kuma ashanar da ta rike a dayan hannun. Tana tsaye a tsakiyar dakin, kallo ɗaya za ka yiwa idanun ka san ta ci kuka ba kaɗan ba. Tana tsayen amma jan majina take yi, ga wasu hawayen da ke ƙara sauka saman fuskarta.
"Ramlat? Me ya haka?"
Ya furta cikin nuna dakiya sai dai zuciyarsa tamkar ta fasa kirjin ta fito tsabar tashin hankali. Duban tsana take mishi.
"Ka fini sanin mene haka Hilal tunda ka nace akan lallai sai ka zauna da ni! Nace bana sonka! Na fasa aurenka! Amma ka tursasa lallai sai da aka auramaka ni! Dole ne? A farko wa ya yimin dole? Ba ni na kawoka gidanmu na nuna ina sonka ba? To na fasa! Na fasa! Bana sonka amma ka nunan kai maye ne! Kafin ka cinyeni ni zan soma kashe ka! Dama ni rayuwata ta kare tunda har aka daura aurena da mutumin da na fi tsana! Muddin ba ka sake ni ba wallahi ina maka rantsuwa da Maƙagin dare da rana, yanzu ba anjima ba, zan watsa fetur dinnan kuma na kyafta ashana mu mutu gaba daya! Kar ka yi tunanin guduwa domin na rufe ko'ina a gidannan! Na rufe ɗakunan!"
Tunda ta soma maganar ya ƙuramata ido, mamaki da baƙin ciki suka cika zuciyarsa. Bai taɓa kaiwa ƙoluluwa a ɓacin rai bisa yanda take mishi ba irin yau. Bai kuma taɓa zaton za ta aikata makamancin hakan ba.
"Ramlat? Yau soyayya ce ta koma ƙiyayya? Dama ƙiyayyar ta yi zafin haka? Kin manta Hilal? Kin man..."
Bai kai ga ƙarasawa ba ya ga ta ɓalle murfin jarkar ta hau watsa kalanzir a tsakar dakin har da bangwaye, ba ta ko damu da yanda ya ke jiƙa riga da hannunta ba. Cak ta ji ya riƙe hannuwan wanda ya yi sanadin faduwar jarkar a ƙasa. Idanunsa sun kaɗa saboda tsananin tashin hankali da ɓacin rai. Ganin yanda take kici-kicin kwatar kanta ya sanyashi watsi da hannun har hakan ya yi sanadin faɗuwarta a ƙasa, har lokacin ba ta bar kuka ba, ganin ta na kokarin kyafta ashanar ya sa ƙafa ya buge hannun, ashanar ta faɗi a ƙasa. Durkusawa ya yi saitinta.
"Ba sai kin kai ga kashemu ba! Ki je ki auri wanda kike so, ni Hilal na sake ki. Sai dai ki sani, idan har da hakkina, Allah zai min sakayya. Shakka babu kin yimin butulci, kin tarwatsa dukkan farin cikina. Kaicon wannan ranar." Daga haka ya mike yana kallon yanda take dariya tana share hawayen fuskarta. Ya juya saboda kallonta ma kuma ɓata ransa yake. Shakka babu mai hakuri bai iya fushi ba.
"Ina za ka? Ai da saura!"
Bai yi niyyar tsayuwa ba sai dai dole ya tsaya din jin ya murɗa kofar amman ko gezau. Jakar hannunta ta nufa ta fiddo karamin littafi (Memo) da aka raba na bikinsu, a take ta yage bangon ta yar a ƙasa, ya bi bangon da kallo, hotonsu ne, bai mance ko ranar da za'a yi hotunan sai da ta gasamishi maganganu masu zafi, sai dai hakanan ya danne ya shanye. Kallonta kawai yake yana ƙara mamakin yanda so ya koma ƙi. Ramlat da a baya zai iya bugun kirji ya ce ta fi sonsa kan yanda yake sonta. Yau ita ce ta juyamasa baya lokaci guda. Bai dauka abin zai biyo har cikin aurensu ba. Ba kyawunta ne ko diri ya ruɗeshi ba, kaunarta yake da zuciya ɗaya. Da ace ɗayan biyun da ya lissafa ne, ba zai rabu da ita ba tare da ya gogamata tabon da har ta mutu ba za ta mance ba. Bai kuma mance yanda Ummansa ta ɓatamasa rai ba duk akan ya nace sai ya aureta.
"Tunanin me kake? Karɓa ka rubutamin a rubuce."
Daddaɗar muryarta da a yanzun ta zama kamar ta zakanya a kunnensa ta katse shi. Ya karɓa yana kallon kwayar idanunta, ta yi amfani da wannan damar ta harareshi ta tsuke baki gami da kauda kai. Ya maida kai ga takardar yana kammalawa ta karɓa. Bakinsa na rawa ya ce.
"Ban mukullin."
Ba ta ko kalleshi ba ta ciro mukulli cikin riga ta miƙamasa. Ya karba da sauri ya bude kofar ya fice zuwa falo.
A gaggauce ta mike ta zura hijabinta dogo na sallah da aka daukomata. Ta dauki jakarta ta fito. Yana zaune a falo ya dafe da hannuwansa biyu yana fidda hawaye kirjinsa na suya. Ba ta ko kalleshi ba ta fita, burinta ya cika.
"Duk abinda ya faru, ka so faruwarsa!" Ta furta a fili kuma a hankali sa'ilin da take share hawayen fuskarta.
Tana tafe tana sharar hawaye, ga wata irin iska da ake yi da walkiya. Allah Ya taimaketa ta samu abin hawa kai tsaye gidansu ta nufa. Ta yarda idan ma kasheta za'a yi, su kashe. Ko mene su yi mata. Amman ita kam ba za ta iya zama gidan Hilal ba da sunan mijinta kuma a waje tana cin amanar mijin aurenta na sunnah ba. Ba za ta iya wannan munafuncin ba don ta san karshen abinda soyayyar Aliyu da auren Hilal zai jawomata kenan.
***
Abba ya dubi Hajiya da murmushi a saman fuskarsa.
"Yau ina cike da farin ciki. Na kashe matsalar Ramlatu, fatana yanzu Allah Yasa ta zauna lafiya da mijinta."
Hajiya dake kakkaɓe shimfiɗa ta yi murmushin yaƙe. Har lokacin hankalinta bai kwanta ba. Sam ba ta da wata nutsuwa.
"Amin."
Ba tare da ta kalli Abban ba, ta ci gaba da aikinta. Ya sa hannu ya riko hannunta, hakan ya dakatar da ita ta dubeshi. Tsoro, fargaba su ya hango cikin kwayar idanunta.
"Ya aka yi? Ashe ba za ki fawwalawa Allah komai ba? Ki bar tunanin wani abu akasin alheri."
Ta gyada kai kawai tana jin saukar ruwan hawaye. Hayaniyar da suka jiyo na mutanen gidan ya sanya su kallon juna cike da rashin fahimta.
"Meyafaru?" Fadin Abban hankali a dan tashe, Hajiya kuwa kirjinta ne ta shiga bugu fiye da baya. Da hanzari suka fito suka nufi babban falon gidan na Hajiya.
Tana tsaye jikinta sharkaf sakamakon ruwan da ya yi mata duka cikin adaidaita sahu, kuka take yi yayinda taron dangin uwa da uba suke neman ba'asi hankali tashe. Hajiya ji ta yi jiri na shirin kayar da ita hakan yasa ta samu ta zauna saman kujera tana salati.
"Ya isa haka!" Tsawar da Abba ya daka cike da karfin hali don jikinsa ma rawa yake yi, shi ya katse su duka.
Kai tsaye ya karasa ga Ramlat ya kama hannunta suka shiga bangarensa. Irin su Zulaihat da Amrah da suka san komai dangane da auren, kuka kawai suke yi sanin cewa koma mene Ramlat ta shuka wata tsiyar ne.
***
"Daina kuka Ramlatu, ya isa, ya isa. Ki fadamin meke faruwa?"
A hankali ta ciro takardar a jakarta, babu inda ba ya rawa a jikinta ta mikawa Abban.
"Don sonka da Annabin rahma s.a.w, Abba ka yafemin. Ba zan iya zama da Hilal ba."
Ta furta tana sheshsheka sosai. Abban ya fita shiga tashin hankali,ya fita shiga ruɗu. Hannunsa rawa yake, kirjinsa zafi yake. Yana ji inama mutuwa ta taddashi tun kafin ya haifi ɗiya kamar Ramlat?
Daidai lokacin da Hajiya ta turo kofar ta shigo.
"Wace irin ƴa na haifa? Rabi'atu wace irin ƴa kika haifamin?! Anya ba'a yimin musanye a asibiti ba?! Don ina mamakin kasancewar Ramlatu jinina!"
Ta riga ta gane, ba'a hayyacinsa yake ba, ta san ɓacin rai ne. Ta ƙaraso sosai gwuiwa a sanyaye ta kai karbi takardar da Hilal ya rubuta sakin.
Na saki Ramlatu saki daya bisa tursasawarta. Allah Ya zaɓamin wacce ta fiyemin ita alheri. Itama Ya bata abinda take so.
Abban ya mike zuwa dakinsa. Waya ya ɗauka ya kira Yaya Munir ya fadamishi dukkan abinda ya faru. Ya kara da
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 11 Chapter of 58