Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
wadansu irin bishiyoyi, kalmar da take yawan zuwa kunnen shi kenan. _idan kana tunanin ka wulakanta ni ne, Allah yana nan kuma baya barci! MALIK ka dauki abin da yafi Darajata! Kai da ba zaka iya nuna bajintar ka ba, sai ma sha pills. Allah yana sane dani_ yadda muryan yake rab'ewa bibiyu ne ya sanya shi firgita ya kuma nausawa cikin dajin,  kamar wanda ake bin shi da gudu, ji yayi abu ya rike mishi kafada, ya zube a kasa. Zeeh ya gani a gaban shi tana rike da wani katon wuka, ta d'aga zata caka mishi, sai ganinta yayi ta fadi gefe, tana kuma d'agowa aka kuma likata da kasa, Wata mace ya gani tana dukar Zeeh sai lokacin ya ya tashi, aka ce mishi. _"Ka rike Addu'a, ka mai da hankalinka akan Ibada, idan ba haka ba zata kashe ka"_ A firgice ya farka yana me share gumin da ya sharb'e, cikin sanyin jiki ya mike zuwa ban daki, yana kallon agogo karfe biyar da wani abu, shi yasa Manzon Allah yayi hani da barcin la'asar, a gajiye ya shigq ban dakin tara ruwa yayi a cikin jacuzzi, ya shiga ya zauna. Surar macen da ya gani a mafarkin shi, ta tuna mishi wani alamari, ta tuna mishi wani abin da ya manta duk da ance mafi yawancin mafarki ba gaskiya bace amma yaso yasan me irin jikin matar mafarkin shi. Ajiyar zuciya ya sauke yana rike da sunanta amma ya kasa fadar shi akan harshen shi, ya zaga furtawa, ga dai sunan a bakin shi. Amma tayi mishi nauyi. Lumshe idanun shi yayi yana lissafin rabon shi da Zeemalik, a shimfid'a,  kusan wata biyar zuwa shida. Ajiyar zuciya ya sauke tare da jin wani irin yanayi na musamman, mace yake muradi! Macen ma hadaddiyar irin wacce ya tab'a haduwa da surarta,mace me dirin halitta. Lumshe idanun shi yayi wasu hotunar shi da wata mace wacce ya gaza ganin fuskarta ya shiga mishi yawo akan idanun shi, a hankali yaji little Malik yayi wani irin motsi, numfashi yaja me ƙarfi, sannan ya kuma lumewa cikin ruwan, yana masifar buƙatar mace irin wanda ya gani yanzun, haka yayi ta nazarin abinda ya tab'a samu ya tab'a haduwa da shi. Zeeh din shi ta haɗu, amma ita wannan haduwarta na musamman ce, sai dai yana ji a ranshi zasu kuma jonewa, zai nuna mata yadda yake iya sarrafa mace sala sala...     --- Cameroon... Wani babban Unguwa ce, me dauke da mutane zuri'a Hammadada, duk da ruga ce amma zaka ga yadda kowani gida aka yi ginin zamani, a hankali Dr Ishaq ya shiga titin da zai kai shi Unguwar, yana tafiya tare da ganin yadda wadattacen arziki irinta Fulanin asali masu haɗin ruwa biyu. Kyawawa masu matukar kyau, idanun su kuwa golden ne irinta Inayat, sai dan bakin su nan, sun kai a kirasu da kyawawan Afrika. Yanayin mutanen rigar kala huɗu ne! Akwai farare! Akwai wanda basu kai su fari ba, kwai kuma wankan tarwada, akwai kuma bakakke sosai, amma kyawawan ne na gaskiya da gaskiya, tsayawa Dr Ishaq yayi sannan ya kira wasu yara ya tambaye su. Basu jin Hausa fulantancin ma ba iri guda bane, sai da ya ambaci Hammadada shine yasa suka kalle shi sannan suka ce mishi. "Ai gidan kakan mu ne, gashi can a cikin garfen Rakuma,!" Godiya yayi musu, sannan ya ja motar har kofar gidan Iyayen Maman Inayat. A hankali ya fito tare da Balkisu, suka nufi inda yake, gaishe shi suka yi ya kurawa Balkisu ido, sannan ya d'an matsar da ita ya leka gurin motar, murmushi yayi sannan yace musu. "Ishaq! Na aike ka ka tawo min da Rukayyah ne?" Da sauri Balkisu ta kalle shi. Sunkuyar da kai yayi cikin nutsuwa yace mishi. "Dattijo ban son kayi min haka ba! Sabida Inanih bata san ni d'an yar uwanta bane, Dattijo meye amfanin wofantar da ita?"  Cikin zafin rai yace mishi." Tsallake ni tayi ta zabi Amadu! Anan yazo ya gaya min ta tafi bariki, a cikin shekaru talatin Inani bata tako tazo inda nake ba, sai yau da ciwon za...." Zuɓewa Balkisu tayi iya karfinta ta fasa wata irin ihu, tare da cewa. "Laifinta rabo? Laifinta ya shafi ta yarda take muradin tazo da kanta,Ba laifi bane dan kayi fusata, kuskuren ne babba jifar mahaifiyar mu da kalmar Assha!" Wani irin kuka ne ya kwace mata tace mishi. "Baba ni na zo fansar laifin da tayi, ka bani duk wanda yayi maka a cikin Zuri'ar ka, koda kuwa mahaukaci ne, don Allah ka kula mahaifiyar mu!" Kallon yarinyar yayi yana kuma girmama soyayyar da takewa Mahaifiyarta, "Ishaq! Maza ka shiga gida ka kira min kawunan ka tare da, Kurma!" "Dattijo! Kuma kurma kuma!"  Cikin ko in kula yace mishi. "Idan bai maka ba zaka iya mai dasu." Da sauri ya shiga cikin gidan, can sai gasu tare da yan uwan Maman Inayat, suka fito. Tunda ta gansu jikinta ya shiga rawa, tana kokarin fitowa daga cikin motar Zehrah tana rike da ita. Kallon Kurma yayi sannan yace mishi. "Tayi maka a matar aurenka?"  Murmushi yayi wanda ya kuma kara fidda kan shi, sosai. Sannan ya gyada kai, kallon Balkisu Baffa yayi sannan yace mata. "zaki fanshi laifin Mahaifiyarki?" Bakinta na rawa tace. "Eh Baffa!" "Shi kenan! Na bashi ke!"  Kallon shi tayi ta sauke wasu irin kwalla masu zafi tace mishi. "Nagode!" Tausayin yarinyar hadi da kaunar Mahaifiyarta ya kuma dawowa zuciyarshi, dama muka  bai cireta a ran shi ba, yayi amfani da kawaici ne ya manta da ita, ya yakince ta daga  cikin zuciyar shi. Kallon su Abubakar ya nuna musu motar, suka isa aka fidda Maman Inayat, baƙinta ya karkace. Jiri ne ya dibe Balkisu zata zub'e,  kurma yayi maza ya riketa, tana kokuwa da numfashinta, rike rigar shi tayi cikin fitar wani irin kuka tace. "Hamma Maman mu!"  A hankali ya janye ta daga jikin shi, ya riko hannunta, suka nufi cikin gidan, sun same Mamah an shimfid'a babban taburama, wanda aka daura dadduma akai, aka jingine Mama, tana mikawa Baffanta hannu. Dakyar tace mishi, "Baffa Diyan!" Wato ruwa, sauri ya isa gabanta, ya bata  ruwan da aka miko mata, tasha duk da ya zube a jikinta, ta rike hannun shi. Hawaye na zuba daga idanun ta. "Baffa ka yafe min!" Wani numfashin yaja, sannan ya rike hannunta, yace mata. "Waye ya gaya miki ban yafe miki ba? Ai tuntuni na yafe miki! Babu wani rike ki a raina, domin na yafe miki, haka ma Mahaifiyarki, wancan yaron da ya kawo ki, d'an Hajjo ne! Gashi nan ya kawo mana ke gida, na yafe miki autar Malam." Tunda yake magana take kallon shi, hawaye na zuba sosai daga idanunta, a hankali ta fisgo. "Inaya...! Daga haka ta sauke ajiyar zuciya, kwalla na zuba daga cikin idanunta, tunda yaga tayi shiru hannunta ya daina motsi, ya juya cikin fulatanci yace. "ku dauki yaran zuwa daki, dan mahaifiyar su ta amshi kiran mahaliccin ta." A firgice Zehrah tayo kan Mamarta, wani matashin saurayi ya rikota, gam. Ihu ta fasa kamar mahaukaciya. Tana fadin, "Wayyo Mamana, don Allah karki tafi ki barmu, Wayyo Allah Addah Inayat." Kurawa Mahaifyar su Ido Balkisu tayi, a hankali ta mike zata isa inda take, Kawun Sha'aibu ya rike ta. "Kawu! Maman mu!" Rikota yayi yace. "Kina fushi da Ubangiji ne?" Girgiza kai tayi tare dacewa. "Alhamdulillahi! Innalillahi wa'inna ilaihi rajioun, Ya Allah mun tuba. Ka yafe mana. Ka jikan Mamah mu. Aunty Inayat ina kike."  Allah sarki. Yan uwan Mamah mata da maza, sune suka tsaya akan gawarta, tare da yan uwan Baffanta suka tsaya aka shiryata, abin tausayi. Zehrah da Balkisu suna dunkule a jikin juna, har aka gama shirya Mamah, aka zo aka kira su. Dakin da gawar Mamah take aka kai su, koda suka shiga suke addu'o'in idanun su ba zubda kwalla. Suna tsugune har Baffa ya fita dasu, cikin tausayin jikokin shi, suka nufi dakin ya dawo yayi mata addu'a, tausayin yan uwansu da basu ga gawar Mama ba suke, musamman Inayat.   Aka ayi sallar ta, a kofar gidan Malam Hammadada. Aka wuce da ita makabarta.      *** Ina tsaye tare da sakawa wata mata ruwa, naji gabana ya fad'i a wani mugun tsoro ne ya kamani, a hankali zuciyata ta furta, min "Mamah!" Take idanuna suka cika da kwalla, lokaci guda naji suna zuba min, kasa aikin nayi na nufi Khadi nayi mata bayani, ta karasa aikin, sannan na wuce ban dakin mu, kewar Mamah da kanena ne ya kamani na fashe da kuka, sosai nake kuka.  Dan motsin da cikina yake shima ya tsaya cak, dakyar na fito ina son na samu guri na zauna na kasa, sai da aka kira Khadi, ta kaini dakin hutu, tunda na shiga nake kuka. Sosai na kasa magana ko an tambaye ni kukan zan cigaba da yi, bani da amsar badawa haka yayi matuƙar daga musu hankalin musamman Khady....  Kuyi hakuri!.... _KOME DA LOKACIN SA_*          https://my.w.tt/2E8h0g7BNab             Chapter 19     Na MrsUsman400 I don’t create companies for the sake of creating companies, but to get things done. Ban tab'a kukan da nayi ba a yau, har muka gama aikin ranar ban daina kuka ba, suka dame ni da tambaya sai dai na kuma rushewa da kuka, daga karshe suka daina damuna. Ina kwancen har dare, ina tunanin Mama da yan uwana, ina son zuwa amma tsoron tozarcin Baba ya hana ni zuwa. Amma yau naji kewar kowa da kowa, kuma ina matuƙar buƙatar su,dan haka zan roki pass gobe Insha Allah naje na gansu. Ina jin wani baƙin al'amari a tare da Ni, har na dawo gida, bana dai dai, kuma bana son damuwa. Ina jin matan gidan mu suna gulma amma haka bai dame ni ba, dan ina ji a jikina kamar nayi rashin me girma a rayuwata. Har dare ko waje ban leko ba, haka yayi matukar basu mamaki, duk da bani da yawan shiga cikin jama'a, amma ina ƙoƙarin idan anyi wani abu nayi musu Jajjen ko sannu, haka ya rage kaifin k'iyayyar da suke min. Ina zaune akan abin sallah Maman Ummi ta d'aga labulen tare da cewa. "Hmm! Inayat lafiya kuwa, naga yau gabaki daya baki da walwala, ko rasuwa aka miki."  Ban san ya aka yi ba, ko dan kalmar mutuwar ce ta fadar min da gaba, amma naji wata irin tsoron da ban tab'a ji ba, a razane na kalle ta. Kafin naji wata irin rauni nace mata.."Wallahi ban sani ba." Shiru tayi na wani lokaci, kafin tace min, "toh ai ya dace ki kira gidan ko? Kiji lafiyar su." Kamar wanda nake jiran cewar haka kawai idanuna ya shiga zubda kwalla. Cikin D'an dana sani nace mata toh. Na amsa ne kawai, amma bani da hanyar da zan same su, tunda na goge Number su a wayata bayan nayi blocking dinsu. A yau naji na tsani kaina fiye da yadda na tsani MALIK, bana son ganin kaina, wai me yasa ma nake raye ne? Nayi wannan tambayar yafi sau goma, amma babu amsa, sai juyin da d'an cikina yake na alamun yana azabtuwa da yunwa, bude wata jug nayi na dauko karamin kofi na cika da kunun koko. Na fara sha ina zubda kwalla, ina kuma jin kewar gida sosai. Har kusan karfe ɗaya na dare idanuna yaki barci,sai da na tashi nayi alola zan gabatar da sallah, sannan na fara jin barci. Amma ban kwanta ba sai da nayi isha tare da shafa'i da wutiri, sannan na daura sallar nafilla akai. Inda na jima ina addu'o'in sosai, na kai kuka na ga Allah na kuma san zai share min hawaye, na kai ƙarar duk wanda ya shirya zalintana, gurin Allah. Shima Malik na kai shi kotun Allah, inda babu kudi ko wata mukami da zata bashi kyautar gaskiya, a hankali nayi kwanciya ta. Ina jin kewar Mahaifiyata, kaunarta yana kara samun karfi a zuciyata, haka na kwanta cike da tunani wanda ya haifar min mafarkin Mamah, cikin fararen kaya. Tana zaune na daura kaina akan cinyarta, murmushi tayi cikin jin dadi. Ba zance ga abin da muke tattaunawa ba, amma naji dadin ganinta. Haka tayi ta murmushi amma bata ce min kome ba, karshe dai haka na farka sakamakon jin sallama a masallacin Unguwar mu.     A hankali na tashi,  duk jikina a mace, nayi alola sannan nazo na gabatar da sallar, ina idarwa na daura ruwan wanka. Ina samu yayi zafi na dauko miyar da na ajiye, na kasa kome, kiran layin Khady nayi na gaya mata ina son pass zan je Gombe, aikuwa tace min naje. Ina gama cin abinci shima dan abin cikin ne da babu abin da zai sani cin abincin. Na shirya da wuri na nufi tasha,               Mun isa da wuri, dan haka na duba jakata, na dauko babban hijab na saka,sannan na nufi inda ake sayar da nikab na saya, a hankali na saka. Sannan na nufi Unguwar mu,  daga nesa na hango kofar gidan mu, na nime wani yaro yaje min gidan ya kira min Mamana, koda yaje suka ce mishi yaje sun tashi, daga gidan take kaina ya kulle, Mama ne suka tashi ko har da Baban mu, gabaki daya bani da amsar tambayar kawai na juya na bar garin ma, sabida ban san me zai iya faruwa ba.   Koda na koma kashare ban wani damu da mutanen gidan mu ba, sai dai ina jin suna cewa." Ai taje zubda cikin ne sai kuma bazai fita ba," Maman Ummi tace musu."A'a kawai dai bata da lafiya ne, domin tana cikin damuwa sosai, kuma ni wallahi bazan kuma zaginta ba, dan shekaranjiya. Ita ta biya mana kudin wuta dana magani da baban Ummi yaje asibiti bai jin dadi. Dan haka Ni na zubda damuwa akanta, yarinya nan bata tab'a shiga damuwar mu ba, amma mu, mun shiga nata, idan gari ya waye zamu gaishe mu, ta tambaye mu yaran mu, toh meye laifin? Ba rokanku take ba, ba shiga hurumin ku take ba, meye nata da bazamu kyaleta ba. Don Allah mu kyale Inayat ta huta, tana cikin damuwa kar mu kara mata matsala akan wanda take dashi ciki ne da ita, kuma tana bukatar nutsuwa domin rayuwarta da na abin cikinta. Amma idan bai muku ba, bismillah." Daga haka ta bar musu tsakar gidan, ni dai ina kwance a d'akina.            Cameroon.     Abun tausayi, idan kaga yadda su Zehrah suka koma, dangin Baba sun zo ta'aziya dukda ba wai zuwan na Alkhairi bane sun zo ganin abinda Rukayyah ta dawo dasu, ladar bariki. Sai dai suna zuwa zasu ga su Zehrah babu abinda suka bari nasu. Har jikin su yayi sanyi, basu gama rud'ewa ba sai ranar addu'o'in uku, zuwan su Nusaiba da Mariam. Tare da mazajen su. Jikin su yayi mugun mugun sanyi, haka suka gama zaman su. Suka bar gidan. Satin su Mariam daya suka juyo zuwa Gombe, lokacin da zasu rabu ne abin tausayi, domin kowa sai da ya zubda hawayen dan kasa janye jikin shi yayi daga d'an uwan shi, abin so touche heart, dakyar aka raba su da juna suna wani irin kuka me ban tausayi.... Suna ji suna gani suka tafi suka bar su, lokaci guda maraici ya sauko musu, dama sun girma amma kullum zaka same su a jikin juna, Kan Zehrah akan cinyar Balkisu.                Dole Baffa yake zama dasu, sun saba dashi ba iya shi ba hatta sauran jama'ar gidan sun saba sosai, Dr Ishaq yana kawo musu duk abinda suke bukata kuma zai zauna dasu ya d'an tambaye su me suke bukata, abu daya suke gaya mishi Aunty Inayat.            London. Durkushe yake gabanta, cikin damuwa da tashin hankali, ya riko hannunta, muryan shi na rawa yana ce mata. "Wallahi ban san ta ba, kawai naji sunan ya zo min ne, sannan ba zan iya tuna kome akan sunar ba. Ki yarda da Ni babu macen da ta isa tsayawa a gabana har naji wani abu akanta ba a haifeta ba, lafiyata dan ke daya aka yita, don Allah kiyi hakuri bazan kuma ba." Tab'e baki tayi tare da barin d'akin ta nufi d'akinta. Abinda ya faru kuwa wai, mafarki yayi. Tare da zabgawa Inayat kira shine zuciyarta ya dauki zafi. Akan yana niman mace, komawa gadon shi yayi cike da bakin ciki, dan shi kadai yasan yadda yake ji akan Zeemalik. Duk ranar da ya sami damar kamata sai yayi mata asalin jahilin duka, wanda jikinta zai gaya mata, irin dukar nan da zai mata. (😜𝐊𝐚𝐧𝐚 𝐫𝐮𝐰𝐚) haka ya gama masifar shi a ran shi sannan ya kwanta tare da tab'a little Malik, iskar bakin shi ya furzar sakamakon jin yadda tayi dumm, tana niman abokin haɗin ta. A yanzun haukar Zeemalik ya laffa sai dai bai da ikon kallon mace kullum yana manne kusa da ita,matukar ya dawo aiki. Bata fada da kowa. Amma shi bai isa yayi rayuwar shi cikin jin dadi ba ne.           Cameroon. "Yanzun sabida rashin hankali yarta shi ya bada ita ga mutumin da bai sani ba, toh yanzun ta ina zaa same ta?" Cikin sassayyatar murya tace. "Ai yace karta zo gidan shi sai ta samo mijinta, gashi Mama ta rasu bata sani ba, kuma bamu san wani hali take ba." Inji Zehrah, wacce take bawa Yan uwan Mamah labarin abin da ya faru, zata kuma magana, Balkisu ta riketa, kallon juna suka yi sannan girgiza mata kai. al'amarin tai shiru haka. Sunkuyar da kai suka yi, dukkan su jikin su yayi matukar sanyi, sabida ko babu kome mahaifin su ne, su taya mahaifiyar su kare kimar shi. Haka da suka yi sun kuma kara sayan zukatar dangin su baki daya, ya zama na kowa so yake ace su je su zauna dashi.         * Abuja. "Don Allah Ammin kiyi addu'a, taya zaki ce babu ruwanki, sannan ki zauna kina fada ya tafi ya barni da damuwa, ki tuna ke uwar shi ce, taya Allah ba zai jarabce shi ba,.kin manta da damuwar shi ki dauki na wasu kin daurawa kanki." "Mahnoor!" Dakatar da ita tayi sannan tace." Ki fahimci wani abu, babu yadda zai manta dake, bayan yana matukar damuwa dake, taya zai tafi abin shi don Allah kiyi nazari da kyau, Malik addu'ar mu yake nima ba fushin mu ba, domin dagula kome yake, kuma zai iya Mantawa da kowa matukar bamu bashi muhimmancin gurin sanya shi a cikin addu'o'in mu ba, Ammih kiyi nazari dakyau." Daga haka ta kashe wayar. Shiru Madam Azizah tayi tana auna abinda Mahnoor ta faɗa mata sai ta ga kusan gaskiya ce. Domin itace ta shagala da yawa, kuma gashi nan D'anta yayi nisa da ita.      Dan haka taji a ranta zata mike ta fara mishi Addu'a..       *** Bayan wata uku... Dake an bani hutun sai na haihu zan koma, na kira Khadi muna lissafin abinda za a buƙata idan haihuwar tazo cikin sauki, na mika mata katin bankina, na kuma gaya mata code din sabida halin Rayuwa, na gaya mata kome dan kar na mutu a rasa inda za akai min abin da na haifa.      "Ki duba kayan babyn kome yayi ko? " Na tambayeta ina kallon sani set din Unsex yayi min kyau pink dashi, tun kala biyu na saya, sabida tun cikin na wata shida suke ce min ana tsammanin ko biyu ko uku zan haifa, Ni dai na sayi koma meye. Na saya, nayi imani da Allah da yau Malik yasan da cikin toh ba makawa da yanzun ya hanani zaman lafiya, yana mamuke da mulki, hadi da nuna min fin karfin. Ajiyar zuciya na sauke tare da jin babu dadi, kwanciya nayi tare da kallon Khady nace mata. "Na gaji da wannan a aikin. Domin ina gab da sauke shi na huta!". Cikin ko in kula tace min! "Amma ai munyi alkawarin duk abin sa suka min, dan haka ku biya ni ko kuma na fara niman rigima." Dariya tayi sannan tace min!" Kibar ganin dan ina lallaba ki, sabida dole ayi jigila damu, ko kuma mu tashi muyi ta rikici tun kafin muzo duniyar ma!.." kuyi hakuri don Allah muna fama da rashin wutar nepa ne.. ᎠᎪႮᏞᎪᎻ...                         𝘉𝘐𝘠𝘜!!!            Persian and Oman       #Destiny of two kingdom ⚔️    𝐔𝐧𝐢𝐭𝐞𝐝 𝐀𝐫𝐚𝐛𝐢𝐚 𝐞𝐦𝐢𝐫𝐚𝐭𝐞𝐫 𝐃𝐮𝐛𝐚𝐢. 1 _WSTO_    (World Slaves Trading Organization) 02:43 am.      "Bamu da zab'i! Bamu da iko! Dole mu dakatar da Iran, zubda jinin ya isa haka, Jama'ar mu!" Ya karshe maganar a raunane yadda zai fahimtar da kai yana cutuwa daga halin da al'ummar shi take ciki.               Cikin nutsuwa mutum min da yake gefen shi ya sunkuyar da kan shi yace. "Allah ya taimaki Sultan Abrad! Ina gani ka basu ƙanwarka tayu a kawo karshen rikicin dake tsakanin masarautu biyu!" Watsar da kayan dake yake gaban shi yayi,  tare da rintsa idanun shi kan mutumin da yayi maganar cikin tsawa yace. "Murad kayi hauka ne? Ka haukace ne? Toh bari na gaya maka, wannan yarjejeniya ce idan baka sani ba, ba zan tab'a daukar kanwata  Almira Ashnah na bawa wancan Mahaukacin ba!    Kasan me suke nufi idan muna son a janye yakin dake tsakanin mu? Na basu kanwata su mai da ita baiwa, akan me zan taso daga daulata nazo nan Dubai nimar baiwa da zata dace da gidan mu. .... Ruwanka ka zab'a min kyakyawa! Ruwanka ka barni na zab'a da kaina. Amma ka tuna Daular Larabawa sunki taimaka mana, sabida kowa yasan kasar Farisa da fitina.!"    Daga haka ya saka kai zai fita, aka kwankwaso kofar dakin. Kallon Murad yayi, da sauri ya buɗe kofar dakin wani mutum sanye da kaya fuskar shi a rufe ya shigo dakin. Kallon Juna suka yi da Sultan Abrad, shi kuma ya kalli Murad ya fita da sauri, har yana tuntube.     Rufe kofar yayi sannan ya zuba mishi ido. "Har yanzun baku nime hanyar sasantawa da kasar Farisa ba ko? Toh kuwa yaki zai ci kasar ku, dubanin duniyoyin dake cikin masarautar zata lalace, kasa zata sha jini. Sannan mata zasu zama zawarawa, yara zasu zama Marayu. Bamu son  ƴa me yanci!          Baiwa muke nima! Baiwa muke so! Idan kuka bamu ƴa ba zata iya zama shiru ba, bamu bukatar sarauniya a cikin masarautan, sarki kawai ya ishe mu!" Mik'ewa mutumin yayi zai fita, Abrad ya rike hannun sa, cikin damuwa. "Ka taimake ni! Idan ban sami baiwar ba ya zanyi! Wallahi bana son azubda jini a daulata!"      murmushi mutumin yayi sannan yace. "Ina da wani Agent a nahiyar Afirka yanki yammacin su, akwai kyakkyawan mata a gurin, amma ba asalin kyakyawa muke bukata ba, domin bamu son soyayya ta tsaga tsakanin zukatar mutanen masarautan."            Wani wawan ajiyar zuciya ya sauke, sannan yace mishi. "Toh! Waye shi?"         "Yana kasar Andolus! Shaibaan. Dan kasar Saudiyya ne *_KOME DA LOKACIN SA_*          https://my.w.tt/rIRF00voOab             Chapter 20     Na MrsUsman400      Happiness is when what you think, what you say, and what you do are in harmony. "Kin wannan shi zaki saka min a cikin basket din nan, sannan duk abinda ake bukata na sayi kome babu abinda ya rage min don Allah, a zaman taren da muka yi idan nayi miki kuskure ki yafe min."matsowa gabana tayi tare da rike hannuna, tana kallon fuskana tace min, "tun daga lokacin da na ganki, ban tab'a jin ko ganin laifin ki ba dan kina Kawata ba, sai dai ke din ma'abociyar adalci ne, dan haka ki kwantar da halinki ina tare dake.". Murmushi nayi tare da saukar kwalla daga cikin Idanuna na rike hannunta. Ina faɗin "nagode sosai!" Daga nan muka cigaba da hada kayan muna gamawa na mike a hankali naje ban daki na dawo, anan naga Maman Abba, tana amai. Kauda kaina nayi a hankali na cigaba da tafiya tace min."Inayat ko zaki taimaka min ne,.tun safe amai nake!" Ban da zuciyar musulinci yaushe zan kalli wannan matar, dan haka na dawo gabanta, na fara tambayar ta. "Me kika

Chapter 9 of 22