ba." Kallonta nayi domin jikina yayi sanyi, nifa irin wannan goyon na tsane shi ace yaro babu fada, Allah sarki Bawan Allah, babu ruwan shi tunda ya rike daya, bai kuma ɗaukar wani ba, haka na gama mana tuwon na kwashe a leda, gashi yayi fari kal, sannan na shiga aikin daura miya, sai kunya ta kamani ko dan nama babu, haka na wanke kayan miya aka kai mun markade shi, ana kawowa na zuba, a tukunyar, sannan na kwashe kayan a na ba'ata na wanke, kafin na dawo dakin na samu Anoosha tana bata labarin da ya kusan sani faduwa, wato duk abinda kake a rayuwa kayi tunanin me zai je ya dawo, "Ammahmu kulin kuka, Maman Aban, a ce mana cegu. Yalan kaluwa." Wani irin takaici ne ya kamani na kaiwa bakinta duka, naji an rike hannuna, hawaye na zuba daga idanuna. "Rukayyah bana hanaki wannan surutun ba? Bari Mama ta tafi sai na zaneki." Sake min hannuna tayi cikin mamaki. "Kuma sai ki daketa a gabana?" Zama nayi a gefen su, kuka na kuma zuwa min, a hankali ta mike sannan tace min. "Naso naci abincin ki, amma na fahimci, akwai wata wutar a cikin zuciyarki, na fahimci na shigo miki ta yadda baki zata ba, Amma zan tafi kiyi nazari, ba iya wannan ba, hatta rayuwar Yarki yana cikin hatsari, zan dawo nan da sati biyu, zan tafi daku, ki saka ido a kan Yaranki dan amanarki ce su." A raunane na ke kallon ta, kafin nace mata, "babu wani wuta wanda bai mutu ba, sai dai na fansa. Don Allah ki zauna kici abincina, haka shine zai iya sani yarda da Allah da Manzonsa, tunda na girmama bakona, don Allah kici koda kadan ne." Murmushi tayi sannan tace min. "Zanci amma kiyi min alkawarin ba zaki sake dukar yaran nan ba, kinji.". Bakina na rawa nace mata, "Insha Allah bazan kuma ba." '''Nifa zan tafi hutu gaskiya 🤣😵 comments share and Vote! Ya gaggara Why not na tafi hutu nima'''
*_KOME DA LOKACIN SA_*
https://my.w.tt/qVfUlLqXTab
Chapter 26
When I do good, I feel good. When I do bad, I feel bad. That’s my religion.
Riko hannun na tayi cikin nata, tana kallon yadda nake kuka, "be a stronger person, wacce zata iya yaki babu taimakon kowa, Ina mijinki yake?" Kaina a sunkuye naji tambayarta kamar ta watsa min ruwan zafi, damke hannuna nayi, ina jin wani irin takaici na caccakar zuciyata da Ruhina, me zance mata, a hankali na bude bakina nace mata. "Ya rasu." Kura min ido tayi cikin tashin hankali, "Ya rasu?" Ta kuma mai maita min tambayar, gyada mata kai nayi, "Meye yasa bana jin kome akan abinda kika faɗa ko baki son nasan abinda ya faru dake ne? Cikin had'iye kukan nace mata, "ya rasu, sai dai nasan Allah yana tare dani." Murmushi tayi sannan tace min." Basu min kama da marayu ba, bazan takura ki ba, amma gaskiya bazan iya barinki anan da yawan nan ba, dan basu da tsaro." Mik'ewa nayi na karasa miyar da nake, sannan ya zuba mata bayan na ajiye mata warmer din abincin mu, murmushi tayi sannan na ajiye mata plet da spoon, sai miyar da na zuba a bowl, na bata guri. Yar Naira dari biyu da ya rage min na tura ka sayo min maltina da pure water. Ana kawo min, na koma cikin dakin dashi, na ajiye mata. Shi jininka jini ne, domin na samu a hankali take bawa yaran tana kuma ci, dibawa driven da ya kawota nayi tare da motar yan sandan da suka musu rakiya, bata ce min kome ba, na fita na kai musu. Ina shigowa ta wurga min tambayar da yasani zare ido. "Da kika kwashe abincin ina baki yake?" Murmushi nayi kawai na duba wata yar bokitin na dibo garin kwaki, na jika babu siga na fara sha. "Me yasa kike kuntatta kanki?" "Babu kome! Kawai nan da abinda zan bawa bakina ne! Da ina da abinda yafi haka zan basu." Tana bawa yaran sunata kiriniya nace mata, "ko zaki rabu dasu ne! Kici kawai dan su basu son cin abinci." "Karki damu, nima haka nayi goyan yarana sai dai zaƙi. Kuma naga suma haka," shiru nayi, sai da suka ci sannan ta cinye nasu, gashi na kwashe abincin na kai waje. Tana idarwa na mike na zuba mata ruwa abuta, na kai waje. "Duk matar da ta same ki a matsayin surukarta zata rayu cikin godiyar Ubangiji. Idan ba zaki damu ba.",. Cikin sauri nace mata. "don Allah karki tambaye ni, abinda ba zan iya miki ba." Gyada kai tayi sannan muka koma daki ta dauki babban mayafita. Kallon yadda, yarana su shirin tadda rikici. "Jini kawai yake nuna kanshi. Karki damu." Da haka ta saka kai zata fitae, yaran suka riketa suna ihu. "In biki." Inji Anoosh. Lumshe idanuna nayi tare da kauda kaina akan su, jini ba wasa ba, haka tayi ta rarrashin su, sannan na dauki jakarta muka fita sai kuka suke fuskar su tayi jajjur, ita kanta daurewa take amma bata ki tayi ta tsella ihu ba. Sabida wani irin kaunar yaran da take, duk sai naji na takura, kamar Barauniyar da tayi mugun sata. Murmushi tayi sannan ta cigaba da cewa, " a iya wannan kadai ya ishe ni, ko gaida min iyayen ki." Sannan ta saka kai zata fita, wayyo Allah zoku ga yadda ake mugun gado, hatta tafiyar da take sak da na MALIK, Uwa uba haka yaran suke tafiyar kamar ka musu, muna fita yaran suna ihu, har gurin motar ta, tana shiga ta juyar da kai dan jin muryan Anoosh take kamar Malik. Dan haka tana shiga motar ta kifa fuskarta a tafin hannun ta, wani irin yanayi take ji me matuƙar damuwa, taya zata iya nisa da yaran." Muna tsaye suka ja motar, ihu suke yi har da tsalle. A hankali naja hannun su muka shiga cikin gidan. Na same su kamar zabi, suna gani na suka dare, taɓe baki nayi dan nasan gulma suke yi ni kuma ba ni da lokacin su. Shiga na gyara inda suka ci abinci na fitar da kayan. Ina wankewa aka yi sallama wai ana kirana, cikin mamaki na kalli Sabir, da sauri nace mishi. "Waye " "wasu ne a waje." Hijab naja sannan nafito." Kayan abinci na gani cikin mamaki na zuba musu ido, "gashi nan inji Madam wai a kawo miki." Shiru nayi tare da cewa. "don Allah!" "Kinga muna sauri ne a iya zamu ajiye miki?" A hankali na juya suka biyo ni da abincin, daga bakin kofa suka ajiye min sannan daya ya mika min wata takarda. "Kuce mata nagode." Suka fita da sauri. A sannu na kwashe abincin na kai daki. Ina ganin magulmata, kowacce ta turo dogon wuyar. A hankali na bude takardan naga yar rubutunta. So perfect, _Am sorry daughter nayi miki karambani, ki tambayi mace a gaye ta baki school bag dinta. Allah yayi miki Albarka, ya baki ladan hakuri sannan ina kuma niman alfarma a bani yaran next zuwa na naje dasu gida_ had'iye yawu nayi na kalli Anoosha, tare da kallon jakarta, "mi komin jakarki!" Tashi tayi tana kuka, ta miko min shi., Hannuna yana rawa na buɗe shi, zazzage shi nayi a hankali kudi ya fado, shiru nayi ina kallon kudin da kayan abincin da aka tulamin wanda ko zanyi wata hudu bazan cinye shi ba. A hankali na share kwalla dake zuba a idanuna, shata biyu da suka wuce, na kwana da yunwa saboda kayan abincin mu sun kare, an wayi gari Yaren sunyi rashin lafiya a tare babu kudin magani, kayan da nake sayarwa mutane sun ci bashi sun kuma hanani, ga albashin mu an hanamu na wata uku. Yau sai gashi Allah ya kawo min, ita. Ko kudin da nayi mana cefene. Bashi aka biyani, na dauka nayi amfani da shi. Sai ga dubu hamsin, kuka ne ya kamani lokaci guda na tuna da hakkin Iyayena yake bibiyar rayuwata. Dan haka na kudiri aniyar karshen watan nan zan je gida. Duk abinda zai faru sai dai ya faru. Haka na gyara zaman kayan abincin sannan na karasa aikina, kafin na kuma daura mana shinkafa da wake, naje na sayo, wanke. Sannan na daka mana yaji, sai da na basu suka ci, sannan na dauki nawa naci. Tare da bude data. Duk halin da nake ciki bana gayawa Khady sabida bana son ta shiga damuwa, dan haka daukar hoton kayan nayi na tura mata, da sauri ta buɗe sakon, nace mata. _Ga kayan da Maman ku ta kawo min! Sannan tana rokon na bata aron jikokinta na kwana biyu_ *🤨 Ayi haka? Nifa bana son a rabaki da Flowers! Kinsan reason dina kuwa?* _🙏🏼🤔 Ina jin ki uwar Flowers!_ *Dakyau matar MALIK! Kin san me? Idan ta dawo, karki yarda ki sake jiki da ita! Idan kika ki sake jiki da ita zata san cewa Yaran suna da daraja! Sannan ba zata tab'a tunanin sabida abin hannunta kika sake mata yaran ba, kiyi hakuri amma dole sai kin ja mata rai karki yarda zuwa na biyu ki sake mata su, ki nuna mata you Are scared da ita haka zai sanya ta fahimci, kudi zai iya sanya kome amma banda soyayyar da kuma y'ay'an ki, ki san abinda zaki yi ki nuna mata ke kin iya talaucin ki.* _Toh amma kuma! Ina ganin girman ta fa!😓_ *Toh fa ranki shi dad'e Gimbiya! Sai ki cigaba ba!* _A'a'h ba haka nake nufi ba, don Allah, ya zanyi😭🤧_ *😏😒😎! Toh na yafe miki tunda kin nime yafiya! Dole idan kika gama ja mata rai zata ce sai dai ku tafi tare, sannan ke zaki nuna mata aikinki nada muhimmancin a rayuwarki da Yaranki, idan kika bita ya zaki yi da aikinki, hmm! Mamar Malik tana da manyan asibitoci biyu a garin Abuja! Akwai daya a Gombe, sannan akwai daya a garin Azare, karki manta zata nemi ki mata aiki a nata asibitin! Omo dan Ubanki karewa ta kama miki wata ƙatuwar Apartment! Sannan tasan irin wahalar da tasha kika biyo ta!😏😒 Toh cikin ruwan sanyi zaki ci Uban Malik a saukakken hanya, kuma zata tsaya miki! Dan wallahi duk ranar da ya ganki na Allah sai yayi sumar hucin gadi. Kuma idan kuka hadu dole zaku raba hali* _kuma kina ganin haka babu wani damuwa?_ *ke nifa kusan waliyiyya ce Insha Allah sai kin kirani kin gaya min abun da ya faru!* Mun tattauna sosai, kuma na gamsu da shawarar Khady, abokiyar arziki kike ji..
Mai Nassara Clinic
Kallon files tayi sannan tace musu, "waye Dr Ishaq Ahjo" a sanyayye ya fito. Murmushi tayi sannan tace. "Naga aiyukanka, zaka koma Abuja kayi mana aiki." Kamar wanda ta watsa mishi ruwan zafi haka yaji shi. Lokaci guda zuciyar shi ta shiga harbawa.*INAYAT* kalmar da yazo bakin shi kenan, ta Inayat. Shiru yayi ya kasa cewa kome, tace mishi. "Muna da asibiti biyu a garin Abuja, kuma nasan zaka ji dadin aiki a can, idan kuma nan yafi maka zan iya barin ka anan tunda kamar ranka yafi son nan din" murmushi yayi sannan yace mata, "a'ah duk inda na samu ina so Allah ya saka mishi albarka." Sannan ta mike tare da barin Office din, hadi da wasu manyan likitocin. Kowa murna yaƙe taya shi ban shi, dan sam bai so barin gombe sabida kanen shi ba. Amma babu yadda ya iya. Daga gurin aikin gidan Nusaiba ya wuce inda ya kira mijinta ya gaya mishi gashi nan yazo. Tunda suka shiga suka tattauna, tare da Adduar Allah ya bayyana musu Inayat, wacce yake son lallai ya maida ta Cameroon kafin kome ya zama normal. Amma babu ita babu dalilinta.
***
London
"Mr Malik! Dole zaka kasance da ita, sabida lalurar ta yana bukatar kulawa, a daina barin ta ita daya. Sabida yin haka hatsari ne, dan zata iya illata rayuwarta. Sannan kaima kaga misali akan ka, a kiyayye abinda zai iya zama hatsari ga rayuwar ta." Shiru Malik yayi domin yanzun kan tausayin Zeeh yake kamar yayya., Bayan ya fito daga ofishin likitan ya nufi dakin da take, tana zaune sai share kwalla take, yana shiga ya rungume ta, aikuwa ta sake fashe mishi da kuka, tare da rike hannun shi, "don Allah karka rabu da ni, wallahi zan iya mutuwa." "Ina tare dake bazan tab'a barinki ba, ki bar kukan." Shiru tayi tare da jan zuciya tace."Ya MALIK! Promise me bazaka kuma niman haihuwa ba!" "Dem!" Ya faɗa a zuciyar shi, matse ta yayi a hankali tare da zama a kujeran dake kallonta. " Zan miki alqawarin ba zan tab'a niman Haihuwa ba! But da sharadi ɗaya!". D'ago manyan idanunta tayi, ta kafe shi da shi, hawaye na zuba mata, riko hannunta yayi tare da sakawa a gefen fuskar shi yace mata. "Karki kuma cutar da wata mace sabida ni!" Bude idanu tayi na wasu lokuta, kafin tayi kasa da kanta, ta faɗa dogon tunani, taya zata bar MALIK yayi mu'amala da wasu matan? Zata sake yayi rayuwa da wasu mata, tana ji tana gani zasu yi hunging din shi, kuma suyi dariya. How? Fashewa tayi da kuka tare da rike hannun shi gam, jikin ta yana kyarma, ta rasa yadda zata ce mishi ta amince, mik'ewa yayi tare da ɗiban ruwa ya bata tasha tare da sake ajiyar zuciya, sannan ta rike bakinta ya kuma mai maita mata abinda ya fada na farko, bata da wani zabi kawai tana kuka tace mishi. "Na amince!" Anan kukanta ya karu har kirjinta na sama da kasa, zunzurutun kisha, by now zata fi son ya cigaba da gasata da ace ya mata kishiya, ko ya kula wata mace, kai neva 4reve, ba zata tab'a barin Malik ɗinta yayi sharing bed da Sexually language da wata ina gwara taga mutuwarta da taga Malik Aliyu Mai Nassara, ya shige dakin wata mace, tayi alqawarin ko da zata yi yawo tsirara sai ta kashe duk matar da ya tunkara da niman aure, koda kuwa Kanwar Uwar shi ce sai ta kasheta a kasan ranta tace. *mark my Word MALIK*
_YANZUN AKA FARA WASAN toh me kuke tunani Zeemalik ta shirya fa ni kuma zan tayata yaki! World a war na 3😎_
*_KOME DA LOKACIN SA_*
https://my.w.tt/k7BxNgYhUab
Chapter 27
If you want your children to be intelligent, read them fairy tales. If you want them to be more intelligent, read them more fairy tales.
🤔 ```Zaku karanta labarin ne ko kuma Marubuciyar kuke nima? Idan kuka dame ni da na bayyana kaina! Toh zan ajiye rubutun 🙏🏼 Don Allah ku karanta labarin Na zabi haka ne kawai sabida ra'ayin kaina, ba suna nake nima ba! Rubutu muradina ne! Ba population ba, Please karki dame ni da sai na bayyana kaina! Idan nayi haka toh wallahi zan canza ra'ayina akan labarin! Dan zan bayyana kaina amma ba zai muku dad'i ba! Please karki dame ni da wacece ni🙏🏼🤔```
Sake damke hannun shi tayi, wani irin mugun kishi yana dabaibayin a cikin zuciyarta, idan ta kama tayi Sacrifice da rayuwarta domin Malik ya zama nata zata yi, a shirye take ta aikata kome dan ya zama nata, dan haka dole tayi iyaka kokarinta gurin muna mishi ta amince, wasu irin fake teas ne suka zuba da mugun gudu, ta bude bakin ta dakyar tace mishi. "Na amince! Insha ALLAH" murmushi yayi domin da yana tsammanin zata botsare mishi ne, sai yaga ba haka ba. A hankali ta rungume shi. Cikin tsananin kishinsa tana hango yadda wata mace ta lafe a jikin shi, rintsa idanun yayi sannan ta kalle shi, tana faɗin. "Bani da kowa sama da kai." "I know, shi yasa nake son ki kama kanki akan damuwa da mutane,.kawai kiyi hakuri da kauda kan ki, akan duk wani abinda zai faru." "But MALIK!" "Shiii! Silent. Kiyi shiru bana son magana." Sake mai da kanta tayi kirjin shi, tana sauke kwalla, goge kwallar yayi da hannun shi, sannan ya rike hannunta suka bar dakin, yadda ya rungume kafad'ar ta, yasanta relief! Dan ko babu kome ya samu kan shi, na wani lokaci. Daga nan gida suka wuce, koda suka isa, d'akinta ta shiga shima ya shiga nashi cikin sauri ya dauro alola, yazo ya gabatar da sallar la'asar. Ajiyar zuciya ya sauke dan da jin shi yake a uzurce, yana idarwa ya zauna ya fara aiki da laptop din shi, yana shigar da wasu abubuwan, har ta shigo d'akin, kallon juna suka yi, tare da sakewa juna d'an murmushi, tana haurawa gadon ta zauna, kallon yadda gashin kirjin shi ya kwanta luf luf tayi. Tana kuma hango iyakar yadda wata mace zata gigice, idan gargasar jikin shi ya hadu da boons din ta, "Neva! Ba zai taɓa faruwa ba!" Kallon ta yayi tare da zare Medical glass din shi, yana kallon yadda take zare ido, "Lafiya?" Turo baki tayi. Sannan ta kai hannun ta, boxes ɗin shi. Janye hannun ta yayi cikin nutsuwa, tare ɗage mata gira daya. "Ina hutu ne, a barni na gama gabatar da wani project don Allah!" Murmushi tayi, sannan kuma shige jikin shi bayan ta sauke laptop din akan cinyar shi, tana kallon shi cikin wani irin yanayi, janye rigar jikinta tayi wani gown ya bayyana, babu abinda bai fito a jikinta ba, murmushin mugunta tayi mishi sannan ta kuma matsowa tare da zare zaren da ya rike boons ɗinta, suka kuwa sake kansu, murmusawa yayi. Sannan ya cigaba da aikin shi, sabida a duniya ba zai kuma ganin boons masu matukar burgewa da daukar hankali irin na Inayat ba, suna tsaye kam. Gashi da laushi kamar auduga, had'iye yawun yayi, cike da takaici zata daddo mishi batun Inayat. Sosai take jan hankalin shi, yana kin biye mata karshe sai da ta kai, da ta lallaba shi kamar me, shi bawai wani abu bane, kawai baya sha'awan alaƙar su tayi nisa a yanzun ne, ba dan kome ba, sai dan yadda yake matukar bukatar haihuwa, kuma da Inayat. Duk da bata da kunya idan ta haihu dashi zai sallame ta ya bawa Ammin shi yarinyar ko Yaron, dan yadda yaga mahaifinta nan yayi imani bawani tarbiyyar arziki zai basu ba, balle ita da take idanunta a soye kamar, penut. Sai kuma ya sake murmushi, abu daya da ya cuce shi a rayuwar shi. Yadda har suka rabu bai sumbaci bakin ranshin kunyar nan ba, yayi imani da Allah, ya sumbaci Bakin da duk wani rashin kunyarta ya kare, yarinyar tayi kome Matsalar ta rashin kunyar da take dawainiyya da ita, ko ina nata ba laifi domin ta isa a kirata da kome Compelet. Shafa shi Zeemalik tayi ranshi ya b'aci kamar wanda aka dodana mishi wuta take mood din shi ya sauya haka yayi matuƙar razanata sai ta kame kanta ta koma gefe, tana share kwalla, duk na yaudara ne, bai sani ba. Gabaki daya sai yaga rashin dacewar abin da yayi mata, karshe ya ajiye laptop din tare da mika mata hannu, da sauri ta zo gurin shi tare da fadawa kirjin shi, kara rungumo ta yayi, a hankali kome yake tafiya. Duk dauriyar da take kokarin mishi sai da ta kasa domin tayi kuka ba kadan ba, kafin ya rabu da ita,yana me sauke ajiyar zuciya, sosai yake jin wani irin yanayi domin bawai ya gamsu bane, kawai yadda take nuna ta gaji yasa shi, kyaleta. Bayan sati biyu. Sun shirya sosai har suna fita cin abinci, bai hana idan Malik yaga yara a hannun iyayen su yayi musu hidima, abun yana masifar mata ciwo, dan haka ta shiga bin dukkan hanyar da zata samu abinda zai katange Malik, da dawainiyya akan yara, cikin wannan yanayin wata rana, sun je beach. Suka haɗu da wasu yara masu kyau duk mata, nan Malik yayi ta kashe musu kudi ita kuwa ta dawo, gefe tana kallon su bakin ciki yana kara turnuketa. "A duniyar nan zaka iya chanza kome ban da ƙaddarar, domin kuwa ba zaki tab'a canza ƙaddarar ki ba, kuskuren da kika aikata shi yake bibiyar shi, karki sake ki barshi ya tsallake kasar nan, domin daga ke har shi zaku ga samu zaku ga rashi, kuma kece zaki janyo haka " daga haka ya juya abin shi da jajjayen kayan shi, da sauri ta mike tabi bayan shi, tana mishi magana. Kallonta yayi sannan ya ce mata. "Bani tafin hannunki!" Mika mishi tayi ya dade yana kallon hannun kafin ya bude baki yace mata. "Kin kashe yarinyar da bata san kome ba! Sai soyayya. Lallai karki sake mijinki ya bar kasar nan, domin kuwa burinta zai cika. Kuma cikar shine ƙarshen ki, karki yarda ya bar nan ƙasar sabida kafin kashi yana jikinki, karki sake ya san inda kika ajiye kwalbar tare da zoben hannunki. Karki sake karki yarda ki rabu dashi."
Shiru tayi jikinta yana kara mutuwa, anya zata iya barin Malik ya numfasa kuwa, tsoro take ji, kar wata rana kome ya kwab'e mata, mika mata wata sarka yayi, tare da cewa ta sanya a wuyarta, jikinta na rawa ta amsa, sannan yace mata. Karki rabu da sarkan. Muna nan zamu tayaki." Gyada kai tayi sannan ta bar gurin shi dan bai nemi kome daga gareta ba, ya dai bata abinda zata iya rayuwa da Malik ne. Sai dai kash! Malik kowa ya tashi tsaye akan shi musamman mahaifiyar shi.
***
Kwanaki na tafiya mu kuma burinmu yana kara yawaita, wasa wasa yara na tun suna kiran sunan Kaka, har suka daina, gashi bata zo ba. Asalima kamar tayi battar dabo ne a raina nace. Tabbas! Da ba bata yarana ta gudu dasu fa? Allah Nagode maka da baka bani ikon bada su ba, ai da na mutu da kwanaki na, dan nayi imani sata rana Malik zai nime ni. Dan haka ya cigaba da sana'a na ina kuma kokarin kulawa da Yarana na saka ido akan su, dan bana yarda da nabarsu da kowa, wani munmmunan al'amari da ya same ni, kawai ina kwance aka kira ni a gurin aiki, dan haka da wuri na tafi, ina zuwa na samu munyi baki. Nan suka shiga mana tambayoyi, tare da wasu abokan aikina, ba tare da wani abu ba, kawai akace an dakatar damu, sabida muna cikin ma'aikatan bogi. Kamar zan fadi dan tashin hankali, karshe suka tura mu, ministry. Wai muyi comfirming kanmu, nayi kuka a ranar. Sabida wata nawa basu biya mu hakkin mu ba, yanzun kuma dakatarwa kuma babu ranar mai damu. Ina barin asibitin na nufi gida, dakyar na kira Khady ina kuka na gaya mata, ita da kanta tace min, "baki musu kome ba?" Shiru nayi kafin na tuna ashe akwai wani likita da aka turo shine, asibitin mu aiki. Abun haushi yadda kuka san taure haka ya takura mana, kuma babu ruwan shi da budurwa ko matar aure, dan haka kusan mu hudu da yasa aka dakatar damu. Nan na gaya mata, hmm ! Tace min sannan tace min. "Karki damu, amma Allah zai saka muku, sannan naji ai dayawa sun fada cewa, bawai shi yake bin matan ba, sanya shi ake yana nimo yan matan, kiyi hakuri kome da lokacin sa, kuma Maman Malik bata zo bako." "Bata zo ba, idan tazo kiyi hakuri ki bita domin san zata bukaci hakan, shi kuma d'an iska karki damu karshen cin abincin shi yazo!" Haka muka tattauna, sannan muka yi sallama, ina zaune na saka yaran a gaba. Ina girmama laifin da nayi, domin na manta da iyayena. Na bar kowa nawa. Kamar wacce aka ya kusa na tashi na shiga hada kayan mu, zan tafi gombe. Yadda muka shirya tsaf, ba zaka ce muna cikin damuwa ba. Muka bar garin kashere. Koda muka isa unguwar mu, kai tsaye na nufi gidan mu. Duk da akwai nikab a fuska na, sabida bana son damuwar mutane, ya sani sakawa, ina shiga gidan mu na d'aga tare da sallama. Juyawa suka yi ganin yaran dake biye dani. "Ayeeriri nanaye! Lallai ribar bariki ya tabbata, Baban Inayatu zoka ga Inayatu har da ribar bariki, lallai lale maraba, irin wannan tagomashin arzikin haka?" Sunkuyar da kaina
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 13 Chapter of 22