mi..." A fusace na juya tare da watsa Mishi harara, "taimako! Taimaka min zaka yi? Sabida ga nakasashiya, wacce bata da amfani, Iyayen ta sun gudu daga gareta, bayan an wargaza min farin cikina, toh dama ai bani da shi, Ishaq bana bukatar taimakon abokin halitta, kaje kaji da damuwar ka." Daga haka na dauki kayana na fara ja a hankali. Biyo ni yayi tare da cewa."Inayat!" D'aga mishi hannu nayi sannan nace mishi."Ni matar aure ce! Nima kuma ban yiwa igiyar dake kaina adalci ba, na haɗaka da Allah ka bar bina, sabida martaban aurena, karka ja min tsinuwar Ubangiji bayan wanda nasha a gurin Mutane nagode sosai da kulawar da kayi min." Daga haka nayi juyawa ta da sauri na bar asibitin, dukda hakin da nake, saboda har zuwa yanzun gurin bai gama warkewa sumul ba, kafin na isa bakin hanya nayi hutawa ya kai bakwa...
Sorry 💖
*_KOME DA LOKACIN SA_*
https://my.w.tt/Uku9bYyQBab
Chapter 11
Na MrsUsman400
Da gaske ne bawa baya tserewa ƙaddarar shi, shi yasa tawa ta riske ni a dai - dai lokacin da ya dace dani. Zama nayi akan dan dakalin bakin hanya na shiga tsare abin hawa, dakyar na sami keke napep din da ya dauke ni, na gaya mishi ya kaini banki, naje na cire kuɗi kusan dubu talatin, sannan na duba wayata naga sun kaini. Kashare suka mai dani, kwalla ne ya cika min ido. "Allah gani gare ka" na fada a hankali, tasha nace ya kaini daga nan na sami motar kashere. na biya kudin motar sannan na zauna can karshen kujeran. Kaina a kife, hawaye na zuba min Malik ya gama dani ya gama da kome nawa, amma ba komai Allah yana sane da alamarina. Ina zaune har kusan la'asar kafin motar ta cika, tunda muka tashi. Nake addu'o'in har muka isa, daga nan nufi asibitin da aka tura ni, ina zuwa na je har office din da nake tsammanin nan ne zan yi aiki. Na musu bayani.
"Yanzun dare yayi kije kawai gobe Insha Allah sai ki dawo kiyi sign!" Cikin tsananin gajiya na kalle shi sannan nace mishi.
"Ni bakuwa ce! Kuma ban san kowa ba.kuma ban san inda zanje ba, ko zan zauna anan zuwa gobe." Kallona suka yi sannan kuma, suka ce min. "A kwai wani gida a nan gaba da Asibitin kad'an, ga key din zaki iya kwana a gurin kafin zuwa gobe ki samu inda zaki zauna." Amsar key din nayi jikina yana rawa, nayi musu godiya. Sannan na fito. Yunwa nake ji, amma babu yadda na iya haka na nufi gidan dakyar. Ina shiga naga tsarin gidan Quarts ne, dakuna kusan uku ne, dan haka na bude na farko na shiga. Ajiyar zuciya na sauke, sannan na duba d'akin naga babu ruwa. Sake fita nayi na nimo shayi da bread sai pure water. Rufe kofar nayi na shiga ban dakin nayi alola na zo na gabatar da sallar da ake bina. Bayan na idar nasha shayi sannan na maganina. Na kwanta a gurin. Zuciyata babu dad'i. Lokacin da na ganin a dakin babu kowa, sai anan kuka ya kwace min, kuka nake sosai kamar raina zai fita. Ina yi ina jin ciwon abin a raina. Sai da nayi kukan har idanuna na zafi. Kafin na samu barci ya dauke ni. Kiran sallah asuba ya taddani, na zubawa dakin ido. A hankali na mike na shiga ban daki. Nayi Tsarki dukda bana son saka ruwan sanyi a jikina amma haka nayi na fito. Ina idarwa nayi kwaskwarima tare da alola na fito. Na gama abinda zan yi sannan na fito na rufe kofar d'akin. Sannan na nufi asibitin lokacin ba suma fito ba, haka na zauna har karfe goma, kafin suka fito tare muka shiga muka yi abinda zan yi sannan na fito. Na gaya musu zan nemi masaukin, abun takaici ina shiga dakin na samu an kwashe min kayana, tass babu ko daya sai atm card dina shima dan an san bazai amfane wanda ya dauka bane, zama nayi a hankali na sake wata irin kuka. Har jikina yana rawa, sau da nayi me isata, sannan na mike na tattara sauran, Allah yaso ni basu tab'a min takarduna ba, barin gidan nayi. Wayata da na fita da ita, Nagodewa Allah da ban barta ba. Dakyar na samu gidan haya, sannan naje bakin kasuwa na ciro kudin. Da na duba balance naga saura dubu goma. Wani irin hawaye ne ya zubo min, haka na shiga kasuwa na sayi abubuwan bukata, tare da dogayen riguna guda uku na kanti. Sannan na fito bayan na hada kayan abinci da yar karamar abin gawayi dan kudin bai kai na sayi gas ba. Haka na samu aka kawo min gidan, sannan na biya kudin hayan. Na shiga na share dakin tass, sannan na dauki leda na shimfid'a, ina gamawa na jefa yar karamar katifar da nasaya irinta yan makarantan kwana. Sannan na gyara dakin tsaf, wasu sayayyar na barshi sai na fara dauka albashi na, sake dakin da aka bani hanyar lungu ne suka ce na saka buhun gawayina a gurin, sannan na gyara ko ina, kafin na dauki bokitina na ciko ruwa na zuba a randan da nasaya, na gyara d'akina tsaf, sannan na saka yar karamar tukunya na dafa farar shinkafa, sai manja da na soya babu yaji sai na samu lokaci na daka dan na sayo shi. Haka naci a hankali, ina tuna yan uwana, hawaye ne ya shiga zubo min shi kenan mun rabu da juna kenan har abada.
BAYA BATA ƘADAN..
Bayan barin Inayat Asibitin sai ga Maman ta, tazo tana nimanta, dukda haushin ta da Dr Ishaq yake ji, haka bai hana shi gaya mata Inayat ta bar garin, zaman dirsham tayi ta fashe da kuka, kasa jurewa yayi ya shiga bata hakuri dakyar ta mike zata bar Asibitin yace mata.
"Akwai sakonki a hannuna, na gidan da Inayat ta gina, saura wuta ya rage za aja muku. Shima na bada kudin, amma ina ga duk lokacin da kika bukaci sanin haka zan baki, sai dai matukar kina tare da Baba bazan baki ba, kiyi hakuri." Daga haka yayi wucewar shi. Ya barta tsaye abin shi. Tayi kuka kamar ranta zai fita, yau tana girban abinda ta aikata, na tsawon shekaru talatin baya, yau itace take ganin sakamakon bin abinda ranta yake so. Bata tab'a sanin cewa biyo Amadu daga can garin shi zai zame mata masifa ba sai yau da tana ji tana gani yayi mata gorin da farar kafa, dama Baffa yace mata.
_Boddi! Karki biyewa Madu! Domin zai kai ki ya baro ki. Rumada basu da alkawarin, karki yi abin da zai dame ki._
Kuka ne ya kuma kwace mata, ta auri mutumin da bai san darajan ta ba, bai kuma san na Ƴaƴan shi ba, balle kuma na kan shi. "Innalillahi wa'inna ilaihi rajioun Ubangiji na tuba" ta fada tare da sake kuka, tana barin asibitin.
---
Bayan wata biyu..
London.
Zeemalik, duniya sabuwa kasuwancin mijinta take d'an dubawa, can ta mike tare da leka d'akin shi, domin ta gama duba laptop din shi, bata ga abin da take zargi ba. Wato ko yana mu'amala da mata, yau kusan kwana uku kenan baya jin dad'i, kusan ma zata iya cewa tun dawowar su Uk bai da lafiya ba wai ciwo yake ba, auren da Ammih take nima mishi ne yake tsoro kar Zeemalik taji ta kuma haukace mishi. Shiga dakin tayi ta same shi yana zaune. Haurawa gadon tayi ta kwanta a jikin shi tare da d'ago kai ta kalle shi. "YA Malik! Meke damunka?" Murmushi yayi sannan ya kauda kan shi yace mata babu kome. "Ko kana boye min wani abu ne?" Zuba mata ido yayi sannan ya rike hannu ta yace. "Zeeh ki fahimci ne, Zeeh bani da yadda zanyi da Ammih, amma ta nima min auren kanwar...". Kamar wacce naka cillata da wani abu tayi wani tsalle jikinta na rawa. Kamar wacce aka jona mata lantarki."Aure fa!? Aure zaka yi? Lallai zan kashe koma wacece! Wallahi sai na kashe ta, sai na kuma kashe ka!" Ta fita da mugun gudu, tsautsayin yaja mata. Tana fita kamar wacce aka tadeta ta zube akan gwiwar ta, ihu ta saka ya fito na same kafar ya juya mata, dole ya kira motar asibiti. Tana ihu tana cewa."wallahi sai na kashe ka na kuma kashe yarinyar, ka ajiye magana ta, idan baka janye auren ba." Kamar wani dolo ya gyada mata kai, ana kaita asibitin ya kira Ammih, kamar zai yi kuka ya gaya mata." Ammih don Allah ki janye maganar auren nan, wallahi Zeeh tace sai ta kashe duk wacce aka aura min!" "Kace a fasa auren! Toh shi kenan! Kaje na barwa Zainaf kai, har duniya ta tashi, kayi mata biyayyan da kake min!" Katse kiran tayi ba ma shi ba, kamar sha-sha-sha haka yake bin wayar baki sake, sannan ya zura a cikin aljuhun rigar shi. Yabi motar su Zeemalik asibiti.
---
Buga kofar dakina aka yi na tashi dakyar, kusan rarrafe ma nake nazo na bude kofar, tare da zama akan gwiwarta, sanye nake da wata jan rigar kanti. kaina babu dan kwali, kallona sister Khady tayi cikin mamaki tace min. "Inayat! Dama jikin yayi zafi ne haka." Kwallar da nake dannewa ne suka zubo min nace mata. Yunwa nake ji! Bani da kome domin kayan abinci na ya kare. Mura ya rike min kirjina da wuya na, sister Khady ban san meke damuna ba!" Na faɗa ina hakki. Tsaki tayi sannan tace min. "Kece kika so kashe kanki da abin cikinki, dan wallahi ina kyautata zaton ciki gare ki, dubi yadda kika kuma kara haske, sai kace ba malamar jinya ba, haba Inayat, me ya sa ba zaki zo gidana ki amshi kayan abinci ba kafin wata ya kare ki samu albashi, kenan babu zumunci a tsakanin mu, sai na aiki?"
Fita tayi zuwa asibiti dake gidan mu na bayan asibitin ne,dan haka kana fita daga gidan asibiti zaka samu ta gaban gidan, idan kuma ka fito daga asibiti sai ka bi ta bayan lungun sannan ka iso gidan mu, dan haka asibiti ta koma ta kwaso min kayan aiki, kafin ta wuce gidanta ta dibo min abinci tazo dashi, sai da ta sanin drip, sannan ta zauna ta min girki dan tazo da wake da irish. Ta girka min dake ta sa ruwan yana tafiya a hankali yasa take girkin a nutse. Ina barci har ta cire ruwan bayan ya kare..ta kuma saka min wani, sannan ta zuba min alluran cin abinci, lokacin da ruwan ya shiga jikina. Ina barci wata irin yunwa ya tashe ni a guje na bude idanuna. Kallonta nayi nace mata. "Sister Khady yunwa nake ji!" Zuba min abincin tayi ta dauki brush da maclean. Ta bani sannan ta samin ruwa a buta da wata yar karamar bokiti na wanke bakina. Sannan ta zuba min abincin, ina ci ina zuba kwalla Sosai domin ina son abincin amma bakina babu dad'i dakyar na ci spoon uku nace mata. "Khady don Allah ina niman Alfarmar ki!" Zuba min ido tayi, duk da nasan ta jima tana bina na bata labarin abinda yake damuna nake yawan kuka da kunci. Dakyar tace min. "Ina jinki!" Domin jikinta ya mutu! Baki na yana rawa nace mata! "Kawai ina son na zubda shine!" Kallon al'ajabi take min sannan tace min" me fa?" Had'iye kukan nayi ina rike bakina nace mata. "Abun nan mana!" Don wallahi kunyar kiran cikin nake, bana son wani abu ya Hadani da Malik, kuma tun watan da ya gabata na fara wannan yunkurin zubda shi, amma wani ikon Allah. Sai yayi bori kamar zai fita jini ya d'an zuba kad'an zuwa gobe kuma ya dauke, idan naje scanner sai su ce min cikin nan, dan abin ya faru ne daga lokacin da na cika sati Uku a garin jimlar wata daya da hada shimfid'a da Malik kenan, na fara ganin sauyi. Na mura da yawan ciwon kai, idan dare yayi zan kwana da zafin jiki, idan kuma gari ya waye dakyar zan tafi aiki sabida zazzaɓin da kasala. Ban kawo ciki ne a jikina ba, sabida period dina baya zuwa sai na shanye wata tass da kwana goma yake zuwa min, shi yasa ban kawo haka ba, Sister Khady ce ta fara zolayata dake sun matsa min da tambaya ina da aure ko babu, nace musu ina dashi, mijin ne ya tafi karatu, kawai na fada musu haka ne dan su barni. Tun da taga ina yawan zubda yawu, nan ta shiga min tsiya. "Kai Inayat wato dan oga ya tafi karatu shine kike fushi toh gashi ya bar miki abokin hira," murmushi nake mata kawai sabida ban kawo cikin ne sani ba, sai da na shanye wata cif har da karin na shiga na biyu ne, afujajjan na nufi shashin maternity ana min test suka tabbatar min da ciki ne, karshe suka bini da Zungurerren takardan scanner. Katse min tunani na tayi sanan tace min. "Dake daga duniyar mahaukata nake! Da zan zubda cikin bayan uban shi yana nan ki gaya mishi." Kuka ne ya kwace min nace mata."bai san da cikin ba, don Allah ki taimaka min a zubda cikin wallahi ya cutar dani da yawa! Idan na haifa mishi cikin jikina haka wata rana zai dauke ya kuma barni da ciwon zuciya, sabida shi na rasa kome nawa." "Dama baki da aure ne?" Ta tambaye ni! Kuka ne ya kuma kwace min nace mata. "Ni matar Aure ce kamar ke! Sai dai ni, a wulakance aka aurar dani" "kamar Ya?" Ta tambaye ni. Lumshe idanuna nayi sanan nace mata. "Kowani matsala da kika gani yana da mafarin shi! Kafin na na baki labarin Malik Aliyu Mai Nassara! Bari na baki daga inda kome ya lalace.
MAFARIN LABARI...
............ _Don Allah zaku min Uzuri na kwana biyu wani Uzuri zai rike ni, Amma Insha ALLAH monday zaku ji ni da Yardan Ubangiji! Keep Vote And Comments And share💖😍_
*_KOME DA LOKACIN SA_*
https://my.w.tt/b9JbZsNMDab
Chapter 12
Na MrsUsman400
If you judge people, you have no time to love them
Adamawa Comeroon.
Muna da Adamawa a Nijeriya! Sannan muna da wani a Kamaru, musamman ta yankin arewacin kasar! Bode sune ƙabilar Fulani da suka zagaye nahiyar Afirka baki kudu da sahara, Rumada kuma wasu kabilu ne na Fulani kaskantattu, wanda Fulani suke kiran su da bayin su. Malam Manu Hammadada, shine kakana wanda ya fito daga kasar Sudan ta arewa, kusan ruwa biyu ne zan iya cewa. Domin shi din Bafulani ne wanda ya kasance Balarabe, Mahaifin shi Bafulani mahaifiyar shi basudaniya, kasancewar sun fito da ayari masu yawa sai suka iso kasar Kamaru, sabida kasancewar ana samun damina biyu a kasar Kamaru, duk da sun zo sun sami ƙabilar rumada haka bai hana su kyamar ta su ba,(am sorry My Fulani people 🙈🙊 Zanyi magana kadan akan halayyar ku da na sani) kaf zuri'a Malam Manu Hammadada, fararre ne kamar larabawa, ga kyau ga halitta, Kakana da yan uwansa sun zauna a kasar Kamaru na kusan shekaru talatin, dan tun suna matasa suka zo ƙasar, kuma sai aka yi dace basu damu da shiga cikin gari ba iyakar su dajin Adamawan kamaru, Dabbobin da suke kiwo sun hada da Rakuma da Shanu, awakai da tumaki. Kaji da zabbi, tare da agwagi. Sannan matan su basu cika talla ba, sabida akwai ilimin addinin musulunci a tattare dasu. Malam yana da yara maza da mata goma cif, shida mata huɗu. Kuma sune kusan kananun, Abubakar wanda suke kira da Buba, sai Muhammad wanda suke kira da Yawale, sai Zailani, da Shuyibu, a mata kuwa Akwai Suwaiba, suna kiranta da Suwai! Sai Nafisatu wacce suke kiranta da Hakama, da kuma Sa'adatu da suke kiran da da Ade, sai Rakiyah Maman mu, wacce takasance autar malam, Duk mace daya ce ta haifi su, Iyatu itace matar Malam babu wata bayan ita, malam nada yan uwa a cikin wannan rugar, akwai yan uwan shi ciki daya da kuma cousin brothers din shi wanda suke auren kanen malam Dan haka ya zama dukkan mutanen rigar yan uwansa kuma koda za ayi auren a tsakanin su babu bare. Haka yayi matukar kara musu zumunci, baka tab'a jin kansu. Duk kusan matan yan uwan Mama duk auren zumunta aka musu kuma suna zaune lafiya. Amadu wanda ya kasance ya fito daga ƙabilar rumada, sune asalin Fulanin kasar Kamaru, kasancewar basu da wani kyakyawan nasaba yasa dayawa Fulani ke ƙin auratayya a tsakanin su. Ahmad wanda suke kira Amadu, shine mahaifina. Kuma babba a gidan Malam Hamisu, Mahaifina yana da kyau, ba laifi sai dai matsalar shi baya jin magana, yana da fitina gashi bai iya niman na kan shi ba, haka yasa dayawan mutane har cikin ƙabilar mu ta rumada sunki nashi auren Ƴaƴan su, sabida sunce bai da zuciyar niman na kai ba zasu sayar da akuya ta dawo tana ci musu danga ba. Shi yasa sai yayi fushi ya tattaro ya tafi Gyambu cirani, abin da ya matukar bawa baban shi haushi yar yace ya cire hannun shi dan koda zai tafi bai gaya musu zai yi tafiyar ba, kawai yayi tafiyar ne. Sai da ya shekara biyu kafin ya koma lokacin bikin sallah dan haka Fulani muna da al'adar wasan shadi, toh a lokacin Baffa yakan ce Yaran shi su tafi kallon wasan shadi. Anan Allah ya hada Mama da Baban mu, abu kamar wasa tun yana Binta tana kaucewa har ta kai babu yadda ta iya dashi, ya biyo ta, har gida. Tun da Baffa ya gan shi yasa aka mishi bincike akan shi, ya fahimci waye shi ne take ya gargadi Rakiyah kar ya kuma ganinta da Amadu. Amma ina kunenta maganar tabi ta wuce, domin sai da tasan yadda ta shiga haduwa dashi idan sun tafi rafi dibo ruwa. Tun suna haduwa a boye har aka samu mutanen da suka gayawa Malam ga Rakiyah da Amadu, nan Baffa Yasaka Buba da Yawale suka mata duka, amma taki ji. Kowa yayi mata fada ta kafe, ganin haka wani kanin malam ya same shi da maganar yace mishi." Yaya ina ga kabar yaran nan suyi auren su, tunda yaron yace aurenta zai yi, sannan bamu san karfin rabon da yake tsakanin su ba, don Allah ka bar su ayi auren." Shiru Malam yayi sannan. Yace wa kanin shi.
"Babu ruwana, babu hannuna sannan ba zan shiga cikin al'amarin ba, gobe da safe yazo da sadaki da waliyan shi a daura musu auren su tafi." Cikin nutsuwa kanin shi me suna Mustapha suna kiran shi Baffa almu, yace mishi. "A'a! Dai kawai kayi fushi ne don Allah ka saka mata Albarka ayi kome cikin amincin Allah." Sauke numfashi yayi sannan yace masa. "Allah ya tabbatar da Alkhairi." Daga haka bai kuma ce masa kome ba, har Baffa Alamu ya fita, sannan ya saka aka kira Mama tazo, kallon aurar shi yayi cikin damuwa yace mata." Rakiya lallai kome da lokacin sa! Yau yar yarinyar nan da nake sakawa a kafad'a na itace yau take jayayya da abinda bana so! Yar yarinyar nan da take cewa Baffana hauroni bayan raƙumi itace take son abin da bazai amfane ta ba, karki manta zaki yi kuka mara amfani, domin kuwa akwai ranar kuka, ranar da ba zaki tab'a amfanar kanki da kome ba, Rakiyah Maduh ba zai rike ki da amana ba, mutumin da bai san darajar kan shi ba taya zai san naki, mutumin da bai rike kanshi ba taya zai rike baki, mutumin da bai rike cikin shi ba taya za rike naki, Rakiya bana son ganinki a damuwa shi yasa nake kin ki auri madu Amma tunda Allah ya kawo mu, zamani da D'a zai nuna abin da yake so koda zai cutar da shi, toh Allah ya baki zaman lafiya! Kije gobe Insha Allah kina gidan Amadunki." Haka tayi ta kuka, Amma ta kasa cewa yayi hakuri dan gani take kamar da gangan ya hanata auren wanda take so, shi kuma bai mata magana ba, haka yayi ta kallon ta, har ta bar d'akin. Bayan fitarta ne ya share kwallar da ya cika mishi ido, Tabbas duk cikin Ƴaƴan shi yafi sonta, amma bata fahimci haka ba. A ranar ya ware mata saniyarta wanda yake basu tun suna yara, da tumakinta sai sauran dabbobin, bayan ya gama bata, ya kalli dabbobin yana jin ciwon rabuwa da Rakiyar. Washi gari da safe aka daura auren kallon yan uwan shi da yaran shi yayi, sannan yace musu. "Ku Zama shaida! Idan rakiya tazo kan gawata ban yafe muku ba, tsakanina da ita na yafe mata, kawai bana bukatar ganinta a cikin wannan gidan. Ku kira mijinta ya tafi da ita bana son ganinta." Kuka take tare da rarrafawa gaban jama'a tana rike su da su bawa Baffa hakuri babu wanda ya kulata domin suna jin haushinta, tayi kuka har ta godewa Allah, shigowar Amadu ya kuma sanyata ta rikice musu, haka ya riketa suka fita bayan ya kad'a keyar dabbobin su, suka fita. Malam na cikin dakin shi. Hawaye yake sosai, domin Allah ya daura mishi son aurar shi ba na wasa ba, haka ya share kwallar da yaji motsin wani zai shigo d'akin shi..... A hankali rayuwa take tafiya, cikin tsarin Ubangiji. Tare da jarabta. A bangaren su Rakiya kuwa. Bayan sun isa gidan iyayen Amadu, nan ne ya fara shimfid'a musu soyayya irin wanda yake ganin ya iya, sai da suka kwashe wata biyar sannan ya koma gyambu, tafiyar shi Innar shi me suna Mero tasaka Mamah a gaba da fitinar yau daban na gobe daban, ga gori, dabbobin ta da Amadu zai tafi ya mata dadin baki ya kwashe ya sayar dashi, ya ajiye mata tsabar abinci ya gayawa Mahaifiyar shi idan ya matso ta fara zuwa tallar nono, tunda akwai masu sayar da shi sari. Haka kuwa Inna Mero ta fara daura mata, Rakiyah kyakyawa ce na kwatance, fara sol ga fuskarta yasha zanen kalangu tare da fasana goshi. Mace har mace sai gashi ta fara lalacewa da fitinar uwar miji, tare da rashin wadattacen abinci. Wani Jumma'a ta kai nono kasuwa, ta tafi layin yan Kore anan ta haɗu da Buba, Allah sarki d'an uwa, gudun kar ya ganeta sai ta dauki Kwarya ta rufe fuskarta, tana wucewa ya kwala mata kira Bododo! Jikinta na keerrma, ta sake nonon kanta, ya zube kukan kawai ta saka mishi. Tasowa yayi ta riko hannunta suka shiga wani rumfa sai a lokacin kukan yazo mata cikin shashekar kuka tace. " Hamma Buba! Anya nayiwa kaina adalci? Tun banyi nisa da a tafiyar na gaza! Nasaka Baffa damuwa na hana shi ya hukuntani, yau gashi duniya tana hukuntani, dama ai ya gaya min kome da lokacin sa, ni nawa lokacin ya wuce na wasu ne!"
Shafa fuskar shi yayi sannan yace mata. "Kowa da kaddarar shi! Ke taki ƙaddaran kenan, don Allah karki kuma kuka, ga wannan ki sayi sabon kore da kayan da kika lalata ki tafi gida." Haka ta mike tana share kwalla, tace mishi. "miyyati Hamma!" Daurewa yake amma da za a bar shi kuka zai yi, sabida tausayin autar su. Dan haka da ya koma gida,bayan sallar isha ya sami Baffa da maganar ta, kamar bai damu ba yace. " Ai toh me zan iya mata? Ni dai babu wanda zai tilasani nayi mata wani abu, dan haka ka bar min batun ta." Da Buba yaso ya matsa mishi haka ya mishi fata fata,.. a bangaren Mama bakin ciki kawai ya ishe ta, domin fasa kwaryan da tayi gidan tare da yan uwan Amadu kamar zasu mata duka ga gori da cin mutuncin wasa sai da suka mai da ita kamar baiwa, ga wulakancin kamar me, Amadu bai dawo ba sai da ya shekara daya sannan ya dawo, nan ma haka yayi kwanaki inda ya sanyata taje gidan su, ta musu rokon a bata abinci, kasa zuwa tayi ta sami zailani da maganar, sake Baffa ya koyar da yaran shi soyayyar junan su, shi yasa basu dauki dogon fushi da ita ba, amma yau ganin
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 6 Chapter of 22