sai munyi suna. Shiru nayi ina bawa Anoosha nono, "Inayatu Rahman!" Da zaran naji ta kira sunan nasan cutatta zata yi, murmushi nayi sannan nace mata. "Bafa zanyi kome ba, raguna biyu, na saya sannan bani da kowa sai ku. Don Allah ki bar maganar sunan nan. Bana jin zan iya shi ne." "Toh amma abokan aikin mu me zaki basu." Ta kafe ni da ido, "ba zan basu kome ba." . "Zaki basu mana, rago daya ayi abincin walima daya kuma a saya miki.". Zanyi magana ta dakatar dani, sannan tace min, "zaki yi fa?" Babu yadda na iya da ita dole na amince mata..
***
A yau ake buga wasan kwallon kafa na nahiyar Turai, kuma za a buga wasan ne tsakanin Manchester United da Barcelona, dan haka cikin sweater har gwiwar shi, tare da Zeemalik din shi suke takawa, kanta a kafad'arshi. Suna hira ta sarkafe hannun shi da nata, bawai hirar arziki bane, kawai bakar magana ce take gaya mishi, akan wallahi babu shi babu mace, zare hannun shi yayi daga nata, ya hango wata mace da yara biyu. Duk maza sun mishi kyau, a cikin keken su, mijin da matar suna zaune kafin a shiga cikin gurin kallon, durkusawa Malik yayi a sanyayye, yana kallon yaran cikin son ina da nashi ne, kai hannun shi yayi zai tab'a su Zeeh ta rike cikin fusata. Janye hannun shi yayi sannan ya wani watsa mata kallon banza, dan kwana biyu nan yana jin zafin tsiyar da take mishi,"meye nufinki? Kar suma yaran na tab'a su? Kinga bana son Jahilci, idan zaki yi kishinki kiyi abinki karki kuskura kice zaki hanani kula Yara, ko ance miki tsoronki nake ji da zan dinga biye miki kina hauka da sunan SO! Wallahi kika Kuskura wani abu ya sami yaran hmm!" Sake baki tayi, sannan ta kuma kallon shi bakinta na rawa tace mishi."Ya Malik!" Tsaki yayi sannan ya wuce ta, abin shi bayan ya bude wallet din shi ya ciro fam dubu goma ya ajiyewa yaran, iyayen yaran sai godiya suke, tunda ya sayi ticket din kallon gasar, ya juya zai bar gurin suka yi karo da wata yarinay, ta sayo drink a cikin yar cup me murfi da tsinke shi. Kawai murfin ya bude duk ya zube a jikin shi, a fusace Zeemalik tayo kan yarinyar, zata shake wuyar ta, yayi maza ya dawo da yarinyar bayan shi, yana kallon Zeeh. "Da gaske baki da hankali, waye bai san kuskure ba? Toh me zaki mata? Kasheta zaki yi? Bana son hauka, dan haka na yafe mata," sannan ya juya ga yarinyar ya sallameta, bayan..komawa yayi inda ake ajiye tissue ya dauka yana goge jikin shi, yana kallon Zeeh da wutsiyar ido, yarinyar nayi hanyar ban daki tabi bayan, shima ya rufa mata ba, yana shiga ya same ta ta saka wata igiya ta shake wuyar yarinyar, duka-duka bata wuce sha biyar ba, dan ma yaran turawa ne da shegen girman jiki. Yana shiga ya kifawa Zeeh mari abinda bai tab'a mata ba, a tsawon shekaru goma da auren su, abun ya bata mamaki. Sake marinta yayi sannan ya murɗeta ya kwace yarinyar, ya fitar da ita, tana haki, sanan ya dawo ya ja Zeemalik wacce bata gama dawowa hankalin ta ba, dama yau tun tashin su da safe taga ya wuce dakin motsa jiki, ta bishi da ruwan sha, ya wurga da goran cikin fusata yace mata, "bana bukatar ruwa! Abincin da zanci nake bukata, macen da zan kwanta da ita nake bukata, idan kuwa baki nima min dukkan biyu ba, wallahi sai na baki mamaki na gaji da cin abincin restaurants, a cikin garin London babu gidan abincin sa basu Sanni ba, maye amfaninki. Ina tare da mace amma babu amfani, toh wallahi ki shiga kitchen ki min abinda zan ci sannan kuma dole kiyi hakuri dani inba haka ba, kome zai iya faruwa, matan da baki son na kula zan fita na nime macen da zata dace dani a dare nan! Get out!" Ya nuna mata hanyar fita. Kura mishi ido tayi ya kuma saka mata tsawa wanda yasanya ta fita dan dole tana shashekar kuka, lumshe idanun shi yayi cikin b'acin rai, "Inayatu! Inayat ina kewar lamarinki! Ina ji a jikina kina fusace dani," a haukace ta leko dakin tana kallon shi. "Wacece ita?" Wani kallon banza yayi mata, sannan ya cigaba da abinda yake.! Abin da yazo mata rai kenan, ta fashe nashi da kuka, yau ita ce Malik ya daka, ya kuma mata rashin mutunci tun safe, "Ubangiji meye nayi haka yake wulakanta ni" tsaki yayi sannan yace mata, "ban da jahilci, yaushe rabonki da sallah, amma kin iya tambayar Ubangiji meye kika yi mishi." Cikin jin haushi tace mishi, "Ai kai ma, hada salollin kake yi! Kuma cikin dare kake yi sun uban me yasa baka yi akan lokaci?" Lallai yau Zeeh ni kike takala da rigima, haka yayi ta kwafa domin yau Zeeh ta gama dashi. Suna isa gida kowa ya wuce dakin shi, ko ajiye jakarta bata yi ba, ta kira Tabawa, cikin kuka take gaya mata abinda yayi mata yau, dan haka tabawa ta gaya mata tazo da wuri, bata gaya mishi ba tafita daga cikin gidan, hankalinta a tashe.. koda suka isa sun same matar a zaune, tana ganin su ta kura mata ido sannan tace mata. "Uwar mijinki! Ta tashi daga barcin da take! Kuma tana bukatar Yaron ta a gare ta, kiyi yadda zakiyi ki tabbatar yau ya ci wannan a cikin abincin shi, ba zai kuma tuna batun gidan ba, amma akwai wani abu da ya sanya shi birkice miki, kuma yanajin yanayin ne a tare dashi, dan haka karki kuma yarda ya kamaki da laifin cutar da wata ina ba haka ba. Zaki lalata aikinki, domin ba zai cigaba da ganin kina janyo mishi magana ba, yin haka shi zai sanya ya tattara ku koma ƙasar ku ta Haihuwa, daga zanen kaddarar ku zata iya sauyawa." Shiru Zeeh tayi hawaye na zuba mata, yau ta shiga uku, ya zata yi idan Malik ya fara niman mata. Mika mata wani irin abu tayi me kama da mashroon sannan tace. "Ki tabbatar yaci yau. Idan ba haka ba, zaki yi ta rasa damarki. Har abada, domin mahaifiyar shi ba zata kuma d'aga miki kafa ba." Daga haka ta juye kudinta tsaf ta fito daga cikin gidan, ita da tabawa, suna isowa gidan suka hango Malik yana kallon su... Kuyi hakuri babu yawa amma gashi nayi iya kokarina 💋🙏🏼💝
*_KOME DA LOKACIN SA_*
https://my.w.tt/p06r1fOJRab
Chapter 23
First, think. Second, dream. Third, believe. And finally, dare.
Maman Sheikh\Ummul Adam\Mum Sayeed! My Dear Ma'uh ga pagen din ku nan,💋 thank You so much 😍..
Yadda yake tafiya cikin tsarin, tare da wani irin yanayi him luk so sexy, b'cos button din rigar shi a bude suke sannan ga asalin natural gashin jikin shi kwance yayi wani luf, kura mishi ido Madam tabawa tayi cikin wani irin yanayi, da bata tab'a ganin wani d'a namiji cikin shi ba, tunda ya fito daga cikin gidan, ya kira musu ido, zuwa yayi ya zauna akan wasu plastic chair, yana kallon su ya buga tagumi da hannu daya, jikin su duk ya gama mutuwa ga wani a zaɓaɓɓen tsoron da ya kama su, cikin tashin hankali Zeeh ta bude baki zata yi magana yace mata.,"keep silent!" Shiru tayi dan bata tab'a jin wannan kalmar ba, sannan ya sauke hannun shi yace musu. "Daga ina kuke?" Tsuru tsuru suka yi! "Nace daga ina kuke?" A tsora ce, Madam tabawa tace mishi."am sorry sir, matar nazo dubawa yanzun." Yadda ya zabga mata wani irin kallon banza yasata sunkuyar da kai,"well! Kar na kuma ganin bakar fuskar ki a gabana! In ba haka ba, don let me to be harsh. Zaki iya tafiya." Sannan ya juya gurin Zeeh da yau daya mugun tsoron shi ya kamata. "Zaki iya komawa inda kika zab'a sama dani!" Sannan ya mike zai koma cikin gidan ta zube a gaban shi tana me rike kafar shi cikin kuka tana fadin."don Allah kayi hakuri" cikin fushi ya janye kafar shi, yana me jin wani irin zafi ya d'agota. "Meye na miki da zafi? Na fita ina jin yunwa! Na dawo baki bani damar naci abincin ki ba, And na fito na samu kin fita me kike nufi dani?" Wani irin kuka ne ya kwace mata shikenan sun lalata mata shirinta, na wata kusan goma, yau sun lalata mata kome nata, Kukan da take ya matuƙar kashe mishi jiki, dan yasan kome tayi sabida shine, amma ba zai iya kyaleta ba, dan idan ta cigaba da haka wuta zata shiga, shi kuma baya jin zai barta a haka tunda ta iya zabarshi a abokin rayuwarta yasan ba karamin son shi take ba. "Kiyi min shiru, ki wuce ki nima min abinda zan ci!" Daga haka yayi tafiyar shi, binshi tayi da mugun kallo, tana jin ciwon abinda ya faru, kuma tana da shiri na musamman akan shi, dole ta bautar dashi yadda gobe sai yaji tsoron marinta, dan haka ta shiga kitchen tayi mishi jagwalgwale, ta zuba mashroon din, ta kawo ta ajiye mishi, sannan tabi shi daki ta gaya mishi, yana fitowa yaga abincin. Ji yayi kamar ya kurma ihu. "Luk! Wannan abincin zan cusawa cikina, kin hanani daukar masu aiki. Maza da mata kince tunda akwai restaurants, muje mu saya, ina son cin abinci ba wannan jagwalgwalakin ba, ni ina son cin abinci nace ki je ki dafa min abinda zanci kamar yadda matan Hausa Fulani suke girki, wallahi kika sake yau banci abinci ba, jibi sai dai ki ganni da mace dan bazan zauna dake baki gamsar dani baki kosar da ni, sannan kice zaki hanani na karo wata mace ba." Huci yake itama tana hucin amma kasa kasa, lashe bakin ta tayi, sannan ta dauki kayan abincin ta koma daki, kitchen ɗin ta koma, ta dauki wayarta ta bude data, a hankali ta fara browsers na abincin musamman na Afrika, sannan ta sauko kan shinkafa da miya. Ta nutsu ta karance abinda aka rubuta, sannan ta fara gwada wa tayi tana duba wayar, aka gama da shinkafa ya hau kan wuta, miya kuma aka dibo tomatos, da kayan yaji aka hada da namar bayan an yanka namar aka nika kayan miyar aka zuba namar da kayan miyar lokaci guda, sannan aka rufe. Ta koma kan shinkafar, wayyo ta zuba mishi ruwa, har ta dafe lugub, karshe tsantsamewa tayi ta mai dashi kan wuta, ta rufe sai goge zufa take, kamar wacce a ka bata wani babban al'amari. Tana idarwa ta juya motsa namar, yana nan kamar yadda ta zuba, sai dai alama yana bukatar hakuri na wani lokaci, tunda ba a tafasa shi ba. Juyawa tayi ta koma kitchen..ta dauko kaza, ta wanke. Tare da zuba mai. Yana zafi ta shiga soyawa bayan ba a tafasa shi ba. Ba kuma Orange chick ba. Haka ta gama hada girkinta iya haduwa ya hadu, akan ido amma a baki kan(🙄🤣Mama me Voice bismillah) tana gamawa ta shiga juyewa a warm, shinkafar ta koma kamar tuwo, miyar kuwa a idanu ba laifi, yaji mashroon ba iyaka, sannan aka juye na me gidan, aka nufo dinning table, aka shiga jirawa. Ban daki ta shiga tayi wanka tare da gyara jikin kinta, sannan ta fito. Tana gamawa shiryawa ta nufi dakin shi, ta zauna a bakin kofar. Daga shi sai yar karamar boxes, yana shiryawa ne dan idan bata gama abincin ba zai wuce gidan cin abincin ya sayo abinda zai ci, "ya Malik! Food is ready!" Tab'e baki yayi sanan ya dauki rigar shi yayi wucewar shi, ya zauna akan kujeran tunda ya bude kular miyar yayi tozali da miyar jajjur da ita, kawai ya had'iye yawu, sannan ya zauna zai yi serve kanshi ta amsa ta zuba mishi, sannan ta nutsu burinta yaci abincin, tunda taga zuba shinkafar a filet din yaji ina , amma ganin miyar ne ya sanya shi, jin zai iya ci. Tana gama zuba mishi. Ya dauki cokali, ya dibe abincin da bismillah,ya kai bakin shi. Da sauri ya zuba mata ido, abu biyu a lokaci guda, ya furza mata a fuskarta, sannan ya mike tsaye yace mata. "Wannan haukar nasan sai kece zaki iya yin shi, comman food ba zaki iya sarrafa shi ba, Zainab! Abincin ba zaki iya dafa shi naci ba, ina niman shekaru arba'in matar da na aura more than ten year ba zata iya min abincin da zan kawo baki suci ba?" Cikin ciwo da abinda take aikatawa, ya tako gabanta. Yana kallon yadda take tsuma. Kura mata ido yayi cikin damuwa yace mata. "Ya kike so nayi? Ina son idan naci abinci na same kulawar mace, amma babu Zeemalik idan na kuma jin ki dauki any stupid action akan wata mace! Sai na.." daga haka ya wuce yar barta a gurin, dakin shi ya shiga, tare da ɗaukar Jacket ya daura akan rigar shi, sannan yayi ficcewar shi daga gidan. Ya nufi gidan abincin na yan Afrika. Tunda ya gama gaya mata magana ta zauna tayi kuka kamar ranta zai fita,tana kallon abincin da kuma kuskuren da take son ganowa, tabbas MALIK yayi da yar halak, sai ta mai dashi tamkar yadda ya sanyata kuka. Ba zata tab'a barin shi haka ba. Ya sanyata asara. Kwashe abinta tayi zuwa kitchen, kawai tq hango ingredients na kayan abincin da bata zuba ba, sake kular miyar tayi a kasa, tare da rike bakinta. Wani irin kuka ne ya kwace mata, tana faɗin "na shiga uku na lalace, shi yasa yayi ta faɗa." Wani sabon kuka ne ya kamata, tana yi tana kallon kayan haɗin kome har dasu kayan lambun da zata yanka mishi... Fita tayi ta kira Tabawa ta gaya mata, dakyar ta amsa mata da cewa. "Zeeh! Kawai abinda zan iya miki gobe idan naje zan turo miki da Su'adah tazo sai ta nuna miki yadda zaku yi girki da ita zata kawo miki wani abun da zaku saka a cikin abincin yaci." Cikin wani irin farin ciki tayi ta godiya, sannan ta kashe wayar... A gidan Madam Tabawa kuwa kallon yarta take Su'adah, cikin nutsuwa tace mata."kin dace da MALIK, kin cancanci zama a matsayin matar shi, daga gidan shi gurin Lili na koma ga hadin da ta kuma min, ko tabbatar kun zuba mishi yaci. Karki yarda ki bar gidan bata zuba mishi ba, ki tsaya kiga yadda kome na gidan ya hadu ya kuma dace dake!" Haka uwar tayi ta daura ta akan tsani yadda zata mallake MALIK, su kuma juya su ci Uban Zeemalik, tacewa yar. Ta nutsu ta gano matsalar Zeemalik din kafin ta bar gidan. Da wannan suka ajiye maganar.
.........yana gama sayan abincin ya shiga motar shi ya tawo gida, a sannu kome yake dawowa hankalin shi, babu kamar daren da yayi da ita, babban damuwar shi tana raye? Dan kar dai ya kashe musu yar mutane ya gudo, bai ma san da wata fuska zai tsaya a gaban Mahaifiyarshi ba, ya gaya mata yayi aure a b'oye. Innalillahi wa'inna ilaihi rajioun, ya furta a hankali yau yaga takan shi. Da sake sake ya koma gida, koda ya shiga ya sameta a zaune a step tana kallon shi, ko inda take bai kalla ba, ya zauna ya juye kome ya ajiye mata mata, mik'ewa yayi ya shiga kitchen, ya fito har ta zuba mishi garin Mashroon din ta zauna tana kallon shi. Bai damu ba bai kuma san me tayi ba, sai da ya zauna yayi basmala ya fara cin abincin, a nutse. Yana gama ci ya tattara kome ya kai kitchen sannan ya haura zama, ya wanke bakin shi tare da wanka, yazo ya kwanta, kashe wutar dakin yayi a hankali, hoton surar Inayat ya shiga ƙoƙarin dawo mishi, kawai irin halittar jikinta, ba zai iya manta yadda yaji take ba, nutsa kan shi yayi a pillown shi, yana kuma tuno yadda ya rufe idanun shi yayi ta gurje ta, ba tare da ya damu da halin da take ciki ba, duk da bata numfashi yaji yadda jikinta yake bashi damar kutsa cikin ta, wani irin ni'imar da tayi ta saukewa a ranar babu iyaka, shi kan shi bai tab'a jin dadin wannan lokacin ba, bai tab'a sani mata suna suka tara ba, sai da ya raba shimfid'a da Ita, yaji baiwa da zubin halittar da Allah yayi mata, abinda zuciyarshi ta bashi itace _ina ma da ace Allah zai kuma hada mu koda cikina ne ya bayyana a jikinki! Da naso abin da duk zuciyata, da nazo na amshi abuna ke kuma na sake ki,.ki auri wanda yayi miki!_ take wata shashi na zuciyarshi ya jefa mishi tambaya kamar haka. _Dagaske zaka iya saketa?_ tsaki yayi tare da juyar da kan shi, yana me kuma ji a kanshi zai iya mana, amma idan ya tuna da yadda yake zubda erecting a jikin shi sai yaji wani irin sanyi dan ko babu kome Inayat ta bashi farin cikin da yake nima, a sanyayye ya faɗa dai dai shigowar Zeeh din shi yace. "Inayat kin jiyar dani dadin da ban tab'a ji ba, Allah ya sanyawa rayuwarki albar..." "Ya Malik! Wata tsinaniyar ce take son raba ni da kai?" Banza yayi da ita, a hankali ta hauro gadon tare da juyar dashi, kuka ta sake mishi. Ya hada bakin su lokaci guda, dan a bukace yake da mace, musamman Inayat. Ba tare da ya damu da wacece a tare dashi ba, ya shiga Binta da wasu irin romancing kamar ba zai barta, ba. Rike shi tayi cikin jin dadi dan ya fara dawo mata da Happiness dinta, so sun dauki long time, kafin ya shiga ƙoƙarin kusantarta. Ba tare da ya san me yake fada ba, ya fara faɗin. "Wowwww my slim fit lady, Yawwa my Inayat, you deserve me. My sugar baby, my baby doll. Kina da kyau da albarka, let me be with you, wow so sweet. Auchw. Kin san yadda kike kuwa, waye zai ce baki hadu ba, Inayat i like your sexy body. Ina son kome naki ina son wannan boons din them luk tender, suna min dadin tab'awa, kinsan yadda suke soft and warmth, smoothie and gorgeous. Thank you I love then" kura mishi ido tayi cikin tashin hankali, wacece Inayat? Wacece ita da ta rabata da MALIK, kuma tabbas wani abu ya shiga tsakanin su, dan yadda yake zuzzuta kyan jikinta da kan kasarta tasan ya kwanta ne da ita,, kuka take wiwi..kamar an dake ta, domin kuwa bata tab'a sanin MALIK zai iya rayuwa da wata mace bayan ita ba, sai da ya juye mata all seed water din shi sannan ya koma gefe, yana ajiyar zuciya. Cikin kuka ta juya gare shi tana faɗin. "Wacece Inayat?" Kallonta yayi sannan yayi shiru tabbas ya sake magana, taya haka ta faru? Juyawa yayi ya kalle ta, sannan ya tab'a baki yace mata, "mafarki nake kullum ina having sex nake da ita, shi yasa nake yawan kiran sunanta!" Kura mishi ido tayi sannan tace. "Duk a mafarkin ta gaya maka sunanta?" Cikin nade taburman kunyar shi yace mata. "Baki yarda dani bane? A cikin mafarkin ta gaya min sunanta." "No no, kawai naga kamar nima ina bukatar nasan mafarkin ne, don Allah idan zaka kuma mafarkin ka gaya min sai muyi tare." Tsaki yayi tare da rufe ta da faɗa. Sannan yace mata. "Gobe ki shirya muje asibiti domin ina son kids a gidan nan." Sannan ya shiga ban d'akin abin shi...
Kashere
Ranar suna walima kawai aka yi, shima kuma ɗan kar a nace ta dame ni ne, Amma Wallahi ban so haka ba, sai dai kuma yaran sunyi wani irin goshi, musamman Khady take tofa musu addu'a, na baki da kambun baka, addu'ar da Annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallama, yake tofawa Hassan da Hussaini, shi take musu ko ni na musu, bayan anyi walima da dare ta tayani kwashe kome, washi gari Suka wanke kome ita da Ummanta da matar Baba , sai Maman Ummi. Matan gidan mu, kuwa kyashi da hassada ya hana su sukuni, bayan an gama suka ci-gaba da soya min nama, Khady tayi min kome a rayuwa, dan sai gashi har da yajin da ban samu haɗawa ba ta haɗa min, yara kuwa tayi musu kaya yakai kala biyar, sannan nima tayi min kala biyu. Ban hidimar da tayi, shi yasa ita da mutanen da suka tsaya min na raba naman biyu na basu, kin karba Khady tayi sauran kuma tasa su, dole suka amsa. Har fushi nayi bata damu ba.
Kullum zata zo duba yaran, ta kawo min abin da bani dashi, sannan ta bar gidan. A hankali muka shiga rayuwar jego, yarana suna kara girma, ina kuma mai da hankali akan ginin jikina, yadda zan amfani kaina gaba. Har muka cika arba'in, sannan da umma zata tafi na hada mata shatara na arziki, muka rabu lafiya, Khady ta kuma nima min wacce zata taya ni renon yaran, Maman Ummi kuwa, ina kyautata mata, kuma yanzun sana'ar ta Allah ya sami shi albarka. Har tana sayan abinda da bata iya saya. Mijinta yakan ce mata, "ai Mamar tagwaye macen arziki ce, matar rufin asiri ce, shi yasa duk abinda ta saka hannu zaka sami albarkan shi ya wuce yadda kake tunani." Haka yake sambatu. Tayi ta dariya tana gaya min, shareta nakee. A hankali yarana suka shiga wata shida, anan suka yi yar mashasharan hakori, bayan ya fito nima kuma na koma aikina, na kuma ɗaukar su muka nufi gombe, tsoron Baba ya hanani karasawa, haka na gama karewa gidan mu kallo zuciyata tana wata irin bugawa, sannan na juyo cikin damuwa ma dawo kashare, koda na dawo nayi kuka a d'akina, inda nasaka Yaran a gaba nayi ta kuka ina tausayin su da kaina, yaran sak fatar uban sune dashi, kome nashi sun ɗauka. Gashi basu da rigima sai dai rashin son mutane, haka yayi min dad'i dan bana son ana yaean daukar su ana kiran su yaran Turawa. Watan su goma sha daya aka turamu karatu Ghana da Khady. Kallon ta nayi cikin sanyin jiki nace mata. "Zaki iya tafiya, ni babu inda zani. Da ace yaro daya ne ko yarinya daya zan tafi da ita, amma biyu ga wahala ga abubuwa waye zai daukar min nauyin reno, kiji Allah ya baki sa'ar tafiya." Duk yadda taso naje ba zai yi bane, sabida rashin wadata, Ghana ba kamar sauran ƙasashen Afrika bane, tana da tsadar rayuwa, idan Nigeria uwar Afrika ce, Ghana itace zuciyar Afrika, sabida yadda suka ci-gaba kuma ko South Africa ba zata nuna mata wannan Cigaban ba, haka muka rabu da Khady gashi shekaru uku zata yi, idan ta dawo zasu riketa a garin Abuja, na shekara daya. Munyi kuka sosai. Sannan muka yi sallama na rakata har gombe. Bayan tafiyar ta na dawo.
Wata sabuwa rayuwa.
Ban tab'a halkanta da tsaya min da Khady tayi ba, ban fahimci taimakon a kaina ba, sai bayan tafiyarta, na Fahimci hatta abincin da nake bata kudi tayi mana sayayyar shi nata kason yafi nawa yawa, asalima bata amfani da kome da na bata, Maman Ummi take bawa tana sakawa a asusun. Sai da wata ya kare, nayi lissafin abinda zan saya mana, naga babu kudin da zan rike koda wani abu ya taso, ranar nayi kuka, sabida Khady mutum ce sukutun da guda, Maman Ummi taga ban fito ba, shine tazo duba ni taga na saka yaran a gaba ga kudin na ajiye ina kuka. A take maganar Khady ya dawo mata. _Maman Ummi! Idan na tara mata kuɗin, zata iya biyan kudin haya cikin nutsuwa, wallahi bata san hidimar iyali ba, sabida da asibiti biyu tayi aiki lokaci guda, sannan Kinga yaran suna buƙatar kulawa, domin idan a gidan Uban su suke wallahi sunfi karfin kulawar mu, idan ma ba a dauko masu kula dasu daga kasar waje ba, Ina fatar uban su yazo gareta kafin rayuwarta ta sauya, domin ciyar da iyali babban al'amari ne. Sannan
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 11 Chapter of 22