ta a bukace yasa sun mata faɗa, na rashin zuwanta, sannan suka hada mata kayan abinci, tana gidan sai ga Dangin malam daga sunan ya'yan yan uwan Maman shi, sanda suke zaune a kasar Larabawa, sunyi farin ciki tare da daukar hoton sabida su Larabawa. Sun zo da abun daukar hoto sai ake gaya musu ai zata koma gidan mijinta ne kuma ba lallai su kuma haduwa ba da juna ba, sannan Mama ta bar gidan. Tun daga hanya da ya hangonta hannu rabba babu itaccen koran saniya, ya daure fuska, ganin kayan abincin ne ya sashi balbale ta da fada,bata iya cewa kome ba, nan ya zageta tass,kamar zai buge ta. Daga nan kuma yayi tafiyar shi cikin gari tana shiga cikin gida suka kwace kayan tare da make mata goshi. Tayi kuka sosai, koda ya dawo yaga bata yi girki ba, ya tambaye ta ba asi, ta gaya masa kwace kayan suka yi. Fita yayi ya samu har sun kasafta, kasa hakuri yayi ya kwace kome bayan ya dauki adda zai sare musu kai. Aikuwa suka kulaceta. Amadu sai da yayi wata hudu sannan ya koma, yana komawa suka bude mata Bala'i, ga azabar yunwa da wulakancin toh baya barin abinci. Dan haka ta tafi gida, yayunta da Innarta suna hada mata kayan abinci aka kai mata, da haka ta samu sauƙin wahalar rayuwa, wannan karon sai da ya doshi shekara uku sannan ya dawo gida, anan ne Yan uwan Mama suka ce basu iya ji ba sai ya saketa, yana basu hakuri tare da rokon Allah dakyar suka barta da zai tafi ya haɗa mata kayanta suka nufi Gyambu, shine ta huta da wahalar uwar miji da yan uwansa, garin Gyambu Amadu ya lakato rigimar na bashi domin bashi da wata sana'a sai cacca, anan ya lakato aka cinye shi saura kiris da zai saka Matar shi wasu mutane suka mishi nasiha, ya hakura karshe wai dan an cinye shi ya gudu da ita suka bar garin.....😹🤗 Nagode anya gobe zanyi muku kuwa🙈🙊 ina busy sosai
*_KOME DA LOKACIN SA_*
https://my.w.tt/oTzON9DWEab
Chapter 13
Na MrsUsman400
*https://youtu.be/8Hg9_LNEm7c*
```Domin samun garabasar cigaba da baku Kome da lokacin sa! Pages Biyu kuyi mana Subscribe a YouTube! Sannan sarin Armashi! Masarauta biyu shima Free ne! Amma sai kayi mana Subscribe idan har muka kai 1k Subscribe Na muku alkawarin Sanya ku a grp din Masarauta biyu! Iya mutanen da suka yi Subscribe idan kika bari damar ya wuce ki daga yau sha bakwai da wato October zuwa Goma ga wata November! Zaku yi mana idan kuka wuce wannan lokacin an sorry ba zaka samu shiga Group```
Koda suka iso nan gombe, gidan haya suka nima, dakyar sakamakon basu da wani abu a hannun su, Unguwar da suka sauka Unguwa ne na talakawa, wato Unguwar jeka da fari, zaman haka babu abin yi yasa Mama fara amsar aikatau, wankin tare dasu surfe da daka, shi zata yi a biya ta, ta kuma nima musu abin da zasu Ci, wasa wasa tafiyar ta mike tun Baba yana dan kawo abin da zasu Ci, har ya daina ya barta da wahala, har dai suka sami shekara uku da dawowa Gombe, a lokacin ya shiga wani wasan caca, ya sami kudi dayawa. Samun kudin shi yayi dai dai da samun cikin Mama haka tayi ta wahala, gashi ya samu kudi amma abin mamaki. Shine babu tausayi a tsakanin su. Idan ya samu yadda yake so magana ya ƙare, a haka har kudin da ya samu suka kusan karewa, sai gashi ya fallo aure. Lokacin Mamah tana da tsohon ciki, tun kafin matar ta tare, auren ya mutu, sabida sun ce bai da sana'a. Ana dai ya huce haushin sa kanta wai itace tayi sanadin rashin auren shi. Ita bata ce kome, ba har dai Allah ya sauke ta lafiya, ta samu yarta mace, koda ta haihu. Taga rayuwa na rashin gata da galihu, sai makota da abokan arziki suka mata shatara na arziki ranar suna inda yace shi ya bata damar tasaka duk sunan da yayi mata, dan haka matar da take gidan kasancewa tsohuwa ce, ita ta dauki jaririyan ta kaiwa liman ya mata huduba da Inayat! Dan itama Mamah tace bata da suna duk wanda aka saka daya ne. Ranar suna kuwa na amsa suna Inayat, haka ta cigaba da kula dani har na fara tafiya, Baba bai tab'a saya min pant ba. Duk wani fadi tashi Mamah ce. Har na kai shekaru shida matar da muke gidanta ita tasaka Danta ya sani a makaranta, kuma me tsada, haka ya kuma bawa Baba haushi. Gashi Mamah bata kuma Haihuwa ba har sai da Baba ya kara aure matar Inna Jumala tana shigowa ta haifa mishi da namiji, dan haka yayi ta turawa Tsuhuwar gidan da muke yaron, ita kuwa tayi banza dasu. Shekaru Inna Jumala bakwai dan ana goyen kanwata da take bina, ya Auro Hajjo, itama tana zuwa ta fara zazzaga yara maza, kafin ta samu mata, sai ya zama dakin mu mune babu namiji, lokacin da na gama primary school Baaba ta kuma sawa aka kai ni secondary, ta kuma sake tallafawa kanena, Baabah sai da ta tsaya min na gama Secondry, Allah cikin ikon shi mu daliban da muka fito da sakamako mai kyau muka samu makarantar jinya anan gombe, murna a gurin Mama kamar ta zuba ruwa a kasa ta sha, a lokacin tana sana'ar sayar da abinci. Da wannan sana'ar take rike mana cikin mu, Ni kuma ina zuwa koyan dinki, Gashi ina karatu, dake mun sami tallafin karatune kyauta, shi yasa na mai da hankali sosai. Sai da na shekara uku, sannan na gama makarantar, ina gamawa ne na samu aiki da babban asibitin gombe, anan na hadu da Dr Ishaq, shi kuma da zasu bude asibitin mai Nassara clinic, ya gayyace ni, a zamana da Dr ya sha nuna min alamun yana sona. Amma bai tab'a gaya min ba. Duk ƙanena sun yi aure musamman wanda ba mu daki daya dasu,, wanda muke daki daya ne, nayi kokarin ganin kowacce ta fara neman na kanta kafin tayi aure, Nusaiba tana N.C.E, Mariama kuma ta kuma tana High Islam, sai Balkisu da take aji biyar na secondary, Zehrah tana aji uku na secondary, dukkan su nan suna da abin yi dan Nusaiba tana kitso, Mariama tana kunshe da daurin dan kwali, Balkisu kuma kwalliya take yi, Auta Zehrah. Tana koyan dinki irina. Yanzun hka na bari za ayi bikin Nusaiba da Mariam, dan yace ya gaji da ganin su. Daga nan na bata kabarin MALIK da irin cin mutuncin da yayi min, sai da ta zubda kwalla.... Ajiyar zuciya ta sauke sannan tace min. "Gaskiya Inayat halin da kike ciki ba laifinki bane na Mamah ce, domin da bata bijire musu ba, har abada da kuma baki fada wannan halin ba, sai dai ina me baki shawara kiyi hakuri da cikin jikin ki, dan wallahi matukar kika zubda shi, toh ba makawa, zaki yi dana sanin. Kuma nasan ai ba yau kika soma yunkurin zubda shi ba, kuma yaki fita, haka ya nuna miki Allah yana tare da ke. Sannan Malik Aliyu Mai Nassara, ki zuba ido, kina nan Allah zai kawo miki shi sai yayi kuka da idanun shi." Ba haka naso ba, kawai bani da yadda na iya ne, amma da na zubda cikin... Tun bayan tafiyar ta, na zauna nayi kuka kamar raina zai fita, sabida na tsani kaina na tsani cikin jikina, a kullum bakin cikin rayuwa dashi nake..
***
London.
Kamfanin Malik yau cike yake ana ta fama aikin bude wani shashin na musamman da za ayi ta karin magani, wata baturiya Poland, tazo sabida sun jima suna kasuwanci da Malik. Kuma tana ganin haske sosai, kasancewar tana matuƙar kaunar shi, yasata bin shi duk inda zai bude kamfanin sai ta zuba hannun jari a kamfanin. A hankali suke tattaunawa Zeeh tana kallon su. Daga nesa, idan ranta yayi duba ya ɓaci domin ji take wani abu ya tsaya mata a wuya, dan haka ta dauki fork ta shiga cakawa a hannunta, haka bai mata ba. Ta shiga jan shi a fuskarta tana kallon yadda Malik yake dariya tare dawa baturiya bayani yadda ya sami nasara a kamfanin shi. Da kuma target din shi na gama ba da kuma gudummawar da zai bawa kasashen Afrika. Mik'ewa Zeeh tayi ya dauki tissue ta fita da sauri ban daki ta isa tana shiga taga yadda kumatuna suka ji ciwo, lumshe idanun ta tayi, sannan ta bude sunyi wani irin jajjur, ta saka dan ruwa ta wanke jinin hannunta, sannan ta fito bayan ta kare fuskarta, ta nufi inda aka ajiye ruwan tana zuwa ta watsawa matar..tare da ce mata "sorry." Kallon Malik tayi sanan ta kai bakinta kunne shi. "Ka tab'a ni, nima sai na rama!" Ganin matar ta bar gurin, ya kalle Zeemalik. "Don Allah karki aikata wani abu, don Allah na roke ki!" Buge hannun shi tayi tare da zuba mishi ido, da suka yi jajjur, sannan ta cire tissue da yake kumatunta. Ta kura mishi ido. Sanan ta sake murmushi tayi komawar ta gurin zamanta, sai da ta tabbatar ya mai da hankalin shi kan mutane tabi matar ban daki, bayan bata saka abu fuskarta, ba iya fuskar ta ba, hatta kayan jikinta sai da ta sauya, tana shiga ban dakin kawai ta samu fuskar matar nan da fork ta shiga yaga mata shi, sai da ta bata mata fuska da hannu, kamar yadda tayi nata, sai da ta bata mata fuska sannan tayi ficewarta ta bar matan cikin jini, sai da wasu mata suka shigo ban dakin suka fita suna ihu. Koda Malik ya shigo rike bakin shi yayi tabbas aikin Zeeh ne, dan haka ya sa aka kai matar asibiti, yaja hannun Zeeh suka fita. Murmushi tayi tana kallon shi, kafin tace mishi. "Sai da na gaya maka karka tab'a fushina, ta godewa Allah da ba kashe ta nayi ba." Cikin sanyin murya yace mata. "Zeenah! Me yasa kika min haka? Me yasa kike son jefa ni cikin damuwa?" "Eyye sabida Ni kadai aka yi ka! Sabida soyayyar da nake maka! Sabida babu wacce ta isa ta rabe ka! Idan kuwa naji labarin ka kwanta da wata mace! Sai nayi kicking Manhood kanka, ka Fahimta joystick din ka san kwashe na rantse da Allah, abin da xan maka kenan, ita muka yarinyar da ta baka kanta kaci, wallahi sai na saka mata ruwan battery a gabanta, kai mace idan tayi maka dariya hukuncinta na zubda mata hakora ne! Balle kuma ta kalle ka cikin jin dadi sai na lalata mata fuska, kai jin ka tunda na iya fidda jinin kanwata zan kyale wata shegiya ce! Wallahi na ganka da mace, next abin da zan maka, basan me zan gaya maka ba, amma zaka ji a jikinka kai ma, mutum sai kace bunsuru. Wata uwar ce bana maka, amma dake akuya ce ta haifeka shine bari kayi ta kula kulan yan mata, zasu ci Ubansu dan kutumar Uba su, sai na kashe yarinya dan Ubanta." Bai kuma magana ba, duk yadda zuciyarshi ta kai da tafasa kafa magana yayi, yana me jin haushin Zeemalik amma ya kasa nuna mata, kallon shi tayi cikin tsawa tace."fushin Uban me kake? Maza kayi min dariya idan ba haka ba, wallahi zan aikata abin da nayi niyya." Dariya ya saka mata, ba tare da ya damu da halin haka suka isa asibitin inda aka shiga da matar ana dinka fuskarta. Malik sai da ya kusan kuka dan bakin ciki musamman yadda Zeemalik din shi take nuna alhininta, tare da kuka 🤪
*_KOME DA LOKACIN SA_*
https://my.w.tt/QunMEM22Fab
Chapter 14
Na MrsUsman400
https://youtu.be/8Hg9_LNEm7c
BAHWA HAUSA NOVEL sunan channel din..
..When you undervalue what you do, the world will undervalue who you are....💖
Kamar wani dolo haka yake binta da ido, duk ta rikice kowa sai kallonta yake yana tausaya mata, kuka kuwa da take. Sai ka rantse da Allah, bata san kome ba haka yake binta da idanu, ji yaƙe kamar ya shaketa yayi ta bugu ya, tare da kai mata duka ta ko inarta, amma babu dama. Shi yasa ya tsura mata ido. Takaici na kuma cin shi. Yadda take b'arnan tissue sai ka sha mamaki, domin tana kuka tare da goge fuskarta.
***
Gombe
"Kasan Allah! Na gama zama da kai! Kai masifa ne a tare dani, sanadin ka na aikata abubuwa dayawa, na sab'awa iyayena. Na kuma lalata rayuwar yarinyar da yake ji kamar ta kwanta nabi ta kanta, dama sabida bikin su Nusaiba na d'aga maka kafa, ka cigaba daga inda ka tsaya wallahi ba zan zauna da kai ba." Inji Mamah Inayat tana fadar haka ne lokacin da take kwashe kayan ta daga cikin gidan zuwa Kofar gida, ita da Balkisu da Zehrah, kasa zaune yayi ya kuma shan gaban ta yana mata kallon masifa. "Wallahi ba zaki bar nan ba! Na gaya miki" "ai haba? Toh wai idan na zauna me zaka min? Wani baƙin cikinka ne ban gani ba? Naji wannan ba kome bane saboda nice na baka damar ka wulakanta ni, da yau nabi iyaye na baka isa ka min haka ba, Alhamdulillah Nagodewa Allah da ban gama kashe kaina ba, ka cigaba daga inda ka tsaya Allah zai bi min hakkina." Shiru yayi kamar wanda yake nazari can kuma yace mata. "Kiyi hakuri autar Malam! Na sani ban kyauta miki ba, don Allah karki bari wani abu ya lalata zaman mu, sannan ki bani gidan da Inayat ta gini mana..." "Ai dama ba zaka sauya ba! Ba zaka tab'a sauya ba. Zama da kai itace mafi girman kuskuren da na aikata." Daga haka ta kwashi kayanta ita da yaranta aka zuba a J5 da Dr Ishaq ya kawo mata dan kwashe kayanta zata koma sabon gida.
***
Kashare.
Amai nake sosai, kamar yan hanjina zasu yi waje, da sauri Sister Khady tazo ta rike ni! "Amma baki jin magana, sai da na gaya min ki hakura da zuwa aikin nan, kika ki toh gashi daga shigowar ki." Wani daki ta kai ni, tare da kwantar dani a gado, can sai gata da kayan aiki ta saka min ruwa da allura, har zata fita na rikota. "Don AM bored da wannan wulakantaccen cikin,.Please And please ki raba ni dashi wallahi bani son abin cikin..." "Sake min hannuna! Ai kece wulakantacciyar, wallahi kika kuma zagin cikin jikinki sai na mare ki. Wacce bata san ƙaddara ba, ke jin ki ban da wannan cikin meye zai janyo rigimarki da Malik? Toh tsaya ban da Allah ya soki da arziki da yasa aka ɗauko ki a mota kika kwana a cikin gidan shi da ya biya bukatarshi dake cikin ya bayyana me zaki cewa mutane? Ki godewa Allah da ya kawo cikin ta sanadin aure da wallahi sai kin gaya musu, yadda kika dauko magana babu sanin iyayenki, poor lady kawai wacce bata san akwai Allah ba." Juya mata kai nayi ta Karachi masifarta ta barni a d'akin, ina shashekar kuka. "Insha Allah Malik sai na rama, sai na sanyaka kuka sai na raba maka hankalin ka, sai na zame maka fitina ni wallahi sai na maka rashin mutunci idan ka shiga tarkona" haka nayi ta masifa ni daya na, babu wanda ya tayani, ina cikin damuwa sosai cikin wata biyu zuwa uku ya hanani rayuwa, kome nawa a takaice. Ga yunwa amma bana son cin abinci, a hankali barci yayi gaba dani, sai da nayi barcin awa daya kafin na farka, ina farkawa nayi gamo da abinci, jikina har rawa yaƙe, sabida yunwa, ina ganin abinci kamar zan fada ciki, abin haushi kuma ba zan iya ci ba. Zuba min tayi sannan ta ajiye min a gabana, na fara ci da cokali, kallona tayi cikin tausayi sannan tace min. "Don Allah! Ki daina danganta cikin jikinki da suna mara amfani, wallahi ina matuƙar kaunarku da cikin, kiyi hakuri ki rika mishi Addu'a." "Wa zanyiwa addu'a? Ba dai wancan Azzalumin ba?" Tsaki Khady tayi, sannan ta cigaba da cewa. "Ni ba da baban su baby nake ba, da baby nake. Addu'arki karb'abiya ce, ki cigaba da Addu'a Allah zai tsare miki Yaranki da rayuwarki." Gyada mata kai nayi kawai, sannan na cigaba da cin abincin da ba wani abu bane, faten tsakine wanda yaji tsami da yaji. Sai Yar gauta a ciki. A hankali na warware, kuma ina mai zuwa aikina babu laifin kunsan yanayin aikin kauye ba kamar na cikin gari bane, da mutane suke turiruwan zuwa, na nan kuwa basu cika zuwa ba idan ba matsala ta afku ba. Cikina ya hanani wasu abubuwa, kamar yawan magana yawan cin abinci sai lokacin da yunwa ya addabi rayuwata zan ci, dan haka na tsiri azumin Alhamis da litinin haka yayi matukar tasiri sosai, wutar da take ci a zuciyata ta rage karfinta, sai dai k'iyayyar MALIK tana nan daram dam, domin idan da za ace min na harbe mara mutunci zan aikata mishi.
A yanzun nafi mai da hankali na, gurin ibada da aikina. Sosai hankalina ya kwanta kuma na sami nutsuwa yadda ya dace, dake an bani hutun dan laulayin da nake, ina cika wata uku aka cigaba da turo min kudina, dake Allah yayi ni da tsoron bashi ban ci bashin kowa ba, dan maneji nayi tayi da rayuwata, dan abincin da nake ci Khady ke kawo min, dake bana son warin girki..
***
Abuja.
"Ammyn don Allah kiyi hakuri! Ki sanya shi a cikin addu'a, wallahi bayin kan shi bane." Kallon Mahnoor tayi sannan ta sake murmushin takaici kafin tace mata.
"Babu ruwana da Malik! Nace suyi gwaji ko shine da matsalar rashin Haihuwa yaki, nace yayi aure yaƙi! Toh me zan mishi? Me zan kuma ce mishi? Allah ya ganar dashi yasan tutund dafawa, ƙafin lokaci ya kure mishi."
***
Kallon shi take a nutse, tana kuma girgiza kafarta, tana jin a ranta me zata yiwa Malik ya zama nata ita ɗaya. "Ina son yau na fita yawo!" Kallon ta yayi cikin nutsuwa sannan yace mata. "Akwai kudi a wancan gurin ki dauki abin da yayi miki, ina sauri ne akwai wata mata..." Fita tayi daga dakin bai kawo kome ba, kawai yana tsaye yana gyara neck ties din shi, ta baya tace mishi. "Honey me kace ma?" Allah Sarki ba tare da ya damu ba, ya juya kawai matar nan ban da Allah ya takaita kaiwa ta kai mishi wukar hannunta a kirjin shi, cikin zafin nama yayi baya tare da zaro idanu waje, ta kuma kai mishi yanka, Allah ya bashi Sa'a ya cafke hannunta ya murda sai da wukar ta fadi. Cikin sauri ya kai mata wani irin mari. Sai da ta kifa da hancinta, sannan ya tsallaka ta yayi ficewar shi daga gidan. Sai da ya bar gidan ya kuma ji tsoronta. Dan haka yana isa inda zasu hadu da matar dan kasuwancin da yafita.
Tunda ya fita bai dawo ba, ashe wannan marin da yayi mata suma tayi, bata farka ba sai wajen karfe hudu na yamma, tana shafa wuyar ta, cikin tashin hankali ta duba wayarta, Number boka ta kira bayan sun yi waya ta gaya mishi halin da take ciki, kashe wayar yayi haka tayi ta niman shi wayar baya shiga. Dan haka ta dauki abaya ta saka a saman kayan jikinta ta fita, ko Allah zai sanya ta haɗu dashi. Haka ta gama yawo bata ganshi ba. Kamar zata yi hauka. Tana tafiya tana kuka dan tasan yana can yana sharholiyar shi da mace. A hanyan dawowa ne saura kadan motar wata mata ya bugeta, sai da ta koma gefen hanya, bata ma lura da matar ta tsaya ba, sai da tace mata. "Yar Najeriya ce?!" Jin Hausa a bakin matar yasa Zeeh ta tsaya tare da goge fuskarta, ta sake wani irin kuka, tana cewa matar."eh daga Bauchi nake?" Murmushi matar tayi sannan tace mata. "Toh kukan na meye?".ai kamar wacce ta zagi Ubanta nan ta kuma rushewa da sabon kuka tana gaya mata ai ga abin da mijinta yayi mata,. "Shigo na kai ki gurin wasu yan Turkiyya! Zasu share miki kukanki, daga yau babu ke babu kukan d'a namiji." ✍🏽 Don Allah kuyi hakuri...
*_KOME DA LOKACIN SA_*
https://my.w.tt/T79AmcI3Hab
Chapter 15
Na MrsUsman400
I am the master of my fate: I am the captain of my soul.
Free book
"Karki damu! Zasu share miki kukanki! Daga yanzun har zuwa lokacin dake kika ji kiyi kuka dan kanki." Kallon ta Zeeh tayi sannan tace mata. "Me yasa kika ji ko taimake ne? Ko kina dana da wata manufa akai na ne?" Cike da mamaki matar take kallon Zeemalik, sannan tace mata. "Ok sauka tunda bai miki ba." Kallon matar Zeemalik tayi cikin gaggawa, sannan tace mata. "Zan bi ki, amma ki sani ba zan dauki cin amana ba!" Murmushi matar tayi sannan tace mata, "suna na, tabawa Jan daga Barikin Ladi na Jos." "Zeenat MALIK! Mr Malik Mai Nassara, dan former vice president, Aliyu Mai nassara Katagum!" "Wow ashe ina tare da matar matashin mai kudin nan ne, nima mijina yana nan, Dr Kashim Indimi. Da fatan alaƙar mu zata kara karfi." Murmushi Zeeh tayi sannan suka yi tafiyar awa guda kafin suka isa wani ƙaramin gari a can gaba da cikin garin London, sannan suka nufi wani gidan katako, suka shiga a hankali bayan sun ajiye motar su daga nesa, suka sami wata tsohuwar mata, sanye da kaya bakakke. Tana rike da wata irin ruwa mai yauki, tana zubdawa. Cikin tsawa matar ta fara magana."Dışarı çıkın ve içeri girmeden önce ve giydiğiniz siyah kıyafetle işiniz bittiğinde kıyafetlerinizi çıkarın." (Ki fita sannan ki cire kayan ki, kafin ki shigo min, sannan idan kin gama ga wancan bakaken kayan ki saka.) Tab'awa ta gaya mata, da sauri Zeeh ta cire kayan, tana kallon matar, ta dauki bakaken ta saka, sannan ta tsaya a tsaye. Kallonta matar tayi sannan tace mata, " Kıskanç mısın? Kıskanç mısın? senin Boğaz ağrın var! Bunu senin gözlerinden anladığımı söylemeden önce bile! Ama birkaç gün önce kaybettin Buraya gelseydin, kocan asla hata yapmazdı. , ne hatırlayabilirsin! Unutma, kariyerime başlayacağım" (Kina da bakin kishi? kina da mugun kishi? kina da ciwon kishi! Tun kafin ki fada na fahimci haka daga idanunki! sai dai kinyi asarar kwanaki da suka gabata, da ace nan kika zo mijinki ba zai tab'a Kuskure ba, kin jagoranci mijinki da aikata B'oyayyen al'amari, kafin nayi miki aiki a cikin kwanakin da kika yanka kanki kafin zuwan ku nan, meye kika iya tunawa! kiyi maza ki tuna dan zan fara aikina,) tabawa ta gaya mata, a hankali ta d'ago kanta, ba tare da cewa kome ba, haka tayi ta tunani. Shiru tayi tare da sake ajiyar zuciya sannan tace mata. "Eh gaskiya na manta, amma Ni koma maye matukar zan mallake shi bani da wata damuwa "
"Kötü iblisler ve şeytanlar gelin ve hizmetçinizi çağırın, bu işe, kötü ruhlar, hizmetçinize gelin, yardımınıza ihtiyacı var, Adem'in kanıyla sarhoş olacaksınız, hayvanların kanını içeceğiz."(Mugayen aljanun da mugayen shaidanu, ku shigo kirata baiwar ku, wannan aikin,mugayen ifiritai, ku tawo ga baiwarku tana bukatar taimakon ku, Za'a shayar daku jinin Da Adam, zamu shayar da ku jinin dabobbi" wani irin iska ce ta tashi bak'ikirin. Tare da wasu irin tsuntsaye, dakin yayi bak'ikirin. Washewa dakin yayi tayi maza ta kalle ni cikin rawan murya tace."me kika aikata? Kin zubda jinin innocence lady! Me yasa me yasa! Toh wasu ifiritai sun dauki ruhinta. Amma dole ruhin ishinainaaaah Ruhin ishinainaaaah ruhihhhhhhhhhhhhhhhhhhhh Ruhihhhhhhhhhhh... Ishinainaaaaaaaaaaaaaaah ta'alla....Azbatuuuuuu hubbbukaaaa.". Haka tayi ta ihu tana kiran shaidanun aljanu, kafin kace kwabo garin ya haɗa wani tsawa tare da duhun ya karaɗe garin da suke, dakin ya dauki wani irin sanyi me had'a wani irin sanyi, kamar kankara, saukar wasu irin abu dimm dimm! "Bukatar ta ya biya, sakamakon Mantawa da uwar shi tayi dashi babu addu'o'in, ta manta da kiran Allah, mu kuma haka muke! Zagayayyen bakar ƙaddarar ta faɗa mishi karki kuskura su hadu da juna su, domin kome zai lalace daga
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 7 Chapter of 22