Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
kawo min dan ta kome da lokacin sa, lokacin da ta amsa ta manta zata biya, idan na tuna mata sai ta kau da kai wai na yafe mata shine Allah ya matse min ita yau ta kawo kayanta sun mata yawa, wai dan renin Hankali wai na biya, Ni kuma ba zan biya ba, tayi lokacin ta nima lokacina ne yanzun" kallon su nayi sun bani sha'awa, yadda take sakewa da yaran sai ta tuna min da Mama, murmushi nayi sam na manta da Dr Ishaq a waje, sai da Haysam yazo yace min. "Ammah Anoosh, kin manta da bakon ki fa." Dafe goshi nayi sannan mike nace mishi, "don Allah kace yayi hakuri, yaje kawai."  "A'ah kace ya shigo" kallonta nayi ta ce min. "ba ayin haka!  Ki tawo da mutum ki barshi yanzun kuma kice ya tafi." Fada tayi min sannan tace na wuce na sauya kaya sai na fito. Wucewa dakin nayi na fara gabatar da sallah sannan nayi wanka na sauya kayana, sannan na fito na same shi har lokacin yana zaman jirana, sai hira suke da Ammyn, murmushi nayi mata. Ta harare ni. Sannan tace min."Yanzun yake gaya min ashe kun san juna tun a gombe,. Shine kika bar shi a waje."  Sunkuyar da kai nayi tare da addu'a Allah yasa bai sake baki ba.  "Eh! Hmm!". Zan yi magana yan makaranta suka shigo da mugun gudu, tare da hayewa cinyata, "Amma yau munyi tuwatu! Da bulutu. Hal muka jana oton wannan bad man da yayi hurting dinki, ya m caki kuuka." Zaro idanu nayi tare da toshe mata, baki kallona Ishaq yayi cikin nutsuwa, tare da tabbatar da zafin haushin abinda Malik yayi mata, mik'ewa yayi zai fita, ya kalli Madam Azizah yace mata. "Ammih zan tafi, Yaran ya sunan su?" Itama jikinta yayi mugun sanyin tace masa. Namijin Aliyu Anoosh Macen Rukayyah Anoosha! Baki gaya mishi sunan su bane?" Ta jefo min tambayar,"a'ah em na ga" murmushi tayi sannan tace min, "ki nutsu ki  rakashi." Yadda tayi maganar ya sani fahimtar ranta ya b'aci, ina raka shi waje ya juyo a fusace, kamar zai mare ni, sai da nayi baya kad'an, " me kike nufi? Mahaifiyar shi ce fa! Kike gayawa Yarki ta tsane Ubanta, dama yayi miki shaidar rashin tarbiyya! Kuma kin nuna hakan! Wannan ba halin Inani bace, Inani ta rasu, mahaifin ta yana me yafe mata, haka ta tarbiyyar ta da Yaran da suka sadaukar da farin cikin su domin goge laifin Mahaifiyarsu, amma ke har kin sami damar, kara aikata abinda wancan Mahaifinki ya aikatawa kanwar Mahaifiyata, wallahi kinci darajar auren dake kanki, da sai na miki shegen duka. Sakarya kawai!" "Eh naji ina ruwanka! Kamar yadda ya ja min tashin hankali wallahi nima sai na rama, gwara tun wuri ka juya kabar nan." "Ni kike gayawa magana?" Murguda mishi baki nayi na juya zan tafi ya dawo dani tare da falla min mari, "na hukuntaki a matsayina na dan uwanki, ki jira kiga yadda zanyi dake, a cikin Asibiti daya muke ba, zaki gane baki da hankali. Sakarya an gaya miki. Kuma ki je ki goge haukar da kika koya mata ko kuma na gayawa Itama Maman shi tasan da sha-sha-shar da suke zaune da ita, wannan rashin kunyarki shi zai ja miki tashin hankalin a rayuwarki tunda baki horu da abinda Malik yayi miki ba.". Yana gama fadar haka ya juya yabar Ni cikin zubda kwalla. Dan na bashi haushi inji shi. Ni kuma ban ga abin jin haushi ba. Koda na dawo, cikin gidan na goge fuskana ta, bani labarin yadda ta dawo da Ishaq abuja tayi sannan cikin nasiha, ta shiga min fada, tare da nuna min illar muzanta mijina, kasa hakuri nayi sabida har yanzun ina jin zafin marin da Ishaq yayi min,  a hankali na bata labarin irin wulakancin da Malik ya min, amma ban gaya mata sunan shi ba, cikin kuka nace mata. "ammyn tafiya yayi ya barni ban san wanda ke kaina ba, sai da na kwana na wuni ban san meke faruwa ba, Karshe mahaifina ya kore ni, bayan ya aureni a wulakance, Mahaifinta ta rasu Sabida bakin cikin abinda ya faru, wai don Allah idan ban gina k'iyayyar shi a zukatan yarana ba dame zan fanshe abinda yayi min, nifa baki daya ya lalata min, tare da sanyawa kowa ya guje ni, taya bazan rama abin da yayi min ba." "Amma ayita sara ana duba bakin gatari kiyi hakuri da abinda yayi miki, sannan ki saka a ranki zaku shirya. Mrs..." Inji Mahnoor, takaici ta kara min dan haka ta juya tare da ɗaukar yarta, sannan tafita tana mana sallaam, miki min wasu kaya tayi. Sannan tace min. "Wannan man shafawa ne, sai Vitamin E. Kingan su ba sha ake ba, toh zakina shafawa ne da bai, musamman face dinki, sai kuma. Wancan feminine. Shi na tsarkine.". Jan hannuna tayi muka fita cikin dariya tace min "wai! Kice Yayana bai miki ta wasa ba first night! Wai har na hango irin wulakancin sa yayi miki, shi yasa nake saka Ammyn ta haɗa miki har da maganin gyaran jiki domin kafin ya dawo ko ina ..." "Allah yayi min tsari da rayuwa da mutumin da bai san ciwon kanshi ba, kiyi hakuri, ko duniya ta rage daga ni sai shi, bazan koma gare shi ba, Ba zan tab'a ba, Malik ya cuce ni! Kiyi hakuri da abinda na fada amma, dan uwanki ba abokin rayuwata bane, tuni na manta da Pagen shi, don Allah idan kina son na cigaba da zama a cikin gidan nan ki bar kawo min zancen Malik dan na manta dashi baki daya, na manta da rayuwar shi. Nagode" na juya a hankali tare da barinta a tsaye. Tana mamakin abinda na gaya mata.🤦🏼‍♀️ Na gaji... *_KOME DA LOKACIN SA_*   https://my.w.tt/xAclmmBiXab             Chapter 30 I think if you do something and it turns out pretty good, then you should go do something else wonderful, not dwell on it for too long. Just figure out what’s next. Koda na shiga d'akina, kiran Khady nayi na labartar mata kome! Kai ban tab'a ganin b'acin rai irin na ranar ba, ban tab'a ganinta cikin damuwa irin na ranar ba, tayi min fadar da ko Mamah idan tana raye ba zata min ba, sannan ta kawo min misalai da yawa akan halin da nake ciki, da kuma yadda Mamah tayi tarbiyyar mu, ko sau daya ta taɓa nuna mana mu wulakanta baban mu, yadda take maganar sai naga tabbas ban kyauta ba, dan haka nayi kokarin bata hakuri amma ina tayi fushi. Haka nayi ta damuwa akan halin da nake ciki, har dare. Bayan nayi sallar isha na daura da shafa'i da wutiri, sannan na kama yaran nayi musu wanka tare da saka musu kayan barci. Na kwanta a tsakiyar su, ina nazarin abinda na aikata yau. na jima a gurin kafin barci yayi gaba dani. Tunda na fara barci nake wani irin mafarki, na firgici amma dake kafin nayi barci ina azkar, sai ban ji tsoron mafarkin ba sai dai yadda naga wata mata da MALIK, hannunta cikin jini, tana rike da wuyar shi ta hana kowa kusantar inda ya ke, ya sani firgita har zan farka Naji kamar an danne ni, sunan Allah na shiga kira, ba kakkautawa, sai ji nayi an d'agani, a hankali na bude Idanuna naga kofar dakin a bude, mik'ewa nayi cikin addu'o'in niman tsari, na shiga ban daki nayi alola ina fitowa na kuna wutar lantarki dake d'akin,  karfe biyu na dare, yadda sallar nafilla nayi, ban fasa ba ban kuma daina ba, har karfe uku saura na mike akan abin sallar na koma gado, na jima ina tofawa yaran addu'a, sannan na kwanta, zuciyata ta samu nutsuwa, babu wani abinda zai dame ni... Washi gari har sai da na kusan makara, dan kafin na tashi bar masu kula da yaran sun zo sun dauke su, ina barci. Jijjiga ni Anoosh yayi tare da cewa. "Ammah aduwa!" Da sauri na bude Idanuna, na kamo kan shi nayi mishi Addu'a sannan na kira Anoosha itama nayi mata, kafin suka fita. Na koma na kwanta yau sai karfe biyu nake da aiki dan haka na kuma mai da kai naja Ragona da tushe. Tunda bani da fitar wuri.      *** LONDON Kura mata ido yayi, suka kwance. Ta wani narke a jikin shi, ga zafin da jikinta yayi, duk ta sake mishi har tausayi ta bashi, sai dai haka ba zai hana shi niman mace da zata bashi abu uku ba. Juriya a gado, abincin da zai rike tumbin shi sai kuma haihuwa. Su abinda zai sanya ya nimo Inayat! Dole ya karasa cin Sadakin shi. *Haba Malam ka ci sadakinka da?* Wani bata rai yayi kamar yana magana da wani ne, har da hararar gefen shi.  A hankali yace . "Wannan da magani nayi shi so nake naji yadda kalar ta yake." Yadda yayi maganar a sanyayye sai ya baka tausayi. Sai da yayi dogon nazari kafin ya, yanke shawarar karshen sabon shekara, Insha Allah zai tafi yaga Ammyn shi. Dan yana matuƙar kewar shi, janye jikin shi yayi daga na Zeeh, ya zauna tare da kunna asalin wayar shi da yake da number yan gidan. Ya jima yana kallon yadda take yi kafin ta kawo wuta, hostpot ya bude na wayar sannan yayi connect din shi da wifi na gidan, abin da ya fara dubawa sakonin gida, tare da hotunar kanen shi, a hankali ya rubuta a Status din shi na Whatsp. *Ina kewarku! Ina kewarta! Sosai!* Tweeter ya duba yaga rubutun Ammyn su, murmusawa yayi sannan ya kuma duba sakon Hajnan! Kafin ya bude sakon, yaji an kwace wayar tare da kallon shi, wurga wayar tayi a cikin ruwan da yake glass cup, juyowa yayi zai mata magana ta kwantar da kanta a kirjin shi. Dole ya hakura, ba dan kome ba sai dan wata Mahaukaciyar hikimar da aka musu, wai zata iya daukar ciki. Shine aka kafa mishi sharudda, wanda ita ta sanya likita ya kafa mata, ba wai likitan dan kanshi ba, asalima ta kirkiri wannan al'amarin ne dan ta raba mishi hankali gida biyu., Kuma hakan ya faru, sai dai ko sati ba ayi ba ta soma zubda jini, dole suka nufi asibiti, koda suka je aka ce mahaifar ba zata iya rike d'an ba komi kankantar shi, dan haka ya haifar mata da zazzabin da ciwon jiki tare da cikinta zuwa mara.  Kwal kwal tayi mishi da ido ya bude mata hannun shi ta shiga jikin shi. Dake tana yawan shiga damuwa yasa likita bashi shawara a karo na biyu, da ya bata lokacin shi sosai, domin haka ce zata rage mata raɗaɗɗin da take ji na rashin haihuwa. Haka dai suka kasance har yamma likis, sannan ya dauke ta suka fita yawo,tun a gurin shan shayi taga wata baturiya, tazo kusa dasu, tana kallon MALIK. Har zata wuce sai ta dawo tace mishi. "Mr MALIK Aliyu! Kaman kaine naga BBC sunyi hira da kai ko?" Murmushi yayi sannan ta mika mishi takarda ya saka mata hannu, zuciyarshi daya ya amsa tare da saka mata sannan suka kuma gaisa tare dayi hoto. Wannan abun yayi mugun bakantawa Zeeh rai dan haka ba tare da suna ganinta ba, ta dauki daya daga cikin kofin da suke gurin ta saka a kasar tabirin, tayi ta kwalawa gwiwar ta, har matar tayi tafiyarta, sannan Malik ya nufi gurin biyan kudin coffeen da suka sha. Koda ya dawo ya mikawa Zeeh hannu, ta mike tana d'aga kafa daya ta nemi zuɓewa kasa,r daukarta yayi tare da nufar gida, dukda tana jurewa bata son ya fahimci halin da take ciki, bai hanata jin ciwon gwiwar ba, dan ji take kamar kafar ba nata bane, suna isa gida ta fito daga motar abu ya gaggara. Dole ya duba gwiwar ta kumbura, kallonta yayi cikin nutsuwa sannan yace mata. "Me kika aikata?"  Kallon shi tayi na wani lokaci, kafin ta kauda kanta hawaye na zuba, juyawa yayi suka nufi asibiti, dakyar aka mata gyaran gwiwar da kokon gwiwar ta goce baki daya. Koda suka dawo gida, nan ta samu damar juya shi sosai. Domin shi yake mata kome, minti ɗaya zata fara kiran shi, ga aikin shi, a lokacin suka kuma dinkewa da Tabawa inda ta buge da koya mata girki tana baza sharri a gidan tare da saka ido, akan damuwar MALIK. Ranar ya dawo da yamma, ya zauna a falo ya kalleta yace mata. "Baby! Mamar baby. Allah ya bamu Haihuwa koda daya ne mu samu." Dai dai tabawa zata shigo gidan kenan, dan haka ta tsaya na wani lokaci, kafin taji Zeeh ne kuka. "Ince kaga bana Haihuwa shine kake gaya min magana, na gode." Wani tsallen dad'i tabawa taji, "Dama na gaya miki kome da lokacin sa, yanzun lokacina ne. Zaki ga yadda Sa'ida zata zo tayi ta Haihuwa." Dan haka ta juya tabar gidan ya nufi gidan Lilih ta zauna a gaban Lilih ta koro mata jawabi. Kallon Tabawa tayi, tare da lumshe idanun ta, ta jima tana wasu sambatu, kafin ta bude idanunta jajjur. Har da ruwan kwalla, muryanta na rawa tace. "Karki tura Yarki da kika daura buri akanta rayuwar Malik! Domin matar shi tayi nisa, kuma zata iya kashe ta, ba tare da kin mata kome ba, ki kyaleta lokacin ta ne, tana tab'a kowa zata tab'a wanda zai dame ta, domin akwai burin da ake niman tagazawar wata akai, sai dai al'amarin da kamar wuya domin Malik ya samu abinda yake nima. Ki rabu dasu. Karki saka rayuwar Yarki cikin damuwa, ki barta zata sami mijin da zai sota koda bai kai Malik ba arziki ba." Dake tayi imani da matar, domin kuwa Zeeh tayi nisa djinn suna tare da ita masu masifar taurin kai, karki kai Yarki gurinta, dan zata kasheta ta kashe banza." Godiya Tabawa tayi mata, sannan ta juyo zuwa gida taso ta kure Iskancin Zeehmalik..       Abuja A sanyayye na shiga Office din sa, wanda yake awa na biyu, na samu yana kula da wata mara lafiya, tunda na shiga na zauna daga bayan matar,kaina a sunkuye. Ina jin yadda kwayar idanun shi yake yawo a kaina, na fahimci kallona yake, matar tana fita. Ya tawo inda nake yaja kujeran dake kusa dani ya zauna, sannan ya kura min ido, kaina a sunkuye ya fara bani labarin abin da ya faru, kuka da nake ya sashi mik'ewa, ya dauko min ruwa ya ajiye min. Sannan ya cigaba da cewa. "Malik ya hukuntaki sabida kinyi mishi rashin kunya, ba laifi bane amma cutar da Yarki kike, domin zaki so wata rana tayi miki da'a amma taki. Yana da kyau kiyi koyi da halin Inani, tunda mahaifin ku yake mata abu bata tab'a nuna muku ku rama mata ba, sannan tayi muku tarbiyyar da babu inda zaku zagaya ba a yabe ku ba,  yanzun dai kiyi waya dasu Balkisu, dan tana goyon yaro sai Zehrah da har yanzun Allah bai bata ba, sannan Mariam da Nusaiba." Ya ajiye min wayar sannan ya fita. Tunda na kira Zehrah wacce ya saka mata auta Zehrah,  tunda nace mata "autan gale!" Wani irin ihu ta saka tare da fashewa da kuka, Ni kaina nake, mun jima sannan muka shiga hira, sai da muka yi minti talatin da shida, na kashe ina share kwalla, na kira Balkisu. Itama sunan da Mamah take kiranta dashi. "Mai gadon Zinari! Mai gadon azurfa! Anya me ado da Lu'lu'ah nan ce!"  "Addah Inayat!"  Bakina na rawa nace mata. "Na'am!" Aikuwa muka sake fashewa da kuka, mun jima muna kuka da hira sannan muka rabu, koda na kira Nusaiba wayarta a kashe Mariam ce ta d'aga hankalin ta sai tazo, na lallabata amma fir taki, har muka yi sallama tana jaddada min zata zo.  Koda ya dawo ya same ni nayi kuka har na godewa Allah, nan ya kawo min abinci, ya shiga jana da hira, tare da tambayana yadda na fuskanci rayuwa da kuma cikin su Yan biyu, nan nake bashi labarin tare da yadda kome ya faru, sannan ya gyara zaman shi ya shiga bani labarin halayyar MALIK! Tare da gaya min kyawawan dabi'un shin. Murmushi nayi sannan na ce mishi. "Bana bukatar sanin kome akan shi, sannan nafi bukatar na rabu dashi, nan da watanni uku zuwa huɗu nasan ya cika shekaru hudu da tafiyar shi, sannan kai da ka wakilce shi, dole kai zan kai kotu a raba ni dashi." "Baki da hankali! Karki kai shi kotu! Sabida Yaranki da Mahaifiyar shi, sannan zaki nime malamai akan batun, har idan bai dawo ba, kafin shekaru hudu, aurenku babu shi. Kina da damar auren wani." D'ago kai nayi sannan nace mishi. "ina son zuwa Kamaru! Sabida nima na ga gida."  Murmushi yayi sannan yace min. "Toh amma kuma kinsan dole sai kin samu hutun aiki ai, ko zaki tafi ne sama da ta ka!" Mik'ewa nayi tare da cewa. "Mariama zata zo! Ban sani ba ko zata zo da mijinta ne! Amma ka copy min duk Numbers dinsu zan zo amsa."  Share ni yayi tare da cigaba da cire Numbers din. Juyawa nayi zan fita yace. "Karki kuskura ki tafi baki amsa ba, dan ba zaki ja min Bankad'a a cikin asibiti ba, kowa yana kallon kofar d'akin nan!" "Ai haba!" Na bashi amsa cikin tsokana, mika min takardan yayi, na fita, tun daga ranar muka kulla zumunci, karshe nayi waya da kakan mu, fada sosai nasha a gurin shi, sannan yan uwan Mamah suma suna fatan naje musu, aiki da Uzuri sun rike ni, Mariama itama mijinta yace zai kawo ta, sai ya dawo tafiya, Nusaiba a gida na kirata na hada ta dasu Anoosha. Tayi kuka da nace mata ai sunan Mamah ne. Yadda na mai da hankali akan aikina yasa tare da turani wani jarabawa na sati biyar, ba ni da lokacin kowa sai na karatu, haka ya sanya ni zama busy sosai, muna gamawa aka tura ni, gwagwalada yin jarabawa Dr Ishaq kuma aka tura shi Nsukka, sai da muka yi wata biyar, wanda yayi dai dai da cika shekaru hudu da tafiyar Malik, ai ina dawowa na shiga niman malamai nice ta online, nice turawa ta email, zancen gaskiya a musulunce dai babu aurena da Malik karshe ma aka tabbatar min na nime wani alkali ya shiga maganar, ai kuwa har Suleja muka tafi da Dr Ishaq sabida shine waliyin Malik aka raba auren, tare da bani takardan saki na. Duk da nice na so, sai da nayi kuka  sabida babu macen da zata so sakinta. Bayan kwana biyu nake gayawa Ammyn batun, tayi min fada sosai, har take cewa. "Haba Inayat! Meye nayi miki da zafi! Na zata a uwa kika dauke ni! Zaki iya gaya min damuwarki ashe ba haka bane, baki dauke ni a bakin kome ba, sai dai ki gaya min hukuncin da kika zarta, Misali yau da ace Malik ne ya aureni yayi tafiyar shi wallahi tun wulakantaki da yayi zan sanya kotu ta raba auren ku, wallahi bani da don zuciyar da bazan miki adalci ba. Sabida rayuwarki aka tauye.ba zan taba barin a wulakantaki ba, sabida nima ina da yara mata ba zan so ayi musu haka ba, idan akwai babba a guri yana hana aikata laifukan masu yawa, dan haka wannan ya zama na karshe za zaki kuma aikata hakan,..; shiru tayi na wani lokaci, tana kallona tare da rasa abin cewa, gudun kar na zargi tana son kanta, ta riko hannuna, tare da sauke ajiyar zuciya, tace min. "Don Allah ina niman wata alfarma, Amma don Allah, karki zarge ni da sonkai, don Allah tsayar da wani namijin, Insha Allah zan miki bayani nan gaba, sannan ba zaki kuma yin kuka ba." Shiru nayi sannan nace mata. "Ammyn don Allah! Kiyi hakuri, ba lallai ki fahimci halin da nake ciki ba, rabuwa da mutumin da ya zalince ni, amma ina son ki zame min Uwata har abada, Ammyn a shirye nake na miki duk wata alfarma, ko wacce iri ce. Amma kiyi hakuri kamar yadda kika ce min zaki min bayani nima wata rana zamu yiwa juna bayani. Kiyi hakuri ke uwace me adalci da halaccin, ba zan tab'a mantawa da haliccin ki ba, kin rike ni ba tare da sanin wacece ni ba, Yarana kin mai dasu jikokin ki, kin inganta min rayuwata, Ammyn Nagode sosai, na kowa keda Babbar zuciya irin naki ba. Domin kin min kome, nagode. Ammyn kome da kika gani da lokacin sa, Insha Allah lokaci yana zuwa, kuma zaki ga kome kamar almara." Daga haka na mike na bar gurinta a yau naji ina son kuma shiga dakin Neemrah, a hankali na haura sama, ina zuwa na tura kofar d'akin. Kamar gizo na hango ta tana kallon window, "ki fita min daga cikin d'akin. Kije kiyi zaɓi ranki, kije ki barshi ya cigaba da wanka cikin turb'aya! Ta mutu da burin fidda shi, daga cikin halin da matar shi ta wurga shi! Koda yake ba zaki fahimci halin da Neemrah ta shiga ba, lokacin da taga kwalbar...". Ji nayi ta tunkudani waje ta rufe kofar ta. Muryanta na rarrabewa! "Ki tafi saura taki kad'an ki gane wacece Zeemalik!" Addu'o'in da nayi babu iyaka, na mike da sauri. Zuciyata tana kokwanto, shi fatalwa ce ko Mutum, ganin zan dami kaina na watsar da zancen dan duk abinda zaka hada ni da da MALIK, watsar da shi nake. WASHI GARI Ina isa Asibitin aka ce naje na duba sunana ya fito a cikin masu tafiya London couser na shakara daya....🤣🙏🏼 Don Allah kuyi hakuri na b'ata shiru! Ina busy ne Insha Allah karfe 11pm zaku samu wani amma bai zama dole ba, idan na canja alhajin ra'ayina 😜 sai gobe Insha Allah. Cas *_KOME DA LOKACIN SA_*   https://my.w.tt/7vnB4fQkYab             Chapter 31 Truth, like gold, is to be obtained not by its growth, but by washing away from it all that is not gold. Zaro idanu nayi waje, tare da b'ata fuska, na duba wayata na turawa Dr Ishaq sakon. _Ni fa babu inda zani! Don Allah kayi wani abu mana!_  sannan na mai da wayar cikin jakata, take naga wasu daga cikin mutanen da nazo na samu, suna min kallon kaskanci, ko a jikina da sun san wacece ni a nan Asibitin ba zasu damu kansu dani ba, ina isa Office din mu zan ajiye jakata, naji suna magana. " Baki ga yadda ta makalewa Dr Ishaq ba? Shegen girman kai, sai kace tafi kowa kyau, an naji wai yar alfarma ce?" "Hmm! Hafsat kyale ni da takaici yaushe tazo da za a turata  karatu kasar waje, yau shekaru biyar ina aiki da Asibitin ban cancanci zuwa bane?" Cikin takaici, na juya na kalle su na ga duk sun juya zasu fita nace musu. " Kuyi kokarin ganin kun nemi abinda zaku rufawa kanku asiri ba hassada da kyashi ba, idan da zan bayyana muku matsayina a cikin asibitin nan, toh wallahi baku isa a dauke aiki ba, dan haka kuyi hidimar ku nayi nawa, idan kuma kuna sha'awan a sallame ku ni toh ba damuwa." Daga haka na juya nayi ficcewata, na Barsu tsaye suka jin haushina, Ni ina ruwana.  Su suka sani tunda suke da wahala, duk inda na gifta maganar daya ce daga zuwa an min alfarma har na samu damar tafiya course wannan abin ya musu ciwo, ganin baki yayi yawa ya sani tafiya har office din Admin! Mutumin kirki. "Inayat Ahmad ko?" Gyada kai nayi sannan na gyara zama na, nace mishi. "Baba! Don Allah a janye suna na a cikin masu tafiya London,ni bani son don Allah."  Jan numfashi yayi sannan yace. "Bani ce na zab'e ki ba, Madam Azizah ce ta bukaci hakan. Bani ba sannan idan wani yana jin zafin haka toh ya sami Madam Azizah ba ke ba, dan haka ki kwantar da hankalinki mutane haka suke."  "Shi kenan!" A hankali na bar Office din, dukka inda na gifta na gifta sai anyi magana abun har ya dame ni, babu shiri na bar asibitin na dawo gida. A gajiye na zube a manyan kujerun falon, ina

Chapter 15 of 22