meye a jiki ba, gumi se karyo masa yake ya ciro biro a Aljihun sa, hannun sa na rawa ze sa hannu yaji tace
"that means you accept the terms and conditions i have mentioned?"
Jinjina kai yayi alamar yana ƙoƙarin ya saka hannu tace
"if you are here to spy don't sign this paper"
(idan kazo nan ne dan leƙen Asiri kar kasa hannu a takardar nan)
Ras! Gaban Yusuf ya faɗi, Anya babu wata a ƙasa, yarinyar nan bata san komai ba? Cikin ƙwarewar Aikin sa ya dake yace
"ranki ya daɗe menene Spy kuma?"
Banza tayi masa ba tace komai ba.
Seda Yusuf yayi Addu'a a zuciyar sa sannaan yasa hannu akan takardar.
Ta sa hannu ta ɗauki takardar ta jujjuya ta sannan tace
"signing this paper is like signing on your death contract!!! Jeka sena neme ka"
Tana gama faɗin haka ta miƙe ta bar falon
Ras! Ras!! Ras!!! Gaban Yusuf ya faɗi
A fili yace "My death Contract kuma?"!!!
Ayshercool
07063065680
_*AƘIDA TA*_
*PART1*
_Page 3_
*Story and written by*
_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_
The experience writer of
*ABDUL JALAL*
I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum
Special thanks to my Association Members
Perfect writers Association
Maimaita death contract Yusuf ya dinga yi, ya rasa abunda ya kamata yayi, a hankali ya miƙe ya biyo hanyar da Isa ya biyo da su ya fice.
Abbas yana tare da Isa yana jiran fitowar Yusuf, kallo ɗaya Abbas yayi masa yasan akwai matsala, da ƙyar Yusuf yake ɗaga ƙafarsa, Isa da Abbas suka dinga tambayar sa meyafaru? Amma yaƙi cewa uffan, Abbas yayi wa Isa Sallama ya ja Yusuf suka tafi, be ƙara tambayar Yusuf ba har suka je gidan su Yusuf.
Da suka je gidan ma Yusuf yai mursisi yaƙi faɗa wa Abbas yadda suka yi, daga ƙarshe dai Abbas ya ƙyale Yusuf ya ɗauka ire iren wulaƙanci ya fara fuskanta, dan haka yaita bashi haƙuri yana kuma rarrashin sa kan ya daure kar ya karaya.
Sam hankalin Yusuf baya kan Abbas, gaba ɗaya ƙwaƙwalwar sa ta shiga lissafe lissafe daban2, a karon farko da shigar sa Aiki wannan ne aiki me matuƙar wahala da sarƙaƙiya a gare shi, yana buƙatar nutsuwa da taka tsantsan akan komai.
"Yusuf naga kaman hankalin ka baya kaina fa?"
Yusuf yayi ajiyar zuciya yace "ta yaya zaka samu hankali na, tace ba'a mata ƙarya bata yafe wa wanda yayi mata ƙarya, Nikuma akan ƙaryar ma naje nake aikin, yanzu idan ta gane gaskiya fa?"
Abbas yace "karka damu kayi abunda ya kamata kawai tana ƙoƙarin yi maka ba razana ne, idan kabi a hankali ba zata gane komai ba"
"to Allah yasa?"
Abbas yace "Ameen"
Bayan tafiyar Abbas fa tunani ya auri Yusuf, kasa jurewa yayi seda ya gayawa Umman sa aikin daze jeyi a matsayin direba gidan Alhaji Nasir Daula amma ya ɓoye mata gaskiyar halin yarinyar da sharuɗai da ta saka masa.
"Yusuf wace irin lalacewa ce kana aikin ka gwanin sha'awa zaka koma wani direba?"
"Umma ba lalacewa bace, harkar aiki ce ta kawo haka"
"hakane amma ni bana son sabga da masu kuɗin nan yaran su ba tarbiyya suka cika ba, bana so a wulaƙanta min ɗa a banza, gurin aikin naku babu wanda zasu saka se kai"
Yusuf yace "Umma Addu'arki da goyon bayanki nake buƙata, idan kika soki abun zaki kashe mun gwiwa ne"
Umma ta numfasa tace "shikenan Allah ya tabattar da Alkhairi, Allah yabada sa'a, ka kula da kanka"
"insha Allah umma na nagode sosai"
'yan kwankin nan Gaba ɗaya bacci ya ƙauracewa idaniyar ta, duk motsin da zata yi surar Yusuf take gani, rashin walwalarta da yawan son kaɗai cewa ne yasa 'yar uwatta lura da akwai abunda yake damun ta kasancewar ta me surutu da san hira.
Ramla ta dubi yadda' yar uwar tata tayi shiru tana jujjuya spoon a cikin cup ko sau ɗaya bata kai abunda ke kofin bakin ta ba, bayan shafe kusan mintuna goma da zaman da tayi da niyyar cin Abinci.
"Amal wai me yake damunki haka ne, na lura tun jiya kin zama wata iri"
Amal ta ajiye spoon ɗin hannun ta a ranta tace "Mhmm Yaya Ramla ina cikin damuwa tabbas, kuma na shiga damuwa ne domin ƙoƙarin samo mafita akan gagarumin lamarin dake barazanar jefani wani bigire da be kamata ba, Amma nasan bazaki taɓa bani goyon baya ba" Amma a zahiri tace
"karki damu bana jin daɗi ne kawai"
"Amma yakamata kije kiga likita"
Amal tace "ba abun damuwa bane, zan ware Insha Allah"
Tun Yusuf yana fama da tunani tareda sauraren kira daga uwaɗakkinsa har ya fidda rai, ya fara mantawa ya shiga sabgogin sa.
Kusan sati uku kenan da zuwan Yusuf gidan daga nan Amal bata ƙara saka shi a idon ta ba, wasa wasa abu ya ci gaba da damun zuciyar ta, gashi abu na ta faman damun zuciyar ta.
Alhaji Nasir Daula ne zaune a wani ƙaton falo shida wani mutum wanda zeyi sa' ansa, sukw hira tareda ƙyaƙyata dariya kai da gani kasan akwai kyakkyawan kusanci da fahimtar juna a tsakanin su.
"Alhaji Nasir nikam daughter tunda ta dawo ƙasar nan bata zo mun gaisa ba, kota manta dani ne?"
Alhaji Nasir yace "haba Bulama yaza'ayi daughter ta manta da kai, kawai dai kasan halin ta ne Nason kaɗaici har yanzu a haka take, Amma insha Allah zan turo maka ita har gida ku gaisa"
Alhaji Bulama yace "kana nufin har yanzu bata dena wannan ɗabi'ar ba, ba ta warke ba kenan?"
"kai dai bari kawai, lamarin daughter yana damuna, ace kaf rayuwar ɗan adam be yadda da kowa ba, ba za ta sake da kowa ba, to koni wataran ina ƙasar nan idan bata ga dama ba se tace bata son inje inda take, narasa menene mafita "
Jinjina kai Alhaji bulama yayi yace" "wai shekarun ta nawa ne yanzun?"
"18 to 19, amma menene ma fitar?"
Alhaji Bulama yace "mafita ɗaya ce shine kayi mata Aure, idan har aka yi mata Aure zata dena wannan halin nata"
Alhaji Nasir yace "Aure kuma? Dudu du guda nawa daughter take? Yarinya ce ƙarama kuma waze iya jure halayen ta?"
Alhaji Bulama yayi murmushi yace "kai kake ganin yarintarta idan ka aurar da ita daram zata zauna, samun wanda ze zauna da ita da halin ta abune me sauƙi, semu haɗa ta Aure da Fahad yaron guri na da yake karatu a china, dama bata sanshi ba kaga se a haɗa su, hakan ze ƙara zumunci dake tsakanin mu, kuma kaga tunda ita kaɗai Allah ya baka seka samu 'yan jikoki"
"Masha Allah gaskiya naji daɗin wannan shawarar taka, amma kasan semun bi a sannu idan nace zan tursa sata, za' a iya samun matsala"
"bakomai mu bi komai a sannu insha Allah babu wata matsala"
Suka cigaba da hirarrakin su.
Misalin ƙarfe goma na dare Yusuf yayi shirin sa tsaf ze kwan ta, wayar sa ta fara ringing, Sunan Abbas ne akan screen ɗin wayar, ya ɗaga suka gaisa
Abbas yace "Yusuf ɗazu Isa megadi ya kirani, yace min yarinyar nan ta bada saƙo tace zaka kaita unguwa gobe misalin ƙarfe goma na safe, ta jadadda goma na safen nan dan haka ka kiyaye"
"Shikenan zan je Insha Allah"
Tunda Yusuf ya kwanta ya gagara cikakken bacci, da yaje sallar Asuba sam be koma bacci ba, ya zauna ya ci gaba da lazumi, da sassafe ya tashi yayi wa mahaifiyarsa aikace2, kaman yadda 'ya mace za tayi haka Yusuf ya share ko' ina yai wanke2 yai girkin karin kumallo.
Koda Ummansa ta tashi tayi mamakin inda Yusuf yake gaggawar zuwa, bata son yawan takura masa dan haka ta ƙyaleshi.
Ƙarfe tara dai2 na safe Yusuf ya isa gidan Alhaji Nasir.
Isa na ganin sa yace "kai sannu da ƙoƙari Allah yasa ka ɗore, idan ka ɗore da zuwa akan lokaci saura kuma ƙalubale na gaba"
Yusuf yayi murmushi yace "Malam Isa kenan, Kowace sana'a tana da ƙalubale, sedai fatan Allah ya bamu ikon aikata dai2"
Da yake Isa akwai surutu kaman an ƙona shi aka, haka ya dinga zubawa Yusuf surutu kuma surutun nasa ba'aakan kowa bane se kan 'yar masu gida
Yusuf yace "wai ya sunan ta ne?, nifa har yanzu ko sunan ta ban sani ba"
Isa yace "Ai abune me wuya kaji sun kira sunan ta, ban san sunan ta na gaskiya ba, amma sunan ma dai da' ake kiran ta dashi akwai wuya dan ban riƙe ba"
Yusuf yace "ikon Allah wahalar sunan ta kai ka kasa riƙewa"
"haba Malam Yusuf kaman baka san iyayinku na 'yan binni ba? Wasu sunayen ma karasa sunan tumakine kona taurari"
Ba ƙaramin dariya Isa ya bawa Yusuf ba.
Suna ta ɗan taɓa taɗi, Isa yace "Aff gata can ta fito"
Yusuf ya ɗaga kai ya hango ta, ba ƙaramin kwarjini take da shi ba, taku take na ƙasaita akan wani dogon takalmi, dogon wando ne a jikin ta dark blue da riga light blue me dogon hannu, ta ɗaure kanta da ɗan kwali, amma gashin ta seda ya fito ta baya, fuskarta sanye da wani ƙaton glashi, wayar tace kawai a hannun ta babu jaka se key ɗin mota.
Guri ta samu ta tsaya, yayin da Yusuf yai sauri ya ƙarasa inda take tsaye, gaban sa na ta dukan uku2, yaje gabanta ya ɗan risina yace "barka da safiya ranki ya daɗe"
Bata amsa ba, ta miƙa masa mukullin mota, yasa hannu biyu ya karɓa a hankali ta furta masa Lambar motar da zata hau, kowace mota dake parking space tana da lamba, dan haka be sha wuya gurin gano wadda take nufi ba, abun da ya ɗaure masa kai shine kaddai a haka da wannan shigar zata fita?.
Ya fito da motar, ya fito ya buɗe mata ƙofar Bayan motar, wuce shi tayi taje ta buɗe gaba ta shige ta zauna.
Ya zagayo ya buɗe shima ya zauna yana ta Addu'a, gashi besan inda za suje ba, haka yai shahada ya kunna motar Isa ya buɗe musu gate, taiwa Isa Alama da hannun ta yazo, a guje jiki na rawa Isa ya ƙaraso gefen window ɗin da take zaune ya risina
"kwatanta masa gidan Bulama" ta furta kaman wadda aka yi wa dole, Isa yace
"kina nufin Alhaji Bulama Abokin Alhaji?"
Ɗauke kai tayi tana kallon wani gurin daban, se Yanzu Isa ya tuna bata maimaita magana, ya gyara tsayuwa yayi wa Yusuf kwatancen gidan.
A hankali Yusuf yaja motar suka bar gidan, tunda suka fara tafiya babu wanda yayi wa wani magana, Yusuf ya dinga bin kwatancen gidan da Isa yayi masa, har zuwa ƙofar wani katafaren gida da suka zo ƙofar gate ɗin Yusuf ya kalle ta yace
"Nan ne ranki ya daɗe?"
Shiru tai masa ko motsawa ba tayi ba balle ta kalle shi, ɗan taɓe baki yayi, yai horn megadi ya buɗe ƙofa ya leƙo yana ganin motar ya ja da baya da sauri, ya koma ya buɗe gate ɗin gidan, gidan yayi kyau ya tsaru matuƙa sedai be kai gidan Alhaji Nasir ba.
Yusuf yaje parking space yayi parking, kafin ya sakko ya buɗe mata ta buɗe motar ta fita.
Fitowa yayi shima ko da wani abu dazata buƙata ya fito ya tsaya a bayan ta, me gadi ya ƙaraso cikin girmamawa yana gaishe ta, bata amsa ba tace "Bulama yana nan ne?"
"Eh ranki ya daɗe, Amma bana jin ya tashi"
"Ace masa gani na zo, ya tashi ko be tashi ba be dameni ba, bazan haura mintuna talatin a gidan nan ba"
Da sauri megadin yace "Angama ranki ya daɗe" nufi cikin gidan.
Ba tare da ta kalli inda Yusuf yake ba tace "biyo ni" ba musu yabi bayan ta, Wata rumfa dake harabar gidan me ɗauke da fararen kujeru ta nufa taje ta zauna akan kujera, bayan ta yusuf ya tsaya ba tare da ya zauna ba.
Me gadi ne ya fito tare da wani matashi, matashin na ganin ta ya fara murmushi ya ƙara so inda take zaune
Matashin yace "Manya maganin ƙanana, Dama yaran talaka irin mu na ganin ku?"
Ɗan taɓe baki tayi tace "Gurin Alhaji Bulama nazo, yace yana son gani na, a ce masa gani nazo"
Matashin yayi murmushi yace "Yau kuma a Alhaji Bulama yake ba Daddyn ba, WIDAD kenan, to ki shiga ciki mana ku gaisa da su Hajiya da Iman mana"
Yusuf a ransa ya maimaita "Ikon Allah wani irin suna ne wannan? Widad?
Widad tace "banzo da niyyar ganin su ba a yanzu"
"Shikenan bari ayiwa Daddy magana"
Har ze wuce ya kalli Yusuf yace "am Sorry young man bamu gaisa ba"
Ya miƙawa Yusuf hannu, Yusuf yayi murmushi ya miƙo masa hannu da nufin suyi musabiha, Amma Widad ta kalli Yusuf ta haɗe rai tace
"don't try it"
A hankali Yusuf ya janye hannun sa suka fasa gaisawar, saurayin ya girgiza kai yace "Hmm bari in kira Daddy"
Yusuf a ransa yace "wai ita wannan shikenan kowa se dai yabi abunda take so? Kowa ma wulaƙanci take masa?"
Sunan a harabar gurin, aka turo 'yar aiki da kayan drinks da fruit ta kawo musu, yadda aka ajiye kayan ko kallon su ba tayi ba.
Ba tare da ta kalli inda Yusuf yake ba tace "duk wanda yazo gurin nan ban yadda ka kula shi ba, ba ruwan ka da kowa"
Yusuf yace "angama ranki ya daɗe"
Wani babban mutum ne ya fito sanye da jallabiya fara ƙal, aƙalla zeyi sa' an mahaifin widad.
Ya ƙaraso gurin fuskarsa ɗauke da murmushi, yaja kujera ya zauna ya kalli widad yace
"daughter yau kuma cikin gidan nawa ne baza'a shiga ba?"
"Eh bazan shiga ba banyi niyya ba, yanzu ma Daddy ne yace kana nemana nazo" ta bashi amsa kai tsaye
Alhaji Bulama yace "yanzu daughter ace kina Nigeria amma ki kasa zuwa ki ganni mu gaisa, ko na miki laifi ne?"
Ɗan girgiza kai tayi tace "nafison zamana ni kaɗai ne"
Alhaji Bulama ya kalli Yusuf yace "daughter shi kuma wannan fa?"
"driver nane, ba ruwan ka da shi"
"Shikenan naji ba ruwana da shi, amma idan bodyguards kike buƙata ai za'a iya samo miki, wannan ba abunda ze iyayi miki"
Ba kunya Widad Ta kalli tsabar idon mutumin nan a gadaran ce tace "bana buƙata, bana son kowa ya raɓeni"
Alhaji Bulama yace "A'a daughter sama miki masu tsaron ki yana da mahimmanci, musamman tunda kin san amfanin hakan a tare da ke"
"Bana buƙatar kowa a tare da ni, bana buƙatar saka rayuwar kowa a hatsari, ban yadda da kowa ba dan haka bana buƙatar su"
Alhaji Bulama ya jinjina kai yace
"Amma daughter kin san likita ya hana ki wannan ɗabi'ar kaɗaice kan naki, rayuwa ba zata taɓa yuwuwa a ce kina gudun mutane ba, ya kamata ki samu kiyi aure zaki samu nutsuwa, da kuma farinciki zaki rage kaɗaicin nan"
Karon farko da Yusuf yaga dariya a fuskar ta, ba ƙaramin kyau tayi ba da tayi Dariya ta wani jinjina kai cike da rainin hankali tace
"Alhaji Bulama kenan, an gaya maka rayuwar kaɗaicin da nakeyi tana damuna ne? Karnuka na da maguna suna ɗebe min kewa sosai fiye da yadda mutane zasu yi min, tunda nasan sun baza su cutar dani ba"
Ta miƙe tsaye tsam ta kalli Alhaji Bulama ta haɗe rai kaman ba ita ta gama dariya ba tace
"Ka cire wa zuciyar ka cewar ni widad zanyi Aure, ban yadda in zauna a ƙarƙashin wani ba yana juyani yadda yake so ba, in anyi Aure ana neman Aljanna ne, ni kuma idan nayi Aure sedai Rahamar Allah ta shigar dani Aljannah, ba dan zanyi wa wanda nake tare da shi biyayya ba, na faɗa bazan zauna ƙarƙashin wani ba, babu wani farinciki da'ake a tsinta a Aure, babu komai cikin rayuwar aure se takura da matsaloli, NO MARRIAGE IN MY POLICY!!! Rayuwa ta da nake nika ɗai ta fiye min bazan gayyato wa kaina matsala ba bayan wadda nake ciki"
Ba Alhaji Bulama ba hatta Yusuf maganganun Widad sun ɗaure masa kai, ita kam wannan wace irin zuciya ce da ita haka?
Inda motar su take ta nufa, hakan yasa Yusuf bin ta da sauri ya riga ta ƙara sawa inda motar take ya buɗe mata.
Suna tafe yana lura da ita, ranta a ɓace yake sosai, haka yayi tuƙi a hankali koda suka je gida part ɗin ta ta nufa ba tare da ta kula kowa ba.
Yusuf kam rasa abunyi yayi, ita ba tace ta sallame shi ba ko A'a, ga mukullin mota bata karɓa ba.
Bayan ya kulle motar Isa ya nufoshi yana murmushi yana zuwa yace
"har kun dawo kenan?"
"Eh min dawo malam Isa"
"to yaya, fatan dai bata maka halin ba?"
Yusuf yayi murmushi yace "niba abunda tayi min, ni yanzu damuwa ta ban sani ba ko ta sallameni ba tace min komai ba, ina son tafiya gida ne"
Isa yace "kaje ina? ai zama zakayi setace ta sallame ka"
Harar Isa Yusuf yayi yace
"shikenan ni bani da Abunyi na kaita inda zan kaita meya rage banda in tafi tawa sabgar, mahaifiya ta Nason ganina dan haka bazan zauna ba"
Yana gama maganar ya nufi ƙofar shiga cikin gidan, yana jin Isa yana kiransa amma yai masa banza.
Yana shiga yayi karo da Amal ta taho da sauri zata fkta.
Tana ganin sa ta tsaya tana ajiyar zuciya, taji wani farinciki na ratsa zuciyar ta Yusuf yace "barka da rana"
"Yawwa barka ya kake ya aikin?"
"Alhamdilillah, ga key ɗin mota nan bata karɓa ba ta tafi, ina son zan tafi gida ne inga mahaifiya ta"
Ya miƙawa Amal, be jira me zata ce ba yai waje abun sa.
Jinjina kai Amal tayi tace "lallai wannan besan wacece Widad ba, da alama shima kansa yana ɗan rawa"
Babban abunda ya bata haushi irin yadda be tsaya ko gaisawar kirki sunyi ba.
Koda Yusuf ya koma gida ya sha tambayoyi a gurin Ummansa, seda ya tabattar mata da babu wata matsala sannan hankalin ta ya kwanta.
Tunda ya shiga ɗakinsa yake saƙawa yana warwarewa, abubuwa da yawa sun bashi mamaki yana da tarin tambayoyin da besan me bashi amsar su ba, Amma kusan akwai alamar tambaya akan dukkanin iyalan gidan akwai wani ɓoyayyen abu da kowa yake ɓoyewa a ransa.
"Amma me yasa Widad ta zaɓi rayuwar kaɗaici akan rayuwa da mutane? Me yasa tayi wa Aure mummunar fahimta haka? Me yasa kowa yake biyayya ga Umarnin ta abunda take so, ko da kuwa hakan na nufin ɓacin ran mutane ne?"
Bashi da Amsar tambayoyin nan, Shi ze nemowa kansa amsoshin tambayoyin.
Widad tana kan gadon ta ta ƙurawa sama ido, Hawaye na bin gefen idon ta, Mahaifin ta yayi Sallama a ɗakinta, tana jinsa amma tayi masa shiru, ta miƙe zaune a hankali, ya ƙaraso gefen gadon ta ya zauna ya kalli idon ta yace
"daughter ya akayi ne? Meke faruwa? Abbanki ya gayamin ko gidansa baki shiga ba iyakarki harabar gidan, daughter me yasa?"
"Bana son hayaniya ne, shiyasa na tsaya kawai a harabar gidan" ta bashi Amsa
Alhaji Nasir yayi ajiyar zuciya yace
"Alhaji Bulama ya gayamin yadda kuka yi, Lovely bamu yanke shawarar batun yi miki aure ba sedan na gaji da ganin halin dake ciki, Widad zuciya ta na shiga ƙunci da irin wannan rayuwar da kike yi, kin san larura dake damunki, likita ya hana ki kaɗaicewa, idan kika cigaba a haka fa ze cigaba da taɓa ƙwaƙwalwar ki, dan Allah daughter ki amince da roƙona, kiyi Aure ina son ganin farincikin ki, ko baki yadda da kowa ba, idan dai zaki buɗe ido kiga 'ya' yanki da mijinki zakiji daɗi sosai, dan Allah Widad bani da kowa yanzu seke, se kuma Aminina Bukar Bulama, naso Inkuma samun yara bayan ke, Allah be bani ba, zanji daɗi idan naga 'ya' yanki, please Widad help your Dad, nasan bana tunanin akwai wanda kika tsayar kike so, Amma nida Bulama mun yanke shawarar zaɓa miki mijin da zakiyi Alfahari da shi, wanda ze nuna miki so ya kula dake ko bayan raina, Widad a yau idan na faɗi na mutu bayan Alhaji Bulama bana tunanin Akwai wanda ze kulamin da Rayuwar ki, sannan kinsan a haɗarin da muke daga ni har ke, please Widad ki Amincewa batun Auren nan, am sure if you got true love you will never regret been married, Akwai Soyayya da tausayi a cikin rayuwa da wanda yake son ka, na tabattar da Aure ze wanke miki dukkanin wani pain da yake ranki"
Tunda ta ƙura masa ido ko ƙyaftawa ba tayi, seda ta bari ya gama, ta miƙe tsaye ta fice ta bar masa ɗakin ba tare da tace komai ba.
Alhaji Nasir ya jinjina kai, babu alamar Nasara, Amma ya yanke wa zuciyar sa ze cigaba da lallaɓata yana bin kanta, dan babu wata mafita da ta rage masa se Amincewa da shawarar Alhaji Bulama.
A fili yace "Wannan karon ke zakiyi biyayya ga unarnina daughter, duk wannan abun inayi ne saboda ke"
Widad kam gaba ɗaya maganganun mahaifinta haushi suka bata, kaman korarriya haka ta sakko daga kan bene, ta samu corridor ta tsaya tana zancen zuci, "wai Aure, waya gaya musu akwai Aure a tsarin Rayuwar ta? Taɓɗijan inyi Aure in zauna a ƙarƙashin wani yana juya ni yadda yake so? Ko kuma a haɗa kai da shi a cutar dani, kaman yanda yake ɗabi'ar mutane ne cin amanar wanda ya yadda da su, idan har Akwai mutane masu amana da suka rage a doron ƙasa to sunyi nisa da duniyar da ni Widad nake ciki, waima waye ake cewa za'a haɗa da shi ne Aure? Idan kuma ya zamana yana ɗaya daga cikin mutanen da nake nema fa, hakan yana nufin in masa Alfarma ko in ɗaga masa ƙafa?
A fili tace
"Baze yuwu ba wallahi, ba wani Aure da zanyi, what is their in marriage apart from pains!, hurting each other!, tensions!, regrets and restriction of rights,!! No Impossible i want free life, i can't live under someone's control, i better live alone and die alone than to got married to irresponsible man of now a day's, bazanyi Aure ba, idan har Soyayya da shaƙuwa basa hana ɗan Adam ya cutar da ɗan uwan sa, to tabbas Love doesn't exist is just an imagination, love does not exist talk less of true love, So shike sa ayi Aure, kuma yadda ce ke kawo so ban yadda da kowa ba, Daddy Bulama kayi min katsalandan bisa ga kawo wannan shawarar da ɗaya take da ƙarasa gurgunta rayuwa ta" hawaye ne ya wanke mata fuska sharkaf se ajiyar zuciya take yayin da take maganar.
Ramla da tazo wucewa ta tsaya taji surutan da Widad take yi, ta jinjina kai a ranta tace "to Aure kuma? Waye ze auri wannan Jarababbiyar? Kuma mahaukaciya? Anya Mummy ta san zancen nan kuwa?
Widad kam ji tayi zuciyar ta tana wani irin raɗaɗi, ta fito harabar gidan da sauri kanta ko ɗan kwali babu, dan gaba ɗaya ji tayi kaman tana cikin wuta dole ta fita dan ta samu sassauci,
Tana fitowa harabar gidan ta nufi inda Isa yake tace
"ina direban nan yake, yazo ya fita dani ya bar arear nan dani"
Isa ya kalleta ya kalli kayan jikin ta, mini skirt ne a jikin ta se wata riga armless, gashin kanta a baje kaman ta zare, Isa ya ɗan ƙare mata kallo, a ransa yace "Masha Allah, Allah ya yi halitta anan" yace
"Ranki ya daɗe a hakan za'a fita dake?"
Kallon da yake mata ne da tambayar da ya tsareta da shi, yasa ta ƙara fusata ba zato ba tsammani Isa yaji saukar
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 3 Chapter of 35