cigaba da zama har se lokacin da tace ya tafi.
Saleh ne zaune shida Abbas a wani ɗan madaidaicin falo, Saleh yace
"Neman me kake min ne haka?"
Abbas yace "dole in neme ka ai, Yusuf se alheri yake samu a wannan aikin da yake, ta sakarmasa kuɗi kawai take sakarmasa, seda nayi dana sanin rashin yin aikin nan da kaina"
Saleh yai murmushi yace "tabbas Widad akwai kyauta ta ban mamaki, Sedai kasan aikin da yake a rayuwar sa a hatsari take ko?"
"Nasani amma babban abunda ya ɗauremin kai shine yau naje gidan gurin sa, Amma tana ganina tace kar in ƙara zuwa ko area gidan"
"zata aikata saboda bata da yadda sam, dan haka bata son baƙuwar fuska, gani take kowa ma cutar da ita zeyi, yanzu ya ake ciki game da binciken da yake yi, naga alamar yaron yasan aikin sa, duk yadda kaso ka daki cikin sa ba ze gaya maka komai ba, na jarraba shi rannan da suka zo tare, Amma naga yana da wayo "
Abbas yace " Hmmm, aiki kam yasan kan aikin sa sosai, dan ina tabbatar maka da yana aikin yadda ya kamata yana tattara abubuwa masu mahimmanci sedai har yanzu ban san meye sakamakon binciken nasa ba"
Saleh ya numfasa yace "yanzu abunda nake so da kai shine, ka kawomin rahoton duk binciken da yayi, ka kawomin file ɗin zan miƙa shi ga wannan mutanen dan su sakarmin ɗan uwana dan ina zargin su suka yi poisoning ɗinsa yake kwance ba lafiya"
Abbas yace "yana na'aikaci ina ma'aikaci tayaya kake tunanin ze yadda ya bani kundin binciken sa?"
"wannan ya rage naka kuma Abbas, ni na gama magana kuma ka saka ido ka cigaba da bibiyar sa dan jin yanayin kusancinsa da ita"
"Shikenan zanyi iya abunda zan iya, Insha Allah zan kawo maka abunda ka buƙata.
Ba ƙaramin haushi Yusuf yaji ba da Widad ta hana shi tafiya da wuri, dan haka se bayan isha'i sannan ya tafi gida, bayan yaje gida yaci Abinci yana shirin kwanciya message ya shigo wayarsa
"HAR YANZU MUNA SANE DA KAI, KUMA ZAMU CIGABA DA BIBIYAR KA HAR SEKA BAMU ABUNDA MUKE SO A HANNUN WIDAD"
Tsaki Yusuf yayai ya ɗanyi shiru yana tunanin wai wani abubne wannan haka da'ake son karɓa a gurin Widad, da har ake masa barazana haka?
Ganin bashi da amsa yasa yai kwanciyarsa.
************************************
"Fahad kasan meyasa na kiraka muyi magana a daidai wannan lokacin?"
Fahad ya girgiza kai yace "a'a Daddy"
Bulama yace "Yawwa, na yanke wani hukunci ne kafin ka dawo, shine nake so ka baani aron hankalin ka da kunnuwan ka da kyau ka saurareni"
"To Daddy ina jinka"
"Kasan Widad ai ko? 'yar gidan Alhaji Nasir daula"?
"Eh Daddy nasani"
"Kasan alaƙar dake tsakanina da mahaifinta ko?"
"Nasani Daddy" Fahad ya bashi amsa
"Masha Allah, Kasancewar ka yaro me biyayya shiyasa na yanke wani hukunci wanda nasan ba zaka bijiremin ba Insha Allah"
"Ina jinka Daddy".
"Kamar yadda kasani, yarinyar nan ta gamu da larurar Ƙwaƙwalwa, ta ɗau wata AƘIDA da wata irin rayuwa ta nayi, ta zaɓi rayuwar kaɗaici wanda hakan ke barazana ga lafiyar ƙwaƙwalrwata, shine muka yabke hukuncin yi mata Aure nida mahaifinta, koda Allah zesa a dace a samo kan hankalin ta"
Fahad yace "to ai Daddy ni banga meye nawa a ciki ba"
"Fahad kai muka yanke shawarar zaka auri Widad"
A razane Fahad ya kalli Mahaifinsa yace "Kamar ya ni Daddy, kawai se in auri mahaukaciya kaifa kace bata da hankali ta yaya zan Aure ta?"
"ta yadda na gaya maka mana, aiba hauka take tuburan ba se lokaci lokaci yake tashi, dan haka umarni nake baka ba shawara ba, idan bamu haɗu an temaki yarinyar nan ba waze aure ta da wannan larurar?"
"Amma Daddy a rasa wanda za'a bawa seni? Ina da wadda nake so meyasa za'amin haka? Ta yaya za'a yanke min hukuncin yarinyar da zan aura ba tare da izinina ba"
Cikin tsawa Bulama yace "rufemin baki, na gaya maka wannan umarnina ne, kuma dole kabi gobe in Allah ya kaimu zakaje ku gaisa da ita, kuma wallahi naji wani abu daga gareka wanda be gamshe ni ba, kasan halina sakarai kawai"
A hasale Fahad ya tashi ya bar falon mahaifinsa, ɗakin mahaifiyarsa ya tafi yana kumbura fuska.
"lafiya ka shigomin ɗaki ba ko sallama kana ta haɗe rai kamar tsohon raƙumi?"
"Mumsy kina gidan nan, kina raye za'ayi min Auren dole? Kamarni ta yaya za'a auramin mahaukaciya?"
Ajiyar zuciya tayi tace "Fahad this is out of my control, I did my best to destroy this matter but is beyond my control, ba yadda banyi da mahaifinka ba amma fafur yaƙi, ya zanyi sedai kayi haƙuri"
"Au Hakama zaki ce? Wallahi se yarinyar nan tayi dana sanin Aure na, sena mata wulaƙancin daba'a taɓa yi mata ba se naci mutuncin ta, zata gane kuskurenta"
"Kai Fahad ka shiga hankalin ka, 'yar gidan Daula ce fa, ita zaka ciwa mutuncin? Amma kasan me ci mata mutunci ke nufi ko?"
"ko' yar gidan bushashace ba Daula ba ba ruwana wallahi"
"shikenan kaje kayi abunda ka ga dama kaida ubanka ba me ɗagamin hankali wallahi"
Fuuuu Fahad ya fice ya bar ɗakin yana tsaki
Da safe Yusuf yanata shiri, dan yau gurin aiki yake son zuwa dole yana son ganin Yallaɓai Suleiman, Amma message ya shigo wayar sa.
"ka tabattar ƙarfe takwas tayi maka a gidanmu, zakamin aiki yau"
Yana ganin message ɗin yasan daga Widad ne, haushi ne ya kama shi gaba ɗaya bashi da lokacin kansa sena wannan fitsararriyar yarinyar.
Haka ya shirya a gaggauce ya tafi gidansu Widad, mutan gidan ko tashi daga bacci basu yi ba, tsabar takura irin ta Widad da son nuna isarra yasa take masa wannan ikon.
Wani ɗan ƙaramin lambu dake gidan Yusuf ya tafi yai zaman sa, yana kallon shuke shuke da tsuntsayen dake gurin.
Jin tsayuwar mutum yayi a bayan sa dan haka da sauri ya juyo.
Amal ce tsaye a bakin lambun tana ƙare masa kallo "barka da Safiya Yusuf"
"Yawwa barka" ya faɗa a taƙaice
"Yusuf wai ya naga kana wani baya baya dani? Dan Allah kayi haƙuri da abunda ya faru, wallahi ina matuƙar kishin ka ne"
"Amal dan Allah kiyi haƙuri, ni bana son abunda zesa ki jamin matsala, ki ƙyaleni dan Allah"
"Idan kaga na ƙyaleka to tabbas ɗayan mu ruhinsa ya rabu da gangar jikinsa, ni matsala duk girmanta duk ƙanƙantar ta bana gudun ta, indai akan biyan buƙata tane, kalleni Yusuf me na rasa? Wace tawaye Allah yayimin da ban kai ka kalleni ka karɓi soyayya ta ba, kana ganin irin mazan da suke sintiri a gidan nan da sunan suna sona, Amma na ajiye class ɗina na ajesu a gefe nace kai nake so, me zesa kace baka sona"
"Saboda bana Soyayya, bata gabana babu ita a tsarina, dan Allah ki ƙyaleni"
"ƙarya kake Yusuf kana Soyayya, koma baka yi zaka fara a kaina bazan taɓa ƙyaleka ba, zan cigaba da bibiyar ka sena hanaka jin daɗi muddin baka amince da soyayya ta ba "
"Masoyiyar gaskiya ba zata taɓa faɗar haka ba, ke ba abun yadda bace dan haka bazan taɓa yadda da wannan shirmen ba"
"Yusuf ko nawa kake so zan mallaka maka, in har zaka yadda ka karɓi soyayya ta"
"Shi son gaskiya tsada ne dashi, kuɗi komai yawan su basa siyansa, dan haka Allah be baki arziƙin da zaki siyi soyayya a gurin Yusuf ba"
Yana gama maganar ya juya ya fice daga lambun yana mamakin wannan naci irin na Amal.
************************************
Ramla ce kwance hannunta riƙe da waya tana magana a hankali cikin iyayi
"Abun ƙauna ta, yau kwananka huɗu da dawowa Nigeria, yakamata ace kazo na ganka fa, Allah badan inajin nauyi ba da tuni ni zanzo inda kake in ganka"
Daga can ɓangaren Fahad yace "Am Sorry beb, ina cikin damuwa ne gidan naku ne gaba ɗaya bana son zuwa, Ramla wai Daddy ze haɗani Aure da wata mahaukaciya a gidan ku, Ramlah kamarni za'ayiwa Auren dole? Auren ma da mahaukaciya, kuma Daddy se masifa yake wai se nazo mun gaisa da ita"
"Fahad nasan maganar nan tun kafin ka dawo, ban gaya maka ba saboda bana son ɓacin ranka, Amma ina cikin damuwa Fahad you know I love you" tai maganar cikin damuwa
"easy baby, ki kwantar da hankalinki, idan nazo se nayiwa yarinyar nan rashin mutunci, ni bazan aure ta ba dan ba sonta nake ba, bazan taɓa yadda da Auren nan ba, naga Daddy ya fara fushi, in anjima zan shigo gidan naku in ganta, Amma ni ke zanzo gani Beb"
Murmushi tayi tace "Ohh my God, amma naji daɗi Fahad seka zo".
Ta kashe wayar tare da yin wani tsallen murna.
************************************
Se ƙarfe sha ɗaya na safe tayi miƙa, ta farka daga nannauyan baccin da take, ta sakko daga kan gadonta magen ta yana biye da ita.
Corridor ɗin ɗakin ta tabi wanda ze sada ta da barandar benen, miƙa ta sake yi tana ambaton sunan Allah tare da shaƙar sassanyar isakar dake kaɗawa, haka nan take jin wai irin nishaɗi da bata san dalilin jinsa ba, tsyawa tayi tana kallon komai dake harabar gidan.
Yusuf ji yayi kamar ana kallon sa dan haka ya ɗaga kansa sama, ai kuwa karaf idanunsa suka sauka a cikin nata, alama tayi masa da hannu ya zo, dan haka ya miƙe ya tafi.
Dukda yana jin haushin abunda tayi masa akan kayan daya bata, amma yau yaga fuskarta ba yabo ba fallasa haka nan yaji hakan yayi masa daɗi.
A ɗakinta ya sameta, tana tsaye a gaban madubi ta janyo drower mudubin tana ƙoƙarin ɗakko wani abu.
Idan kunnuwan ta ba ƙarya suke gaya mata ba tabbas Yusuf cewa yayi "Good morning daughter" kamar yadda Daddyn ta yakan faɗa, shiru tayi ta cigaba da duba abunda take nema tsawon wasu daƙiƙu, sannan ta ɗago ta kalle shi tace "Roux taƙi cin komai tun jiya, na rasa meke damunta na bata Madara taƙi sha, ka siyo mata ko cabin ne, in gani in zata ci ban san me yake damunta ba" (wato magenta)
Haushi ne ya kama Yusuf, saboda tsabar wulaƙanci mage ze fita siyowa Abinci.
Bece komai ba ya juya ya fita yana ƙoƙarin ɓoye jin haushin sa.
Yana tafiya ya tuna da Message ɗin da'aka turomasa da daddare dan haka ya samu guri ya kira Oga Suleiman.
Bayan sun gaisa Yusuf yace "Yallaɓai na so in shigo yau in nuna maka report ɗina amma abu ya gagara, Wannan rigimammiyar ta kasa ta tsare ban samu na shigo ba"
Suleiman yace "Aikam dan har na fara ƙorafin, yanzu me ake ciki?"
"Yallaɓai akwai abubuwa na ban mamaki a binciken nan, zan turomaka report ɗin ta Email ɗinka ka duba, Yallaɓai case ɗin akwai sa hannun mutanen dan ban zata ba, sannan karo na biyu ana min barazana wanda ya ƙara tabattar da tabbas ana bibiyar yarinyar nan ana son karɓar wani abu a hannunta wanda ni kaina ban san menene ba"
"Masha Allah, har kayi aiki haka Yusuf? Ka turo zan duba in Allah ya yadda inda yuwuwa zan miƙa report ɗin naka gaba, nasan zaka iya dama bazan can zaka daga kan aikin ba"
"Yallaɓai da karɓar aikin za kayi?"
"karka damu da wannan, ka turomin zan duba dan daga sama ana tambaya ta ina muka tsaya a binciken?"
Yusuf yace "Amma Yallaɓai wai wa yasa ayi wannan aikin ne? Waye yace ayi binciken?"
"Yusuf nima ban saniba, daga sama aka bada order ayi wannan aikin"
"Yallaɓai ya kamata kasan gawa zaka bada aikin, dan abun akwai sarƙaƙiya"
"Karka damu Yusuf, komai ze tafi daidai insha Allah, kamar yadda kace ana maka barazana, duk lokacin da ka buƙaci temako kayi magana, sannan ka kasance cikin shiri ka dinga yawo da makaminka"
"Ina lura sosai Yallaɓai, Allah yayi mana jagora gaba ɗaya"
"Ameen Yusuf Allah ya tsare"
Yusuf seda ya tsaya ya turawa Suleiman aikin sannan ya tafi.
Koda Yusuf ya dawo daga aiken yiwa mage siyayya, ya tarar da uwar ɗakinsa ta fito daga wanka, pink ɗin rigar wanka ce a jikin ta, ta naɗe gashin kanta da towel shima pink.
Zare towel ɗin dake kanta tayi, gashin ta ya zuba a kan kafaɗunta, Satar kallon ta Yusuf yake, tabbas Allah yayi mata halitta mekyau, tana da kyau sosai ga dogon gashi, Yarinya ce sedai izza da gadara, tana kallon Ya dawo amma taƙi kula shi.
Wani ƙaramin plate ta ɗakko ta miƙawa Yusuf tace "ka sa mata cabin ɗin anan, ga madara ka haɗa mata dashi"
Yusuf yai shiru yana sauraren ikon Allah, yanaji yana gani aka sashi haɗawa mage Abinci.
Still dai magen bataci ba se kwanciya da take.
Cike da damuwa Widad ta kalli Yusuf tace "taƙi cin wannan ma, inaga bata da lafiya idan akwai wani private veterinary se mu kaita" ta faɗa cike da damuwa tana sake shafa magen, hakan ya ƙara fito da tsantsar yarintar ta.
"waye ze buɗewa wani private veterinary? Babu wani private veterinary dana sani nidai, yunwa take ji kawai bata ƙoshi ne"
"kamarya? Ina bata Abinci sosai fa"
"Ai kema ba Abinci kike ciba balle magen, kullum abu ɗaya ai dole ta gaji ta dena ci"
Cikin damuwa tace "to me zan dinga bata?"
"Abinci me nauyi na hausawa, amma kullum daga popcorn se madara ai dole ta mutu"
Da sauri ta kalli Yusuf tana girgiza kai tace
"A'a ni bana so ta mutu ina sonta fa"
Gaba ɗaya yau Yusuf cike yake da mamakin yadda take masa magana cikin nutsuwa ba izza, yasan kuma saboda magen ne, dan ya lura tana tausayin dabbobi fiye da yadda take tausayin ɗan Adam, tana matuƙar ƙaunar dabbobi Yusuf a ransa yace "ta wani fannin rayuwar turai ba tayi ba"
"to muke rasa 'yan uwanmu mutane ma balle dabba, idan ta mutu seki ɗakko wata"
"Ni nafison wannan gaskiya, tun ire iren magunan Ammi ne, idan ta mutu zan shiga damuwa"
Shiru yayi yana kallon Widad data sunkuyar da kanta tana shafa jikin magen, magen tayi lamo a jikinta, gashin kanta har rufe mata fuska yake, Yusuf yana mamakin wannan dogon gashin na kan Widad dan har yanzu yana tantama idan nata ne.
A hankali ya matso daf da ita ya shafa jikin magen dake hannun ta yace "Allah ya bata lafiya, don't worry Madam zata warke Insha Allah"
Widad ta jinjina kai, tare da jin ƙaruwar bugun zuciyar ta kasancewar yadda suke daf da juna, ta ɗago idonta ta kalle shi tace "da ina so mu fita zanje Saloon, Amma zan zauna inga yadda jikin nata ze kasance ko zuwa yamma ne semu tafi"
Yusuf ya ɗan ƙura mata ido sannan a hankali yace "As you wish your majesty" ji tayi tsigar jikin ta tashi, wanda ta rasa dalilin jin hakan, haɗe rai tayi tace
"karka sake ka fita kaje ko'ina idan ba nina baka izini ba, ka zauna zuwa la'asar insha Allah zamu fita"
Murmushi yayi mata tare da ɗan duƙawa cikin girmamawa yace "Considered it done Gimbiyar Daddy"
Ya yunƙura ze miƙe Amal ta shigo hannun ta ɗauke da waya, turus tayi tana binsu da kallo, yayin da taji wani abu tundaga ƙafarta zuwa ƙirjinta ya to kare mata wuya.
Da ƙyar ta miƙawa Widad waya tace "gashi Daddy zeyi magana dake"
Widad bata kalle ta ba, bata bata amsa ba ta kalli Yusuf tace "bani wayata akan mirror"
Amal bata kuma cewa komai ba ta juya ta tafi a hasale.
Widad ta karɓi wayar ta kira lambar Daddy, ya ɗaga suka gaisa yace "Lovely meyasa wayarki bata shiga?"
"Jinyar Roux nake, bata da lafiya"
"To Allah ya bata lafiya, dama munyi waya da Daddynki yau baƙonki zezo"
"waye baƙona?"
"Fahad mana, zezo ya ganki ku gaisa dan Allah Lovely banda wulaƙanci ko makamancin haka, shima ɗanuwankine Yayan Ramadan ne, yana nan tafe Anjima Insha Allah"
Nan da nan dukkan annurin fuskarta ya ɗauke ta dire wayar tace
"Ina nan ina jiran zuwan sa, yazo ya sami Widad Nasir Daula, yazo yaga mahaukaciyar da'ake shirin ƙaƙaba masa"
Ayshercool
07063065680
_*AƘIDATA*_
PERFECT WRITERS ASSOCIATION
(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)
https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*Story and written by*
_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_
The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *
I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum
Haƙƙin Mallaka ⚠ : Littafin nan mallaki nane, tun daga sunan labarin zuwa abunda ya ƙunsa, ban yadda wani ko wata ya sauyamin ko yin Amfani da wani ɓangare na labarin ba ba tare da izinina ba, Nagode
https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends
ELEGANT ONLINE WRITER'S
PART1
Page 18
Binta da Kallo Yusuf yayi, ganin yadda ta canza lokaci ɗaya annurin fuskarta ya ɗauke, tabbas akwai drama yau.
"Jeka anjima zamu fita" ta faɗa ba tare da ta kalli Yusuf ba
Miƙewa yayi ya fito daga ɗakin ya nufi hanyar fita, ba zato Amal tasha gabansa wanda ya tilasta masa tsayawa.
"Yusuf ka fara ƙoƙarin tsallake iyaka, Yusuf meyasa baka tsoron Allah ka dinga nuna kai na Allah ne amma baka kyautawa rayuwarka, Yusuf kai mugune mara tausayi baka da tausayi baka tausayina, ko kaɗan soyayyata bata da daraja a idonka, na rasa meye a tsakaninka da Widad, wallahi akan Son da nake maka banƙi komai ze faru ya faru ba, wallahi akanka koni ko Widad "
Girgiza kai Yusuf yayi yace " keya dace a nemawa maganin mahaukata ai, nayi iya ƙoƙarina in ganar dake amma kin kasa ganewa, bana Soyayya bani da ra'ayinki, ba abunda ya kawoni nan kenan ba, ki ƙyale rayuwar Yusuf ta huta, tun kafin in nuna miki ainihin kalata na gaya miki"
"Haka kace?"
"Eh haka nace, ko baki da kunne ne?"
"bayan ƙalubalen dake gabanka saboda Kasancewar ka da wannan mahaukaciyar, ka shirya ƙalubalen da zaka fuskanta daga gareni"
"duk wanda ya dogara da Allah, to ya isar masa"
Yusuf ya bata amsa yasa kai ya fice, ya barta tana mamakin wannan taurin kai irin na Yusuf.
Bayan Suleiman ya gama nazarin abunda Yusuf ya tura masa, yayi mamakin jajircewa da kuma ƙoƙarin da yayi, tabbas Yusuf jajirtacce ne me kuma hikima da iya aiki, amma meye dalilin da yasa Abbas yakeson lallai a ƙwace aiki a bashi? Lallai akwai wata a ƙasa Abbas yana da fuska biyu.
Yusuf yana nan zaune yana ganin yadda aketa aiken su Murtalah, anata shirye shirye da alama akwai baƙon da gidan zasu tara yau, shi dai yana guri ɗaya nasa ido.
Ƙarfe biyu na rana Yusuf ya dawo daga masallaci sallar Azahar, wata dalleliyar mota ta shigo gidan, wani matashi ne ya fito daga motar, jikinsa sanye da ƙananan kaya kallo ɗaya zaka masa kasan ɗan hutune, ya ɗaga kai ya ƙarewa gidan kallo tsaf, su Isa mai gadi suna gaisheshi yana ɗaga musu hannu ba tare da ya amsa ba.
Shidai Yusuf be kula shi ba, sema ɗauke kai da yayi kamar bega Matashin ba, ba zato suka jiyo muryar Ramla ta taho da gudu tana faɗin "Oyoyo my heart beat"
Ba kunya suka rungume juna a gurin.
Fahad yace "I miss you so much Baby"
"I miss you too mine" Fahad yayi kissing ɗinta a forehead yace
"kin ƙara kyau my Ramlat"
"Kyau ai kaine ka ƙara kyau, mutanen Amurka muje daga ciki ko"
Suka shige hannunsu saƙale da juna.
Nura direba yayi tsaki yace "ƙaryar banza burodi a lefe, waisu a dole turawa ba kunya taje ta rungume ƙasurgumin gaddi tana ce masa Baby tir da wannan hali"
Shidai Yusuf bece musu komai ba suka ci gaba da gulmarsu.
A babban falon dake ɓangaren Hajiya Halima aka sauki Fahad, suka dinga hira yana basu labarin Anwar shima ya kusa dawowa.
Fahad ya ɗan ɓata fuska yace "Hajiya wai ina Yarinyar take ne? Ance inzo in ganta karta ƙullamin wani sharrin a gurin father ta jamin magana, danni sam ba'a kyautamin ba da'akace zan Aureta"
Ɓata rai Ramla tayi ta miƙe ta bar falon, Hajiya Halima tace "Aikuwa dai an gama da kai, dan yarinya ce ba tarbiyya ga kuma uwa uba hauka"
"wallahi Hajiya na rasa wani irin tunani Daddy yayi haka, da yasa yake son illata rayuwa ta, nazo ne dai kar'ace banzoba amma sena tabattar da na mata rashin mutunci yadda ko ganina tayi ba zata nuna ta sanni ba"
Amal ta kalleshi a yatsine, sam Fahad haushi yake bata yana ta wani iyayi shi lallai ya dawo daga Turai, indai Widad ce ze gane kurensa ne.
Ba kunya Fahad ya miƙe yace "Hajiya bari inje gurin Ramla, naga tayi fushi"
"Shikenan kunfi kusa ai"
A ɗakinta ya sameta tayi kicin kicin da rai, ta haɗe fuska, ya zauna kusa da ita ya janyota jikinsa yace "haba Baby, meye abun damuwa nifa danke nazo gidan nan, ba dan wata banza ba meye na ɓata rai, ki tsaya kiga matakin da zan ɗauka yau akanta"
"Fahad inajin tsaro fa, su Daddy suna san Auren nan naku, zasu iya tursasa maka fa"
"waye ya gaya miki? Kamarni aina wuce ajin amin auren dole, calm down Baby" ya faɗa yana jan hancinta
Murmushi Tayi tace "bari in shirya maka Abinci a dining, na maka girki"
Kafin yayi magana wayarsa ta fara ringing yace "excuse me Daddy ne"
Ya ɗaga wayar yasa a kunnensa yace "hello Daddy"
"Fahad kaje gurin nata kuwa?"
"Amm.. Eh ina gidan amma ban ganta ba"
"to ka tsaya ku gaisa, sannan yarinyar nan ka bita a hankali bata da cikakkiyar lafiya, kabi a sannu ka kwantar mata da hankali"
Tura baki Fahada yayi yace "Haba Daddy sekace uwata, yarinyar ma ashe mahaukaciya ce"
"ba zakayi ba kenan?
" Naji zanyi "
" idan naji wani abu na rashin kyautawa daga ɓangarenka sena saɓa maka, shashasha wanda be san halacci ba, aiko wani kaga ze Wulaƙanta 'yar Nasir Daula kai me tare matane"
Bulama yayiwa Fahad tatas sannan ya kashe wayar
Fahad yace "kar wannan abun ya ɗaga miki hankali kinji babyna, ina tare dake, nasan matakin da zan ɗauka"
Ta jinjina masa kai suka fito babban falo, Fahad yace "kiramin ita".
Ramla ta nufi part ɗin Widad, a falonta ta tarar da ita tana kwance a ƙasa ta ɗora ƙafafunta akan kujera, mageneta na kan cikinta a kwance, itakuma tana danna waya.
Ramlah tace "Fahad yazo, yana falo yana jiranki"
Ai kamar da kujerun gurin Ramla ke magana ba da Widad ba, dan ko motsi ba tayi ba.
"Magana fa nake miki"
"And then? Ko bayan hauka kuma inada larurar kurmanta ne? Kinyi magan na jiki kin cigaba da tsayawa a kaina, ki matsa daga kaina"
"Amma se ki bani amsa ai, tunda keba kurma bace"
Miƙewa Zaune Widad tayi tace barmin falo.
"Amma...
" ki fice nace, ko Bulama ne yazo da kansa be isa ya tursasani in saurare shiba, kije ki gaya masa ya cigaba da jira idan ze iya daga nan zuwa lokacin da zan fito, idan baze iyaba ze iya komawa ya tambayi Bulama tsarukana, idan ya shirya ɗauka ya sake dawowa, fita ki barmin ɗakina"
Buɗe baki Ramla tayi tabi Widad da kallo, wato ita kullum rashin mutuncinta ƙara ta'azzara yake, ina ita ina zuwa ta Sanarwa da Fahad wannan baƙin saƙo, mussman shi dabe san kan Gimbiyar ba.
Ramla ta juya ta fice ta koma main falo tace "Baby naje yanzu ta tashi daga bacci zata shirya ta fito"
Ramla ta zauna a kusa da Fahad suka shiga hirarsu, tun Fahad yana tsammanin fitowar Widad harya fara ƙulewa.
"Ramlah wai yarinyar nan ba zata fito bane?"
"Fahad baka ga komai ba, indai akan wannan Yarinyar ne, idan ka kuskura ka aureta taka ta ƙare wallahi"
"zan saita mata zama kuwa, dan nafi ƙarfin wata banza ta Wulaƙanta ni, bari inje akwai wani friend ɗina a quarters ɗin nan, inaso mu gaisa ina dawowa"
"to ka fara cin Abincin mana"
"karki damu
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 18 Chapter of 35