ya kamata ku ƙyaleni da maganar nan"
Numfasawa Bulama yayi yace "Amma kin san mahaifinki ma bahaushe ne, kike wannan maganganun akan mazan hausawa"
"da nace ban dashi a ciki ne? Shima badan yayi rayuwar Turai ba he will have the same negative habits on his wife, it seems it is in your genes, Alhaji Bulama daga yarin tata sanina da kai mata nawa ka aura bakwa tare yanzu? Go back to your senses Sir, Am not ready to ruin mad, i don't have interest of getting marriage, i don't know maybe later, but I can't married a man from hausa people, they don't value their wives "
Ba Bulama ba, Yusuf kansa yaji haushin cin mutuncin da Widad tayi wa ƙabilar Hausawa, duk lalacewar Al'umma akwai mutanen kirki ai, Amma ba shida ta cewa, tunda shi ɗan karere ne.
Ta miƙe tsaye tayi gaba abun ta, Yusuf ya rufa mata Baya, yauma har suka je gida ba wanda ya kula wani, sedai da suka koma gidan, a mota ta bar jakarta da wayarta, dole Yusuf ya ɗauka ya bita da su ba dan yana so ba, dan sam baya son shiga cikin gidan, ba ƙaramin tsarguwa yake da irin kallon da mutan gidan ke masa yake ba.
Yanzu kam ba 'a hankali take tafiya ba cikin gaggawa take tafiya, kaman tana son tayi wani abune, ta falon da zata bi ta wuce ta tarar da Mahaifinta a zaune da shi da matarsa, ko kallon su batayi ba tasa kai zata wuce.
"Widad" Mahaifinta ya kira sunan ta ba tare da juyo ba ta tsaya cak, be damu ba ya ɗora da cewa
"Munyi waya da Bulama ya gayamin abunda kika je kika ce masa, ki sani wannan karon dole kibi abunda nake so, bani zan biki ba, am doing all this for your benefit, in the next two Months insha Allah Fahad zezo ƙasar nan, ina son ayi Auren ku kafin ya koma"
Cigaba tayi da tafiyar ta ba tare da cewa Mahaifinta komai ba. Yusuf dake tsaye yana jinsu ya ƙarasa ya gaida mahaifin Widad da matarsa Hajiya Halima.
Ya amsa masa cikin, yayin da Hajiya Halima ta Amsa masa a ciki.
Yusuf ya miƙa wa Mahaifin Widad jakar ta da keys ɗin motar ta, yayi musu Sallama ya fice.
"Yaya Yusuf" yaji an kira sunan sa, tsayawa yayi ya waigo, Amal ce take tahowa da sauri hada ɗan haɗawa da gudu.
"Sannu ashe kun dawo?"
"Eh mun dawo, akwai wani abu ne?"
Ɗan sosa kai tayi tace "dan Allah in babu damuwa so nake ka raka ni Shopping"
"Shopping kuma? Niɗin?"
"Eh amma idan ban takura maka ba"
"ina batun takura ni da nake muku aiki, idan kin shirya kimin magana"
Murmushi tayi tace "nagode sosai Yaya Yusuf"
Shima murmushi ya mayar mata yai gaba abun sa.
(WASA FARIN GIRKI)
Share please 🙏 🙏 🙏
Comment nake so ba sticker ba ko kuma thanks ba, inda suka fi Comment su zasu dinga fara samun posting
Domin gyara, sharhi, kokuma ƙorafi a tuntube ni akan wannan lambar
07063065680
Watpad Ayshercool7724
_*AƘIDA TA*_
*Story and written by*
_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_
The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *
Haƙƙin Mallaka ⚠ : Littafin nan mallaki nane, tun daga sunan labarin zuwa abunda ya ƙunsa, ban yadda wani ko wata ya sauyamin ko yin Amfani da wani ɓangare na labarin ba ba tare da izinina ba, Nagode
ELEGANT ONLINE WRITER'S
PART1
Page 5
Yusuf ya fita yaje yai alwala yai salla saboda lokacin salla yayi.
Widad kam tana zuwa ɗakin ta ta jefar da Jakarta da wayar ta akan gado ta fara safa da marwa a ɗakin ta
"Bulama ina ganin girman ka, ina maka kallon uba amma kana ƙoƙarin ƙetare gona da iri, kana ƙoƙarin tsallake iyakokinka, a tunanin ka yin Aure ze sa in canza ra'ayina? Daddy kunyi kuskure daga kai har Bulama, kuma bazan taɓa bari wannan kuskuren naku yayi tasiri a kaina ba, dole inyi wani abu" haka ta cigaba da surutai ita kaɗai.
Hajiya Halima ta kalli maigidan ta tace "Nikam wai Alhaji dagaske Widad zakayi wa Aure ko kuma yaya? Na kasa gane kan lamarin"
Ɗan shiru yayi sannan yace "Eh hakane, Bulama ya bani shawarar akan cewa muyi mata Aure hakan ne kawai zesa ta canza wannan halin nata, Amma yarinyar nan kin san halin ta da kafiya da taurin kai, ta tirje tace sam bata san zancen ba, Amma a wannan karon bazan canza ra'ayi ba, ina son inga ta dawo da walwalarta, wannan karon dole tayi biyayya ga umarni na"
"Amma Alhaji baka ganin yin hakan tamkar ze ƙara tunzura rashin lafiyar ta ne, zaka ƙara sawa rashin lafiyar ta ya tsanan ta, ko ka manta sharuɗan da likitoci suka gindaya ne akanta?"
Alhaji Nasir Ya numfasa sannan yace
"Shima zaman ta a hakan bakomai ze ƙara mata ba face cigaba da dawwama a cikin damuwa da rashin walwala, akwai buƙatar ko bayan raina Widad ya zama na tana da kafaɗar da zata tada kai, ya zamana tana da wanda ze kula da rayuwar ta"
"Amma Alhaji wa zaku bawa Auren ta? ina fatan wanda zaku bawa yasan yanayin larurar ta? Tunda kaga ba shiga mutane take ba balle a ce tana da wanda take so, kar a bawa wanda besan ya take ba abu yazo ya ɓaci"
Alhaji Nasir yace "Ai ba wani bane za'a aura matan, fahad ɗin Bulama ne, itace dai batayi wayon saninshi sosai ba, rabon da su haɗu tun tana yarinya ƙarama, Amma shi ya santa kuma nasan baze bamu kunya ba Insha Allah, tunda itama tamkar ƙanwa take a gurin sa"
Jinjina kai kawai tayi ba tare da ta kuma cewa komai ba.
Wajejen la'asar Amal ta shiryo cikin wata irin doguwar riga wadda ta kama jikin ta matuƙa, se zuba ƙamshin turare take wanda turaren har hawa ka yake yi saboda ƙarfin sa ta hau kan wani takalmi me uban tsini, duwatsun jikin rigarta se ƙyalli suke suna rawa.
Cikin iyayi ta ƙarasa inda Yusuf yake zaune da su Nura da sauran ma'aikatan gidan tace "Yaya Yusuf mu tafi ko na shirya"
Ba musu Yusuf ya miƙe yayi wa su Isa sallama.
Ya karɓi mukullin Motar Amal, suka shiga mota suka fice.
Yusuf na barin gurin Murtala me bawa shukoki ruwa yace
"wai kunga abunda na gani ko kuwa?"
Nura yace "mun gani, kai kaga wata irin kwarkwasa da take masa? , anya yarinyar nan Amal ba san shi take ba? Kaga wani iyayi da take yi tana fari da idi"
Murtala yace "Amma kuwa da ta faɗo, duk zuƙa zuƙan Samarin dake zuwa gurin ta? duk iya yin da wulaƙancin nata ta ƙare a direba, wallahi da tayi faɗuwar baƙar tasa"
Isa yace "to ai gara Amal ɗin akan yayar ta Ramla, kun san agola musamman in aka samu guri akwai iskanci, yadda suke hura hanci suna Wulaƙanta mutane kai kace gidan ubansu ne, Amma fa duk da haka gara nasu lafiya ne akan 'yar masu gida wai wa yaga Azaba, idan bata ga dama ba fuskarta idan ka kalla seka yi fitsari a wando, saboda sam bata da rangwame, Azababbiyar Yarinya idonta fiƙi fiƙi kamar me maye"
Nura yace "wallahi ko san haɗa hanya da yarinyar nan bana yi, nagode Allah da yasa ba ita nake tuƙawa ba baban ta nake tuƙawa, ni nayi mamaki ma yadda Yusuf ɗin nan har yanzu basu samu saɓani taci mutuncin sa ba, dan naga wani jin kan sa yake shima, musamman idan yana jan manyan motocin nan se kace na gadon ubansa, kamar har mantawa yake direba ne shi"
Isa ya gyara zama ya waiga sannan ya ƙara ƙasa da muryar sa yace
"ku nifa ban gama yadda da Yusuf ɗin nan ba, kuna ganin sa wani haɗaɗɗe da shi, kullum tsaf tsaf da shi, babu alamar wahala a tare da shi, ga jan aji duk yafi mu kyan gani sannan ace ya ƙare a direba anya babu lauje cikin naɗi a wannan harkar kuwa?"
Murtalah yace "Nima nayi wannan tunanin, amma ya zamu san gaskiyar lamarin? Dan ya fara bani haushi wallahi, yadda megidan nan ya fara wani girmama shi wai yana da sunan yayan sa, har wani Yaya na yake ce masa shi kuma yana washe baki yana sunkuyar da kai, damabidan mutum yavfiye sunkuyar da kai munafuki ne"
Isa yace "ku ƙyale shi zan bugi cikin sani inji ko zamu samu wani bayanin muji, ai duniya seda labari, Amma ina tunanin ta yadda za'ayi kamar wannan da beyi kama da wanda yake cikin wahala ba yazo yana aikin direba"
Yusuf ya ƙudurcewa ransa ze ɗan dinga sakarwa Amal, domin samun sanin wasu abubuwa da suka shige masa duhu game da yanayin tsarin Rayuwar mutanen gidan. Suna tafiya a hanya Amal tace
"Yusuf dan Allah ka dinga haƙuri da abunda Widad take maka, sam abunda tayi maka ɗazu banji daɗi ba wallahi haka take bata san darajar ɗan Adam ba mussman talaka, bata da mutunci, mu kanmu haƙuri kawai muke da ita sam bama jin daɗin zama da ita, shiyasa babu wanda yayi farinciki da dawowarta"
Yusuf da sauri yace "A'a uwa ɗakina ce fa ranki ya daɗe, ya zaki ce bata da mutunci a gabana? ai bazan ji daɗi ba gaskiya banji daɗin yadda kika aibata ta ba"
Kallon Yusuf tayi galala cike da mamaki tace "kana nufin baka ji haushin abunda tayi maka bane? Ai ba ƙarya nayi mata ba, da tana da mutunci da bata muzanta maka ba, harta jefe ka da key a fuska ba"
Yusuf yayi murmushi yace "yana da kyau mu dinga girmama doka kafin muyi ƙorafin anci zarafin mu, ko ba'ayi mana adalci ba, da hannu na na saka hannu akan dokokin ta kafin in fara mata aiki, na saka hannu na amince da zanbi sharuɗan data gindaya min, dan haka tunda ni na saɓa abunda na sakawa hannu, komai tayi min be kamata inji haushi ba, ko kuma ince bata da kirki ba, idan nayi haka banyi wa kaina adalci ba"
Amal tayi ajiyar zuciya tace "indai wannan ce kai da kanka zaka dawo daga rakiyar ta saboda wulaƙancin ta, dan wataran seta maka abunda zesa ka tsaneta tamkar mutuwar ka, tun bamu kai haka ba mahaifiyar mu ta auri mahaifin ta muke zaune tare, Amma bamu da daraja ko ƙima a idon ta, kai bamu ba har mahaifiyar mu bata ɗagawa ƙafa, Alhaji Bulama ne ya bada shawarar a bar ƙasar nan da ita, shine ma muka samu muka huta na wasu shekaru kafin ta dawo, se a dinga fakewa da bata da lafiya, tana taka mutane tana nuna isa da Izza"
Yusuf yace "bata da lafiya kuma? Kamar ya bata da lafiya, Meke damun ta?"
Ɗan taɓe baki Amal tayi tace "wai bata da lafiyar ƙwaƙwalwa, ko da yake me lafiyar ƙwaƙwalwa baze abunda take ba, wannan dukiyar ta mahaifin ta, da ita take taƙama da ita take wulaƙanta mutane, ta yaga duk wanda yayi mata abunda yake saɓanin raa'yin ta, aikin banza, dukiyar da'ake farautar ranta akanta, Amma take da damar Wulaƙanta mutane saboda ita"
Da sauri Yusuf yace "kamar ya farautar rai? Ranwa ake farauta, saboda dukiya?"
"Ran Widad ɗin mana, yana ɗaya daga cikin dalilin da yasa ta bar ƙasar nan fa, bayan larurar Ƙwaƙwalwa da take dashi ana farautar ranta ne, tunda maman ta ta rasu take fama da larurar ƙwaƙwalwa, kuma a kazo ana nema a kashe ta, abundai gashi nan, Amma kodan wulaƙanta mutane da take dole wani yai ƙudurin kashe ta ya huce takaicinsa, bayan wulaƙancin da take wa mutane, har ɗaure mutane take sa ayi"
Jinjina kai Yusuf yayi yana kuma nazarin maganganun Amal, baya so ya cika ta da tambayoyi, karta fuskanci wani abu dan haka yayi shiru yana ɗan satar kallon Amal yana tunani a ransa.
Yusuf ya kai Amal wani katafaren mall kaman yadda ta buƙata ta dinga ɗibar kaya, sannan tace Yusuf ya ɗauki abunda ya keso.
"A'a nagode amma ni bana buƙatar komai"
Amal tace "haba Yusuf dan Allah ka ɗauka, karka ji komai"
Fafur Yusuf yaƙi yadda ya ɗau komai se haƙura tayi.
Bayan sun dawo gida tace dan Allah ya taya ta ɗaukar kayan da ta siyo, babu musu ya ɗau kayan yabi bayan ta kamar yadda suke da Widad, Sedai tun a babban falon ƙasa suka ci karo da hakimar ƙafar ta ɗaya kan ɗaya tana shan tea, gefen ta kuma tana bawa magenta madara, bata kula su ba su kayi gaba za su wuce, muryar ta suka jiyo tace
"Stop there" ta faɗa kai tsaye cikin bada umarni, gaba ɗaya suka tsaya suna jiran me za tace.
Se da ta ja wasu seconds sannan tace
"Amal yaushe muka fara sharing ɗin abu nida ke ne ban sani ba? Ya akayi matsayinki har ya kai kiyi amfani da abina ba tare da kin nemi izini na ba?" tai maganar tare da miƙewa tsaye, tavtako ta zo har inda suke tsaye ta kalli Amal, ta tsaida dubanta kan Amal, Amma tace wa Yusu
"waye ya ɗauke ka aiki a cikin gidan nan?"
"kece ranki ya daɗe" ya faɗa cikin girmamawa
"Wa kayi wa aiki yanzu?" tai maganar me cike da bayyanar da tsantsar Izzar ta
" 'yar uwarki ranki ya daɗe" ya bata amsa
Ta ɗan lumshe ido sannan ta buɗe tace "Na taɓa gaya maka ina da ɗan uwan ko' yar uwa ne?"
"A'a"
"lokacin dana ɗauke ka aiki na gaya maka nida wani zakayiwa aiki?"
"A'a" ya sake bata amsa
Ta maida idon ta kan Yusuf cikin ɗaga sauti tace
"Ka karyamin doka karo na biyu da wani suna ya kamata in kira kane? Bagidajen ina ne kai? Ko kuma ince daga wani jejin kake? a haka you look civilized amma kwata2 shashasha ne kai, hala ka manta akan death contract kayi signing? Inaga ka manta ne, ko kuma ka ɗauka wasa ne shiyasa kake wasa da rayuwar ka"
Ya girgiza mata kai alamar A'a
Hayaniyar da Hajiya Halima take ji sama sama ne ya sa ta fito ita da ramlah suka tsaya suka yi cirko cirko a falon Widad tana ta zuba tsiyata kunta san ranta.
Widad tace "Yanzu ina maka hukunci se ka kirani azzaluma ko? Saboda haka ɗabi'ar ku ta matsiyatan mutane take, ku kullum akan daidai kuke masu kuɗi kuma Azzalumi ko?, dukda bana maimaita magana yau zaka sani na maimaita, Ni Widad ban yadda da kowa ba, duk yadda muke da mutum karyamin dokoki na daidai suke da yunƙurin cin amana ta, kuma penalty ɗin wanda yaci amana ta, bana jin tantirin talaka wanda bashi da komai kamar ka ze iya ɗauka "
Amal tace " haba Widad be kama......
Ɗaga mata hannu Widad tayi ba tare da ta kalli Amal ba tace "har yanzu 'yar alfarma ce ke a cikin gidan nan, matsayinki be kai na 'yar masu gida ba, karki ƙara gangancin ina magana ki katseni ko kisamin baki, idan ba haka ba kin san sauran, kai kuma daga yau nikaɗai kake wa aiki a cikin gidan nan, ban yadda wani ya saka aiki kayi ba, duk wanda yace kai wani abu kace Widad kake wa aiki ba wani ba, sannan kayi a rabin salary ɗinka shine hukuncin karya min doka da kayi har sau biyu dismiss from here"
Yusuf ya risina ya ɗanyi murmushi yace "godiya nake uwaɗakina, Allah ya ƙara girma Insha Allah zanyi ƙoƙari in kiyaye dokokin ki, bazan ƙara karya miki doka ba, Allah ya huci zuciyar ki"
Gaba ɗaya suka bi Yusuf da kallo wato shi duk wannan cin zarafin da aka yi masa godiya yayi, lallai wani talakan Jaki ne, besan ciwon kansa ba, Ramlah ta faɗa a ranta.
Widad ta kallesu ɗaya bayan ɗaya tace "bana buƙatar kowa a falon nan, madam zaki iya jan zugarki ku ɓace min daga nan"
Saboda tsabar baƙinciki da takaici Amal watsi tayi da kayan shopping ɗin da tayi a falon, tai cikin part ɗinsu da gudu tana kuka, abun yayi yawa taji zafin cin mutuncin da akayiwa Yusuf ga tsabar wulaƙanci da suke fuskanta a gidan nan se kace Almajirai, kokuma wasu bayi.
Ramlah ta kalli mahaifiyar su tace
"Mummy am tired wallahi enough is enough are we slaves? see how this little baby is shouting at both of us including you, Mummy you have to do something"
Kafin Mummy tayi magana Amal ta shigo tana kuka.
Mummy tace "Amal meya saki kuka?"
"gaskiya ni Mummy zan tattara kaya na in bar gidan nan na gaji, wannan wane irin cin zarafi ne?"
Mummy tace "duk nasan da haka amma kuyi haƙuri ku ƙara wataran se labari da munsamu abunda muke so shikenan fa an wuce gurin"
Amal tace "dan Allah Mummy yaushe wataran ɗin nan zata zo, shekara nawa muna zama kaman bayi? Wallahi nagaji kalli cin mutuncin da tayi wa wannan bawan Allah dan kawai ya kaini unguwa"
A fusace Ramlah tace "dallah rufewa mutane baki, dan taci masa mutunci seme ina ruwan wani? Shi ta fara yiwa cin mutunci? Dama naga yadda kike wani zaƙewa a kansa tun wuri ki nutsu dan ni natsane shi wallahi sam ban yadda da shi ba"
Amal tace "Malama ba ruwan ki da abunda nake yi seki ta tsanar tasa ai, seki kashe shi tunda kin tsane shi"
Mummy tace "kunga dan Allah ya isa haka kar kuyi min faɗa, ni kaina ban yadda da wannan Yusuf ɗin ba, narasa yadda aka yi megidan nan ya wani ɗaukake shi haka, ina son sanin daga ina yake"
Haɗe rai Amal tayi ta zumɓura baki
Mummy tace "ku kuke tada hankalinku, Ramlah zancen da kika yi min ranan na tambayi babanta ya tabbatar min da cewa Aurar da ita zeyi"
Da yake Amal bata san zancen ba da sauri ta waigo tace "Aure kuma? A hakan za ai mata Aure? Waze kwashi wannan Jarabar"
Ramlah tace "Mummy dama na gaya miki, Amma wane me tsautsayin za'a liƙawa wannan Mahaukaciyar? Nasan dai bata da saurayi to waze ma kulata taci masa zarafi"
Mummy tace "ba wani bane Fahad ɗin Alhaji Bulama ne"
Asahar Ramla ta saki tace "Wane Fahad ɗin?"
Murmushi Amal tayi tace "Bulama nawa muke da shi? Fahad dai da kika sani, Fahad naki shine me tsautsayin"
Ramlah tace "Taɓɗijan wallahi da sake, baze yuwu ba akan me? Ita Hajiyar sa tana me za'a aura masa wannan tantiriyar ga hauka gashi maybe ta gama watsewa da turawa, shekararta nawa a turai, Allah kaɗai yasan me take acan baze yuwu ba"
Ta miƙe ta bar ɗakin tana masifa.
Yusuf be bar gidan ba ranar se bayan sallar isha'i.
Koda yaje gida ya tarar Umman sa ba taci Abincin dare ba shi take jira, seda sukaci Abinci suka yi hira sannan ya koma ɗakin sa.
Ya ɗakko laptop ɗin sa ya shigar da duk abunda ya faru da date da komai, dukkanin hirar da suka yi da Amla seda ya rubuta sannan ya kwanta.
Tun daga ranar Yusuf yake taka tsantsan gurin bin dokokin Widad, Sannan yana ta ƙara lura da yanayin mutanen gidan da ɗabi'ar kowa daga cikin su.
Widad ta aika Ramla ta kira mata Yusuf.
Ramlah tana zuwa inda suke zama ta kalle shi a wulaƙance tace
"kai wa kake kazo inji waccan yarinyar"
Yauma Yusuf ya shirya tsaf ze kai Widad Store za tayi siyayya bayan fitar su, Hajiya Halima ta aika aka kira mata Isa mai gadi, yaje ya same ta a ya durƙusa ya gaishe ta, ta amsa masa a wulaƙance sannan tace
"kaine ka kawo wa Widad direba ko?"
"Eh nine Ranki ya daɗe"
"Good, ina son sanin daga ina yake?"
Isa ya risina sosai sannan yace "Wallahi ranki ya daɗe ban san daga inda yake zuwa ba, nima wani abokina ne Sani ya kawomin shi yace ɗan uwan sane amma ban daga ina yake ba"
"ka buɗe kunnen ka da kyau ka saurareni"
Isa yace "to Hajiya"
"Ina so duk yadda za'ayi in san daga ina yake? Daga ina yake zuwa gidan nan, sannan ina so ka ƙara samun ido akan sa sosai ina tunanin akwai wani ɓoyayyen abu a tare da shi"
"An gama ranki ya daɗe insha Allah zanyi yadda kike so"
"sannan wannan maganar ina so ta tsaya daga ni se kaine, bana son wani ya san munyi ta"
"babu me ji ranki ya daɗe"
"tashi ka tafi" Isa ya tashi fita.
Yusuf kam wani katafaren shago ya kai Widad, ta siyi kayan da take buƙata, hatta ruwan roba da zata sha seda ta siya abun ta.
Banda kayan ciye2 da sauran kayan ƙyale2
Seda sukaje gurin biyan kuɗi ta kalli Yusuf tace "jeka mota ka ɗakko jaka ta"
Ba musu yaje ya ɗakko 'yar ƙaramar jakar ta ya kawo mata"
"buɗe ka ɗakko ATM card ɗina"
Ya ɗakko ya riƙe aka lissafa kuɗi, kuɗi ne masu yawan gaske, ko a jikin ta tace
"basu ATM ɗin" ya miƙa musu suka saka a POS suka miƙo masa yasa ka password ya sa hannu ya karɓa ya miƙo mata domin ta saka lambobin da zasu bada damar cirar kuɗin, a hankali tai ƙasa da muryar ta tace
"7724" Yusuf ya gane me take nufi haka ya danna lambobin ya miƙa musu.
Suka ciri kuɗin su yana mamakin me yasa ta gaya masa password ɗin cirar kuɗin ta.
Sun fito harabar Store ɗin zasu tafi suka wuce ta gefen wani mutum dake ƙoƙarin rufe motar sa yabi Widad da kallo tare da faɗin subhanallah.
Da sauri yabi bayan su Widad, Yusuf yayi gaba yana zuba kaya a mota mutumin ya sha gaban Widad yace
"Ahh excuse me Madam you look so hot"
Zare glashin fuskarta tayi tai masa kallon sama da ƙasa ta mayar da glass ɗin ta, tai gaba abunta.
Sake binta mutumin yayi ya sha gaban ta zeyi magana Widad tace "wai me kake nema ne?"
Yusuf kam ganin ta tsaya ya sashi komawa inda take tsayen dan ganin meke faruwa.
Mutumin yace "Wow ashe bahaushiya ce? Gaskiya beb bazan ɓoye miki ba kin tafi da imanina, kin min ina sonki, ki bani contact ɗinki mana se muyi magana, you look sexy" yai maganar yana wani kashe ido irin na 'yan bariki tare da miƙowa Widad wayar sa
Karɓar rantsatsiyar wayar tayi kaman gaske, ta sake ta a ƙasa ta fashe sannan tace "waya gaya maka samun lamabr mace kamar ni a gurin ƙasƙantattun mutane marasa amfani irinka abu ne me sauƙi, dalla matsa a gabana ko in tsinka maka mari sakarai kawai"
Waro ido mutumin yayi "ni zaki tsinkawa mari? Kin san waye ni kuwa? In baki wayata ki fasa min"
"Waye kai banda banza wofi, matsiyaci mara amfani? Kauce a gaban kafin inyi maganin ka"
Kan Widad mutumin yayo yana kumfar baki "Wallahi sena nuna miki koni waye a garin nan, 'yar uban waye ke da zaki min haka? Sena ci zarafin ki na wulaƙanta ki"
Tuni Attention ɗin mutane ya fara yowa kansu kaman ze daki Widad, Yusuf ya shiga tsakanin Widad da mutumin ya kalli mutumin yace
"kana ta mana kumfar bakin ba' a san waye kai ba, ita kasan wacece? Ina ruwan ka da ita da zaka biyo ta kafaɗi maganar banza akan ta, ka kiyaye harshen ka kafin a nuna maka ƙarfin ikon data ke dashi"
"Kaikuma waye kai waye ya sakoka a cikin wannan maganar?" mutumin yasa hannu a aljihu ya miƙowa Yusuf id card ɗinsa, kafin Yusuf ya karɓa Widad tasa hannu ta karɓe ta duba id card ɗin nasa sannan tace
"Ashema matsiyaci ne taƙamarka kaki ko? Zan iya sawa a keta kakin naka a gaban mutane a wulaƙanta ka, a tozarta min kai, sannan in ɗaure ka, kuɗi sunfi wannan kakin banzar da kake tin ƙaho dashi, Widad Nasir Daula inada Arzikin da zan wulaƙanta ka ka ƙare a gidan yari sakarai kawai "
tayi jifa da ID card ɗin nasa ta tofa miyau akai
Ai Sunan ta data faɗa yasa mutumin nan
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 5 Chapter of 35