in kin haɗa se in ɗiba inje in wanko su"
Widad tace "kaine zaka wankemin kayan?"
Yusuf yace "eh mana, ko kinga alamar injin wanki a garin nan, tunda muka zo kin taɓa ganin wuta?"
"to gasu nan na haɗa, kaje kace a bani ruwan wanka"
Yusuf ya girgiza kai yace "to"
Ya miƙe ya ɗau bokiti ya fita, Widad ta buɗe Akwatinta ta ɗakko towel ta ɗaura, ta saka hijjabi ta biyo bayansa yadda ana haɗa ruwan se ta shiga tayi wanka.
Mutan gidan sunata hada Hadar yadda za'a haɗa karin kumallo, ga dukkan alamu yau mutuniyar Widas ce da girki, wato Harira.
Yusuf ya durƙusa ya gaishesu, cikin jin nauyi kafin yayi magana Gwaggo tace "Yusufa na ganka da bokiti, ruwan wankan za'a zuba mata?"
Yusuf yace "eh Mama"
Tace "kawo in zuba maka anan, ya jikin nata kuwa"
Yusuf yace "jiki Alhamdilillah"
Tace "Madalla, nikam ya sunan nata ne? Bamu san sunanta ba"
Yusuf yayi murmushi yace "Sunanta Widad"
Hari dake gaban murhu ta juyo da sauri tace
"Bala'i, wannan wane irin sunane? Hudas ko wudas sekace kayan citta da masoro wane irin sunane wannan"
Tsakin Widad ne yasa Yusuf juyawa, yadda ta tamke fuskane ya tabattar maaa sa taji abunda Hari tace, Yusuf kamar yayi dariya Amma ya basar kar suyi faɗa a gaban mutane.
Gwaggo tace "kaga 'yar halak, ana zancenta se gata, sedai ni wannan sunan nata na Larabawa bazan iya faɗa ba, Amarya ya jikin naki?"
Widad a ranta tace "wai Amarya Taɓɗijan"
Yusuf yace "Ana miki ya jiki?"
"Naji sauƙi"
Galala Hari ta bita da kallo tace "Ashe bahaushiya ce, wallahi ganinta nake kamar bata jin hausa, yo aini harna fara tunanin ko kurma ce, ashe tana magana sannu Amarya wudas, ashe kina magana Allah sarki, ya jiki?"
Sake yamutsa fuska Widad tayi, 'ita dai wannan matar bata gajiya da magana, kodai bata san yadda haƙoranta suke bane take buɗesu tana surutu haka, bar wani kore kore ne a jikinsu, ga maganar tsiya da take dashi"
Widad bata kulata ba, aka haɗa mata ruwanta, Yusuf ya kaimata inda take wanka.
Aka haɗa Yusuf da yaro ya rakashi rafin da matasan garin suke haɗuwa suyi wanki.
Amlace ta shiga ɗakin Ramlah, ta dinga bubbuga mata filo, da ƙyar Ramlah ta tashi a fusace tace "Meye haka Amal?"
Amal tace "Anya lafiyar ki kuwa? Ƙarfe biyi fa, amma har yanzu bacci kike, yakamata ki tashi haka ai"
Miƙewa tayi zaune tana miƙa tare da duba agogo, dagaske biyu na rana, haka ta miƙe ta tafi banɗaki tayi wanka sannan ta ɗanji ƙarfin jikinta.
Koda Saleh ya dawo kano, be biya ko'ima ba Asibiti ya fara zuwa duba jikin Alhaji Nasir, amma yanayin jikin nasa se godiyar Allah, Nurses suka gaya masa Anwar yaje masallaci.
Saleh ya zauna a kusa da Alhaji Nasir, wanda idanunsa ke lumshe yake numfashi da temakon Na'urar dakw bashi iskar Oxygen, ya riƙo hannunsa da suka yi sanyi ƙalau, cike da tausayawa ya kai bakinsa daidai kunnensa yace
"Allah ya baka lafiya Yallaɓai, 'ya' yanka sun kuɓuta daga hannun miyagun nan, yanzu haka suna wasu ƙauye na basu mafaka, saboda tseratar da Rayuwarsu, Yusuf yayi ƙoƙari matuƙa ya kula da Amanarka, yana kula da gimbiyarka sosai, Amma munyi maka wani laifi da ban san ya zaka ɗauki abunba, Na wuce gaba Yusuf ya Auri 'yarka, dan kasan bata yadda da kowa seshi, kuma baze yuwu ya cigaba da kula da ita ba, tunda ba muharramarsa bace"
Dukda Alhaji Nasir ba iya magana zeba, da alama yana jin abunda Saleh yake faɗa, ƙara riƙe hannun Saleh yayi gam sannan yayi masa murmushi.
Saleh yace "Amma karka kuskura ka gayawa kowa, kayi shiru da bakinka"
Anwar ne ya shigo bakinsa ɗauke da Sallama, yana ganin Saleh yayi murmushi yace "Saleh sannu da zuwa, naje Sallane"
Saleh yace "bakomai Anwar, ya me jiki?"
Shiru Anwar yayi, ƙwalla na taruwa a idonsa yace
"Saleh na rasa wane irin abokai Allah ya bawa bawan Allah nan, sam hankalinsu baya kansa, amma lokacin da yake da lafiya sune kan gaba gurin nuna masa ƙauna, Amma dubi yanzu, look at how he's suffering alone, ba wanda ya bani mamaki kamar mahaifiyata"
Anwar ya ƙarasa maganar, jijiyoyin kansa na tashi idonsa yayi ja, Alhaji Nasir ne yayiwa Anwar Alamar yaje da hannunsa.
Anwar ya ƙarasa gaban gadon Alhaji Nasir ya zauna.
Alhaji Nasir ya kamo hannun Anwar, sannan ya miƙa hannunsa ɗaya yana shafa kan Anwar tareda yi masa murmushi a hankali yace "Nagode, Nagode"
Kawai Anwar ya rungume Daula ya fashe da kuka, shima Daula hawayene suka fara bin gefen idonsa, da ba ƙaramin mamaki ya shiga ba, ganin yadda gaba ɗaya mutanensa da suke tare dashi suka watse suka barshi, ciki harda matarsa da take morarsa.
Yusuf yaje ya tarar da matasa da magidanta a gurin wankin nan, wasu na wanki wasu na wanka a ruwan, in an koro dabbobi suma suzo su sha ruwan, amma a haka yaga wasu na ɗiba na tafiya dashi abun ya bashi mamaki, dama a gurin salla megari ya gabatar dashi, dan haka wasu daga cikinsu sun sanshi.
Duk rashin son mutane irin na Yusuf ya ɗan sake dasu, suka dinga hira suma bashi labari akan yanayin garin nasu.
Abun ya dinga bawa Yusuf mamaki, suna rayuwa cike da son juna mutanen ƙauyen, sedai abun mamaki ɗan majaillisar dake wakiltar yankin kakannisa 'yan garinne, amma abun mamaki sukace lokacin da yake campaign har falafalan wuta aka samu su, ya gina musu borehole guda ɗaya can wajen gidan kakaninsa shima se anyi tafiya me nisan gaske borehole ɗin yake, yace idan suka zaɓe shi yaci ze janyo musu wutar lantarki, tundaga wannan campaign da yazo tsawon shekara uku basu sake ganinsa ba, ko gidan kakannin nasa baya zuwa ziyara gaba ɗaya ya koma Abuja.
Haka Yusuf suka cigaba da hira shikuma yana wankinsa, seda ya gama suka bushe ya ninko kayan tsaf, sannan suka taho sa wani maƙocin gidan megari zuwa gida.
Yana zuwa gida ya tarar da Widad a ƙofar ɗakinsu a zaune, zaman dirshen a ƙasa fuskarta tayi jawur saboda kuka, Yusuf ya razana ko ciwonta ne ya tashi.
Gwaggo na ganinsa tace "yawwa Yusufa, wallahi muna tsakar gida muna aiki muka jiyo ihunta, ta fito da gudu mukaje kanta, juyin duniya taƙi magana tayi zamanta a nan gurin, munce ta bar ranar ta shiga ko ɗakina ta zauna taƙi.
Yusuf ya ƙarasa inda take ya ajiye bokitin hannunsa me ɗauke da ninkakkun kayansu yace "lafiya kuwa? Meyasameki haka?"
Cikin harshen turanci tace masa, "wasu ƙwarine suka yi ta cizona, sekuma naga spider manya guda biyu a ɗakin, dana fito nan ma ƙwarin suka cigaba da cizona"
Girgiza kai yayi yace "shikenan tunda na dawo tashi mu shiga ɗaki, kalli a yadda kike kin zauna a tsakar gida kowa yana kallonki a haka, kuma kinga kin tayarwa da mutanen gidan hankali"
"wallahi bazan shiga ba se an cire wannan spider ni bana sonshi, bana son ganinsa it's irritating me, looks at my body"
Se yanzu ya lura da yadda kafofin gashinta suka buɗe, jikinta yayi wani irin burɗin_ burɗin, fuskarta ma tayi ja saboda cizon sauro.
Hari tace "Allah dai yasa ba wani abun mukayi mata ba, dan naga alamar makirace, tun ɗazu muke fama taƙi magana, Amma tana ganin mijinta ta fara magana hadda karairaya"
Widad ta ɗaga kai ta ƙurawa Hari ido, yayin da gwaggo taji haushin abunda Harin tayi.
Yusuf kam ba ƙaramin dariya Hari ke bashi ba idan ta kunna Widad, yasan Widad tana mata kawaici ne kafin ta ɗan sake.
Yace "ba wani abun kukayi mata ba, wai wani abune ya cijeta amma, bakomai yanzu zan shiga in duba"
Yusuf ya shiga ya duba bega gizo2 ba, sedai cinnaku dake yawo a ɗakin, da alama su suka cijeta.
Yasa tsintsiya ya shashsharesu tsaf, sannan yace ta dawo ɗakin.
Yusuf "Yace meye ya cijekin?"
Guri ta zauna ta janye rigar jikinta, ta nuna masa cinyarta, fara tas fiye da fuskarta, sedai tayi ja saboda cizon cinnaka, banda wanda ya gasa mata a hannu.
Yusuf yace "Sannu bari in tambayi gwaggo inda zaitun ta bani ki shafa"
Zumɓura baki tayi tace "ni banyi wanka ba"
Haka ya karɓo ruwa tayi wanka, sannan ta dawo ɗakin, ya bata guri ta sa kaya, ya ɗakko zaitun ta zauna ya shafa mata a na hannun, ya fara shafa mata a ƙafarta ne a hankali, haka kurum taji jikinta wani iri, kawai seji yayi ta doke hannunsa tace
"meye haka?"
"Me kuma nayi miki?"
"ban sani ba" ta bashi amsa tare da miƙewa, ɗan sunkuyar da kai yayi yana murmushi.
Daga Asibitin gurin Alhaji Musa Saleh ya wuce, yaje ya sames hi a office ɗinsa.
Saleh yace "Ranka ya daɗe kwana biyu bani da lafiya, ko ƙofar ɗaki bana iya fitowa, shiyasa kwana biyu bana zuwa"
Alhaji Haruna yace "Akwai damuwa fa, ko Kasan me Adda ya cemin yarinyar nan sun gudu"
A razane Saleh yace "wace irin maganar banzace wannan? Kamarya sun gudu?"
"Nima dai abunda na gani kenan, gaba ɗaya sun mayar mana da aiki baya, yanzu Bukar yace ko a raye ko'a mace anemosu a kashesu kar Asirinmu ya tonu, sannan kaje ka bincika mana wa'aka bawa aikin binciken nan a cikin jam'ian tsaro?"
Saleh yace "Amma fa wani hanzari ba gudu ba, ina kyautata zaton me Adda yana sane ya sake su, wataƙila tace zata bashi kuɗine koma ta ninka masa abunda kuka bashi, shine ya sake su, in bahaka ba ta yaya zasu iya tserewa? Kokuma a cikinku ne wani ya zagaya ya haɗa baki dashi, idan an karɓo abun a gaya masa shikaɗai ba"
Shiru Alhaji Haruna yayi yace "Biri yayi kama da mutum, kuma fa Saleh kayi magana, tabbas dan nasan zata iya, kuma babu Abunda me Adda baze iya akan kuɗi ba"
Jinjina mara adadi ga ɗumbin masoya littafin AƘIDATA, niba abunda zance muku se godiya Allah ya bar ƙauna, ga dogon page nan, nima inga dogon sharhi, ga link ɗin telegram nan a ƙasa
https://t.me/joinchat/SYIfEaoQo_JlNDM0
Share, share and share please 🙏 🙏 🙏
Domin gyara sharhi, ko shawara
Ayshercool
07063065680
_*AƘIDATA*_
PERFECT WRITERS ASSOCIATION
(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)
https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*Story and written by*
_*AISHA HUMAIRA _
(Daddy's girl)*_
The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *
I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum
Haƙƙin Mallaka ⚠ : Littafin nan mallaki nane, tun daga sunan labarin zuwa abunda ya ƙunsa, ban yadda wani ko wata ya sauyamin ko yin Amfani da wani ɓangare na labarin ba ba tare da izinina ba, Nagode
https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends
NOT EDITED
ELEGANT ONLINE WRITER'S
PART1
Page 34_35
Saleh ya cigaba da ziga Alhaji Haruna, akan lallai yayi bincike, dan zata iya yuwuwa abokan harƙallaesa ne wani yasa a karɓo masa abun hannun Widad, shiyasa me Adda yace masa sun gudu.
Alhaji Haruna yace "Nagode sosai Saleh, Insha Allah zanyi tunani akai"
Saleh yace "bakomai yallaɓai, bari in ɗanje gida in huta, kasan bana jin daɗin jikin nan nawa"
Alhaji Haruna yace "shikenan Allah ya sawwake"
Saleh ya tashi ya tafi
Sakina ce fuskarta ɗauke sa damuwa ta shiga ofishin Suleiman, Suleiman yace "Sakina lafiya kuwa?"
Sakina tace "Yallaɓai akwai damuwa, yau sati biyu sa sace Yusuf amma har yanzu babu wani kyakkyawan rahoto, da yake nuna ana bincike akan lamarin nan, anya anyi adalci kuwa duba da yadda Yusuf yake bada gudunmuwa akan harkar tsaro, amma ace shi wannan iftila'in ya faɗa masa amma babu wani yunƙuri da'ake gurin ceto shi, idan ya rasa ransa fa? " ta ƙarasa maganar kamar zata yi kuka.
Suleiman yace "look Sakina, kiyi wani tunani kodan Albarkacin 'yar babban attajirin da' aka sace su tare, yaci ace an maida hankali akan nemansu, amma har yanzu shiru, shikansa Daulan yana gadon Asibiti a kwance, na kai ƙorafi akan abari muma mu gudanar da namu binciken, amma daga sama aka bani umarnin cewar ba'a samu ba, ana gudanar da bincike akan al'amarin, babu wani abu da zamu iya banda muyi musu Addu'a "
Sakina tace " shikenan Yallaɓai, ubangiji Allah ya kuɓutar dasu lafiya, bari in koma kan aikina"
"Shikenan Sakina, Allah ya taimaka"
Sakina na tafiya, telephone ɗin gaban Suleiman ta fara ringing, ya sa hannu ya ɗaga, jin muryar wanda ya kira shin yasa shi miƙewa tsaye cikin girmamawa yana amsa wayar.
"A cikin ma'aikatanka wa'aka saka akan binciken masu bibiyar Alhaji Nasir Daula?"
Suleiman yace "Yallaɓai Yusuf ne, wanda aka ƙarawa matsayi kwanan nan"
"A gaggauta kammala binciken nan, a miƙo bayanan binciken nan headquarter"
Suleiman yace "Ok Sir"
Yusuf ya kalli Widad da tayi kicin kicin da fuska yace "ga kayan nan na wankesu, sun bushe ma gaba ɗaya"
Tasa hannu ta ciro kayan daga bokiti, taga kayan a haɗe dana Yusuf, kwashe nata tayi ta zube masa nasa a gurin, Yusuf yasa hannu ya kwashe ya zuba a jakarsa.
Ya kalleta yace "kinci Abinci kuwa?"
"ni banci wani Abinci ba, kaga fa abunda aka kawo"
Kwano ta miƙa masa, yasa hannu ya buɗe dafaffiyar masarace a ciki da ɓawonta da komai, Yusuf yace "to me yasa baki ciba?"
"ta ina zanci ? Kawai se in kama cin masara, ni ban taɓa ganin anci masara ba, nidai kawai nasan Abinci akeyi da ita, amma ba'aci"
Yusuf yace "ikon Allah, wannan wace irin hausa ce? Waye ya gaya miki ba'a cin masara"
Ya zauna ya ɓare masarar tsaf, ya ɗaurayeta, yace "nasan kece baki taɓa ciba, amma ana cin masara dafaffiya ko gasashiya, ci kiji"
Ɗauke kai tayi taƙi karɓa, Yusuf kuwa yasa masara a gaba ya fara ci, zuba masa ido tayi tana kallon ikon Allah, yana nufin itama haka zata ɗau masarar ta dinga wannan kokawar haka sekace wata saniya.
Plate ya ɗakko ya shiga ɓanɓarowa yana tara mata a plate yace "gashi na ciro miki ɗauki kici"
Ba kunya tasa hannu ta fara tsinta tana kaiwa bakinta, dan bilhaƙƙi ita bata taɓa ganin ana cin masara a haka ba, amma kuma tabbas da daɗi, ya dinga cirowa yana tara mata tana tsinta tana ci, kamar wata 'yar yaye, cikin ikon Allah a haka kuma ta ƙoshi.
Shiru tayi ta tuna lokacin da sukaje restaurant cin Abinci, Yusuf yake gayamata Naira ɗarin cin Abinci tana gagarar wasu, take ganin kamar ƙarya yake, se gashi yanzu ta gani da idonta, da wanine ya bata labarin ana dafa masara aci a matsayin Abinci zata ce ƙaryane dan bata taɓa gani ba.
Can Yusuf yace "inda ƙwaron ya cijeki ya dena zafin?"
Ta gyaɗa masa kai alamar eh, yace "hannun da'aka harbe ki fa?"
"yayi sauƙi, ina iya motsa hannun sosai, sedai idan ma bige ne nake jin zafin"
Yusuf yace "masha Allah, Allah ya ƙara miki ingantacciyar lafiya"
Shiru tayi kamar ba taji ba, Yusuf yace "Addu'ar ma bakya so?"
Shiru tayi masa tana sake ƙarewa roofing ɗin ɗakin kallo, tana son gane dame akayi shi.
Yusuf yace "me kike kallone?"
Widad tace "kai subhanallah, wallahi ka dameni da surutu haba, sekace waccan matar me haƙora"
Yusuf yace "to shikenan na dena gimbiyata"
Ɗagowa tayi ta masa wani irin kallo, ba shiri ya miƙe yayi waje ya bar mata ɗakin yana murmushi.
Wasa2 Ramlah ta ganewa shaye2, bata salla se wajen ƙarfe takwas na safe, da ta idar zata ɗakko Coca-Cola tasha, seta kai ƙarfe biyun rana tana bacci.
Yanzuma Amal ce ta shiga ɗakin Ramlah, ta tarar da ita tana girgiza jarkar Coca-Cola.
Amal tace "Ramlah, wai me yake damunki ne haka? Wane irin coc ne kike sha ba yau ba gobe ga shegen bacci kamae kin haɗiyi kasa"
Ramlah ta kalleta tace "kina da matsala da hakanne?"
"ba wai batun ina da matsala da hakan bane, sedai cewa kina ganganci da rayuwar ki, baccin da kike ya wuce ƙa'ida, kuma wannan coc da kike sha yayi yawa sosai, nifa na fara zargin wani abu kike sha a cikin coc ɗin nan"
"Ke Amal! Ki kiyayeni, dalla wuce ki barmin ɗaki, ina ruwanki dani idanma wani abun nake sha?"
Amal tace "shawara ce nake baki, amma
" wallahi Amal in baki barmin ɗaki ba sena miki rashin mutunci, Dalla ƙara gaba kije kiji da kanki"
Amal tace "shikenan Kije ki ƙarata" ta fito daga ɗakin.
Yanzu kusan kullum se Ramlah ta fita, ko tare da Fahad ko ita kaɗai, kuma Hajiya Halima bata taɓa yi mata magana akan hakan ba.
Anwar kam ya tattara yasa musu ido, ya maida hankali akan kula da Alhaji Nasir, kwata kwata ya dena shiga sabgarsu ma.
Abubuwa suka fara cakuɗewa su Alhaji Musa, suka kuma hayar wasu 'yan ta' addan domin a nemo musu su Me Adda, yayin da Alhaji Haruna ya keta tunani akan maganar da Saleh ya gaya masa game da tserewar Su Yusuf.
Meeting suke akai akai akan yadda zasu ɓullowa al'amarin,
Alhaji Munir yace "tabbas idan har yaran nan suka kuɓuta suka dawo Asirinmu ze iya tonuwa"
Alhaji Musa yace "yakamata ku kwantar da hankalinku, babu yadda za'ayi Asirinmu ya tonu, yanzu naga Likitan nan yana aikin da muka sashi, dan yanzu baya gane waye akansa sam"
Alhaji Haruna yace "hakane Daula ya zama abun tausayi, talakawan da yake fafutuka akansu, an hana kowa zuwa inda yake, manyan ƙasar nan ma kowa yayi watsi da lamarinsa, yanzu haka nasa Jam'ian tsaro su hana kowa shiga inda yake, se ɗan matar nan tasa, shi kuma wannan soko ne, ba abunda yake ganewa, shekaranjiya wasu baƙin turawa sunzo duba shi, amma an hana su ganinsa ance yana ƙarƙashin kulawar likita baza'a ganshi ba"
Alhaji Musa yace "Good hakanma yayi, a hana kowa zuwa inda yake muyi yadda muke so, Amma Nifa har yanzu ina mamaki akan guduwar yaran nan, kuma da suka kuɓuta aida zasu dawo a gari a gansu, amma har yanzu babu wanda yaji ɗuriyarsu"
Alhaji Munir yace "ni kaina abunda yake ɗauremin kai kenan, zuwa yanzu ai yaci ace anji labarin sun dawo, amma babu wanda yaji hakan"
Alhaji Musa yace "shiyasa nake tunanin akwai wata a ƙasa ruwa baya tsami banza, akwai munafiki a cikin mu"
Alhaji Haruna yace "kamarya? Kana nufin a tsakaninmu munafikin yake kokuwa?"
Alhaji Munir yace "kunga ya isa haka, nima nayi zargin haka amma babu lallai da munafuki a tsakaninmu, sedai a wanda suke mana aiki tabbas, kokuma akwai wani a gefe daya ke farautar abunda muke nema"
Alhj Haruna yace "ba abunda baze iya faruwa ba, Amma kar mu ɗora komai akan zargi semun tabattar"
Kamar yadda Saleh ya bada umarni, aka ginawa Widad nata banɗakin, akwai wata ƙatuwar rijiya a gidan ruwan sam bashi da kyau, haka nan ake amfani dashi a gidan, ko kuma mutum yayi tafiyayyiya yaje rafi ya Ɗebo.
Yusuf kuwa tafiya yake me nisa, yaje ya ɗebo ruwa a wannan borehole guda ɗaya tal ta garin, yazo gida ya tafasa idan ya huce seya zuba a randarsu suke amfani da shi a matsayin na sha.
Har yanzu Widad bata saba da kowa a gidan ba, ba ruwanta dasu sedai in sun haɗu a tsakar gida suka mata sannu ta amsa, amma bata shiga sabgar Hari sam, saboda Hari baƙar magana take gaya mata.
Yanzu ma tana tsugune tana brush da yamma, yaran Hari suka kewaye Widad suna kallonta, mussman dogon gashinta dake ɗaukar ido, gata ba ma'abociyar saka kallabi ba, abun haushi hadda 'yan matan gidan da suka tasa, se kallonta suke ita ta rasa se yaushe zasu saba da ganinta su dena mata wannan kallon haka?.
Widad tace "kai me kuke kallone, haba bana son kallon nan da kuke min, did i look like a beast?"
Hari tace "yo sunga abunda basu saba gani ba, kin fito tiɓitiɓi da wasu irin kaya ai dole su kalleki ni wallahi da ban zaci ma musulma ce ke kina jin hausa ba"
Widad tace "eh ba musulma bace ni, gunki nake bautawa yana ɗaki idan kina so ki ganshi"
Sam hari bata zaci Widad tana da baki hadda baƙar magana ba.
Gwaggo tace "Amarya ƙyaleta kiyi haƙuri"
Sannan ta kalli Hari tace "haba Hari, kin fiye magana wallahi duk haƙurin yarinyar nan kinsa ta fara tanka miki"
Hari tace "yo Yaya yara sunga abunda basu saba gani ba ba dole su kalla ba"
Yusuf yana ta tunanin wace sana'ar ze ɗan fara, saboda ya saukewa mutan gidan ɗawainiyar da'ake dasu, ga Widad bakomai take ciba duk ta rame, ya dawo daga sallar Azahar ya tarar an kawowa Widad gujjiya, tanaci hadda ɓawon, Yusuf yace "mekike ci ne?"
Ta ɗan taɓe baki tace "na manta sunanshi, amma inaga wake ne wannan maman ce ta bani"
Yusuf ya kwashe da dariya, ta haɗe rai tana kallonsa, yace "haba Madam, wannan ne waken? Kuma da ɓawo kike ci bari kiga"
Ya zauna yana ɓarewa yana bata, ita tunda take bata san wata gujjiya ba, da taci a baki se taji kamar wake, ta zata ma wake ne yazo a haka.
Tun Yusuf yana mamakin bata san abubuwa da yawa ba, har ya dena mussman duba da yanayin rayuwarta, ita ba sakewa take da mutane ba, kuma mafi yawa a waje tayi rayuwarta, dan haka yake mata uzuri a wasu abubuwan.
Yusuf yace "Ina son in fara zuwa kasuwar garin nan, inga me zan fara siyarwa saboda mu ragewa mutanen gidan nan ɗawainiyar da suke damu"
"dama akwai kasuwa a dajin nan?"
"daji kuma?"
"Eh mana" ta bashi amsa
Yusuf yace "eh akwai kasuwa amma se anyi tafiya me nisa sosai, nayi magana da megari ya haɗani da yaronsa tare zamuje kasuwar gobe in Allah ya kaimu inga yanayin abubuwan"
Tace "Shikenan" tana ci gaba da cin gujjiyarta, seda ta gama ta kalle shi tace "Wanka"
Yusuf yace "to" ya haɗa mata ruwa sannan ya fita sallar la'asar
A gurin salla Yusuf yaga abun mamaki, akwai ƙaramin gurin da suke jam'in salla, akwai ƙarancin ilimi ga mutan ƙauyen, liman ya makara wani yaja salla a raka'ar ƙarshe liman yazo, raka'ar ƙarshe kawai ya samu, itama an ɗago daga ruku'u, da'aka idar Yusuf yana jira yaga liman ya tashi ya kawo wadda be samu ba amma yaga liman yayi ƙyam yaja gefe yana laziminsa.
Yusuf ya dinga kallonsa ko ze tashi ya canza sallane, amma yaga aka jima liman ya shafa addu'a ya miƙe ya gaisa da mutane ya ƙara gaba.
Yusuf yayi shiru a ransa yace "wannan mutumin dabe san hukuncin salla ba, shine kuma yake jan salla? Tabbas akwai matsala babba, mutanen garin nan suna buƙatar ilimin Addini, ya barwa ransa cewa zeyi wa megari magana, yaga ta inda ze iya basu gudunmuwa.
Ya shiga cikin gida ya shiga ɗakinsu da sallama, Widad ta fito daga wankan tana shafa mai, ba tare da ta kalle shi ba ta amsa ƙasa ƙasa, ta cigaba da abunda take.
Kusa da ita yaje ya zauna yana kallonta, duk cikin salon son yasa ta kula shi, dan idan har bashi yayi mata magana ba in zasu kwana idan ba wani abu take buƙata ba, ba zata kula shi ba.
Tana jin yadda ya zauna daf da ita ya ƙureta da ido, kamar tasan maganar yake so tayi, taƙi magana.
Cike da fargaba dan yasan ze sha masifa, amma ya maze ya kai hannunsa gashin kanta yace
"wannan gashin yaushe rabonsa da a taje shi? Insha Allah idan na fara zuwa kasuwa indai naga comb zan siyo, in taje shi da kaina"
Bige hannunsa tayi tace "wai kai meye haka? Me yasa kake son taɓani ne? Na gaya maka bana son karka ƙara taɓani na gaya maka, in ba haka ba
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 28 Chapter of 35