ENTERTAIN OUR READERS)
https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*Story and written by*
_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_
The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *
I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum
Haƙƙin Mallaka ⚠ : Littafin nan mallaki nane, tun daga sunan labarin zuwa abunda ya ƙunsa, ban yadda wani ko wata ya sauyamin ko yin Amfani da wani ɓangare na labarin ba ba tare da izinina ba, Nagode
https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends
NOT EDITED
ELEGANT ONLINE WRITER'S
PART1
Page 30_31
Yusuf ya tsaya cak ya waigo ya kalle ta yace "are you serious kin amince?"
Shiru tayi, taƙi ce masa komai, har yanzu izzar tana nan, abune mawuyaci ta maimaita magana sau biyu, Yusuf yace "Shikenan, idan Saleh yazo zanyi masa magana, kokuma in samu maigari in masa bayanin komai"
Gyara kwanciyarta tayi tace "kuma ranar da zamu koma gida zaka sakeni,gara kasa wannan a ranka"
Yusuf yayi murmushi yace "karki damu, nidai fatana ki samu lafiya komai ya lafa mu koma gida"
Nurat ta koma gida, ta lallaɓa zata silale ta shiga ɓangarenta, "daga ina kike?"
Taji muryar mahaifinta, tsayawa tayi amma takasa cewa komai, cikin tsawa yace "Nace gidan ubanwa kikaje?"
"Amm.. Ammmm. Dama... Damanaje gidansu ƙawata ne shine....
" shine ubanki, yaushe kika fara fita ke kaɗai babu direba? Daga gidan ubanwa kike? Zaki gayamin ko sena kwantar dake na yankaki a gurin nan"
Nurat ta faɗa a Shagwaɓe "Nifa ba inda naje"
"Ubanwa ya kaiki duba Daula a Asibiti ubanki ne?"
A razane ta ɗago ta kalleshi, ta shiga rarraba ido.
"ba magana nake miki ba?"
"Daddy waye ya gaya maka naje duba shi?"
"Ubanki ne ya gayamin" Alhaji Musa ya bata amsa
"Kin san a duniya mutumin nan maƙiyinane, shine kika kwashi jiki kika tafi?"
Nurat tace "Daddy, 'yarsa ƙawatace kuma dukda abunda ke tsakaninku tazo gidan nan birthday na ta bani kyautar mota, yanzu kuma a sace ta mahaifinta a gadon Asibiti in kasa duba shi"
Kafin ta ƙarasa ya ɗauketa da mari, wanda seda ta dena gani na wani ɗan lokaci.
Da sauri Mahaifiyar Nurat ta fito tana cewa "lafiya kuwa? Me tayi maka ne?"
"dole ki tambayi me tayimin mana, munafuka daga ke har ita, wato da saninki ta fita taje Asibiti duba Daula, babban maƙiyina ko?"
Mahaifiyar Nurat tace "haba Alhaji kai waye ya gaya maka can taje"
Alhaji musa yace "Rufemin baki kafin in haɗa dake in muku duka, na wuce duk yadda kuke tunani, duk wani motsinku a waje ina da masu kawomin rahoto, kuma daga yau na saka doka, kada ki kuskura Nuratu ta sake fita daga cikin gidan nan, ban yadda ta sake zuwa ko'ina ba, idan kuwa ta sake sena saɓa muku daga ke har ita"
Maman Nurat taji zafin marin da yayiwa 'yarta, dan ba taga laifin da tayi wanda harta cancanci wannan marin ba.
Taja hannun Nurat zuwa ɗakinta, ta kalleta tace "kema Allah ya ƙara, gobe ma ki sake, gashi nan ya mareki a banza, kin fiye rawar kai Nurat"
Nurat ta share hawayenta tace "Ni ban san wani tantirin munafikin ne ya gaya masa naje ba, Amma idan harna cika 'ya ta halak inason mahaifina ya dace da rahamar Ubangiji, dole in shiga rusa duk wani mummunan ƙudirinsa, ta haka ne kawai zan huce wannan marin da yayi min"
"kinga karki jawa kanki wani tashin hankalin, ki ɗakko mana magana kin san halinsa sarai"
"Mummy, wallahi zubawa Mahaifina ido yana abunda yaga dama, alhalin nida ke munsan ba dai dai yake ba bamu kyauta ba, babu ruwanki a ciki nikaɗai zanyi komai.
" Na sani, amma Nurat ina jiye miki matakin daze ɗauka akanki, idan ya gane abunda kikeyi "
Nurat tace "ba abunda ze gane, sedai inke zaki gaya masa"
Ta ɗau jakarta ta bar ɗakin, ta nufi nata ɗakin.
Amal ta zama kamar wata me jinya, ta rame sosai dan ko Abinci bata iya ci Sam, sedai abunda ba'a rasa ba, yanzu ma Mummy ce da Ramlah suke cin Abinci suna hirarsu, yayin da Amal juya cokali kawai take, ba ta kai ko loma ɗaya bakin ta ba.
Ramlah tace "wai Abincin ne bakyaci, kokuwa? naga se juya spoon kike"
Hajiya Halima tace "na lura da yarinyar nan, kwanakin nan sam bata walwala ta takure kanta da yawa"
Amal tace "Nifa wallahi ɓatan Yusuf ne ke ɗaga min hankali, wallahi na damu sosai beji ba be gani ba am sace shi, Allah kaɗai yasan wahalar da yake sha"
Ramlah tace "Ai kece 'yar wahalar, dama abunda yasa kike wannan damuwar kenan?"
Hajiya Halima tace " waini Yusuf ɗin nan ko tare mukayi Naƙudarki ne muka haifeki ban sani ba? Ubanki ne shi? Ko haifarki yayi idan baki kiyayeni da maganarsa ba sena fasa miki baki, kije ki kashe kanki saboda wani ɗan iska, Allah yasa su haɗa dashi su kashe"
Zare ido Amal tayi tace "Mummy a kasheshi kuma?"
"Eh a kashe shi, munafikin yaro na tsani yaron nan wallahi ba ƙaramin daɗi naji ba da aka sace dashi"
Ramlah tace "wallahi nima naji daɗin hakan, munafuki yaita sunkuyar da kai kamar na Allah, saboda shi ba irin wulaƙancin da wannan makirar ba tayi mana ba, yanzu da suka ƙara gaba se hutawarmu muke"
Amal ta dire cokalin ta miƙe ta bar musu dining ɗin.
Mummy tace "Allah ya kawo lokacin da burinmu ze cika, ita kuma tana wani shirme daban"
Ramlah tace "kedai bari Mummy, nifa harna fara tunanin irin bushshar da zanyi, da yadda zan fantama in kece raini a cikin manyan yara, wayyo Allah daɗi"
Mummy tace "kedai bari yarinya, ai komai yana tafiya daidai"
Suka kwashe da wata uwar dariya, hakan yayi daidai da shigowar Anwar, hakan yasa suka ja baki sukayi tsit.
Ganin yadda sam halin da Daula ke ciki baya gaban mahaifiyarsa da 'yan uwansa yasa ya girgiza kai, tunda Daula ya kwanta a Asibiti bata taɓa kwana a gurinsa ba, se tafi kwana uku ma bata je ba.
Hajiya Halima tace "Allah sarki yaron kirki, Anwar duk ka rame fa, anya baza' a nemi me kula da Alhaji a dinga biyansa ba, ba haƙƙinka bane yin jinyarsa, duk kayi wani iri jinya ba sauƙi fa"
Ya kalli mahaifiyarsa yace "Ciyar damu ɗaukae ɗawainiyar karatunmu da sauran buƙatunmu da yake haƙƙinsa ne? Me yasa lokacin da yakw ɗawainiyar damu baki ce masa ba haƙƙinsa bane, babanmu yayi mana ba tunda yana raye?"
Ya ajiye kayan hannunsa yayi waje zuciyar sa na ƙuna, da irin wannan hali na mahaifiyarsa.
Ramlah taja wani ɗan gajeren tsaki tace " Mummy ya kamata anemo wanda zasu ɓalle ƙofar ɗakin yarinyar nan, mu ɗibi abunda zamu ɗiba, kuma mu shiga ɗakin ubanta mu kwashi abunda muka samu kafin wancan manyan suzo"
Hajiya Halima tace "hakane, amma dole muyi komai a hankali naga Anwar yana neman ya gane halin da'ake ciki nikuma bazan so hakan ba"
Ramlah tace "Ai Mummy ki rabu da Yaya Anwar ɗin nan kawai"
Saleh ne a hukumar 'yan Sanda na farin kaya, ya nemi ganawa da Sulaiman, ai kuwa be sha wata wahala ba saboda Kasancewar shima ma'aikacin tsarone.
Ya shiga Office ɗin Suleiman suka gaisa, Saleh ya gabatarwa Suleiman kansa sannan yace "kamar yadda nima jami' in tsaro ne nazo maka da wata mahimmiyar maganane akan jami'inku da'aka sace tare da 'yar gidan Daula"
Suleiman yace "ya akayi kasan jami' inmu ne? Ba kowa yasan Yusuf ɗan sanda bane"
Saleh yace "ba abun mamaki bane dan na san hakan, Amma yanzu ba wannan ne mafi a'ala ba, ka tsaya ka saurareni da kyau, na kuɓuttar da Jami'inku tare da 'yar gidan Daula"
Wani irin kallo Suleiman yayi masa yace "ya akayi kasan inda suke harka kuɓuttar dasu? Kenan dasa hannunka akan sacesun da' akayi"
Saleh yace "ka dena wannan muzuran, ka tsaya in maka bayani dan baka da ikon da zaka kamani ko gayawa duniya abunda ya faru, idan kayi haka kayi abakin ranka"
Nan Saleh ya warwarewa Suleiman komai sedai be faɗa masa ƙauyen daya bawa su Widad mafaka ba, Suleiman yayi matuƙar girgiza da jin labarin da Saleh ya gaya masa, Saleh yace "a yanzu haka babu wani bincike da akeyi akan ɓatansu, saboda sun siye jam'ian tsaro gaba ɗaya kuma suna harin rayuwar Daula duk saboda dukiyarsa, na fuskanci idan nayi wani kyakkyawan yunƙuri a gurin ceton Daula tabbas Asirina ze tonu, kuma zasu kasheni, kaima na gaya maka dan ka sani, ka samu iyayen Yusuf ka musu bayani, dan hankalinsu ya kwanta, sannan ka gargaɗesu akan suyi shiru da bakin su "
Suleiman ya jinjina kai yace ai abunda za'ayi yanzu shine, zan ɗaukeka muje gaban mahaifiyar Yusuf kayi mata bayani da bakinka dan ta samu nutsuwa"
Saleh yace "kana ganin babu matsala?, bafa nason a ganeni"
Suleiman yace "babu wata matsala insha Allah, hankalin mahaifiyarsa ne yaƙi kwanciya, ta damu sosai"
Saleh yace "shikenan muje"
Suleiman yayi musu jagora har gidansu Yusuf, ba ƙaramin farinciki tayi ba da jin an kuɓuttar mata da Yusuf ɗinta, sedai jin an ɓoye shi a ƙauye, ga kuma bata san ranar dawowarsa ba yasa tace "Allah sarki Yusufa na, koze iya rayuwar ƙauye? Be saba ba nace ko zaku kaini in ganshi?"
Saleh yace "A'a hakan bame yuwuwa bane, akwai hatsari a cikin hakan, sedai zanyi recoding ɗin muryarki in kai masa, amma baze yuwu in kaiki inda yake ba"
Umma tace "ynzu dai dan Allah dagaske kake ya tsira baya hannun Azzaluman da suka sace shi?"
Saleh yace "tabbas basa nan, ya kuɓuta"
Umma tace "Allah kaine abun godiya, ubangiji Allah ya ƙara tsare su"
Widad kuwa wunin ranar nan ji take kamar ba ita ba, wai ita da bakinta ta Amince da Auren Yusuf, abun da tafi tsana a rayuwar ta yau da bakinta ta amince.
Amma da:ace wannan me korayen haƙoran me kama dana horo tazo ta dinga kwana da ita, ko wannan yaran nasu masu kallon jaraba, gara tayi maleji ta Auri Yusuf ɗin su dinga kwana guri ɗaya, tunda duk abu dai shi ta sani.
Widad sam bata iya cin Abincin da ake kawo musu, saboda gaba ɗaya kwanon da'ake kawo Abincin kansa idan ta kalla be mata ba ba zata ci ba, se taji kamar tayi amai, Yusuf yayi ta fama da ita ga larura tana fama, ga rashin cin Abinci.
Haka a daddafe suka kwana uku, kullum tana kan katifa, Yusuf yana bakin ƙofa a ƙasa, idan ta fito tsakar gidan nan to tare da Yusuf ne ze rakata banɗaki, shima bata shiga banɗakinsu, wannan ɗakin da ba kowa a ciki take wankanta, shima idan tayi abunda zata yi tun safe bata sake yadda ko fitsari ta sake yi.
Ko sannu bata taɓa haɗata da mutan gidan ba, shiyasa suke zaton ko bata jin hausa ma, haka suke wuni a ɗaki bata yadda Yusuf ya fita ya barta, tsakaninsa da ita sedai kallon kallo.
Babban abunda yake ƙara bata haushi be wuce yadda data fito, gaba ɗaya sesu koma kallonta ba, sekace sunga wasu halittu daban, ita tarasa meye abunda suke kallo.
Yanzu tana ɗan iyayiwa kanta wasu abubuwan, dukda bata gama warkewa ba, bata cin Abinci sosai, dukda a da ɗinma ba wani ci take ba, Yanzu kam cimar ƙauyen nan ta sha banban da irin wadda ta saba gani, gaba ɗaya kalar Abincinsu yasha banban da wanda ta saba gani ko ta saba ci.
Yusuf yana son yayiwa megari bayani, amma yana tsoron irin kallon daze masa kuma gashi besan me Saleh yace masa ba game dasu
A haka suka kwana uku, ranar kwana na ukun da yamma ba tsammani suka ji salamar Saleh, ba ƙaramin farinciki Yusuf yayi da zuwan Saleh ba, yayo musu siyayya cikin ledoji.
Saleh suka gaisa da Yusuf, yace "Yusuf ya zaman haƙuri ya me jiki kuma?"
Yusuf yace "Alhamdilillah, me jiki tana samun sauƙi"
Saleh yace "fatan dai komai lafiya, kuna lafiya kuda mutan gidan?"
Yusuf yace "Alhamdilillah komai lafiya ƙalau"
Saleh ya kalli Widad yace "Autar Daula ya jikin naki?"
Banza tayi masa ba tace komai ba, Saleh yace "hmm aike in dan halinki ne ko kashe ki za'ayi mutum baze ceceki ba, sedai amiki dan Allah dan karamcin mahaifinki, mace se tsabar girman kai da izzar tsiya, yanzu dai dole ki sauke su ki rungumi ƙaddarar da tayi kutse cikin rayuwar ki ba tare da kin shirya mata ba, ki sani abunda kika gayawa wanda sukayi garkuwa da ku, sun Sanarwa da wanda suka sa a sace ku, dan haka idanma dagaske kin san wanda suka sa a saceku inama baki sani ba kikace kin sani, sun bada umarnin a kasheku, zuwa yanzu basu san kun kuɓuta ba, da zarar sun farga kun gudu zasu saka ɗambar nemanku, dan haka idan kin gadama ki haƙura ki zauna anan na wani ɗan lokaci domin ki tserar da rayuwar ki, in baki ga dama ba kuma kiyi yadda kike so "
Yadda Widad take a kashingiɗe ko motsi ba tayi ba, balle Saleh yasa ran jin wani abu daga gareta.
Yusuf ne yace " Ayi dai haƙuri, Insha Allah zata zauna ma, kuma mungode sosai da taimakon da kayi mana Allah ya saka da alkhairi, ya Yallaɓai kuwa? "
Saleh yace "Yana nan ƙalau, dan ina daf da sanar dashi cewar kun tsira, kasan komai nima se nayi lissafi nake yinshi, domin ɓadda sahu, jiya munje gidanku na gana da mahaifiyarka ma"
Da sauri Yusuf ya ɗago ya kalle shi zeyi magana, Amma Saleh ya girgiza masa kai.
Yusuf yace "Amma ya akayi kasan wanda suka sacemu, harka kuɓutar damu?"
Saleh yace "labarin dogone Malam Yusuf, uwa ɗakinka tasa an kama ɗan uwana an tsare shi tsawon shekaru goma, akan zargin dasa hannunsa akan kisan mahaifiyarta, na haɗa kai da maƙiyanta domin in rama abunda tayi min, sedai suma maƙiyan nata kansu kawai suka sani basu da adalci, gefe guda dukda zargin da yake kan ɗan uwana mahaifinta be fasa kyautatamin ba, yana matuƙar girmamani yana kyautatamin ga kuma kai Yusuf da babu ruwan ka, shiyasa na ceceku ba dan halinta ba Wallahi "
"I don't judge based on Assumptions, what happens ten years back is still dancing in my memory, abunda ya faru a wancan lokacin ina jinsa a raina kuma ina ganinsa a idona tamkar a yanzu yake faruwa, da sa hannun Bala akan abunda ya faru, kuma ko ka ceceni ko kar ka ceceni hakan baze taɓa canza ƙaddarata ba, nasan wanda suke bibiyar abun nan tsawon shekaru suna da Alaƙa da wanda suka kashe mahaifiyata, kallona kawai kuke but am beyond your expectations, idan kaje ka ƙara tabattar musu ko bayan raina se sun Wulaƙanta se Asirinsu ya tonu wulaƙanta mafi muni a duniya "
Tuni Hawaye ya wanke fuskarta, yadda take maganar zaka san abun yana taɓa mata zuciya sosai, Yusuf yace
"Amm inaga ku bar wannan maganar, it's hurt her feelings kuma kaga bata da lafiya, dama ina son muyi wata magana da kai ne"
Saleh yace "Ina jinka"
Yusuf yace "kaga zaman da muke da ita a ɗaki ɗaya be halarta ba, tunda ba muharrama ta bace, kuma kasan ba zata yadda matan gidan nan su kula da ita ba, ga yanayi na jinya tana ciki, da nace mu raba ɗaki taƙi yadda, amma munyi shawarar zamuyi Aure, yadda zan iya jinyarta lokacin da Allah ya ƙaddara zamu bar garin nan semu rabu, da naso in yiwa megari bayani, amma ban san yadda kuka yi da shi ba"
Saleh yace "eh to ni namanta kam banyi tunanin raba muku ɗaki ba, taɓ amma wannan zaka aura? Allah ya baka haƙuri da juriya, tashi muje gurin me garin, dama Jibi in Allah ya kaimu Juma'a se'a ɗaura"
Widad dai bata tanka musu ba, suka tashi suka tafi turakar mai gari.
Mai gari na ganinsu tare yace "Masha Allah, Saleh fatan dai ba wata matsala ba suce, mun musu wani laifin bako?"
Saleh yace "Lafiya ƙalau babu wata matsala, munzo da wata 'yar magana ne"
Maigari yace "Masha Allah"
Saleh yace "Ina son in Allah ya kaimu jibi da rai da lafiya, ka ɗaurawa baƙinka Aure"
Buɗe baki Maigari yayi yace "dama ba matarsa bace?"
"Eh ba matarsa bace, ƙanwarsa ce hatsarin ya ritsa dasu tare kamar yadda nayi maka bayani, 'yar uwarsa ce amma da Aure a tsakanin su"
Maigari yace "Shikenan babu laifi, amma hakan baze kawo matsala ba idan suka koma gida?"
Saleh yace "kaikam Baffa ba dai tsoro ba,' yan uwane fa kuma ba lallai su koma gida nan kusa, se rigimar da'ake a garinsu ta lafa"
Maigari yace "Shikenan Allah ya kaimu, idan anyi sallar Juma'ar se' a ɗaura"
Saleh yace "yawwa Baffa godiya muke, nima ina nan bazan tafi ba se Allah ya kaimu juma'ar idan an ɗaura Auren"
Maigari yace "to madalla babu laifi"
Suka fito shida Yusuf, Yusuf yace "nikam me ka cewa Maigari ne a kanmu?"
Saleh yace "kasan mutumin ƙauye, kawai kifeshi nayi, nace masa faɗan ƙabilanci ake a garinku, kun samu kun tsira da ƙyara akan hanyarku ta guduwa kuma akayi garkuwa daku, har yanzu garinku babu lafiya"
Yusuf yayi murmushi yace "Allah sarki, yana da kirki da karamci kam,
Amma nifa bani da sadakin da zan bayar"
Saleh yace "karka damu zan bayar, Allah yasa Auren ka yayi silar shiryuwarta daga wannan baƙin taurin kan da izzar, shegiya me kama da Aljanu"
Yusuf yace "dan Allah kadena zagin ta, bana jin daɗi idan ka zageta, ɗazuma ka sata kuka"
Saleh ya yamutsa fuska yace "Yusuf ina zaton kana son yarinyar nan ne, in bahaka ba tun a baya su Nura dama sunce baka ganin laifinta, da'an mata abu sekaji haushi"
Yusuf yayi murmushi yace "Saleh, duk ɗan adam tara yake be cika goma ba, duk rashin kirkinta akwai halayenta masu kyau, su kansu su Nuran yanzu zasu gane Amfaninta"
Saleh yace "eh amma rashin kirkinta yafi kirkinta yawa ai"
Yusuf yayi murmushi yace "koma dai yane ni nasan tana da kirki ai, amma dagaske kaje gidanmu? Ya akayi kasan gidanmu?"
Saleh yayi murmushi yace" Yusuf kenan, har gurin aikinka nasani kai jami'in tsarone na farin kaya"
Gaban Yusuf ne ya faɗi "ya akayi kasan hakan?"
"saboda ina tare da maƙiyan Daula, binciken da'aka saka ma duk cikin shirinsu ne, ni naje na shirya komai, ba lallai kasan komai yanzu ba, amma anaso ka gama ka tattara bayanai akan binciken se akai sama, su kuma su karɓa su basu, duk cikin ƙoƙarin su na goge duk wata sheda da zesa asan sunawa Daula da 'yarsa zagon ƙasa, sedai basu san cewar kai aka saka kayi binciken ba, sudai kawai zaman jiran sakamakon bincikenka suke, basu san kaike binciken ba shi kanaa me gidanka Suleiman be san hakan ba, sedai akwai wani abokin aikinka da nayi connecting dashi, da zimmar idan ka gama binciken ya dinga bani wasu bayanai daga abunda kake binciken, sedai bazan gaya maka waye ba"
Shiru Yusuf yayi gaba ɗaya kansa ya gama kullewa, kenan dama duk wannan wahalar da yake sha shirine, jiki a sanyaye yace "Widas tasan koni waye?"
Saleh yace "Yadda take shiri haka maƙiyanta sukeyi, sannan da ta san kai waye, wallahi da yanzu kana prison saboda bata yafewa wanda yayi mata ƙarya koya yaudare ta, kayi fatan Allah yasa ta fara sonka kafin lokacin da zata san ko waye, wataƙila ta sassauta maka"
Gaba ɗaya Yusuf yayi shiru ya rasa abunda yake masa daɗi.
Saleh yace "zomu je mu ɗan zazzaga, kaga yanayin yadda ƙauyen yake"
Haka akayi Yusuf yabi Saleh, garin yana da kyau sedai ƙauyen ƙayau ne, babu ababen more rayuwa sam.
Ramlah tasha kwalliya cikin wasu ƙananan kaya, tayi kyau sosai, tana zaune a falo tana kaɗa ƙafa, aka kirata a waya, tana ganin me kiran ta miƙe tsaye, ta ɗau ƙaramin gyalenta ta yafa tace "Mummy yazo bari inje"
Hajiya Halima tace "shikenan sekin dawo"
Amal tace "wallahi Ramlah baki da aji, daga zuwansa harkin miƙe kina rawar ƙafa zaki fita da nice da yanzu kina nan kinamin surutu, wani banza dashi gwalagwaji se shegiyar ƙarya da iyayi"
Ramlah a fusace "Mummy kinga kiyiwa Amal magana ba ruwanta dani"
Mummy tace "Amal kar in ƙara jin bakinki a gurin nan"
Amal ta kwaɓe fuska tace "eh ai tuni na gane, kin fi son Ramlah akaina, damuwar ta ce kawai damuwa ni kuma baki damu dani ba, shikenan"
Ta miƙe fuuuu ta bar falon, Ramlah tayi waje abunta, a harabar gidan taga Fahad sanye da ƙananan kaya da tabarau yana tsaye a jikin motarsa, ta ƙarasa gurinsa tana wani yauƙi, tana ƙarasawa inda yake ya rungume ta, ba kunya ba tsoron Allah suka fara kissing ɗin juna a gaban ma'aikatan dake gurin, Fahad ya zame bakinsa a hankali yace
"you look so cute Baby"
Ramlah tace "Really, you look good too baka ga yadda kayi kyau ba"
Ya riƙo ƙugunta yace "mu tafi ko"
"Ke Ramlah!" muryar Anwar ce cikin fushi yace "meye haka? Baki da hankali ne? Malama wuce ki koma gida"
Fahad yace "kamar ya ta koma gida, meyasa kake hakane Anwar"
A tsawace Anwar yace "zaki koma ko sena ɓaɓallaki a gurin nan, ballagaza kawai"
Da sauri Ramlah ta jiya da gudu cikin gida.
Anwar ya kalli Fahad yace "Fahad kayi Asara wallahi, ita waccan da kake iƙrarin zaka aura baka samu ba, shine ka dawo zaka lallaɓa ka lalata ƙanwata, meyasa baka da imani Fahad, kana da 'yar uwa mace fa, baka tsoron ayimata abunda kake wa' ya'yan wasu, ya zakaji idan wani yayiwa Iman abunda kake yi "
Be rufe baki ba ya jiyo muryar Hajiya Halima tana masifa
" Anwar meye haka, yaushe ka zama haka? Ya zasu fita da yarinya zaka ce ba zata ba, tunda wannan shashashar ta ɓata ai ita ze Aura, me zesa ka kore ta haka akeyi? "
Anwar kamar zeyi kuka yace
" Mummy ke uwace, kamata yayi kisa ido sosai akan Yaran nan, yanzu ya dace Ramlah tabi saurayi da yammacin nan, kalli suturar dake jikinta fa"
"rufemin baki ko in gaggaura maka mari, ke wuce ku tafi"
Anwar yana kallo Ramlah ta shige motar Fahad, yayin da Fahad ke masa wani irin kallo na ya kaga lamarin.
Anwar dama Asibiti zashi gurin Alhaji Nasir, dan haka be sake cewa komai ba ya juya ya tafi.
Nura yace "Bala'i ana shegiya a gidan Nasir Daula, duk iskanci shigar banza da izzar Gimbiyar Daula ban taɓa ganin ta aikata makamancin abunda wannan kwazgwamar tayi a gaban mu ba"
Isa me gadi yace "kaidai bari Nura, ai iskanci guri yake samu, kai da Yarinyar nan tana nan waya isa ya shigo gidan nan ya aikata wannan baɗalar, kuma wallahi kayan basu yiwa wannan shegiyar Ramlan kyau ba, wanka ai se Gimbiyar gidan nan, kaga kaya cas a jikinta kamar ita tayi kanta"
Nura yace "kai dai bari Malam Isa, ni se yanzu nake ganin Amfaninta a gidan nan, duk wulaƙancinta idan tana nan se an bamu Abinci sau uku a rana munci mun ƙoshi a gidan nan, amma kalli yanzu sau ɗaya ma ba'a bamu"
Isa yace "kai ba wannan ba, nifa ban gane kan wannan matar ba, kofa Asibiti basa zuwa, Anwar ɗin nan ne kawai yake zuwa yana kula dashi su kuwa ko a jikinsu"
Nufa yace "Hmm kai dai bar kowane munafuki inda ka ganshi, kallon mutan gidan nan kawai nake yi"
A kayan da Saleh ya kawowa su Yusuf, hadda kayan sawa ya kawowa Yusuf, dan Widad Akwatinan ta akawai kayan sawa, ya kawo musu man shafawa da sabulun wanka, dasu Omo, ya siyo musu sabon risho, da fitila sekuma kwalin batir, saboda garin ba Wuta.
Rana bata ƙarya sedai uwar ɗiya taji kunya, Ranar Juma'a bayan an idar da sallar juma'a aka ɗaura Auren Yusuf da Widad akan sadaki naira dubu goma sha biyar, shi kansa inda masallacin juma'ar nasu yake se anyi wata uwar tafiya daga nan inda su Yusuf suke kafin aje, ga shi duk ya lalace ya fatattake.
Nurat ce zaune a ɗakinta da system akan cinyarta, a hankali ta zare earpiece ɗin kunnenta tace "Alhamdilillah, done with this chapter"
Ta ɗakko wayarta ta
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 26 Chapter of 35