kiraka to lallai akwai abinda take bukata a wajenka. Haka kuma da yake Anty Hauwa din tana aiki da WHO ne, su kan ziyarci garuruwa daban-daban, kuma tana yawan zuwa Kaduna. Duk lokacin da zata shiga Kaduna to sai ta lalubi Nadiya sun gaisa. Madam Zarah kuwa idan ba kai kaje inda take ba, to ba zata nemeka ba.
Dakin da zata sauka Aisha ta rakata, nan kusa da na Dada Iyani yake. Dakin yana da fadi, ga katifa babba da aka yada an shimfida mata sabon zanin gado. Ta ajiye akwatunta a gefen Katifar kafin ta fada bandaki ta watsa ruwa. Jikinta a matukar gajiye yake, ko'ina na sassan jikinta ciwo yake yi mata.
Bayan ta fito sallar da aka biyota tayi, kafin ta tashi ta nade abin sallar.
Zanine a jikinta wanda ta dora akan doguwar rigar barcin jikinta. Ta koma falo inda ta samu har Dada ta tafi ta kwanta sai Aisha da take kallo, Al-Ameen kuma yana barci.
Aisha ta daga kai tana kallonta, "yauwa, Adda, jiran fitowarki nake yi dama. Me za a kawo miki ki ci ne?"
Ta zauna yaraf a kan kujera tana mike kafafuwanta, tace, "gaskiya babu abinda zan iya ci yanzu saboda barci nake ji kwarai da gaske. Amma bari in shiga in hada shayi haka sai in sha kafin in kwanta."
Tace, "to bari in hada miki. Zauna huta naga alamun kin gaji sosai."
Cikin mintuna biyar kuwa ta hada mata shayin mai kauri, ta kai mata da burger wadda da alama daga oven ta fitar da ita saboda taji da dumi.
Ta ajiye kayan a gabanta tana dan murmushi, tace, "Madam ce ta kawo mana ita dazu. Kin san Dada ba cin irin wadannan abubuwan take yi ba shine aka ce bari a ajiye miki."
Ta dauka tana ci tana karewa hanyoyin da dakunan gidan suke kallo, tace, "ban ma ganta ba tunda nazo. Ko har ta kwanta ne?"
Aisha tace "wai Madam? Ai tunda yamma ta tafi gidan da take sauka."
Sai ta kame bakinta tayi shiru. Sam ta manta fa tunda dadewa take jin an ce Madam din gida ta gina na musamman wanda take sauka a cikinshi idan taje Maidugurin, saboda a cewarta wai can yafi tsaro.
Suna hira sama-sama har ta cinye burger din. Ta kai kayan kicin, ta dauki gorar ruwa ta yiwa Aisha din sai da safe wadda take ta kokarin tashin Al-Ameen ya wuce dakin da samarin gidan ke taruwa ya kwanta, ita kuma ta wuce wajen Dada tunda a can take kwana.
Tana shiga dakin baki kawai ta wanke ta yiwa kan katifa tsinke. Sama-sama suka gaisa da su Mama kafin ta kashe wayar gabadaya saboda mayen barcin dake janta kamar magnet.
Ranar sallar Asubahi ma sai da aka buga mata kofar daki. Ta tashi tana mika, har lokacin gajiyar bata barta ba. Sai lokacin taga alamun ta makara ashe don kuwa tuni gari ya fara haske.
Ta tashi da sauri ta dauro alwala ta yi sallah.
Bata koma barci ba, ta fita taje suka gaisa da Dada kafin suka shiga kicin ita da Aisha suna hada abin kari.
Suna aiki suna hira tana bata labarin bikin da za a fara a washegari. Wanda yarinyar zata aura dan gidan Sarkin Potiskum ne, shi yasa ake ta zuzuta bikin ba ji ba gani, ga kuma iyayen amaryar da suka kasance suma ba kananun masu kudi bane.
Iyalan Alhaji Idris Nalado, iyalai ne da suka yi kaurin suna a cikin garin Maiduguri. Ko ba daga bangaren arzikin da Allah Ya wadatasu dashi ba, kasancewarsu zuriya masu kyau kadai ya isa ya sanyasu a cikin jerin lissafi. Yawancinsu Kanuri ne gaba da baya, sai kuwa kalilan da suka kasance hadi da shuwa da kuma bafulatanai.
Shi Alhaji Nalado daya kasance shine Kakan Madam Zarah, mutum ne mai rufin asirinshi dai-dai gwargwado. Kaninshi kuma Alhaji Kachalla wanda suka hada uba daya dashi, shine mai arzikin. Sai dai sun taso kansu a hadene duk da kasancewarsu iyayensu mata daban. Kuma kasancewarsu manya a gidan, sun yi iyaka bakin kokarinsu wajen ganin cewa sun hada kawunan sauran kannansu da kuma 'ya'yansu waje guda.
Sai dai duk hakan ya zamana a kawai ne bayan da suka rasu. 'Ya'ya kowa ya kama harkar gabanshi. Hakan yasa suka tashi kai a ware, wani ma sai ya girma ya tashi da wani amma bai san dan uwanshi bane.
Mahaifin Madam Zarah Alhaji Lamin, shine babban da ga Alhaji Nalado, yana da kanne mata biyu da namiji daya. Mahaifiyarshi asalin shuwa ce, kuma da mafi akasari 'ya'yansu ita suka biyo, sai suke tashi tamkar wasu diyan larabawa saboda haske da kuma kyau. Duk cikin 'ya'yanta kuma babu wanda ya dauko kyawunta kamar Lamin din, wasu su kan ce idan ka ganinshi sai kayi zaton ko dan aljanine saboda tsabar kyau.
Bayan rasuwar Alhaji Nalado, rayuwar iyalanshi ta so shiga rikici saboda halin babu da rashi da suka shiga. Da ba don Alhaji Kachalla ba kam da basu san irin halin da zasu shiga ba.
Shi yayi ruwa yayi tsaki wajen kulawa da 'ya'yan marigayin, ya dauki Lamin ya mayar dashi cikin gidanshi da zama inda matarshi, Uwale, wadda ta kasance haifaffiyar garin Kaduna ta rike shi hannu bibiyu. Basu taba samun haihuwa da Alhaji Kachalla ba, kusan sau hudu tana samun cikin tana b'ari, ta haifi wani sau daya shima ko satin haihuwa bai cika ba ya koma.
Lamin ya cigaba da zama a hannun Alhaji Kachalla inda ya sanyashi a makaranta, a gefe guda kuma yana cigaba da daukar dawainiyar mahaifiyarshi da sauran kannenshi.
Cikin ikon Allah kwatsam sai Uwale ta samu ciki, tun suna taraddadin zubewarshi har dai suka saduda, da lokacin haihuwa yazo ta haifi diyarta mace sankaceciya aka sa mata suna Ummulkhairi. Lokacin kuwa Lamin ya haura shekaru sha biyar a duniya.
Tafi-tafiya rayuwa na ta juyawa, Lamin ya girma ya zama magidanci. Idan ba sani kayi ba, baka taba cewa ba Alhaji Kachalla bane ya haifeshi. Bayan Ummulkhairi Uwale ta sake haihuwar wata diyar taci sunan Sumayya.
Duk wasu harkokin Alhaji Kachalla suna hannun Lamin, shi yake kulawa dasu, kai sai da ta kai ta kawo ma gabadaya duk wasu shaguna nashi da kadarori Lamin dinne yake kulawa dasu, shi ya zamana kawai dai yana zuwa ya dan kewayasu ne ya dawo.
A haka cuta ta farat daya ta kamashi. Aka shiga zarya asibitoci da wajen Malaman gargajiya. Bayan doguwar jinya dai daya sha, daga karshe dai yace ga garinku nan.
Fadar irin tashin hankalin da iyalinshi suka shiga a wannan lokaci ma bata baki ne, sun yi kuka ba na wasa ba.
Aka yi zaman makoki aka gama, dangi da 'yan'uwa suka watse. Aka zauna aka zubawa Lamin idon ya tattara dukiyar mamaci ya ba magada amma shiru kake ji kamar an shuka dusa. Da aka ji shiru sai Uwale ta tunkareshi da kanta ita da yayanta da yaje daga Kaduna lokacin.
Ya rufe ido rikif ya hau fadan shi wata dukiya ke a hannunshi bayan wadda aka cinye a zaman jinyar Alhajin? Idan lissafi suke so ayi to su jira yayi lissafin, amma su kuka da kansu duk abinda zai biyo baya su suka ja saboda yana da tabbacin idan har yayi wannan lissafin to ko gidan da suke zaune a ciki ba zasu tsira dashi ba.
Aka kada aka raya, amma mutumin nan yace shi fa babu ko asin kwabo a hannunshi. Mahaifiyarshi kuma ta mara mishi baya.
Wannan dalili dai shi ya kawo lalacewar zumuncin wannan ahali. Dama tsakanin Uwale da Salma ba wani zumuncine na azo a gani ba, suna yi ne don ganin idon mazajensu ba wani dalili ba.
Daga baya dai zance har sai daya kaisu ga shiga kotu. Sai a kotun ne da yaji matsi ya dauki takardun filaye biyu ya bada a cewarshi abinda ya rage kenan. Shaguna kuwa duk babu kaya a ciki kuma ya sayar dasu, wai ai lokacin da Alhajin yana jiyya da su aka dinga amfani.
Da haka dai zance ya kare saboda babu wasu takamaimun shaidu da zasu karyata zancenshi. Saboda ko da Alhaji Kachalla din yana raye shi dai bai cika fadin iyaka adadin dukiyarshi ba da abubuwan daya mallaka. Shi Lamin din shi ya san komi. Ya kuma zambacesu da hakan.
Babu jimawa da yin hakan ya kyankyatsa ginin gidanshi mai kyau kamar a gidan sarauta, ya je cikin dangin mahaifiyarshi ya samu budurwa lafiyayya aka daura musu aure ta tare.
Shekara kwana ga mai yawan rai, abubuwa da dama kuma sun faru cikin dan kankanin lokaci. Mahaifiyarshi ta rasu jim kadan bayan da Iyani ta haifi Yasir. Tsakaninshi da Hauwau shekaru biyu ne. Bayan wasu yan shekarun kuma ta sake haihuwar Fatima Zahra.
Arziki kullum yana ta tumbatsar mishi, dukiya da duniya sun zauna mishi sosai yan ta facaka yadda yake so. Sam ya manta da marayun Allah da ya ci amanarsu ya tauye musu hakkinsu. Bai ma san a wani hali suke ciki ba tunda ba bibiyarsu yake yi ba. Danginsu ma kuwa kowa ta kanshi kawai yake yi, daga yan karkashinshi yan abi yarima a sha kida wadanda dukiyarshi suke wa, sai masu jin tsoron su tankareshi da maganar saboda kada ya daina hidimta musu, sai kuwa yan babu ruwana wadanda suma suna da nasu arzikin.
Rana guda kawai suka tashi da mutuwar Uwale, ashe rashin lafiya tayi da jinya sosai bai ma sani ba.
Yaji ana cewa dai taso ta koma can Kaduna da yaran, amma wasu daga cikin dattawan yan'uwansu suka hanata saboda sun san cewa idan ta tafi to bata da dalilin dawowa, zumunci da yaranta kuma zai yanke.
Amma su da suka hanata tafiyar kuma sun kasa tsaye mata. Dan sauran abinda ya rage na kadararta duk an siyar wajen jinyarta.
Ya kai kayan abinci ya zube musu, aka yi zaman makoki aka gama. Danginta da suka je suka hade kayanta waje guda tsaf, ba tare da sunyi shawara da kowa ba, ana yin addu'ar bakwai suka hade kan ya'yanta suka tafi. Sai zuwa aka yi aka samu gida kwalam. Daga baya ma ake jin cewa ashe an sayar da gidan shima.
Daga wannan tafiya da Ummulkhairi tayi da kanwarta bata kara bibiyar danginta ba.
Alhaji Lamin tuni shima ya shafe babinsu a rayuwarshi. Ya cigaba da fantamawa da facakarshi yadda yake so.
Daga baya ma sai ya yanke shawarar zai tsunduma harkar siyasa ne tsundum. Ya kuma fita din da karfinshi, nan da nan sai gashi yayi suna a ciki da wajen Maiduguri.
A kuma daidai wannan lokaci ne da yake ganin cewa tauraruwarshi ta gama yin hasken da babu abinda zai iya dusasar da ita, ta dauke wuta gabadaya.
Shagunanshi suka fara kamawa da wuta, kafin a samu a kashe wutar sai komi a cinye sai dai a tadda toka. Sai kwantainoni da suka dauko mishi kaya suka fara nutsewa a ruwa, masu kuma a kama.
Ya fara daga kadarori yana sayarwa, yana bin kan yan siyasa da manyan yan sanda da customs kan a sakar mishi kayan da aka kama, gefe guda kuma yana cigaba da kamfen dinshi.
Kafin shekara ta zagayo ya tashi a huhun-ma'ahu. Shi ba ga kudi da kadara ba, shi ba ga siyasa ba.
Tuni magoya bayanshi suka juya mishi baya da suka ga shima nema yake yi a wajensu, wadanda suka tsaya kalilan ne, suma don su karasa cinye yan canji daya rage mishi ne. Sune masu zuga shi da kara dorashi kan turbar bin malamai, suna kara gaya mishi lallai fa idan zabe ya zo to lallai zai cinye. Shi dai kawai ya saki kudi ya bada ana mishi sadaka da sauka, anan sauran yan kudaden nashi suka lume.
Kafin ya ankare zabe ya zo, kungiyar adawarsu ta ci. Ai hauka ne kawai bai yi ba a lokacin.
Sai gashi shine ya koma yana bin yan siyasa yana musu kanzagi da roko. Rayuwa dai ta juya mishi baya shi da iyalanshi, kamar ba a taba yi ba.
Su Fatima da suka taso cikin gata da jindadi da facaka, lokaci daya rayuwa tayi musu juyin bazata. Ta dilmiya su cikin garari da fadi-tashi.
Tana kan ganiyar yanmatancinta. Rayuwar dadi ta tashi a ciki, kuma ita ta sani, jinta cikin babu da rashi bakon abu ne a wajenta, wanda kuma ba zata iya dauka ba. Ta kasa hakurarwa kanta kamar yadda sauran 'yan'uwanta da iyayenta suka yi.
Ta daukarwa ranta alwashin, komai tsanani da wuya, sai ta sake taka matakin daula, sai ma gabanta ta fi bayanta kyau.
A gefe guda, a can Kaduna kuma. Mace daya ta sha alwashi kamar na Fatima, sai dai ita tayi ne domin ta rama wulakancin da aka yi mata. Ta ci alwashin tara kudi da mulki da duniya domin ta saka sharri da sharri. Ta ci alwashin jefa rayuwar Alhaji Lamin cikin garari irin wanda bai taba shiga ba, shi da iyalanshi, har ma da tattaba-kunnenshi, babu wanda zata bari! Wannan kenan.
8
*WACECE NADIYA?*
Alhaji Auwal Iko wanda aka fi sani da 'Dan Iko', irin yan kanzagin yan siyasar nan ne da sarakuna wanda hakan ya samu asaline tun yana dan kankaninshi daya taba aikatau a gidan wani Sanata.
Iyayenshi talakawa ne tilis, haifaffun cikin garin Kaduna ne. Mahaifinshi ya rasu tun yana dan kankani, mahaifiyarshi ita ta raineshi har zuwa lokacin daya girma.
Bai yi karatun boko ba, na almajiranci ma da aka kaishi ki yayi ya gudo. Yarone mai matukar rashin ji da ra'ayin rikau, don dole mahaifiyarshi ta gaji da kaishi almajircin ta kai idanu ta zuba mishi. Da dan jarin da take ja na koko da kosai ta kaishi makarantar Arabi da boko, su dinma yaje yau ne gobe yaki zuwa.
Lokacin daya fara zama matashi ya samu aikin wanki da guga a gidan wani Sanata, yana kuma yi musu yan share-share da gyaran gida. Tafi-tafiya ya zamana ya fara yin suna a gidan saboda shi mutum ne mai shiga jama'a sosai kuma baya da shayin shiga ko'ina. A haka mai gidan ya fara sanyashi kananun ayyukan gida, a hankali sai gashi har ya zama direbanshi. Daga nan kuma ya zama na hannun damarshi wanda yake sanyawa yayi mishi yan ayyukansu na yan siyasa. Yau shine wajen wannan Malamin karbar taimako, gobe shine wajen wancan, jibi shine wajen wannan basaraken neman gindin zama da fadanci. Nan da nan sai yayi wani irin kaurin suna, kafin kuma kace me sai gashi ya fara tara yan canji.
A cikin wannan yanayi ya taso. Har zuwa lokacin da likkafa ta ci gaba lokacin da yayi sabon Ubangida wanda ya zama Gwamna.
Shi ya damka mishi filin gidan da yake ciki saboda yabawa da tsayawa da yayi ka'in da na'in ya goya mishi baya. Ya kuma bi shi da kudade masu kauri yace yayi gini dasu. Da yake kuma aure yake so, sai bai yi sanya ba ya tayar da gininshi.
Zance na gaskiya Auwalu akwai tsilla-tsilla, don kuwa babban dalilin da yasa yafi yin kaurin suna wajen abokan huldarshi shine yadda babu ruwanshi da bambance tsakanin aiki mai kyau ko marar kyau, in dai zai samu kudi, to shi fa babu abinda ba zai iya yi ba. Har mata yake dauka ya kaiwa mutanen nashi su biya shi. Harka irin wannan kuwa tafe take da rufewar ido da zuciya, kafin kace me kuwa, ya fada harkar bin mata ruwa tsundum. Mutum ne marar mafadi, babu wanda ya isa ya sanyashi abinda bai yi niyya ba sai dai mahaifiyarshi da a lokuta da dama ita ce take da wannan fadar. To itama ba kullum ba, harkar bin mata dai babu irin fada da nasiha da bata yi mishi ba, daga baya dai sai data dawo ta dinga binshi da addu'a kawai.
Cikin yawace-yawacen da suke yi ne Allah Ya kaisu wani kauyen Wuro-Yanka a can cikin Yola. Mazauna garin Fulanine usul, sai dai mafi yawancinsu fulanin yawo ne, watau wadanda basu da takamaiman gari ko wajen zama. Idan sun je waje ya musu, zasu zauna na iya adadin wasu kwanaki ko shekaru, daga nan kuma su kara gaba.
Anan Allah Ya hadashi da Juwairah. Bafulatana ce danya shataf, idan ka ganta kyawunta kamar wata diyar Aljanu. Allah Ya sanya musu kaunar juna kamar me, sai dai iyayenta suka ce ba zata auri bare ba. Babu ta inda bai bi musu ba amma suka ki, daga karshe dai ya zugeta suka je Dagacin garin ya daura musu aure da yaga iyayen kudin da Auwalu ya zube mishi. Iyayenta na jin haka suka ce aikuwa haihata-haihata ita dasu, sun yafeta har abada.
Nan fa idanunta suka raina fata, don kuwa cikin dadin bakin da yayi mata har da cewa in dai aka dauro musu auren to kuwa dole ma iyayenta su amince, sai kuma akasin hakan ya faru.
Ya kara kalallameta da wani dadin bakin, yace mata ai fushi suka yi da ita, amma zasu sauko. Don haka ta basu dan lokaci, daga baya zasu hakura.
Giyar kauna da dadin bakin Auwalu, da yake gwanine ta wannan bangaren, ta kwasheta, ta biye mishi ta bi bayanshi kamar yadda yace zuwa gidanshi daya gina a Kaduna.
Mahaifiyarshi Inna Deluwa sai ganinshi tayi da bafulatanar mata sama-ta-ka.
Da yake tana zaunene a nata gidan na daban, dan tsamurmurin wajene da marigayi maigidanta ya bar mata gado ita da Auwalun.
A gidan nata ya sauka da amaryarshi, wadda ta kasa ko motsin kirki saboda tsabar kunya data lullubeta.
Daya gama mata bayanin abinda ya faru, idanu kawai ta zuba mishi ta kasa cewa komi. Ji tayi kamar ta kama shi tayi ta hada kanshi da bango ko Allah Yasa ta huce takaicin maganar da Auwal yake daukar mata.
Ta kara kallon budurwar, yarinya ce danya shataf, bata tunanin zata haura shekaru sha biyar. To shima ba wani girma yayi ba, duka-dukanshi a lokacin ba zai haura ashirin da biyar ba, rigima ce kawai irin tashi.
Taga dai idan tace ma fada zata mishi bata baki ne, don kuwa abinda ya faru ya riga ya auku dai, sai dai fatan Allah tsare gaba. Watakila kuma hakan zai iya zame mishi sanadin shiryuwarshi da daina bibiyar matan da yake yi. Ga amaryar tashi da take a takure, tana tsoron tayi mishi fadan a gabanta taga kamar kila bata yi na'am da ita ba.
Don haka ta rufe zancen fada. Ta gyara mata mazauni tare da tashi nan-da-nan ta tayar da sanwa ta dafa musu abinci.
Zuwa bayan isha'i sun gama hutawa, sun ci sun koshi. Ya tashi tafiya bayan ya dawo sallah, ya nemi amaryarshi da taje su tafi gida. Inna Deluwa tayi kicin-kicin da rai tana kallonshi, tace, "wane gidan?"
Fir! Ta ki ya tafi da ita ko'ina tace har sai yayi mata garar kayan dakI sannan. Rai cune ba don yaso ba haka ya tafi.
Shi yasa har a yau da take ba a raye ba, Mama bata taba ganin suruka irin Inna Deluwa ba. Don kuwa ta mata halaccin da ba a taba yi mata ba. Ita ta tsaya tsayin daka sai da Auwalu ya mata jeren daki tsaf kafin ta tare, ita kuma tayi mata gara irin wadda uwa take yi. Duk kuma wanda ya tambayi dangin Juwairah zata ce diyar 'yan'uwanta ce dake Adamawa. Da haka sai ya zamana 'yan'uwanta sune suka dawo 'yan'uwan Juwairah din.
Ita dinma kuma da yake bata da hayaniya da kwaramniya, gata mace mai kawaici da hakuri, sai tasu ta kusan zuwa daya da mutane.
Ko lokacin data haihu ta haifi danta namiji AbdulHadi, haka Inna Deluwa ta sake daukarta ta maidata gidanta wanka. Ta kuma yi mata duk wata al'ada da uwa take yiwa yar ta idan ta haihu. Lokacin shekarunsu biyu da yan watanni da aure.
A kuma wannan zaman jegon ne komi ya sauya a zamanta da Auwal. Gabadaya sai ya bi ya canza mata, wulakanci iri-iri babu wanda baya yi mata ita da danta, ashe wata yar kyakkyawar budurwa ce ya kyalla ido ya hango.
Tana komawa gidanshi ko wata biyar cikakke bata yi ba, ya dankaro mata amarya ya kai.
Sai a wadannan lokutan ne Auwalu yake bambance mata tsakanin aya da tsakuwa, don kuwa yadda ya rufe ido ya dinga nuna kamar ita da babu duk daya a wajenshi abin babu kyan gani.
Inna Deluwa tayi fadan, tayi nasihar, tayi ban bakin, akan ya tuna yadda yaje ya rabota da danginta ya kawota cikin nashi dangin da bata sani ba, kuma duk ta dalilinshi. Daya daga baki sai yace ai ita tayi radin kanta ba tursasata yayi ba. Wannan maganar ta matukar bakantawa Juwairah rai, tayi mata zafi sosai.
Amaryar tashi ko wata shida bata yi ba suka rabu. Kuma kafin a rufa watanni biyu ya sake yin wani auren. Nan da nan sai ya zamana wani idon mata. Mace duk inda ya kyalla idanu ya ganta to shi dai kawai ya aureta. Wanda abin takaicin daya samu abinda yake so a wajenta sai kuma wulakanci ya fara biyowa baya wanda kafin kace me sai a zo a rabu.
Ana cikin wannan yanayin sai ga amaryarshi ta biyu ta kai mishi dan jinjirin data haifa a gidansu wanda shima ba karamin rikici aka ci da Auwalun ba kafin ya kai ga sayen abin yanka. Abinda aka kayyade mishi kuma na maijegon da jinjirin ba kaiwa yake yi ba, don haka tana yayeshi ta kai mishi kayanshi.
Ana kaiwa kuma ya ba Juwairah shi yace ta hada da nata ta kula dashi, nan ne ita kuma tace ba zata yi ba. Ba zata kula da dan da bata haifa ba. Da wanda ta haifa ma ya ta kare?
Anan kuwa suka yi tashin hankalin da basu taba yi ba har ya kai ga mata gorin dangi, daga baya ma yace ta tafi wajensu duk da bai furta mata saki ba.
Bata yi shawara da kowa ba ta tattara yan kudadenta ta dauki danta, asubahin farko ta bar garin.
Sai dai abin ban tsoron shine da taje Adamawa bata samu yan'uwanta ba. A can ake ce mata ai sun fi shekara da barin garin kuma babu wanda yasan inda suka tafi kuma babu wanda ya bar mata sakon inda zata samesu koda taje nemansu daga baya.
Nan fa ake yinta. Idanunta suka raina fata data fahimci cewa bata da wata madafa ko mafita. Gidan Dagacin garin ta zauna na yan kwanaki tana tunanin mafita da tunanin abinda yakamata tayi a daidai wannan lokaci.
A kwanakinta na uku da zuwa garin ne Dagacin ya nemeta da zancen ya kamata fa tasan inda dare yayi mata, saboda shima dawainiyar dake kanshi da iyalinshi ta mishi yawa, gata kuma da danta yana kulawa dasu suma.
Ta kasa ce mishi komi sai idanu data dinga binshi dasu cikin tsananin mamaki da tu'ajjibin yadda dan'adam kan iya canza hali daga mumini zuwa dan iska. Kodayake, a wancan lokacin ai kudi ya gani, a wannan karon kuwa da ita ce take ci mishi kudin dole yayi mata wannan dibar albarka.
Ta iya daga baki da kyar ta ce mishi to ta gode da dawainiyar da yayi da ita. Ta kuma kara da cewa kuma Allah Yayi mata sakayyar abinda suka aikata mata. Idan har sun shiga hakkinta, to bata yafe ba.
Ta tashi daga gabanshi ta barshi yana mata ihun shi bai ga alkaba'in daya aikata mata ba tunda dai ai da kanta ta amince a daura mata auren da wanda iyayenta basu yarda ba, ba wani ya tursasata ba. Ta kwashi yan komatsanta tayi sallama da matanshi ta tunkari tashar mota.
Rasa inda zata nufa tayi, a iyaka tunani da tayi, ba zata iya cewa ga asalin iyayenta ba. Daga ina suke, ina suke nufa, ba zata iya fada ba.
Dai-daikun garuruwa kadai zata iya tunawa inda suka zauna, saboda duk inda suka je ba wani zama suke yi na azo a gani ba. Wuro yanka yana daya daga cikin garin da suka jima a cikinshi. Tasan ko tace zata shiga duniya neman danginta yana dai-dai da cewa tayi damarar neman jaki mai kaho, wanda yake abu mai kamar da wuya gurguwa da auren nesa. To amma ina zata nufa kenan?
Ta biya kudin motar Kano ta shiga. Aka yi ta tafiya kamar ba za a kare ba, sai can talatainin dare sannan suka
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 5 Chapter of 36