basu gawa suka tafi gida da ita, kafin su je gida zancen rasuwar ya zagaya dangi. Wai sai lokacin ne duk kuma suka hadu, suka je suka yi ta matse-matsen hawayen da ta kira na munafurci.
Lamin yaje da kayan abinci ya jibge musu bayan an dawo daga janazarta. A lokacin ne ta tashi ta musu wani dan karamin bori, ta musu tatas daga shi har dangin nashi akan banzatar da su da suka yi. Ta kuma ce a fitar musu da wannan kayan abincin na haram, ko ta konasu. Bata san ya aka yi da kayan ba, don shi Lamin din da tayi hakan dominshi ma tuni ya dade da barin gidan. Bai san tayi ba.
Yayan mahaifiyarsu wanda ya kasance shi kadai ne shakikinta, ya yanke shawara da mahaifiyarsu cewa zai sayar da gidan da suke ciki kawai tunda dai yanzu ya zama na magada, ya daukesu a mayar dasu gabansu kawai. Don basu san irin halin da zasu shiga ba idan suka barsu anan.
Ita kuma tayi na'am da hakan, sai ta bashi shawarar kada su sanar da kowa amma. Gudun kada su sake hanasu tafiya da su kamar yadda suka yi a bayan rasuwar Alhaji Kabiru. Kafin zagayowar bakwai kuwa aka sayar da gida, suka hade kan kayansu tas, ba tare da sunyi sallama da kowa ba suka koma Kaduna.
Ummulkhairi ta tafi zuciyarta cike da matsananciyar tsanar Lamin wadda bata iya misaltuwa. Ta kuma yi alkawari ta maya, komi daren dadewa, sai ta rabashi da duk wani farinciki na shi. Kamar yadda ya kwace musu nasu farincikin!
40.
Komawarsu Kaduna da zama yaje musu da wani irin sauyi wanda basu saba da shi ba. Dangin Mahaifiyarta mutanene su masu matsakaicin karfi, amma kuma suna da wadatar zuciya.
Dama can Hajiya Uwale ce take kula da su musamman mahaifiyarta Nenne wadda karfinta ya fara ja, har ma da Yayanta Tasi'u wanda shi har yau baya da wata tsayayyar sana'a sai tsilla-tsilla da kame-kame kawai. Bayan iftila'in daya sameta kuma sai suka koma yar gidan jiya.
Ga kuma karin su Ummah din da Sumayya da suka tare a wajen Nenne saboda dama ita kadai ce a gidan. Shi gidan Kawu Tasi'un kusa da na Nenne yake, don da duka gidan a hade yake kasancewarshi na gado, daga baya ne ya rabashi da nata din saboda iyalinshi. Yana da 'ya'ya shida maza da mata, don haka dawainiyar kanshi data yaranshi ta isheshi.
Amma duk da haka sai da yayi iyaka bakin kokarinshi wajen jansu a jikinshi. Wadannan kudi da aka sayar da gida da su yayi amfani su dukansu ya maidasu makaranta, Ummah ta shiga aji shida kai tsaye, yayinda Sumayya ta shiga aji uku don haka duk jarabawar fita zasu zana. Ya biya kudin, ya kuma yi musu yan saye-sayen kayan masarufi wadanda zasu amfana. Sauran kuma ya damkawa Ummah a hannunta yace ta kama sana'ar da zata rikesu da su.
Ta shiga tunani da taraddadin ya zata yi? Don kuwa zama bai kamata ba. A haka suka yi jarabawar NECO da WAEC duk bata gama yanke shawara ba. Ga kayan abincinsu sun ja baya sosai, kudaden hannunsu sun tasamma karewa. Don haka ta yanke shawarar fara sayar da abinci kawai.
Ta kuwa fara da hannun dama, shinkafa take yi da wake da kuma doya da miya. Ta yanka salad da albasa da kabeji da tumatir. Sai ta fita can bakin titi kusa da wani gareji inda ake gyaran mota. Kawu Tasi'u ya rokar mata alfarma a wajen mai garejin har aka fitar mata da yar rumfa take sana'arta hankali a kwance.
Abinka da farar mace da masu iya magana suka ce alkyabbar mata, ga ta budurwa danya shataf, kyawun jikinta da sura duk sun gama bayyana a lokacin. Duk da cewa ba kwalliya take yi ba idan zata fita, amma tana gyara jikinta da kyau. Don kuwa macece ita mai tsananin tsafta. Komi take yi cikin nutsuwa ne da tsentseni, wasu a wajen duk suna cewa girman kai ne da jan aji, amma ita haka tsarin halittarta yake. Da dama wasu mutanen basu san da zamanta ba sai data fara tallar wannan. Aikuwa nan manema suka yi mata caaa kamar kudaje, ita kuma ta ki kula kowa a cikinsu. A ganinta idan tayi aure yanzu, ya zata yi da Sumayyah?
Tafi-tafi likkafa tayi gaba, kullum kara yawan abinci take yi don kuwa yanzu har daga wasu wajajen zuwa saye ake yi don Allah Yayi ta da zakin hannu. Ga tsaftarta da tafi burge mutane. Ta kuma fara hadawa da zobo da kunun kanwa.
Da Sumayya ta gama tata jarabawar, itama sai ta fara binta tana taimaka mata da wasu abubuwan. Ita take wanke mata kwanuka idan masu saya sun gama ci, ita kuma take kaiwa wadanda suke tsallake dasu. Amma suka wannan cikin kulawar yar uwar tata, bata bari ta nufi bangaren da idanunta ba zasu hango ba saboda gudun abinda zai iya zuwa ya zo a wannan zamani da amana tayi karanci.
*
Doguwar tafiya suka yo tun daga Nasarawa a mota. Yana daga cikin wadanda suka yiwa Gwamnan Kaduna rakiya zuwa tattaunawa da gaisuwar ban Girma ga Maigirma Gwamnan Nasarawa din. Suna shiga garin Kaduna aka sanar dasu Gwamna kai tsaye zai wuce gidan sarautar Zazzau ne tare da securities dinshi, su kuma anyi releasing dinsu a nasu aikin, za su tafi da wasu sojojin. Su dukansu dama hutun suke bukata. Aikin tsaro musamman na manyan figures irinsu Gwamnoni, ba abu bane mai sauki. Kowa ya matsu ya dangana da gidanshi don ya samu ya huta kafin kuma su ga inda za a sake jefasu zuwa gobe.
Sun kusa karasawa Shagari Low cost inda nan ne main house dinsu yake za a saukeshi, motar tasu ta fara hayaki da rawa akan hanya, ala dole suka gangara gefen titi suka kasheta. Signboard da suka gani na wani gareji anan kusa da su yasa suka tura motar zuwa garejin shi da sauran abokan tafiyarshi su uku. Daya motar da suke tare da ita kuma ta wuce can Jaji.
First Lieutenant I. A Makama (Abdullahi Ibrahim) ya fito daga cikin garejin da suka kai gyaran motarsu bayan yayi sallama da abokanshi, niyarshi ya samu acaba ya karasa dashi gidansu ko kuma ya lallaba da kafa tunda babu nisa sosai. Saye yake da kakinshi na sojoji, ya cire rigarshi ta sama mai dauke da insignia dinshi a kafada wato l aligned silver stars guda biyu. Ya rage daga shi sai dogon wandon na kakinshi da bakar riga.
Lokacin shigarsu bai kula da mai sayar da abincin ba sam, sai bayan daya fito ya tsaya a bakin titi sannan ya ankare da ita zaune a cikin rumfa tana ta aikin zubawa kwastomominta abinci.
Kallo daya tak! Yaji ya samu matar aure yanzu-yanzu.
Yana da matarshi daya da aka yi musu auren lalle, zabin iyayenshi ce a gareshi daya karba da hannu biyu da biyayyar daya saba yi musu a kodayaushe. Amma ya fada mata, su ma iyayen ya fada musu, zai kara aure a gaba idan har ya samu wadda ta kwanta mishi a rai. Suka kuma yi na'am da hakan.
Ba mai kyalle-kyallen kallon mata bane shi, shi yasa ma yake tantamar anya zai ma iya daga ido ya kalli mace har ya samo mata? Sai gashi a yau kwatsam ya sameta.
Ya koma gefe daya yana kare mata kallo a nutse, yadda take gudanar da komi nata cikin nutsuwa da rashin rawar kai. Wani mai azababben surutu ne a kusa da ita kadan, an zuba mishi abinci yana ci yana ta zuba mata surutu kamar an bude kan famfo. Amma bata ce mishi komi ba, sai dan murmushi kawai da take yi.
Allah kadai Yasan iya adadin lokacin daya dauka anan kawai yana aikin kallonta, har aka gama gyaran motarsu abokan nashi suka fito. Itama nata abincin ya kare ta fara tattara kayanta waje daya.
Sai ganinsu yayi sun tsaya a gabanshi, Al-Ameen Tukur ya kalleshi da mamaki, "Abokina, naji kamar kace gida zaka wuce tun dazu? Ko jiranmu kake yi?"
Sai yaji yar kunya ta rufeshi, ya hau kame-kame cikin rashin sanin abin cewa. Bai iya karya ba, Allah Ya gani kuma ba zai iya yinta a yanzu ba.
Shi kuwa daya duba wajen da idanunshi suke, ya kula da yar kyakkyawar yarinyar daya tsurawa idanu, sai ya kyalkyale da dariya.
Yace, "Allahu Akbar! Lallai yau Allah Ya kama wani!Duk fadin ran naka da ihun baka ga macen da ta isa ka yiwa kallo biyu ba, ka tsaya kana kallon wata for hours? Lallai da labari ashe!" Suka ja mota abinsu suka tafi suna kyalkyala mishi dariyar shakiyanci.
Shi kuma ya ci gaba da tsayuwa nan har ta gama kwashe kayanta, almajirai biyu suka daukar mata wasu, itama da karamar yarinyar dake tare da ita suka dauki wasu.
Ya daga kafa as if in a trance, yana binsu a baya har suka gangara suka tsallaka titi, suka shiga gida. Ya kira daya daga cikin almajiran da suka kai mata kaya yana tambayarshi ko nan ne gidansu budurwar nan? Kuma ya sunanta? Yace mishi, 'gidansu ne. Kuma sunanta Ummulkhairi.'
Ya dauki kudi ya ba yaron kafin ya juya ya wuce gidansu.
Ummah na zaune da dare bayan an gama sallar isha'i tana gyaran kayan miya da za a kai mata markade na miyar gobe, yaro yayi sallama ya shiga, yace, "an ce Ummah ta zo ana kiranta."
Ta jefi yaron da harara, "kaje kace ba zata zo ba!"
Saboda duk a tunaninta Nasiru ne. Wani nataccen saurayine tayi anan cikin garejin yake aiki, ta fada mishi bata son shi, amma ko a jikinshi wai an mintsini kakkausa. Kullum cikin zarya yake gidansu, a wajen sana'ar tata ma baya barinta. Bini-bini yana nan yana ta zuba aikin surutu yadda kasan wani aku kuturu.
Nenne ta lallaba ta fito daga dakinta tana dafa bango, "kai kaje kace tana zuwa."
Ta kuma juya tana hararar Ummah, "ki tashi ki fita tun kafin kiga bacin raina wallahi. Ni na taba ganin haka? Yarinya ana binki amma kina wulakanta mutane? Idan baki tsaya kin saurari samari ba ta yaya za ayi auren kenan?"
Ta turo baki, "ni Nenne nace ina son yin aurene dama?"
Ta mata dakuwa, "aikuwa karyarki ta sha karya wallahi! Ba ido zan zuba miki ba kina abinda kika ga dama ba sai kace wata marar aikin yi. Bari kawunki ya shigo gidannan wallahi, cikin maneman naki ya cewa daya ya fito kawai mu aurar dake mu huta!"
Ta tabe baki, "tab! Allah Ya tsareni wallahi!"
Da haka dai ba da son ranta ba ta zari hijabinta ta fita, da niyar ta wankeshi tatas wankin babban bargo. Yadda ko a hanya ba zai yi fatan Allah Ya sake hadashi da ita ba.
Sai ta tarar da abinda bata yi tsammani ba. Don kuwa ba Nasiru bane. Wani kyakkyawan matashi ne da bata taba ganin mutum mai zati da kamala irin tashi ba. Duk yawan samarin dake zuwa wajenta, bata taba ganin wanda ya kama kafarshi a komi ba. Ga iya gayu. Ya sha kaftan dinshi fara tas, ya dora hula a kanshi yana ta bulbula kamshi.
Sai ta karasa wajenshi a nutse tayi mishi sallama.
Abdullahi ya sanya mata idanu yana kallonta cike da wata kauna da sanyayyar soyayya. Wannan yammaci da yayi, da kyar ya iya bari gari yayi duhu ya zo gareta. Wani abu ne da bai taba dandana ba a cikin tarihin kuriciyarshi har zuwa girmanshi da yin aurenshi, wai shi soyayya. Ya daga baki da kyar ya iya amsa mata sallamar yadda ta kashe mishi jiki.
Ya gabatar mata da kanshi a matsayin masoyi, wanda yaje da kokon barar aurenta. Bai boye mata ba, ya fada mata cewa yana da mata har da dansu wanda bai wuce shekaru shida ba. Kuma shi aurenta yake son yi da gasken-gaske idan ta amince.
Mutum ne smart, wanda yake da kwazo da naci, duk abinda ya sanyawa rai to fa sai ya ga abinda ya turewa buzu nadi. Yaje mata da zance wanda ba zata iya kwabar da zancen aure daya mata ba, na cewa zai hada daga ita har Sumayya ya rika tamkar kanwarshi. Saboda a dan tsayuwar da yayi a dazu ya karanceta tsaf, koda bata sonshi, ba zata taba kin zancen kulawa da Sumayyah ba. Don kuwa ya karanci kaunarta da kulawarta zuwa ga yarinyar.
Ta mishi sallama akan cewa zata yi tunani, ta kuma kwana tana tunanin. Daga karshe taga me zata rasa ne a wannan auren idan anyi?
Don haka washegari daya dawo ta furta mishi ta amince. Yayi murna ya kuma ji dadi sosai da sosai.
Cikin dan kankanin lokaci sai ga iyayenshi sun je wajen su Nenne da zancen aure. Bangaren su Nenne sun yi bincike, suka samu gamsasshen bayani game da iyalan gidan Ibrahim Makama. Mutum mai tawali'u da wadatar zuciya kenan. Abdullahi shine babban dan shi, bayan nan yana da kani Hashim wanda shima aikin damara yake yi, Custom ne. Bayan su iyayensu basu kara haihuwa ba. An shaidi zuriyarsu da girmama mutane da bin na gaba, iyayensu mutanene masu tausayi da taimakawa na kasa dasu. Mahaifinsu ba mai arziki can-can bane, amma yana da rufin asirinshi dai-dai gwargwado. Tsohon malamin makaranta ne wanda yayi ritaya. Da suka gamsu da duk bayanan da suka samo, sai kawai suka sanya ranar aure kamar yadda suka bukata, yan kwanaki kalilan.
Aka sha hidimar aure sosai, dangin Uwale sunyi musu kara kwarai da gaske. Mutanen Maiduguri kuwa ko keyar wani basu gani ba, dama dai tuni ta ciresu daga cikin ranta. Don haka bata damu da rashin zuwansu ba.
Amarya ta tareta a gidanta dake Shagari Low cost, tazarar dake tsakaninsu da surukanta ba mai yawa bace, tare da kishiyarta Hadiza.
Hadiza da tabi ta tashi hankalinta ganin irin kudaden da Abdullahi yake kashewa amarya, duk da cewa dai itama yana yi mata bakin gwargwado, amma ba haka take so ba. Ta hau kan zugar yan'uwanta da abokai, kodayake dama can da halinta, ta shiga harkar malaman tsubbu da bokaye hankali tashe, bata so auren ya yiwu. Amma duk abinta sai da aka daura auren, aka kuma kai mata amaryar gidanta. Hakan bai sanyaya gwiwarta ba, tayi rantsuwa ta maya, in zata yi yawo tsirara, to sai ta raba wannan aure. Don kuwa gidan Abdullahi gidanta ne ita kadai, ba gidan da za a raba da wasu ba.
Don haka zancen zaman lafiya ma da Ummulkhairi bai tashi ba. Gaba ta dauka da ita sosai da sosai.
Ita dai tunda aka kaita take zaune da kowa lafiya, daga mijin har iyayenshi da yan'uwansu da ita kanta kishiyar, da zuciya daya take zaune dasu. Don haka duk abinda Hadiza take yi, bata taba tankata ba.
Mutanen unguwa data tsince wadanda suke son zaman mutunci da ita, sai ta kamasu. Ta zubar da masu kai mata zuga da gulma da kuma wadanda dama can a bayan Hadiza suke a gefe.
Abdullahi aka yi posting dinshi anan gidan Gwamnati a Kaduna din, don haka yana gida a zaune. Ya kuma cika alkawari inda tana cika wata daya a gidan, yaje ya dauko Sumayyah da kanshi da kayanta duka, ya maida ita hannunsu da zama tare da sama mata transfer din makaranta zuwa wadda tafi kusa da gidansu.
Wannan abu shi ya kara rura wutar tsanarta a wajen Hadiza. Duk kuma yadda Ummah ta so da su zauna lafiya, abu ya gagara. Danta daya tilo dake gidan, bata bari ya rabeta. Haka bata bari Sumayyah ta rabesu. Don haka Ummah ta kama kanta, ta daina shiga harkarta amma tana bata girmanta a matsayinta na babba.
Anyi auren nasu babu jimawa Allah Ya dauke Nenne. Sunyi kuka kwarai da gaske, don kuwa sai a lokacin ne suka tabbata marayu na gaske. Don ma dai Abdullahi a tsaye yake a kansu tsayin-daka, daga ita har Sumayyah din.
Hadiza dai tana gefe daya, shiga da fita gidajen malaman tsubbu kawai take yi. Sai gashi ta fara nasara da cimma burinta. A sanyawa Abdullahin tsanar Ummah, ko ita taji ta tsaneshi, a sanya ya dinga wulakantasu, a sanya ya hanasu abinci, abubuwa dai iri-iri babu wanda basu gani ba. Amma da yake Ummah din mai kara ce da hakuri, ko iyayenshi basu taba sani ba. Ta dukufa da addu'a babu dare babu rana tana neman tsari.
Akwai ranar da Abdullahi ya shiga dakinta cikin dare yayi mata dukan tsiya, ya kuma ce ta hada kayanta ta bar mishi gidanshi a wannan dare. Ta ci kuka har ta gode Allah a wannan rana, tunanin ina zata nufa cikin tsakiyar daren wannan ita da Sumayya ya rufeta, amma dole zata tafi din. Don ba zata iya irin wannan zama ba.
Haka ta tashi jiki duk yayi tsami, daga ita har Sumayyan kuka suke yi, ta dauki hijabi kadai ta sanya da yan kudaden da yake bata tana tarawa. Ta gama kudirawa a ranta idan ta fita daga wannan gidan, to ita da Kaduna sai labari. Don kuwa garin ma zata bari kwata-kwata ta huta. Yadda kasan wadda ake tunzurawa ko ake ja, haka suka nufi kofa su duka zasu fita.
Tana kokarin bude kyauren gidan ta fita kuma sai taji ya biyosu a sukwane. Da fari tsorata tayi, tayi tunanin ko bugun nata zai sake yi ya karasata. Sai taji ya kamota ya rungume, ya hau bata hakuri da magiyar don Allah kada ta tafi tayi hakuri, bai san me ya hau kanshi ba har yayi mata wannan danyen aikin.
Da kyar da jibin goshi ya jata ya maidata dakinta don itama kakarewa tayi tace kawai ya kyaleta ta bi duniya, abinda bata taba yi mishi ba kenan a tarihin aurensu wato musu.
Shi da kanshi ya hau kikiniyar dora tukunya a risho, ya dafa ruwan zafi yana gasa mata jiki. Ranar ita kuka, shi kuka haka suka kwana.
Tun kuma daga wannan rana ta dage da addu'o'i na kariya, da wanka maganin tsari irinsu ganyen magarya da kaikayi.
41.
Cikin ikon Allah kuma daga ranar ne suka sake daidaitawa ita da angon nata, suka koma tamkar tif da taya saboda tsananin kauna da kyakkyawar zamantakewa.
Suna cikin hakan kuma sai ga ciki ya bayyana a jikin Ummah. Wayyo, ina wuta in saka ki! Hadiza taji kamar ta shaketa ta mutu. Shi kuwa Abdullahi da Iyayenshi suna ta murnarsu, suka fara shirin karbar yaro ko yarinya.
Kulawa ta musamman suke bata kamar su dauketa su goyata. Babu abinda zata ce da iyayen Abdullahi a wannan lokaci sai godiya ga Allah kawai, domin kuwa sun rike amanarsu da suka dauka. Abdullahi ya zame mata mijin marainiya ita da Sumayyah.
Tunda cikin nan ya samu ita kuma Hadiza babu irin kokarin da bata yi ba don ta zubar dashi, amma fa abu ya gagara. Akwai ranar da ta dafa faten masara da wake yadda ta saba ci kusan kullum, ta barshi akan wuta ta shiga daki ta fito, ta juye fate a kwano ta sha. Shikenan jiki ya hautsine, ciki ya hau murdawa yadda kasan mai nakuda. Lokacin Abdullahin baya nan, Sumayyan kuma tana makaranta. Ta fito tsakar gida tana kuka rike da ciki, amma kiran duniya Hadiza tana jin ta a daki ta ki fitowa. Haka ta lallaba da kyar ta shiga makota, su ka tarairayeta aka nufi asibiti da ita. Likitoci suka hau kanta da kyar aka samu aka ceto abinda ke cikin. Suka ce akwai abinda ta ci wanda yayi yunkurin zubar mata da ciki, bata son doguwar magana da yin tashin-tashina, shi yasa bata ma fadi musu tana zargin wani abu ba. Shima Abdullahin da yaje sai kawai tace mishi ciwon ciki ne ba wani abu ba. Aka basu sallama da dokoki da aka kafa mata, suka koma gida.
Sai dai fa tun daga nan, ta kiyaye kanta da yin girki ta bari akan wuta ta fita. Musamman bayan hakan da kamar sati biyu data kama Hadiza din kiri-kiri tana zuba mata abu a cikin tukunyar miya data bari tana simmering ta dan zagaya bayi. Sai ta hau mata kame-kame da kokarin nade tabarmar kunya da bori. Bata ce mata komi ba, amma dai haka wannan miya ta zama haramiyarta. Wannan dalilin ne yasa ta dinga taka-tsantsan da duk abinda zata ci ko sha a wannan gida.
A haka cikinta ya dinga girma cikin kulawa da tattali. Kusan kullum Hadiza sai ta takaleta da fada, ta dinga yada mata kananun maganganu da habaici iri-iri, duk tayi kunnen uwar shegu da ita bata taba tankata ba. Don ta kula so take yi ta tanka din ta kai mata duka, motsi kadan sai tayi kamar zata kaiwa cikinta hari.
Cikinta ya fita wata na takwas, watarana da yammaci ta fito daga bayi tana tafiya da kyar. Duk ta kumbura, ga cikin nata ya fito sosai yayi mata kyau. Duk abinda yake tsone idon Hadiza kenan tana kara tsanarta da cikin jikinta.
Ta wuce Hadiza din zata shiga dakinta sai taji ta saki tsaki, tace, "matsiyaciyar kawai, mayya! Wadanda idan suka kama kurwar mazan mutane ba su saki. Ai wallahi sai nayi maganin dan iska anan gidan! An gama karuwanci wajen sai da abinci an yayimo cikin shege an likawa mijina don maita!"
Maganganun nata suka bata ran Ummah sosai, amma ta dakewa ranta bata tanka ba. Ta wuceta kamar kullum.
Kawai sai ji tayi an shakota ta baya, kafin ta ankare me ke faruwa taji an fara naushin cikinta ta ko'ina. Garin neman ta warci kanta tayi wani irin juyi, Hadiza kuma ta tunkudata. Sai gata ta fadi kasa yummm! akan ruwan cikinta.
Wata irin azaba ta ratsata da tunda take bata taba jin makamanciyarta ba, gabadaya kasa ko mosti tayi balle tayi ihu saboda yadda azabar ta fitar da ita daga hayyacinta. Jini ya tsinke mata a take, kamar an yanka rago.
Amma Hadiza bata sadara ba, sai ma gyara tsayuwa da tayi tana jiran ta ga ta tashi, ta kara mata da wani dukan.
Allah ne Ya jefoshi a dai-dai wannan lokaci, don kuwa yawanci sai dare yake komawa gida.
Ganin abinda yake faruwa yasa ya nufi kan Ummah cikin wani irin kidima da tashin hankali, musamman jinin da yaga yana malala daga jikinta.
Ya daga ido ya kalli Hadiza da bacin rai wanda bai fasaltuwa akan fuskarshi, "wallahi, Tallahi Hadiza. Idan wani abu ya samu da na ko matata, ki kuka da kanki. Ni kaina ban san irin hukuncin da zan dauka a kanki ba!"
Ya sungumeta yayi waje a sukwane.
Sabuwar mota da yayi awo tun daga Kwatano aka kawo mishi yau yaje ya amsa. Wannan ne musabbabin dawowarshi gida, ya dauki Iyalanshi a ciki ya zaga dasu su sanya mishi albarka. Sai kuma ya tarar da wannan tashin hankali. Haka ya sanyata a bayan mota, ya fuzgi mota a sukwane yayi asibiti.
Kakin jikinshi ya ceceshi a ranar, don kuwa da ba za su amsheta bama sai da yan sanda. Haka aka garata zuwa dakin tiyata cikin gaggawa yana ji yana gani, ya dawo yana ta safa da marwa a kofar dakin, addu'a iri-iri a bakinshi. A cikin haka ne ya tuna da Iyayenshi, sannan ne ya dauki waya ya kira ya sanar dasu halin da ake ciki, sai gasu nan da nan sun je sun sameshi a asibitin. Suna nan har zuwa lokacin da aka fito da ita bayan an kwashe kwararan awanni biyu.
"Kuyi hakuri, mun samu mun ceto uwar da kyar, amma bamu iya ceton dan ba. Kafin ku kai ga zuwa ma ya riga ya rasu saboda rashin isasshen oxygen a cikin cikin. Amma ita yanzu uwar tana lafiya, zamu yi mata sauran gwaje-gwaje idan ta tashi zuwa gobe!"
Abinda likita yace dashi kenan, aka mika mishi dan shi lullube a cikin zani. Ya amsheshi fuskarshi na bayyana rauni kwarai da gaske, duk karfin halin da yaso ya nuna sai da hakan ya gagara, ya zauna akan kujera dabar! Hawaye na cika mishi idanu. Ga d'a nan Tubarkallah kamar ka mishi magana ya amsa.
Innarshi ta amshi dan ganin yadda jikinshi yake rawa sosai, yayinda mahaifinshi ya dafa shi yana tausarshi. A haka jiki a sanyaye duk suka kwashi jiki suka koma gida, aka yiwa yaro sutura aka je aka binneshi kafin suka koma asibitin.
Mutane suka fara zaryar zuwa dubiya kamar su ci kansu, don kuwa Ummah macece mai mutane kwarai da gaske, yadda ta kama danginshi ta rike da hannu bibiyu kamar nata yasa suke matukar girmamata. Ga ta dama abin hannunta bai rufe mata ido ba sam.
Sai da ta kwana ta yini sannan ta farfado. Sumayyah ce a kanta da Abdullahin, su duka sunyi wani zuru-zuru da su kamar wadanda suka
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 26 Chapter of 36