bacin ranka ba sai don kawai kaja mata kunne, a matsayinmu na matanka, kuma iyayenta...!"
Tayi gaggawar katse maganganunta masu kama da digar dalma a cikin zuciyarta, "kinyi kadan wallahi, kinyi tsararo, baki ko kama kafar taka wannan matsayi a wajena ba! Mahaifiya daya na sani a gidan, kuma ba ke bace! Ba zaki taba zama ba kuma! Kije can dai ki nemo inda diyan naki suke amma ba ni ba!!"
Abbansu ya zabura yana kokarin tashi, "kun gani ko? Kun gani ko? Wannan yarinya... Wannan yarinya... Tashi ki bani waje kafin in sassaba miki kamanni a wajennan..."
Bata jira ya rufe baki ba ta tashi tayi gaba, ta wucesu tana watsa musu harara kasa-kasa. Tana ji ya bita da wasu kalamai da maganaganun zagi. Bata waiwaya ba har ta dangana da dakin Mama.
Maryam da Aminatu, sauran diyan Mama da suka rage a gabanta, suna falon sunyi tsuru-tsuru suna sauraron diramar da ke wakana a gidan. Ta wucesu ta shige can uwar dakan Maman inda ta sameta tana zaune akan abin sallah tana jan carbi.
Ta haye can karshen gadonta na karfe ta cusa kai a tsakankanin cinyoyinta ta saki wani irin kuka mai cin rai.
Tana jin Mama ta zauna a kusa da ita tare da dafa kafadarta ta shiga bata hakuri da tausassan lafazi.
Tace, "ba tun yau ba ina fada miki, kiyi hakuri da duk wani halin mahaifinku, ki daina ja-in-ja dashi musamman idan yana yi miki fada Nadiya. Iyaye har kullum hakuri muke yi dasu ba wani abu ba!"
Tace, "haba Mama! Haba don Allah!! Shi kenan kuma sai ya kasance kullu-yaumin ba za a taba tsayawa a saurari uzurin mutum ba sai dai duk zugar da za a kai a kanshi a hau kai a zauna babu wani bincike? Wannan ai ba adalci bane. This is not fair wallahi!"
Mama ta dan yi murmushi mai nuna takaici, tace, "kin san halin Abbanku sarai Nadiya, kin kuma fi kowa sanin haka halinshi yake. Don haka ban ga abin tada jiniyoyin wuya da bacin rai ba a nan. Kiyi hakuri ki jure koma menene, saboda watarana sai labari!"
Bata iya cewa komi ba sai jan shessheka data cigaba da yi tana sharar kwalla ranta a matukar cune.
Maryam da Aminatu suka shiga dakin suka zauna a gefenta suna kara tausarta, har dai taji ranta yayi mata dan sauki.
Ta umarci Aminatu da taje dakinta ta dauko musu take away din data je da ita. Maryam kuma ta dauko musu ruwa mai sanyi da kunun aya da Mama take yi na sayarwa. Nan suka zauna a falo suna cin abincin suna hirarsu har suka gama cin abincin.
Da yan wuta suka kawo suka kunna kallo a yar karamar tv dake manne a jikin bango a dakin. Ta zauna tana tayasu Assignment dinsu da bitar karatu. Ba ita tayi musu sallama ba sai da karfe sha daya ta gota.
Ta shiga bandaki ta watsa ruwa tare da dauro alwala, ta koma dakinta ta sanya kayan barcinta riga da wando marasa nauyi. Wandon ya tsaya mata a iya gwiwa, rigar kuma kamar vest take mai siririn hannu.
Tana dora kai akan katifa da niyar barci, abinda take gudu ya fara aukuwa.
Yau kam abin har yayi yawa, wani lokacin ma sai taga kamar da gayya suke yi mata abinda suke mata. Saboda ta kula sun fi kwaratsi da daga murya a ranakun da suka samu sabani da ita. Musamman Lantana din daya kasance ita ce da maigidan ranar, har wani ahi take da wani abu kamar wadda take shirin tayar da aljanu.
Ta dauko earpiece dinta ta makala a kunnen ta jona da wayarta. Karatun Qur'ani ta kunna ta kuma kure volume, ta koma ta kwanta. Amma duk da hakan barci ya kauracewa idanunta. Ta kasa tsayar da hawayen da suke mata zarya akan fuska suna kwarara, haka kuma ta kasa hana kanta daina hasko mata munanan abubuwa da sake-saken da ranta yake mata. A haka wani irin wahalallen barci ya dauketa.
Ko da alarm dinta ya buga da asubah, ta kwashe fiye da minti goma a kwance kawai ta kasa tashi, jikinta kamar wadda trailer ta bi ta kanta haka take ji. Ji take kamar ma wadda bata yi barcin ba saboda yadda take jin kanta yana sarawa kamar zai rabe gida biyu.
Haka ta kokarta da kyar tayi alwala tazo tayi sallah.
Ta koma ta kwanta akan abin sallar, rabin jikinta kuma akan katifarta tana yin azkar dinta har dai gari yayi haske. Kafin ta tashi taje tayi duk abubuwan data saba.
Bakwai mai kyau ta gama shiryawa cikin riga da skirt na atamfa. A-shape ne wadanda suka bi jikinta kuma basu kamata ba. Bayan yar hoda da wet lips data sanya ta kuma zizarawa idanunta kwalli babu abinda ta kara. Ta dauki karamar hand bag ta leather ruwan kasa ta zuba abubuwan da zata bukata, ta fito ta kulle dakinta.
Ganin yan yaran duk a tsakar gida yasa ta shiga dakin Abbansu domin ta gaisheshi.
Sai data dan yi turus, ganin Lantana da Salame a kame a kan kujeru sun sanya shi a gaba kamar wani karamin yaro yana karyawa. Koda yake dama mai take tsammani? Ana gama Asubahi haka zasu shiga dakin su sanya shi a gaba. Da ace zai yini a gidan, to da ko nan da can ba zasu motsa ba. Duk kuma hakan gadin kada su kebance ne da Mama ko kuma ya dan yi tattaunawar sirri da iyalanshi. Magana ko wace iri ce sai dai ayi a gabansu. Shi yasa ai daga 'Ya'yan gidan zuwa abokai da danginshi, basu ganin kan kowa da gashi.
Ta riga ta san abinda zai biyo baya tun ma kafin ya furta lokacin data zube a gabanshi ta gaisheshi. Ya amsa a tsaitsaye, sai kuma ya tsayar da ita lokacin data fara yunkurin tashi, "su kuma iyayen naki ba zaki gaishesu ba saboda rashin ta ido ko? Wai ke Nadiya me yasa ba kya jin magana ne?"
Bata iya cewa komi ba sai dan juyawa da tayi tana kallonsu kamar ta hadiye zuciya ta mutu, tace, "ina kwananku?"
Suka kuwa yi caraf suka amsa kamar dama jira suke yi.
Ta mike gwiwa a sage, rai yana suya zata fita. Sai kuma suka ci karo da Mama ita kuma ta danno kai zata shigo dakin hannunta rike da kwanon da zata dauki abincin da zata dafa tunda ita take girki ranar, kuma store din a cikin dakinshi yake.
Sai ta dan yi baya ta bata waje ta shiga, ta kuma koma ta tsuguna tana gaisheta. Ta amsa tana kallonta fuska dauke da fara'a, tace, "Nadiya har an fito kenan?"
Tace, "ehh wallahi Mama. Yanzu nake cewa bari inje in sanar dake zan tafi."
Tace, "to sai kin dawo, Allah Ya tsare. Yau ma ba zaki karya din ba zaki tafi?"
Tayi dan murmushi, "Mama kin manta yau alhamis? Azumi nake yi."
Tace, "hakane fa. To sai kin dawo."
Daga haka ta sa kai ta bar gidan.
Aikin ranar kamar na kowace rana ne, akwai kwastomomi da tarin ayyuka shi yasa ta koma gida a matukar gajiye likis. Tun ma kafin karfe tara tayi ranar ta kwanta.
Barci mai dadi da nauyi ya sureta. Kawai gabannin asuba sai taji ana maimaita yar gidan jiya kamar a cikin mafarki. Tayi lamo a kan katifa tana kokarin tunano me yake faruwa ne? Musamman data jiyo Salame ce tare da mahaifin nata yau. Girkin Mama ne, kuma ta tabbata ba a nemi izininta ko shawararta ba. Ta hau girgiza kai gabadaya kanta a juye da lamarin wadannan mutane. Su basu san suna take ka'idar Allah bane?
Akwai wani lokaci data taba tunkarar mahaifin nata da zance makamancin wannan. Farkon komawarta dakin ne lokacin tana makarantarta ta jami'a. Gani tayi shiru-shiru da kawaicin da kawar da kai da take yi duk basa yi. Ta fara samun matan nashi da maganar, ta ga dai basu da niyar su fahimceta ko kuma su gyara. Sai ma muzguna mata da suke yi musamman da suka fahimci cewa abin yana damunta kuma bata jin dadinshi sam. Wai sai ya zamana ma suna mata habaici da tutiya dashi. Sai abin ma ya koma yana bata dariya. Ta ga akan wani dalili to ita da ba kishiyarsu ba?
Don haka ta badawa idanunta toka ta tunkari Abban nasu da maganar. Ta nuna mishi rashin dacewar hakan da kuma illolin da hakan zai iya kawowa musamman ga yaran gidan da suke tasowa. Tunda watan watarana dai zata bar dakin ai, kuma 'ya'yansu sune zasu maye gurbinta. Bai dace su taso suna shaida wannan abin ba.
Babu abinda ya fi ci mata tuwo a kwarya ma irin daukar kwanan wata ya kaiwa wata, musamman kwanan Mama. Tunda dai ita tace ta hakura dashi shekara da shekaru, kuma zaman 'ya'yanta take yi.
Ya zauna yana saurarenta tana ta zuba bayanai kamar wani abin arziki. Sai data dasa aya sannan ne kuma ya rufe ido ya fara zuba mata rashin mutuncin da sai data yi dana sanin yi mishi maganar. Har da mata kashedin idan ta sake yi mishi katsalandan a al'amuranshi to lallai kuwa zai koreta ta bar mishi gidan, in yaso sai taje can wani waje na daban ta musu rashin kunyar.
Don haka ta daurewa kanta, ta kai na mujiya ta zuba musu kawai. Ta koma gefe tana addu'ar Allah Ya shiryesu, ita kuma ya bata mijin aure tayi ta bar musu gidan ta huta.
Shekaru ashirin da shida tana shirin haurawa da bakwai, amma har yanzu babu wani tsayayyen miji na a zo a gani.
Ranar haka ta yini cikin yanayi na bacin rai da damuwa da tunani. Rashin yin aure da son barin wannan gidan yana daya daga cikin manyan abubuwa da suka jagoranci damuwoyin da suka dabaibayeta.
Kasancewar Juma'a ce, sun fi samun kwastomomi da rana idan an fito daga masallaci, don haka zuwa lokacin da karfe hudu ta yi, abubuwa sun fara lafawa.
Tana bayan kanta tana lissafin cinikinsu na ranar da shigar da bayanai, Aramide ta shiga shagon hannu rike da makullin mota, gyale a kafada yana neman faduwa kasa.
Aramide abokiyata ce tun makarantarsu ta Jami'a, kuma ita ce jigon shagon nasu. Don haka tare suke kula dashi duk da cewa dai ita tafi zuwa a ranakun mako saboda tana aiki da kamfanin Indomie da bangarensu yake anan Kaduna.
Ta mata sannu da shigowa. Ganin yadda ta amsa a tsaitsaye, tasan watakila ta kwaso gajiya ko kuma bata jin dadi. Don ita din mutum ce mai kazar-kazar da barkwanci, shi yasa ma tasu tazo daya da Nadiyar sosai.
Ta dauki cup cakes da doughnuts da lemu mai sanyi ta kai mata. Ta amsa tana mata godiya, ita kuma ta koma ta cigaba da abinda take yi.
Tana aikin ne wani tunani ya darsu a ranta. Tunanin komawa gida ranar yasa take jin kamar ta dora hannu a ka tayi ta ihu kawai. Ta gaji kwarai da gaske, hutu take bukata daga wannan gidan da wannan rayuwar.
Tayi sauri ta gama abinda take, taje ta samu Aramide tace mata zata wuce gida da wuri. Bata tsaya jan dogon zance ba tace mata ta gaida gida.
Ta fita ta tari abin hawa, kai tsaye ya kaita tashar Kawo ta shiga motar Kano.
Tana zuwa motar saura mutum biyu ta cika da yake golf ce. Don haka ta zauna jiran cikon mutum daya.
Sai lokacin ta ciro wayarta a jaka ta kira Mama wadda ta daga nan take.
Tace mata, "Mama a mana addu'a, gani nan a hanyar Kano!"
Mama tace, "Kano kuma da wannan yammacin Nadiya? Anya? Ga dare yayi kuma ga yanayin hanya da wannan rashin tsaro da muke fama?"
Tayi dan murmushi, "babu abinda zai faru in shaa Allah Mama. Ni dai kawai kiyi mun addu'a!"
Mama tace, "to Allah Ya kiyaye hanya Nadiya, Allah Ya saukeku lafiya. Kin fadawa Abbanku dai ko?"
Nan da nan sai fara'ar fuskarta ta dauke. Tace, "in kira shi in ce mishi me? Na tabbata dai babu wani fatan alkhairi da zai mun, kila ma sai dai ya min fatan inyi hatsari a hanya in mutu tunda dama ba yau ya saba hakan ba!"
Mama tace, "duk da haka, mahaifinki ne ai. Kuma idan kinyi hakan hakkinshi kika fitar. Ki daure ki kirashi din!"
Tayi dan jim, kafin ta gyada kai kamar Maman tana gabanta, tace, "to shikenan, zan kira shi din in shaa Allah."
Mama tace, "yauwa Nadiya haka ake so. Ki gaishe da Jamilar idan kin je."
Tace, "zata ji in shaa Allah."
Nan suka yi sallama.
Lambar Anty Jamila ta kira, sai dai har tayi ringing sau biyu ta gama ba a daga ba. Sai ta kira lambar diyarta Rabi'ah.
Tana shiga ta daga kamar wadda take jira. Ta fara magana cike da azarbabi, "Mommy Nadiya ina yini?"
Tayi yar dariya, "kai Rabi'ah, Allah Ya shiryeki wallahi. Ina sallamar to?"
Sai itama tayi yar dariya cike da alamun jin kunya, tace, "Assalamu alaikum wa rahmatullah"
Ta amsa, "wa alaikumussalam wa rahmatullah. Ina Mommynki ne, ina ta kiran wayar tata amma bata dagawa?"
Tace, "aikuwa yanzu babu jimawa suka fita ita da Daddy. Ina tunanin ko wayar tana jaka ne ko kuma ta barta a gida."
Tace, "ok, to idan ta dawo da wuri ki fada mata ina kan hanya. Don kada ta tarar da missed call ta kira kuma yanayin network bata sameni ba."
Rabi'ah tayi tsallen murna ta dire, "da gaske? Allah kiyaye Mommy sai kin iso! Ki kawo min tsaraba fa!!"
Yadda taji tana murna da dokin zuwanta sai taji itama murnar ta kamata, tace, "to shikenan Rabi'ah, zan kawo miki in shaa Allahu!"
Suna gama wayar aka samu fasinja. Nan da nan aka rufe mota direba ya dauki hanyar fita daga Kaduna.
Sai da suka fita a tashar sannan ta lalubo lambar Abbansu ta tura mishi sakon ita dai ta tafi Kano gidan Anty Jamila. Sai dai har suka fita daga Kaduna suka dauki hanyar Zariya bata ga ya maida mata da amsar sakon ba. Don haka ta kada kanta gefe guda ta jinginar da gilashi tana kallon gari.
Karfe takwas da rabi suna cikin Kano, amma bata karasa gidan Anty Jamila dake can cikin Nasarawa GRA ba sai wajen karfe goma saboda yanayin abin hawa.
Mai napep ya tsaya a gaban tangamemen gate din gidan nasu. Bakin gate ne mai gida-gida sai wasu adon furanni da aka yi a jiki masu kalar zaiba. Kai daga gani ba sai ka tsaya tambaya ba kasan cewa ya ci kudi ba kadan ba.
Ta sallami mai abin hawar kafin ta karasa jikin gate ta kwankwasa, mai gadi ya leka yana tambayar waye? Daya ganta sai ya koma ya bude mata yana mai yi mata sannu da zuwa. Ta amsa mishi a matukar gajiye.
Motocin data gani a cikin gareji ya tabbatar mata da cewa su Antyn sun dawo. Ta raba ta gefen garejin ta bi ta gefen madaidaicin lambu da kuma wajen shan iska na gidan, ta shiga falon farko na gidan.
Babban falone sosai. An sanya kujeru manya-manya na leather sai babban center table, rabin bangon dakin wata katuwar plasma ce yayinda rabin kuma show glass ce mai girma da fadi da aka zuba abubuwan ado na tangaran da gilashi a ciki. Dim lights masu kyau suna ta sheki a ciki suna kara kawatata. Falon an fi amfani dashi saboda manyan bakin Daddy, amma su ma mutan gidan su kan fita su sha iska a wasu lokutan.
Tana bin wata kofa sai gata a tsakar gidan. Dakuna ne a jejjere daga kowacce kusurwa, Yayinda sauran tsakiyar gidan kuma aka shuka wata bishiya babba wadda ta bude daga sama ta saki rassai duk sai ta lullube gidan. All in all dai, gidan Anty Jamila gida ne wanda tsarinshi yayi matukar burge Nadiya. Domin gidane da daga gani kwalwa da dukiya suka jajirce wajen ganin an samar dashi. Kuma yanayin tsarin yana nuna rayuwa ta wayewa da kuma sanin darajar kai, ba irin ta gidansu ba.
Bangaren yaran gidan daban yake, duk da cewa dai a waje daya suke, amma kuma kowa bangarenshi daban yake.
Kana shiga daga bangarenka na dama, nan ne dakin yara mata yake. Idan kuma ka mike straight, nan zai kaika turakar mai gidan. Bangaren hagu kuma wanda ya dan shiga ciki nan ne bangaren maza.
Kai tsaye dakinsu Rabi'ah ta wuce. Tayi knocking kafin ta tura kofar dakin ta shiga. Dakin nasu yana da fadi matuka. Gadaje uku ne a dakin, guda biyu wadanda suka kasance bunk, a hade, suna daga jikin bangon kofar dakin, sai dayan kuma daya kasance single a daya bangon. Daya bangon kuma gabadayanshi wardrobe ce ta jikin bango, sai daya gefen da aka zuba desks na karatu, kowanne makale da laptop dinshi da sauran essentials, sai kuma karamar tv da aka manna. A tsakiyar dakin kuma an shimfida kafet mai taushi an zuba tuntu da wasu abin zama da hutawa masu kyau.
Rabi'ar tana zaune akan desk dinta tana rubuce-rubuce lokacin data shiga. Tana daga kai ta ganta, tayi tsalle ta wancakalar da abubuwan hannunta ta nufeta a sukwane tana ihun murna. Murmushi tayi itama ta rungumeta, nan suka hau juyi a tsakiyar dakin har dai suka dangane da gado suka zube a kai.
Sai data gama murnar tata sannan ta saketa, ta zauna a gefen gadon tana kallonta, "wai! Gaskiya sannunki da zuwa Anty, ya hanya?"
Tace, "hanya Alhamdulillahi, gamu mun iso ai!"
Rabi'ah tace, "sannu da hanya to. Mommy tace idan kin iso a miki sannu da zuwa zaku hadu da safe saboda tuni suka shige turaka ita da Daddy!"
Dan murmushi ta saki a tausashe, sanin halin Anty Jamilar sarai da yadda bata hada harkokin mijinta da komi yasa bata ji komi ba, sai kai data daga, tace, "to Allah Ya kaimu goben lafiya. A gajiye nake ai dama, ruwa kawai zan watsa in kwanta."
Tace, "to ki shiga kiyi, ga kayan barci da Mommy ta shigo miki dasu."
Tayi godiya tare da amsar kayan ta fita daga dakin ta fada toilet da yake fuskantar dakin. Shower stall ta shiga ta saki ruwa mai dumi a jikinta sosai, ta jima a ciki kafin ta fita tana jin yadda jikinta ya fara saki, gajiyar itama ta fara barinta.
Ta tsaya gaban karamar mirror dake makale a bandakin tana goge jikinta da tawul. Data gama ta dauki spray na CC mai sanyin kamshi ta fesa a jikinta kafin ta fasa ledar kayan ta sanya, dogayen riguna ne guda biyu na barci a ciki. Dayar bata da tsayi sosai da kadan ta sauka gwiwarta, kuma hannunta siriri ne haka kuma bata da nauyi. Dayar kuwa doguwa ce har kasa kuma tana da dan kauri haka hannunta dogo ne, tana da madauri a jiki kamar bath robe. Ganin su kadai ne a dakin kuma yanayine na zafi, sai bata dora ta saman ba, ta barta.
Tana komawa daki ta tarar har Rabi'ah ta baza mata kayan abinci duk da dai marassa nauyi ne. Dambun cous-cous ne da yaji hadin kayan lambu sai kuma yankakkun kayan marmari da madarar hollandia yoghurt ta strawberry. Ta zauna tana ci suna taba hira da Rabi'ah, gajiyar tafiya yasa ta kasa cin abincin da kyau sai fruits din data sha sosai, ta kuma sha yoghurt din. Data gama sai ta rufe komi, Rabi'ah ta wuce ta kai kayan kicin ita kuma sai ta koma bayi ta wanke bakinta ta dawo daki ta kwanta. Rabi'ah tana sama ita kuma tana na kasa, ta kira Mama ta shaida mata sun sauka lafiya, ta hadata dasu Maryam suka mata sannu da hanya kafin su yi sallama.
Daga nan ta yada kai akan filo babu jimawa barci yayi awon gaba da ita. Ba ita ta farka ba sai da alarm ya tashesu sallar Asubahi. Bayan sun yi sallar, suka yi azkar, sake komawa suka yi suka kwanta abinsu.
Karfe tara da rabi ta farka. Jikinta ya saki sosai, babu kuma gajiya a tattare da ita sai rashin karfin jiki da kasala.
Ta sauka daga kan gadon ta fita tare da shiga toilet, baki ta wanke kawai. Ta bi dogon corridor din gidan ta shiga kicin. Ko'ina na gidan a gyare yake tas-tas, babu hayaniya wadda ta sanya mata natsuwa. Tana son rashin hayaniya da tsafta ita kam.
Yunwa take ji sosai, kuma ita ta tasheta. Ta fara bude-buden fridge da cupboards tana neman wani abu da zata fara dashi kafin ta yi abin kari, saboda tasan mutanen gidan zasu iya kaiwa sha daya ma basu tashi ba. Tasan kuma abu mai dan nauyi zasu bukata.
Freezer ta bude ta ciro kaza guda, ta fara wanketa ta dora akan wuta bayan ta yanka wadatacciyar albasa ta zuba kayan kamshi.
Sai ta dama quicker oats ta hada ta sha kafin kazar ta gama dahuwa.
Ta fara fito da abubuwan da zata bukata tana warewa. Kafin kace me, ta hargitsa gidan da tattausan kamshin girki mai dadi.
Dage-dagen kaza tayi da kayan lambu, sai ta soya kwai, ta yi toasting din biredi, sai shayi mai kamshi data hada. Ta riga ta gama sanin tsarin gidan, don haka tana gamawa ta samu flask da warmers ta zubawa Anty Jamila nata da na mai gidan, ta debar musu ita da Rabi'ah, sauran kuma ta ajiyesu a wani mazubin na daban. Duk mai so daga cikin mazan gidan wadanda kannen maigidan ne dake karatu a BUK, sai yazo ya dauka duk da cewa bata ji motsin kowa ba yau.
Tana cikin wanke-wanke Anty Jamila ta shiga kicin din. Doguwar macece mai dan jiki, baka ce amma kuma kalar fatarta mai kyau ce da sheki saboda tana bata kulawar data dace. Saye take da doguwar rigar barci cotton, sai ta dora hijabi karama a sama wadda ta tsaya mata a kugu, kafarta saye da takalmin silifas mai taushi.
Nadiya ta juya tana kallonta lokacin data shiga kicin din, fuskarta dauke da murmushi. Durkusawa tayi tana gaidata, Anty Jamila ta jata jikinta tana dariya, "ai tunda naji gida ya karade da kamshi nace lallai Nadiya ta dira gidana!"
Dariya ta sake a tausashe, tace, "haba dai Anty! Ke ma fa bangaren girkinnan ba daga nan ba. Ni ai nawa sharar fage ne!"
Anty Jamila tace, "ba wani nan. Ke kanki ai kin san kafin a kamo kafarki a bangaren girki, za a jima gaskiya!"
Murmushi ta sake yi tana girgiza kai kawai.
Tray din data shirya musu kaya da maigidanta ta nuna mata, tace, "ga abin karinku na hada muku, Rabi'ah bata tashi ba shi yasa bata kai muku ba!"
Saboda ita bata shiga bangaren Maigidan. Bakin iyakarta dashi idan sun hadu a falo ta gaisheshi, ko kuma tayi dakonshi da safe idan tana kicin tana aikin girki.
Anty tace, "da kyau Nadiyata! Wallahi kamar kin san ina kewar girkinki dama. Bari idan Daddy ya fita, zamu shiga kasuwa anjima muyi siyayyar spices don gashin kazar nan da kike mana da kuma local mac-D dinki nake son ci."
Tayi murmushi tana gyada kai, "to shikenan Anty, Allah Ya kaimu!"
Anty ta dauki farantin ta fita, ita kuma ta cigaba da aikinta.
Data gama ta dauki nasu abincin ta kai daki. Sai lokacin Rabi'ah ta tashi, ta shiga bayi. Kafin ta fito har Nadiya ta gyara dakin, ta hada musu shayi. Suka zauna suna kari. Mama ta kira suka gaisa, ta hadata dasu Rabi'ah suka gaisa, kafin hira ta kacame musu ita da su Maryam. Nan ta barsu suna ta yi, ta kwashe kayan abincin nasu ta kai kicin.
Dakin ta koma ta fara tsifar kanta saboda ya fara datti, a gida kuma bata cika samun lokacin yin tsifar ba. Tana jin sanda Rabi'ah ta kashe wayar tazo tana tayata itama. Tana son irin gashin Nadiya wanda ya kasance baki, sassalaka kuma mai tsayi sosai. Ba kamar irin nata ba wanda yake mai tauri sosai duk da cewa itama ba laifi tana da tsayin gashin da kuma baki.
Bayan nan dakin Anty Jamila suka je suka gyara mata, daga nan suka shiga dakin mazan gidan don su gyara. 'Ya'yan Anty Jamila hudu, danta na farko Auwal da suke cewa Yaya, shekarunshi sha bakwai, yana Sudan wajen Yayan Babansu, sai Rabi'ah yar kimanin shekaru sha biyar, sai mai bi mata Abubakar Sadeeq shekarunshi goma, dai autanta Haroun, suna ce mishi Haneep, shekarunshi biyar.
Da yake tana da abokiyar zama, wani lokacin yaran su kan je gidanta suyi weekend ko hutu,
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 2 Chapter of 36