bakikkirin. Ji take kamar ta dinga kwala ihu saboda takaici. Waye shi? Me yake takama da shi? Shi har ya isa ya zo inda take ya dinga zabga mata maganganu marassa dadin ji ma kamar haka? Amma ta kasa daga kafa ta bi bayanshi kamar yadda zuciyarta take umartarta da tayi hakan.
Nan ta kara jimawa tana shakar kuka, da kyar ta iya hada nata-i-nata ta wuce gida.
Ranar sai wajen karfe tara ta koma.
Tana dira kuma Abba ya tareta da nashi fadan, Aiken data dinga mishi na mutane akan maganar ya janye aure. Ya zageta tas, yace aure kuma babu fashi tunda ya karbi kudi. Don kaniyarta ta kashe kanta in taga dama ma karewa.
Ta koma daki nan ma Mama da Amarya suka sanyata a gaba da nasu kalar wa'azin da nasiha, ita dai kam ji take yi duniyar ma gabadaya tana wani juya mata. Ji take kamar duka mutanen duniyar sun hade bakine sun juya mata baya.
Da abin ya isheta Sai ta dargwaje musu da kuka, amarya ta fara aikin lallashinta Mama kuwa sai ta saki tsaki, tace, "don Allah kyaleta taje tayi duk abinda taga dama kuma tunda dai ta ki jin lallashin. Yarinya a dinga dama da ke amma kiyi biris da mutane saboda kunnen kashi ne da ke? Sai kiyi duk abinda kike ganin daidai ne a wajenki tunda mu ba zaki ji maganarmu ba."
Ta karkade zaninta ta barsu anan amarya na kara bata baki.
Aka kai mata abincin dare, ta samu ta tsakura haka nan ta barshi anan. Wayarta ta kashe gabadaya saboda taga Anty Lima na ta danna mata kira, ga Abdullahi da shima har ya gaji da kiran ya koma aika sakonni. ita kuma bata son takura ko kadan.
Saboda ciwon da kanta yake mata sai data sha magani sannan ta kwanta. Ko a cikin barcin ma, tufka kawai take yi da warwara, yadda zata samu ta bulle daga wannan aure. Shi yasa barcin bai haifar mata da komi ba sai tarin ciwon kai da ciwon jiki daya bar mata.
Da kyar ta iya tashi can wajen karfe biyun dare, ta dauro alwala mai kyau ta je ta fuskanci alkibla ta fara sallah. Koda ta daga hannunta sama, bakinta dauke yake da addu'ar Allah Ya hana yiwuwar wannan aure ta huta.
Bata samu ta kwanta ba sai da suka yi sahur sannan. Wannan karon kam barcin mai nauyi tayi sosai, don bata tashi ba sai can wajen karfe goma sannan.
Shima vibrating din wayarta ne ya tasheta. Ta zauna da kyar har wani jiri-jiri take gani ta daga wayar. Tayi tunanin Anty Lima ce ko Abdullahi, amma ga mamakinta sai taga Safiya ce.
Tayi dan murmushi, a ranta tana cewa yau watarana? Watakila itama ta kira ne ta mata tsiya kamar yadda jiya su Aysha suka dameta da Rabi'ah.
Ta daga murya a shake mai cike da barci, "Hello, Sophie manyan kasa. Ya kike?"
Shiru ta ji tayi kamar babu kowa ma akan wayar. Ta fara "Hello... Hello?! Kina ji na?!"
Zuwa can kuma sai taji kamar ana shesshekar kuka. Sai jikinta yayi sanyi, tace, "Safiya? Lafiya, me yake faruwa?"
Cikin rishin kuka tace, "har kina da bakin tambayata lafiya bayan abinda kika yi mun?"
Kanta ya daure da mamakin wannan abu, tace, "ban gane ba, me kike nufi Safiya? Me nayi miki kuma?"
Tace, "in case baki sani ba, Habib was meant to be mine, ba naki ba! Anyi mun alkawarin aurenshi tun ba yau ba, na gama tsara yadda rayuwata zata tafi a matsayin matarshi tun kafin ki san da zamanshi. Me yasa zaki zo ki wargaza min shirina? Me yasa zaki shiga cikin rayuwata? Me na miki?!"
Ta dargwaje da wani irin kuka mai tsuma zuciya.
Nadiya ta kasa cewa komi. Ta rasa abinda zata ce. Sai da kyar ta iya daga baki tace, "ban san me kike cewa ba Safiya, Amma ina mai tabbatar miki da cewa ko ma menene, ban san komi akai ba. Yadda kika ji maganar auren nan sama-ta-ka, nima haka na ji ta. Ni wallahi neman ma yadda za ayi in rabu da wannan karangiyar auren nake yi amma na rasa ta yaya zan yi hakan!"
Safiya ta ja hanci, tace, "kada kiyi gaggawar bari kanki ya fasu don kinga an zabeki a kaina. You don't know half of what's awaiting you a cikin wannan auren. Ki kula!"
Da wannan gargadi mai girgiza rai ta kashe wayar.
Nadiya ta bi wayar da kallo ranta a jagule, har ga Allah ranta bai yi mata dadi ba. Yadda taji Safiya tana kuka ya sanyayar mata da jiki, daga jin yadda take yin kukan kai da kanka kasan cewa da gasken yi take yi, da gaske son Habibun take yi. To ita kuwa me zata iya yi akan haka? Wannan abu ne wanda ya fi karfin tunaninta.
Ta kira Anty Lima, saboda ita kadai ce wadda ta fi kusa da duka Madam da Safiya. Tana da tabbacin zata iya sanin ko ma menene yake wanzuwa.
Anty Lima ta ja numfashi ta aje bayan da Nadiya ta gama kora mata bayanin abinda ya wanzu. Tace mata, "tabbas, wannan zance haka yake. Tun farko, Madam ita zabinta shine Safiya ta auri Habib. Naji ita kanta ta gama tsara komi, har yadda karatun Safiya din zai kasance bayan auren nasu. To kuma abinda duk basu yi tsammani ba shine da aka zabe ki a madadin Safiya din. Babu wata amsa da suka bayar wadda ta wuce cewa kin girmi Safiya, kuma kin fi ta sanin rayuwa. Don haka ne sai itama Madam din ta ajiye zancen auren su Safiyar a gefe. Ita kuma tun bayan da Madam ta bata tabbacin cewa Habib nata ne, saboda tana da tabbacin cewa za a zabeta, sai kawai ta ba ranta cewa ya zama mijin nata. Kawai ta fara son shi abinta da tsara abinda zai faru idan ta aureshi. Nima ta kirani dazu tana kuka ta ce min Madam bata kyauta mata ba."
Nadiya ta dafe gefen kanta da yake matukar sarawa, tace, "me zan yi Anty Lima? Yaya zanyi? Bana son abinda zai sa in shiga hakkin wani ko kadan Anty Lima. Bana so in zalunci rayuwar Safiya!"
Anty Lima tayi kasa da murya cike da lallashi, tace, "Nadiya, babu zancen cin zali a cikin wannan magana. Ba ke kika ga Habibu kika ce kina son shi ba, ba kuma ke ce kika ce kina son shi ba. Me yasa ba zaki zauna kiyi tunanin watakila alkhairin a tattare da ke yake ba da Safiya ba shi yasa aka zabeki a madadinta? Kada kiyi butulci da ni'imar Allah Nadiya. Ke da bakinki kike fada min addu'ar da kike yi akan Allah Ya kawo miki miji kiyi aure, me yasa kuma yanzu kin samu damar hakan kike neman butulcewa Allah? Sai me don manufar Hajja Umma da Madam ta daban ce game da auren? Ke ki yi shi don Allah mana, ki yi shi don saboda raya sunnar Ma'aiki Sallalahu Alaihi Wa Sallam!"
Nadiya tayi shiru hawaye suna tsiyaya daga idanunta, maganganun Anty Lima din suna ratsata.
Tace, "to Safiya fa? Kinji fa cewa tayi...!"
Anty Lima tace, "ki manta da zancen Safiya Nadiya. Ki duba gabanki ke dai. Safiya a yanzu take kan ganiyar yammatancinta. Ina kuma kara tabbatar miki da cewa, ba son Habibullahi take yi ba, son irin rayuwar da zata yi a matsayin matar Habibullahi dinne take yi. Saboda tun farko da irin wannan tunanin Madam tayi galaba a kanta ta shuka mata irin wadannan tunane-tunanen. Don haka ki kwantar da hankalinki, Safiya is an adult, ki barta tayi dealing da matsalar da ita ta janyowa kanta ba ke ba!"
Ta gyada kai a sanyaye, "nagode Anty Lima!"
Tayi dan murmushi, "anytime Nadiya, anytime!"
Ta kashe wayar itama tana dan murmushi. Sai taji ranta ya dan yi mata dadi. Magana da ita ya sanya taji wata natsuwa tana shigarta a hankali.
Mama da take sauraren hirar tasu, tayi dan murmushi itama a hankali. Ta cigaba da jan carbinta tana hailala da salati.
22.
Karfe bakwai saura, ya shiga gidan nasu. Daga Masallaci yake, hannunshi rike da hannun Ammar da ke ta bashi labarin irin abubuwan da suka faru a makarantarsu yau.
Kai tsaye bangaren Hajiya Ummah ya wuce kamar yadda al'adar gidan nasu take. Duk azumin duniya a can suke shan ruwa. Haka karin safe da abincin dare kullum a can suke haduwa da duka iyalan gidan su ci.
Ya samu Shukurah zaune a tsakiyar hadadden falon na Hajiya Ummah. Tsarinshi da komi na falon idan ka gani sai kayi tunanin ko wani gidan sarauta ne ka shiga.
Ta dan kalleshi a kaikaice lokacin daya shiga, ta mayar da kanta kan tarkacen kayan shan ruwa da ke gabanta, har ta rasa wane abu ma zata ci daga ciki.
Hajiya Ummah kuma tana kan dinning a zaune, da alama itama sai lokacin take buda baki. Ya wuce wajenta kai tsaye shima ba tare daya kara kallon inda Shukurah din take ba.
Ammar ya karasa wajen Hajiya Ummah da sauri, ya zauna akan kujerar dake kusa da tata. Babu bata lokaci ya sanya hannu cikin fruits da aka yanyanka ya dauki tuffa ya kai baki. Daga Habibun har ita, murmushi kawai suka yi a tausashe.
Ya karasa haye matakalar da zata sadashi da teburin, shima ya ja kujera dake fuskantarsu ya zauna. Ya bude baki yana gaishe da Ummah din tare da yi mata barka da buda baki.
Ya dauki faranti yana kokarin zubawa kanshi abinda zai ci, yayinda ita kuma Hajiya Ummah ke bude baki tana kiran mai mata girki, Lailah. Nan da nan sai gata ta fito daga kicin kamar dama jiran kiran take yi.
Tace mata, "zubawa Babangida abinci."
Ko kafin ma ta kai ga daga kafa ta karasa kusa dashi, ya dakatar da ita. Yace, "bar shi kawai, zan zuba da kaina."
Don haka ta juya ta koma inda ta fito. Shi kuma ya zuba kayan marmari da kunun tsamiya a cikin kofi ya koma ya zauna. Yawancin lokuta bai cika cin abinci ba idan yayi azumi har sai bayan yayi sallar isha'i.
Ummah ke jan shi da hira game da tafiyarshi Umarah tunda shi zai rigasu tafiya ita da Shukurah, da abubuwan daya kamata ya duba game da kayan lefe da za a hada.
Shukurah da take jin maganganun da suke tattaunawa, ta ture kwanon Sultan chips dake gabanta, ta tashi tana kokarin fita daga falon.
Ummah ta daga murya tana kwala mata kira, "Shukurah ina zaki je ne haka bayan ko sallah baki yi ba?!"
Bata amsa ba, ta bude kofa tayi fitarta tare da maida kofar ta rufe da karfi kamar zata babbagota daga jikin ginin.
Ya kawar da kanshi kamar bai san abinda suke yi ba, Ummah kuma ta dan girgiza kai. Itama bata sake mishi maganar ba sai ta cigaba da zana mishi lissafin abubuwan da take yi.
*
Karfe tara ya koma cikin falon bayan da suka gama sallar isha'i da kuma Tarawihi. Wannan karon Ammar kadai ya samu akan kujera yana barci. Ya gyara mishi kwanciya kafin ya wuce kan dinning kai tsaye. Ya zuba soyayyiyar shinkafa data sha naman sa zako-zako, ya hada da zobo ya zauna ya fara ci. Hankalinshi na kan TV inda ake hasko labaran duniya.
Anan Hajiya Ummah ta sauko kasa daga dakinta ta zauna itama tana kallon labaran da yake ma'abociyar kallonsu ce.
Ya ture kwanon abincin gefe guda, ko rabi bai samu ya iya ci ba. Ranshi a jagule yake kwarai da gaske, akwai wani abu dake mintsininshi a can kasan ranshi a cikin yan kwanakin. Ran nashi ya ki yi mishi dadi sam.
Ya taka a nutse ya karasa inda Ummah take, kafafunshi suna nutsewa cikin tattausan carpet da aka lullube tsakiyar falon da shi. Ya zauna a kasan carpet din kusa da kujerar Umman.
Haka suka cigaba da kallon, jifa-jifa su kan tattauna wani abu idan aka fada a cikin TV din, har dai aka gama shirin.
Ummah ta kira Lailah taje ta dauke Ammar ta kwantar da shi a dakinshi da yake anan bangaren Hajiya Ummah din yake da zama.
Shi kuma sai ya juya yana kallonta a nutse, yayi kasa da murya, yace, "Ummah dama cewa nayi ko wannan azumin a kai Ammar wajen Yadikko ne? Rashida tace tana son ganinshi saboda wancan zuwan da muka yi tana makaranta."
Nan da nan kuma sai tayi kici-kici da fuska, tace, "wani irin zuwa Makarfi kuma? Duka-duka kuma yaushe ne kuka je Makarfin har kuka kwana? Ina ce ko watanni biyu cikakku ba a rufa ba?"
Yayi kasa da kanshi yana jinjinawa, "haka ne Ummah. To zan fada musu hakan. In yaso ita Rashidar sai ta zo nan din, bayan sallah sai ta koma ko?"
Nan ma fuska babu walwala tace, "Allah Ya kawota lafiya!"
Daga haka suka dan yi shiru su dukansu. Zuwa can kuma ta kalleshi a tausashe, tace, "ka tashi kaje ka kwanta haka nan ko? Karfe nawa ne kace jirgin naku zai tashi?"
Yace, "sai jibi in Allah Ya kaimu, karfe goma na safe."
Tace, "ai nayi zaton gobene tafiyar. Allah Ya kaimu jibi din. Nima kwanciya zan je inyi."
Don haka yayi mata sai da safe. Ya jira har sai data haye sama kafin ya leka dakin Ammar ya samu yana barcinshi sosai, ya mishi addu'ar kwanciya barci kafin ya wuce sashenshi.
Ruwa ya watsa, ya fito daure da bathrobe ya tsaya a gaban mirror yana goge jikinshi. Bayan ya gama al'adar shafe-shafenshi daya saba, ya lalubi pyjamas ruwan madara masu taushi ya sanya. Ya sake bin jikinshi da turarenshi ya fesa.
Har ya nufi kan gado, sai kuma ya juya. Ya dauki wayarshi dake kan bedside drawer, ya fita daga bangaren nashi.
Gidan nasu babban gidane, an ginashi tun lokacin Mahaifinshi yana matsayin General ne. Wajene wanda yayi gadonshi tun Iyaye da Kakanni, daga baya kuma bayan rasuwarshi aka fadadashi aka hadeshi da wasu filaye. A yanzu kuma ya zama gida wanda za a iya cewa gari guda. Estate ce babba, wadda ta kunshi gidaje part-parts. Akwai bangarenshi, ga bangaren Ummah, ga bangaren Shukurah, bayan su ma akwai wasu parts din fiye da uku. Akwai waje na musamman da aka ware na motsa jiki, akwai wajen wasan yara, akwai babban garden da wajen shakatawa da shan iska, akwai madaidaicin masallaci a cikin gidan. Ga ma'aikata bila adadin da ko wane lokaci zaka samesu suna ta kaiwa da kawowa abinsu.
Ya wuce bangaren dake kusa da nashi, wanda kuma nan ne za a sauki Nadiya a cikinshi, ya shiga na kusa dana Ummah wanda na Shukurah ne.
Yanayin tsarin gine-ginen kusan duk daya ne da na sauran idan ka debe nashi da na Hajiya Umma.
Falon nata sai kamshin turaren wuta yake ga AC dake kara sanyaya dakin. Ya duba falon yaga bata nan, kai tsaye sai ya wuce dakinta.
Ya sameta tsaye tana kokarin ninke abin sallah, da alama sallah ta gama yi.
Ya wuce ciki kai tsaye ya zauna a gefen gado yana kallonta har ta gama ninkin, ta cire hijabin jikinta. Itama kayan barcin ne a jikinta, da alama ta gama shirin barci.
Ta haye gadon kai tsaye ba tare data tankashi ba, ta fara kokarin jan bargo ta rufa. Ya bita da kallo ranshi yana kara baci, yana kokarin dannewa.
Kawai ya kai hannu ya warci bargon yayi jifa dashi. Ya bita da kallo fuskar nan a hade, yace, "bar ganin wai ina binki kiyi zaton wannan guntun fushin da kike yi yana damuna ne Shukurah. Kawai ina kokarin sauke hakkinki ne dake kaina, tunda naga ke baki san sauke nawa hakkin dake kanki ba. Don zan kara aure shikenan sai in zama makiyi a wajenki, dama ana hakane Iye? To idan zaki sanyayawa ranki ki hakura, kiyi hakan. Idan kuma ba zaki iya ba, sai kije kiyi tayi. Aure dai ba zan fasa yi ba, ina ga ita kanta Ummah ai ta fada miki hakan ko? Ni dai kam ta bangarena, ba zan zauna ina bin kanki ba kamar yadda take yi. Jibi zan tafi Umarah kamar yadda kika ji ana fadi, kuma ba zan dawo ba har sai bayan sallah. Don haka ki zana min duk abubuwan da kike bukata inji, idan kuma har yanzu kina ganin bani da wannan matsayin a wajenki, sai ki fadawa Ummah."
Ya tashi tsaye yana kallonta, tayi zaune tana hararar waje daya idanunta sunyi rau-rau kamar zata yi kuka. Ganin ita yake kallo yasa ta daga baki da kyar tace mishi, "ni ba na bukatar komi!"
Ya tabe baki yace, "ba laifi!" ya juya abinshi.
Har ya kai bakin kofa yana kokarin budewa, ya ji an rungumoshi ta baya. Kawai sai ta fashe mishi da wani irin kuka mai sanyaya jiki. Tayi-tayi har ya isheta, bayan rigarshi ya jike da lema.
Yana da tausasawa, kuma in ta shi ne, mace ba zata yi kuka a gaban idonshi ba. Ko me yake ganin zai yi, zai yi kokarin yi wajen ganin hawaye bai kusanci idon kowace ya mace ba, balle matar da yake aure. Ya kuma san sanin hakan da tayi ne yasa take mishi kukan, bata san ko hawayenta karewa zasu yi ba akan maganar wannan sai dai su kare, amma ba zai fasa auren wannan ba. Ko ba don Ummah da burikanta ba, ko ba don sanin manufar wannan aure ba, to don kanshi kawai, ba zai iya fasa wannan auren ba.
Ya sanya hannu ya zagaya da ita gabanshi suna fuskantar juna. Abinka ga farar mace, fuskarta har tayi ja na kukan da tayi. Ya fara share mata hawayen idanunta yana kokarin tausarta, ta kama hannunshi ta rike kam, hawaye na kara cika idanunta.
"Honey, ba zan iya hadaka da wata ba, ba zan iya rabaka da wata ba, ba zan iya zuba ido in ga kana kulawa da wata kamar yadda kake kulawa da ni ba. Me nene bana maka? Menene baka so a tattare da ni? Zan iya canzawa, zan iya gyarawa. Don Allah Honey...!"
Sai ta sake rushewa da wani kukan tana kara rirrike mishi gaban riga.
Ya kama hannunta ya ja har zuwa bakin gado, suka zauna su duka.
Yace, "wai har sau nawa ne kike so in fada miki cewa babu ko daya daga cikin wadannan abubuwan? Ko baki ji me Ummah tace miki bane ranar nan wai? Ba tace miki kiyi hakuri ba? Me yasa wai ba zaki iya hakuri ki yarda da kaddara bane? Ina ce matan ma bayan ke an halatta min har guda uku matukar zan iya yin adalci? Kuma ina da yakinin zan iya daidaita adalcin. Me yasa ba zaki yarda da maganar Umma ba at least, idan baki yarda da maganata ba?"
Sai tayi shiru tana shessheka. Tace, "to naji, amma kayi min alkawarin koda ta zo, ba zaka taba daukar soyayyarka ka bata ba!"
Ya saki wani dan murmushi yana kare mata kallo, "kin taba jin irin wannan auren ne dama Shukurah?"
Taga dai kwata-kwata abinda take son samu ba zata sameshi ba, sai ta juya mishi ta wani bangaren. Tasan ta wannan bangaren, ba zai taba iya ce mata a'ah ba. Tunda sau nawa take cimma bukatunta ta wannan hanyar?
Ta fada jikinshi tana sanya hannunta cikin rigarshi inda boturan basu gama rufewa ba, ta fara yawo da hannun cikin salo na daukar hankali da kissa. Nan da nan kuma sai ta samo kanshi, abinka da mai neman kuka aka jefeshi da kashin awaki.
Sai data bari yayi nisa a can duniyar data kaishi, jikinshi ya gama dauka gabadaya har wani bari yake yi, sai kawai ta janye jikinta, ta ja bargo tana rufe jikinta.
Ya zuba mata idanu da suka shige ciki, suka fara rinewa cikin wani irin yanayi, bacin rai yasa ya ma kasa yi mata magana. Ta kalleshi tana yin wani takwa-takwa da fuska, "ni dai gaskiya ba zan iya hada jikina da naka ba bayan nasan cewa nan gaba kadan zaka taba jikin wata. Kayi min alkawarin jikinka ya zama nawa ni kadai, kayi min alkawarin ba zaka mallaka mata jikinka ba, ni kuma na maka alkawarin mallaka maka nawa jikin."
Ya lumshe idanu zuciyarshi na wani zafi, jikinshi ma kokarin daukar zafin yake yi. Lokaci mai tsayi ya dauka a haka, kafin ya tashi zaune ya dauki kayanshi da suka yi fatali da su ya sanya, kafin ya kalleta da idanunshi da suka yi mici-mici.
Yace, "mantawa kike yi, cewa daga lokacin dana bada sadakinki kuma shaidu suka shaida aurenmu, jikinki ya gama zama nawa. Zan kuma iya yin duk abinda nake so da shi a duk lokacin da naga dama, ke kanki baki isa ki hana ni ba. Don haka ki daina mistaking cewa kina da ikon hanani, bana son tursasa mutum, ba kuma zan kusanceki alhalin baki so ba shi yasa kika ga nake binki a hankali. A hakan kike so in miki alkawarin ba zan kusanci wata matar bayan ke ba? A hakan Shukurah? Kina hanani hakkin nawa a lokacin da nake so? Kina wancakali da duk wani lamari nawa kamar ba mijinki ba? Kina amfani da abinda yake hakkina ne kina blackmailing dina da sanyani yin abinda ban yi niyya ba bayan Allah ne Ya halasta min? A hakan Shukurah?!"
Kawai ya juya ya bar mata dakin. Saboda yasan idan ya cigaba da magana ma ranshi ne zai kara baci. Bai san ma ya aka yi har ya biye mata ba, bayan dama zuciyarshi sai data dinga mishi saka da wasi-wasin kada ya biye mata ya afka cikin dana sani.
Ya tura kofar dakinshi a zafafe ya shiga, kai tsaye bandaki ya fada ya sakarwa kanshi ruwan sanyi. Yayi shiru yana sauke wata irin ajiyar zuciya mai matukar nauyi. Ranshi ya kara dagulewa. Shekaru uku kenan tun bayan aurenshi da Shukurah. Har yau yana iya tuna lokacin da Ummah take fada mishi cewa ta samar mishi wata matar bayan da suka gama gano cewa wadda yake gab da aure ba son Allah da Annabi take mishi ba. Shi kuma ya amshi auren a take, ba tare da musu ba. Aka kuma daura auren cikin abinda bai gaza wata daya ba. Ita kanta Matar sau biyu kadai ya ganta kafin bikin nasu. A kuma duk ganin da zai mata, bai ga bambancinta da wadda suka rabu ba. Su duka arzikinshi da rayuwar dadi da zai samar musu suke so, ba shi a karan kanshi ba.
Lokuta da dama kuma yana zama ya tuhumi kanshi, me yasa bai ce a'ah ba? Me yasa bai ce a'ah ba?
Ya jima sosai a cikin bayin kafin ya fita, ya sake kimtsawa kafin ya kashe wuta ya lalubi gado. Har zuwa lokacin ranshi a jagule yake. Jikinshi kuma ya mutu murus. Yayinda a can kasan zuciyarshi wani sashe yake tambayarshi, 'me yasa wannan karon bai ce a'ah ba? Me yasa ba zai ce a'ah ba?'
23.
Washegari da yamma, ya shiga sashen Ummah sanye cikin dakakkiyar shadda fara, yana ta baza kamshin nan nashi.
Falon nata tuni ya gama rikicewa da kamshin kala-kalan abincin buda baki da ake hadawa.
Ummah ta kalleshi cike da mamaki, "ina zuwa ne haka Babangida da wannan yammaci?"
Yayi dan murmushi yana gyara zaman hular dake kanshi, "wai wata yar unguwa ce zan leka amma yanzun nan zan dawo."
Ta kalleshi cike da mamaki, "unguwa kuwa da wannan yammaci Babangida, ana gab da shan ruwa?"
Yace, "ehh. Abin gobe zan tafi, Matar abokina Mus'ab ta haihu shi yasa nace zan je in gano baby saboda da dare ina da wata tattaunawa da su Kawu Haruna to ba lallai in samu zuwa ba!"
Sai ta gyada kai cikin alamun gamsuwa, ta san shi da son yara sarai, duk inda yaji anyi haihuwa, to shi kuwa a tafe yake yaje ya ga baby. Baya da wannan kasa a gwiwa din.
Tace "to a dawo lafiya. Kayi kokari dai ka dawo da wuri kafin lokacin shan ruwan ya kure."
Ya amsa mata da, "to Ummah"
Ya fita.
A bakin kofa suka ci karo da Shukurah ita kuma zata shiga. Tana ganinshi ta wani dauke kai kamar bata ganshi ba. Shi kuwa ya ratsa ta gefenta ya wuce shima bai nuna alamun ya ganta ba.
Mota daya ya dauka, kuma shi kadai. Koda direba ya taso da securities dinshi biyu, sai yace musu su yi zamansu kawai saboda ba jimawa zai yi ba.
Aka bude mishi gate ya fita, kai tsaye ya dauki hanyar 'Diamond Ara Cakes and Snacks'
m
Farfajiyar wajen babu komi idan ka dauke ababen hawan ma'aikatan wajen. Yayi parking din motarshi, ya dakata daga ciki bai fita ba ganinta da yayi tana kokarin fitowa
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 14 Chapter of 36