shi, ta kwantar da kan ta a jikin guiwar shi, itama tana kukan, ba qaramin tausayi suka ba Abba da Mama ba, fita suka yi waje, wannan karon Abba ma kukan yake,
"Kar ki tafi ki barmu, muna matuqar buqatar ki a wannan lokacin, yarinyar mu is just 2years she needs u, pls ki taimaka ki zauna da mu, Yah Allah ka d'aga kafadun ta, ka sa mata kaffara, Yah Allah ina son mata ta, ni maraya ne,ka ban ita dan ta zama haske a rayuwata, Allah ka rayan ita ta ci gaba da tallafa ma maraicina," Adnan shiru ya yi da magana dan Yana tsoron kar ya yi sab'o,ci gaba ya yi da kuka ya na riqe da hannun Sakeenaah, kukan shi ne ya sa Ablaerh qara fashewa da kuka, d'aga ta ya yi ya na rarrashin ta,dan shi yanzu ta matar shi yake, a hankali ta yi bacci se ya rungume ta a qirjin shi.
Har safiya ta waye Sakeenaa shiru ba alamar motsi a tattare da ita, hankalin Adnan da su Abbah ya yi matuqar tashi, nan da nan Adnan ya miqe ya fita, a waje yaga su Abba da tin jiyan Suna nan basu tafi ba, Suna leqa su lokaci zuwa lokaci, tashi suka yi suka nufe shi ganin tashin hankali a kwance a fuskar shi,
"Me ya faru?" In ji Abba da tin da gari ya waye ya ga bata farka ba yake cikin damuwa,
" Abba har yanzu bata motsa ba, zuwa zan na kira Doc." Ya qarasa magana idon shi taf da kwalla, numfashi Mama ta sauke, dan ta matuqar tsorata, Doc ya kira, ya je d'akin, duba ta ya yi yace zata tashi nan da kamar awa d'aya inshaa Allah, zama Adnan ya koma ya yi a gefen ta, Mama da Abba suka zauna a saman gadon dake d'akin a gefen ta , tin daren jiyan dama ya kwantar da Ablaerh akai, ido suka zuba mata baki d'ayan su kawai, kowa bakin shi da addu'ar Allah ya bata lafiya ya bata iKon farfad'o wa........
[01/07, 12:42 pm] asiyahabibu93: 💅🏼 KAI NE JARUMI 💅🏼
WRITTEN BY HAERMEEBRAERH
Page 15:
Ko da na bi inda Rasheedah ke kallo sai na hango Mama d'auke da Atiyyaerh a cinyar ta, tana shafa bayan ta a hankali a haka har ta yi bacci, komai akan idon Rasheedah ke faruwa, d'auke idon ta ta yi ta zumbura baki gaba dan ganin ga ta ta yarinyar a gefe amma a qasa ko Maman ta d'an jingina ta da jikin ta, nan da nan abun na ta ya motsa, ta d'aure fuska, ta kira Afrah, maqe kafada yarinyar ta yi taqi zuwa, sai ta matsa kusa da Mama sosai, daidai wajen Atiyyaerh, itama ta kwantar da kanta, murmushi Mama ta yi ta shafa gashin ta, a qasan zuciyar ta tana nema wa Atiyyaerh sauqin zama a wajen Rasheedah Koda ta hanyar Afrah ne.
Bakwai na cika dangi na nesa da na kusa kowa ya tattara ya koma mahallin sa, Mama sai ta wuce da Atiyyaerh gidan ta, Rasheedah ba qaramin Jin dad'in hakan ta yi ba, dan a zaton ta sun manta da wasiyyar da Sakeenah ta bar musu, ko Kuma tinda sun San halin ta ba za su yarda yarinyar ta zauna a wajen ta ba, Dan haka gida ya rage Daga Masu aiki sai Adnan,Adnan d'in kuwa dama shi ko zaman makoki da ake a farfajiyar gidan shi ba zama yake a wajen ba, ko waye ya je masa gaisuwa sai dai ya tarar da su Abba ya musu gaisuwar ya juya, Koda yaushe ya na sama cikin d'akin shi, daga sallah sai tasbihi da roqar wa matar shi da iyayen shi Rahamar Allah, Jin shi yake kamar ba zai tab'a Iya ci gaba da rayuwa Mai dad'i ba a yanzu da ya rasa jigon rayuwar ta shi.
A qarshen satin Abba yace ma Adnan ya qoqarta had'awa Atiyyaerh kayan ta da dik Wani abu da ya dace dan damqa ta wajen sabuwar Uwar ta ita wasiyya ana so a gabatar da ita da gaggawa, hankalin Adnan ba qaramin tashi ya yi ba, yayi kuka ba iyaka, da kan shi ya lallashi kan shi, dan ya san cika umarnin Sakeenaahn shi zai yi ya riga ya mata alqawari, yana daga cikin wasiyyar ta da ta dinga jadaddawa kafin ta mutu, kuma ya kamata a cika mata ita, had'a kayan Atiyyaerh ya shiga yi idanun shi na zubar da hawaye, yana cikin hadawar ne ya ga wasu takardu guda biyu, daya duba sai yaga
*Zuwa Ga Ablaerh My Love*
Sai dayar kuma an rubuta,
*KAI NE JARUMI NA*
Daukan ta Atiyyaerh ya yi ya ajiye a gefe ya bude tashi, gaba d'aya fuskar shi ba komai sai hawaye, tayi jawur da ita,
*Mijina*
*Kai ne jarumi na, kai ne hasken idaniya ta, kaa zauna dani cikin so da qauna, tare da amana, ka zama jigon rayuwa ta, kai ne Wanda in nayi kuka kk sharen hawaye na, in nayi dariya kk tsayawa ka kalli kyau na ka yaba min,in nayi girki kai santi ka yabi aiki na*
*Jarumi na, ina qara roqon ka akan ka daure akan abinda na yi wasici akai, ba dan ba ka da iko akan d'iyar ka ba, sai dan na san Jarumtar ka zata sa ka yi hakuri, dan cikar burina, fatana ka yi ta min addu'ar samun sa'a akan quduri na kar ya zama ba nasara*
*Allah ya had'a fuskokin mu a jannatul firdaus, mu d'ora rayuwar aure fiye da wadda muka yi a nan duniya Mai Cike da tsafta da jin dadi, INA SON KA MIJINA JARUMI NA*
*DAGA MATAR KA SAKEENAA*
Saka takardar ya yi a qirjin shi yana kuka, a qasan zuciyar shi kuma yana jin kwarin guiwar rabuwa da gudan jinin tashi, ci kaba ya yi da had'a kayan ta, bayan ya gama da kayan nata ne ya dauki wayar shi ya koma d'akin shi, (ban san me ya ke fada ba tinda ya rufe ta ciki☹) bayan zuwa kamar awa d'aya cur ya fito d'auke da wasu akwatuna da jaka a rataye a kafad'ar shi, qasa ya sauka ya kira driver din shi, bayan ya shiga ya gaishe da Adnan,sai Adnan ya bashi umarnin d'iban akwatunan daya d'akko daga d'akin shi zuwa qasa, sanan ya koma ya dakko kayan Atiyyaerh, ya zauna a kujera ya na kallon cikin gidan, daga baya ya miqe ya fita cikin hanzari yana share kwalla, zuciyar shi na tinano masa irin zaman so da qauna daya faru tsakanin shi da Sakeenaah a cikin gidan, d'aya motar ya bude ya zuba kayan Atiyyaerh a ciki,ya ja da kan shi, ya nufi gidan Mama, yana zuwa ya yi parking a farfajiyar gidan sannan ya shige ciki, Atiyyaerh na ganin shi ta daka tsalle ta d'ale shi tana masa surutai, wani ya gane wani Kuma bai ganewa, shi dai ba ya buqatar ganewar ma, kallon ta kawai yake kamar wanda ba zai sake ganin ta ba, Abba ne ya fito Mama na biye da shi,
"Aa Adnan kaine tafe, barka da zuwa, Bismillah zauna mana ka ke tsaye"
Isa gaban Abba ya yi ya bashi hannu kan shi a qasa kamar yanda suka Saba gaisawa, bayan sun gaisa ne ya gaida Mama ta amsa cikin sakin fuska da tausayawa, janyo kayan Atiyyaerh ya yi gaban su, sannan ya miqa wa Mama dan akwatin da ake saka mata kayan adon ta, musamman na gashi, share hawayen da ya gangaro masa ya yi sannan yace,
" Abba ina neman izinin ku akan tafiyar dana yanke hukuncin yi, zuwa Dubai, domin ci gaba da kasuwanci na, a yanzu banda sauran dalilin zama anan, sai dai inna tafi zan din ga zagayowa domin ganin ku,ku kad'ai nake kalla a matsayin iyaye, dan haka ba zan dad'e ba zan dinga zuwa ganin ku, sai dai duk abinda nake fad'a yanzu sai fa Kun bani izinin ku zan aikata shi,"
Kan shi a qasa, yana sauraran amsar su,ya na addu'ar Allah kar ya sa su dakatar da shi, dan baya Jin zai iya ci gaba da Zama a Nigeria kusa da 'yar shi ya na ji ya na gani ta na rayuwa a hannun Rasheedah,
"A gaskiya Adnan dole na jinjina Maka domin kuwa na yarda da sunan da Sakeenaah ke Kiran ka da shi na *KAI NE JARUMIN ta* domin kuwa a iya tsahon rayuwar ka ka ga abubuwa kala2, dan haka ina son wannan karon ma ka zama jarumin wajen sanyawa zuciyar ka hakuri, in dai tafiyar ka zata sama maka kwanciyar hankali ni dai na maka izinin tafiya, Allah ya sanya albarka, ya kare mana kai dik inda ka shiga, nasihata a gare ka ka zama mai tsoron Allah, kar ka zama mai sab'a masa ko ketare dokokin shi, in kai haka Allah zai kare ka ya kiyaye ka,sannan Kuma ka samu ka je wajen Baffanin ka da Kawunan ka ka musu sallama kar ka tafi ba tare da sanin su ba"
Kallon Mama suka yi da ta sha majina irin na masu kukan nan,
"Adnan Allah ya maka albarka, ya faranta maka, Allah ya jiqan mahaifan ka da Sakeenaah ya raya abinda kuka haifa Allah ya kare mana Kai a dik inda ka shiga, Allah ya habaka kasuwancin ka Ameen,"
Amsawa suka yi dikan su da "Ameen" sannan sika miqe don raka Adnan zuwa waje, wasiqar da ya ga an rubuta sunan Atiyyaerh ya zaro a aljihun shi ya damqa a hannun Mama sannan ya yi gaba zai fita,Atiyyaerh ce ta riqe shi tana kuka, tana kiran Mummyn ta, Adnan zuciyar shi ta cika fam da quncin rabuwa da mutanen da yafi so a rayuwar shi, bai san sanda ya yakice ta ba ya shige motar ya ja da gudu yana kuka, Mama da ta sunkuya ta d'aga Atiyyaerh dake birgima a qasa, kukan itama take, Abba share kwallar shi ya yi ya taimaka mata sika d'aga ta, dan ji ta yi ta yi mata nauyi, sai tirjewa take, tana kiran Daddy da Mummyn ta, a haka sika shiga,Mama ta goya ta,yar wayar shi Abba ya lalubo ya kira Auwal.
Ba su fi awa biyu a zaune ba Auwal da Rasheedah suka shigo, bayan gaishe2 ne, Abba ya sanar masu da dalilin kiran nasu dika, ya kira su ne dan damqa amanar da marigayiya Sakeenaah ta bar masu, Rasheedah ce ta bata rai sosai, sannan ta ce..........
[01/07, 12:42 pm] asiyahabibu93: 💅🏼 KAI NE JARUMI 💅🏼
WRITTEN BY HERMEEBRAERH
Page 16:
Bakin ta da ta bud'e za ta yi tijara kamar yanda ta Saba ta kulle gam dan ganin yanda kowa ya d'aure fuska dan son ganin qarshen rashin mutunci da qiyayyar da take wa 'yar uwar ta ta, musamman ma Auwal da yake jin in tace zata yi wani gangancin nuna ita fitsararriya ce ba abinda zai hana shi yau a gaban iyayen na ta ya jibge ta ai hukunta ta ya yi tinda Rasheedah dai kamar jakka take sai ta ci bugu take nutsuwa yau kuwa a shirye yake da ya hukunta ta gaban iyayen nata, tana fuskantar hakan daga wajen Auwal sai ta ce,
"Ba sai ka tashi ka dau akwatin mu tafi ba, aiki ma malam kawai ina fama da wasu qananan a gaba na a tashi a wani jonan wata,"
Ta na kaiwa nan ta yunqura ta dau qarama daga jakunkunan Atiyyaerh ta yi waje ta na mita addu'ar shiriya iyayen ta da mijin nata suka bita da shi, Mama sai share hawaye take ta na kukan tausayin marainiyar Allah, da ace Sakeenaah ta yi shawara da ita kafin dasa wannan tunanin a zuciyar ta ai da ta hane ta, ta sauya mata da wata shawarar Mai billewa, domin a iya hangen nesanta na manya bata hangowa Atiyyaerh Jin dad'i wajen Innar tata ba sai wahala, Abba ne ya dinga lallashin ta ya na bata baki ya na nuna mata abinda ya sa Sakeenah yanke wannan hukuncin, fatan su Allah ya sa yarinyar ta yi SANADIN shiryuwar Rasheedah.
Rasheedah na fita waje ta ga mota mai matuqar kyau sosai a fake a harabar gidan, gefen motar kuwa drivern gidan marigayiya ne jingine da ita, drivern ne ya duqa kad'an ya gaishe ta, sannan ya tambaye ta inda mijin ta yake, amsa masa ta yi da,
"Ya na ciki akwai Wani abu ne?"
Sai Wani zaro ido take, komawa gefe drivern ya yi yana jiran fitowar Auwal, zuwa ta yi kusa da shi tace,
"Malam ba aiko ka aka yi ba ne? To ka isar min da saqon mana in ya so in ya fito se na Sanar da shi,"
Kallon ta ya yi kawai dan yana da labarin ta tsaff dik Wani kalar wulaqanci da qiyayya da take nuna wa Madam din su ya sani, dan haka cike da jin haushin ta ya kalle ta ya ce,
"Amma ai da na zo kk ga na maki magana hakan na nuna maki cewa na san ko ke wacece,shi ya sa ma na tambaye ki mijin ki, To saurin Jin saqon da yake ba naki ba na mene ne? Ki Jira ya fito mana mtswww"
Cikin tsananin mamaki da shakkar drivern ta ja baya tana qunquni, dan ba qaramin jibgegen mai qarfi bane, fuskar nan baqiqqirin ba wasa a tattare da shi, komawa ta yi ta qame sannan tace,
"Ka gama b'oye2n uwar da zaka b'oye duk uwar da zaka fad'a zai dawo kunne na ne"
Cikin fushi ya matsa daf da ita yace,
"Uwar wa kk nufi?"
Su Abba ne suka fito dan rako Auwal da Atiyyaerh dauke da akwatunan yarinyar, Abba ne zai Kai su tinda Auwal ba shi da abun hawa,kicibus suka yi da abinda ke faruwa tsakanin Rasheedah da driver,kallon Rasheedah suka yi wadda ido ya firfito waje ya mata gulu2 se wara su take cike da tsoro, a firgice take da mutumin kamar ka ce mata kyatt ta saka gudu, hanlalin ta ya yi mugun tashi to dukan ta wannan basamuden ze yi ko me?
"Niiiii....niiii...ni.. ban ce uwarr ka baaa.. ai,"
Ta qarasa maganar tare da damqe bakin ta da ke rawa, tsoro ne ya mamaye ta ta ji kamar ta saki fitsari saboda maimaita kalmar uwar ka da ta yi, tana kyalla ido taga su Auwal na fitowa da gudu ta kwasa ta yi wajen su tana maida hawayen daya taru mata, Auwal na ganin yanayin ta sai ya ji be ji dad'in hakan ba, ko ba komai ya na son matar shi, halayen ta ne baya so ko kad'an, cikin yanayin daure fuska ya ce wa mutumin,
"Malam lafiya zaka sa min mata a gaba kana muzurai? Kai ba drivern Alhaji Adnan bane?"
Cike da girmamawa ya qaraso, ya gaishe su, sannan ya sanar dasu ya kai Adnan Airport ne se ya bashi umarnin ya kawo motar gidan Auwal,ya je gidan nasu ya tarar ba kowa shine tunanin shi ya bashi ya zo nan, ya San ba za su wuce nan d'in ba, godiya su ka yi sosai, Mama hawayen tausayin Adnan da qaramar 'yar su ne kawai ke kwaranya a idanun ta, shikenan yanzu ya tsallake wata qasar dan kawai ya manta da damuwar rashin matar shi,anya kuwa ba za su nemi fatawa wajen malamai ba? Anya ba a cutar da shi ba? ta na wannan tunanin ta ga Suna Saka kayan Atiyyaerh a motar, sannan Auwal ya ce,
"Mu je ka aje mu ka dawo da motar, Dan ka ga dai mu bamu da inda za mu ajiye ta, kar a sace a wannan unguwar tamu, gwanda a barta nan kawai zai fi"
Da Jin haka sai driver ya ce,
"Ai Yallab'ai cewa ya yi na maida ku can gidan shi, in yaso ko in akwai wani abu da kuke buqata a can gidan naku kun je ku dauka daga bay,amma yafi son ku koma gidan nashi da zama tinda ba kowa ciki se masu aiki"
Auwal ya so ya qi karb'ar tayin komawar su wannan katafaren gidan Rasheedah ta hau rantsuwar ba zata koma tsohon gidan su ba ga gida sun samu daga sama su tsaya Wani halin qauyawa, Abba ma tausar shi ya yi akan ai ba komai ya karb'a su koma can d'in zai fi maslaha, da kyar Auwal ya amince za su koma d'in, murna Rasheedah ta hau yi ko kunya bata ji bakin ta har kunne, ashe da rabon ta a cikin wannan makeken gidan,kaiii jama'a daɗi kashe ta, haka suka d'unguma suka yi gidan, suna isa bayan sun fitar da kaya ne ta shiga ciki da Farha da Ayiyyaerh, driver na ganin ta wuce ya zagaya gefen Auwal ya fad'a masa wata magana qasa2, sannan suka yi sallama ya tafi, yana waiwayen gidan yana hawayen kewar iyayen gidan nashi masu son shi, masu karamci, addu'ar samun Rahamar Allah ya yi wa Sakeenaah sannan ya nema wa uban gidan shi sauqi a wajen Allah daga halin quncin da yake ciki,kafin su rabu se da Adnan ya bashi jari mai tsoka da qaramin gida, shida me gadi, su Shamsiyya ma sai da ya musu ihsani sosai kafin ya sallame su, dik da ya basu zab'i in suna so Suna Iya ci gaba da zama idan sabuwar matar gidan bata da matsala da hakan.
Tana isa ta aje Afrah dake hannun ta ta saki hannun Atiyyaerh da ta tattaka ta nufi sama dan dubo Mommyn ta, ta na tafe ta na kiran mommyn nata da Daddyn ta, Rasheedah kuwa juyi ta hau yi tana kallon gidan, wani daɗi ne ya kama ta, yanzu ta zama hajiya kenan, ga sauran suturun Sakeenaa nan, dan da akai rabon gadon Sakeenah surutun ta kaf an bar wa Rasheedahn ne tinda kusan girman su d'aya, murjewar fata kawai Sakeenaah zata nuna wa Rasheedahn saboda banbancin Jin dad'in rayuwa,a lokacin da aka ce an barmata suturun qunci ta dinga yi ta na fad'in ba a bata komai ba, gani take duk uwar dukiyar su ace ba ta da abin gada na qanwar ta ta se sutura? Auwal ta gani ya shige ta ya yi dakin da aka kwatan ta mai direct, bin bayan shi ta yi da azama,daf zai bud'e qofar d'akin dan ya shiga ne ya juyo ya wurga mata wani kallon da yasa ta koma gefe da sauri, shiga ya yi ya saka key, inda aka masa kwatance nan ya leqa,baya ya yi da sauri, dan bai tab'a ganin abinda ya gani ba a rayuwar shi, kud'i ne maqudai masu yawan gaske, a cikin wata jaka qarama, gaba daya ya rud'e se zufa yake samun gefen gado yi ya zauna,yana kallon kudin daga nesa, takardar dake Kai ya dakko ya bude, karantawa ya hau yi a zuciyar shi, idonun shi sai zubar da hawaye suke, nan danan ya saki kuka sosai, tausayin bayin Allahn nan yake ji matuqa,a yau ya tabbata dukiya ba ita ce kad'ai farin cikin rayuwa ba,komai Allah ya baka ko da tsinke ne ya nufa ta SANADIN shi ne za ka yi farin ciki to kuwa za ka yi farin cikin,nan take ya ji duk soyayyar da yake wa Rasheedah a baya ta kau, domin ta dalilin ta ne wannan qunci ya sami wannan mutum na rabuwa da gudan jinin shi, domin ba dan qiyayyar da ta nuna wa Sakeenaah ba da tini yana tare da diyar shi, daure fuska ya yi ya miqe ya adana kud'in ya cire key d'in ya fita daga d'akin a bakin qofa ya gan ta ta na muzurai, Wani mugun kallo ya watsa mata sannan ya Isa d'akin da ya ke Jiyo kukan Atiyyaerh ya d'auke ta suka bar gidan, bin shi ta yi da kallo da son qarin bayani akan me ya Kai shi cikin d'akin Kuma me ya faru ta ga kamar ya yi kuka, Auwal kuwa ya fita ne saboda baya son ganin ya ta yanzu kwatakwata, ji yake kamar ya rufe ta da duka, ya rasa me zai gaya mata ya fidda mata wannan halayyar tata a jikin ta, kyabe baki ta yi ta ci gaba da exploring gidan.
Ana Kiran sallar azahar Auwal ya dawo da Atiyyaerh ya shige d'aki ya yi alwala zai wuce masallaci, Atiyyaerh da ke Jin yunwa ce ta ke tab'a Rasheedah ta na maimaita mata kalmar,
"Mummy tea, Mummy tea, Mummyyyy"
Jin da ta yi bata amsa mata ba sai ta fashe da kuka sosai, Afrah da ke tsotsar hannu lokaci zuwa lokaci ta tashi zaune tana ta kallon ta tana tsotsar yatsan ta babba, a fusace Rasheedah ta juya ta kalli Atiyyaerh da ke kuka ta ce,
" Wacce irin jaraba ce wannan, ke ba zaki bar mutane su huta ba? Dubi yanda kika tasar min yarinya, kin koma kin zauna a can ko sai kin ci uban ki yanzu,"
Cikin zare ido da d'aga murya take maganar, abinda Atiyyaerh bata tab'a sani ba kenan a rayuwar ta, ai ko ta fashe da wani rikitaccen kuka,ga yunwa na damunta, tin da suka dawo bata ci abinci ba, gashi har azahar ta yi Auwal ya so ya tsaya ya had'a Mata tea d'in amma kawai ya wuce masallaci.
Ko da ya fita ma tinanin halin da ya baro yarinyar yake, kukan ta har cikin ranshi yake jin shi, maqotan su Rasheedah basu tab'a jin kukan Atiyyaerh haka ba,unguwar ta talakawa ce Adnan ya yi gini a ciki domin ya na kwadayin taimakawa marasa shi, ya tabbata in ya yi gini a manyan unguwannin masu kud'i daidai da abincin da za a bayar sadaka ba lallai a samu masu buqata ba, dan haka ya yanke shawarar gina gida anan,Kuma yake taimaka masu sosai, tausayin yarinyar ne ya kama su dan a tinanin su Atiyyaerh na kukan rashen mahaifiyar ta ne,
"Ahhh lallai naga alama zaki fara cin ubanki kuwa,nace ki yi shiru se ki baren baki? Ke baki san menene shiru ba ashe? Tsit nace"
Ta dora yatsan ta a baki tana zaro mata ido, cikin kuka da gigicewa yarinyar ta kwantar da kanta a gadon tana runtse ido, dan a tsorace take da zaro idon da Rasheedah ke mata,amma ta kasa yin shiru, a hasale kuwa Rasheedah ta kaiwa bakin duka tana fad'in,
"Shiii nace kar na sake jin kukan ki"
Damqe bakin ta ta yi tana ci gaba da kukan a hankali, tare da ajiyar zuciya, a haka ta samu ta yi bacci, tana ta ajiyar zuciya, miqewa Rasheedah ta yi ta fice tana banbamin fad'a, Auwal ne ya dawo a gaggauce hannun shi d'auke da biscuits da madarar gwangwani babba da na Ovaltine, sai millo.
"Ki ji tsoron Allah akan amanar da aka baki, Ina jiye maki sanda amana zata ci ki, Marainiya ce fa? Wanne irin hali gare ki? Na yi matuqar danasanin had'a zuri'a da ke, na yi danasanin sanin ki a rayuwa ta, amma bawa baya wuce qaddarar shi, Rasheedah ke ce mummunar qaddara ta a rayuwa ta, Ina roqon Mai dika da ya bani iKon cin jarabawar nan,dana san haka kk da ba zan taba hada zuri'a dake ba?"
Ya na gama magana ya ajiye mata ledar ya wuce d'akin shi dan yin sallah tinda ya San yanzu Kam an riga da an idar a masallaci.
Wani irin haushin Atiyyaerh ne ya qara kamata,yanzu a Kan wannan yarinyar take ganin wutar qiyayya da tsabar tsanar ta a idon Auwal? Ina soyayyar da yake mata ? A Iya sanin ta dik laifin da za ta masa Kuma ko me zai faru tsakanin su Auwal be tab'a dena son ta ba, hawaye ta ji na bin kuncin ta, da sauri ta goge su, ta na ayyana kala kalar muguntar da zata gana wa Atiyyaerh.
Bata ba wa yarinyar nan komai ba kuwa na ci sai dare da suka zo cin abincin dare, ai kuwa ta na gama cin abincin ta hau amai, saboda yunwar da ta mata yawa a cikin ta, masifa da bala'i Rasheedah ta fara yi ta na dungure mata Kai, a haka ta gyara wajen ta na zage zage, tea ta had'o mata ta dangwara mata a pida ta haye sama, dan ta riga ta qudurta yau sai ta gwangwaje a sabon gidan nan halin da Atiyyaerh ke ciki kuwa ba zai hana ta hakan ba,
Auwal kuwa tinda ya fuskanci take taken ta ya wuce d'akin yaran shi maza ya yi kwanciyar shi da su bayan ya gama nuna masu su dinga kula da qanwar su, duk abinda take so Suna yi mata daidai Wanda za su iya,
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 9 Chapter of 21