Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
kullum na tina halin dana shiga ni d'aya ji nake kamar zuciya ta zata fashe ta tarwatse, Umma bata riqe amana ba, bata riqe zumunci ba, Mummy ta yi zaton zata iya canja mata halaye idan ta bata ni, bata san kuskure ta tafka ba, ta azabtar dani, ta azabtar dani, ta azabtar dani, ta min auren da bana so,na koma bazawara, na had'iyi baqin ciki irin Wanda in aka wa mutum auren da baya so ya yi hakuri ya danne domin biyayyar Allah da ta iyaye ya d'and'ana,Yan zu Kuma Ina had'iyar baqin cikin rabuwa da mutanen da na Saba da son su, saboda son zuciya irin nata, su nake gani na ji ina da iyaye, domin sun d'auke ni a matsayin d'iyar su ta cikin su, ba suruka ba, Ahmad ya gwadan soyayya mai tsanani da kulawa, kowa nawa ya gujen har ba a so a zo wajena, na San a lokacin nan dik uzirin da mama ke bani na rashin lafiya da ta so zuwa waje na a mota za a kawo ta ta zo ta ganni, amma har na gama rayuwa da Ahmad bata San ya d'aki na yake ba, na yi hakuri na shanye, hakan ta faru ne saboda ita ta dalilin ki ne Umma ke ce silar komai, ke ce silar shiga ta matsala da damuwa a rayuwa, habaaa ba zuciya a qirji na ne? Kar ku Yi zaton bana Jin zafi da radad'in yada ni da kuka yi, na zab'i na Maida komai baya na ne Dan kwanciyar hankalin kaina, amma ba Dan na manta ba,su kan su 'yan uwana da ke so na da Abbana da ke so na sai dai na ga soyayyar su daga nesa amma ba za a nuna min soyayyar ba yanda zan ji dad'i na San yess ana so na, Afrah ce kad'ai ke take duk wata doka ta nuna min so, me na aikata mara kyau? Me yasa ku ke tsoron ta ku ke kyale ta har ta ke abinda ta ga dama, ba zan tab'a yafe miki ba Ummaa, ba zan yafe ba, ba zan yafe ba, dan haka kar Wanda ya nemi yafiya ta," Duk maganganun nan da take tana yin su ne cikin kuka da buga qirjin ta da qarfi da hannayen ta bibbiyu,Yousuf ji yake kamar ya riqe hannun ta dan gani yake zata jima kan ta ciwo, ga kuka tana yi kamar zata hadiye zuciya, ba wanda baya kuka a wajen, Rasheedah tin tana kukan a tsaye sai da ta durqusa, kukan tsananin nadama take Wanda bata tab'a tinanin zata yi shi ba nan kusa,a zaton ta duk abinda take yi rama banbancin da aka nuna mata tsakanin Sakeenah da ita ne,kuka take sosai irin kukan da take jin asalin tsanar kanta,da halayen ta, muryar Atiyyaerh ce ta sake karad'e kunnuwan su baki d'aya, " Bana buqatar ka Daddy, zan ci gaba da rayuwa ni d'aya cikin raina Ina ji na kamar marainiya, kamar yanda ka saba min tin fil azal shekara 19 baya, ai na d'auki darasin rayuwa yanzu Kuma, zan iya ci gaba da qarasa rayuwata ba kai, tinda haka kk so kuma ka zaba min,I am ok with the kind of love I am receiving from my family, zan yi bakuri da kalar soyayyar da kowa ke nuna min, na riga na Saba da hakan and it is ok for me," Da gudu ta zo zata shige ciki, cikin zafin nama Daddyn ta ya riqe ta gamm a jikin shi yana kuka, yana son yi mata magana ya bata hakuri amma ya kasa, sai qoqarin kwacewa take ta shige ciki, amma sam ya hana ta, duk ta b'ata masa riga da kurkur din da ke fuskar ta, data gaji da qoqarin kwace kan nata ne ta kwanta a qirjin shi tana ta kuka,jikin kowa ya yi mugun sanyi a wajen, sai yau suka San cewa ashe kallon kowa take, a zaton ta har cikin ran su ba sa qaunar ta, to me zata fahimta dama a yanayin yanda abubuwa suka dinga faruwa? Ai ta ma yi hakuri da su, tinda Suna ji su na gani ta ke azabtuwa ba Wanda ya tsaya mata tsayin daka dan ganin ta kubuta daga hannun Rasheedah, " Atiyyaerh my love, ki duba girman Allah da soyayyar ki da Annabin rahama ki yafe min,iyakar abinda zan iya ce wa kenan, bani da bakin magana, nafi son cika wasiyyar Mummyn ki fiye da komai a rayuwa ta a wannan lokacin,wannan dalilin ne yasa na bi umarnin da ta bayar, na tafi na barki zuciya ta na tsananin son ki,ina son jinina a kusa da ni nima, amma ba yanda zan yi, dana zauna naga ana wulaqanta ki, wanda na san dole za ai hakan tinda kowa ya San Rasheedah bata son 'yar uwar ta da suka fito ciki d'aya ba Kuma ta son abinda ta haifa, shi yasa na tafi, kome kk ciki ina sane da shi ta hannun mai gadi na da driver na,  a kullum sai na yi kukan qunci, ta haka ne na samu ciwon zuciya, amma alhamdulillah Allah ya yaye min yanzu na samu sauqi da yardar Allah ciwon be yi nisan da ba zai warke ba Allah ya taqaita min shi,a lokacin da na ji daddad'an labarin da kullum Mummyn ki ke fatan ya tabbata sai na ji hankali na ya yi na dawo gida, musamman tin tana raye ta yi min umarnin in naga maganar auren ki da Yousuf masoyin ta da ke ta taso na tsaya tsayin daka dan ganin auren ya tabbata, ga takardar ki da ta rubuta maki, ki yafe ni ki karba ki karanta,zata maki bayanin komai a nan," Cikin sauri ya hau kiciniyar zaro takardar daga aljihun shi,ya damqa mata, kamar ba zata karba ba can kuma ta saka hannu ta karba, *Atiyyaerh My Love*   *Ina fatan sanda takarda ta zata isa hannun ki, kina cikin qoshin lfy, da cikar imani, My baby, ki yi hakuri,ki yafe min, ki yafewa Daddyn ki, sannan ki yafewa Yayata, abar qauna ta, kome da ta miki a rayuwa, na san ba zata miki mai kyau ba, ba zata so ki ba kamar yanda ta ambata, amma ina roqon alfarmar ke ki so ta, ki qaunace ta kamar ni, ki zama mai yafiya, ki zama mai biyayya, in burin raina ya cika, wato auren ku ke da d'a na Yousuf, ki zama mai ladabi da biyayya ga mijin ki, baki da wanda ya fishi a duk duniya, haka yake ga duk wata d'iya mace, a lokacin da ta yi aure qoqari take ta zama mace ta gari a wajen mijin ta, ki kasance mai tsafta, iya girki, iya kwalliya, da magana, ki zama mai tsoron Allah, da nema a wajen Allah, kar ki zama mai shirka, mai neman wani biyan buqatar ki wajen wanin Allah, in kina haka Allah zai so ki,mala'ikun shi zasu so ki, mutane zasu so ki, mijin ki zai so ki ya qaunace ki.* *" Abalerh dear ban bar ki a hannun yayata dan ki wulaqanta ba, na bar ki ne dan ta koyi riqo da zumunci, ta san me ake kira da zumunci, ta cire tsananin son kan ta da take da shi, sai kaso wani sannan son d kk wa kan ka zai amfane ka, in kana da yawan qiyayya a ran ka zaka rasa soyayyar Allah, data mala'iku, da ta mutane, sannan kowa naka zai qi ka, soyayya ita ke jawo soyayya, ba yanda za ai qiyayya ta jawo soyayya, amma soyayya na jawo giyayya ta koma so, shi nake fatan ki bawa Rasheedah yayata soyayyar ki, dan qiyayar ki ta koma so a wajen ta,"* *A qarshe ina mai tabbatar maki ina son ki, ina qaunar ki, amma wanda ya fiki sona ya kira ni,ki kula da kan ki.*          *I love you so much Ablaerh na* A yanzu kam zuciyar Rasheedah ta gama kakkaryewa in to million pieces, tabbas ta karbi soyayyar 'yar uwar ta da 'yar 'yar uwar ta, ta yi nadamar qiyayyar da ta nunawa Sakeenah da abinda ta haifa ashe haka so yake?saboda kwanciyar hankalin da ta ji ta lullube ta a yanzu ba zata Iya misalta shi ba, Wani qunci da quntata da zuciyar ta ke d'auke da shi na shekara da shekaru se ta ji babu shi, ta rasa ta ina zata fara bada hakuri sannan wa da wa ya dace ta fara bawa hakuri dan kuwa ta cutar da kowa, sai kawai ta yi dif kamar an d'auke ruwa, ta kasa bud'e bakin ta ta ce Ummm ko A'ah, kowa a zaton shi kawai halayyar ta ta ce ta motsa, sai dai ta yi ta bin mutane da ido. Atiyyaerh juyawa ta yi ta rungume Daddyn ta bayan ta gama karanta masu wasiqar da Mummyn ta ta bar mata, sai murna kuma suke, Daddy ne ya kalli Afrah yace, " Yanzu dai tinda qanwar ki ta yafe min ai na san kema zaki yafe wa Daddy ko?" Cike da jin kunya ta miqe ta je gare shi, had'e su ya yi ya rungume, a haka wannan iyali suka kwana ana hirar yaushe gamo, kamar daren sallah, haka suka kasance dan farin ciki, cannn suka ji Rasheeda ta fashe da kuka sosai har tana siqewa, dan tinda suka ga ta ja ta yi shiru kowa ya yi banza da ita, kowa ya nemi yafiyar Atiyyaerh Kuma ta furta ta yafe ma kowa, ganin Rasheedah bata kula su ba ne ya sa mama ta ja su suka nufi kitchen ake ta hidimar azziqi aka barta a wajen, wannan shine dalilin da ya sa a yanzu kowa ke mamakin kukan ta "Na roqe ku da ku yafe min, ku yafe min, ku yafe min, ku...ku...ku yafe min,in ba ku yafen ba Allah ba zai yafen ba, ku tausaya mun ku yafe min ba dan hali na ba sai domin Allah da manzon shi da zumuncin da kuka yi riqo da shi ni na wulaqanta shi, ku yafe min ko zan ga haske a qabari na da rayuwa ta na shiga uku na lalace ni Rasheedah Ina zan Kai haqqin zumunci da marainiya wayyoooo Allah na na shiga uku na," kuka take sosai na tsananin nadama da danasanin abinda ta aikata,Afrah ce ta kalle ta ta kauda kai,zuciyar ta ta yi rauni ganin yanda mahaifiyar ta ke kukan da bata tab'a irin shi ba,amma a haka ta kauda Kan ta gefe dan in dai har  Atiyyaerh bata yafe mata ba itama ba zata ci gaba da sake mata fuska ba, matsawa ta tashi ta yi daga in da Umman tasu take, ta koma kusa da Sulaiman da shima ya b'ata rai sosai, dan shi ya na ma tantamar sahihancin wannan kukan nadamar,anya ba Dan ta ga Daddy ya ninka da arziqi bane? rarrafawa Rasheeda ta fara, ta kama qafar wannan ta saki ta kama ta wancan ta saki, Daddyn Atiyyaerh 'yar shi kawai ya ke kallo, dan Shima ya na jin in bata yafe mata ba shima ba zai yafe mata ba, cike da kukan nadama da kaico take roqon su, Atiyyaerh ce ta taka ta je gaban ta, ta durqusa ta d'aga ta, bata ce komai ba ta rungume ta, wata runguma Rasheeda ta mata kamar zata maida ta ciki, sai da Atiyyaerh ta zaro ido ta yi qara kadan sannan ta ce, "Ummaaaa haqarqarina zasu hade waje d'aya ai" Cike da shagwaba ta fadi hakan, gaba d'aya wajen aka saka dariya,a hankali kowa ya nuna ma Rasheeda ya yafe mata, suka ci gaba da hirarrakin su tare, ita dai banda matsar kwallar da take lokaci bayan lokaci ba abinda take, ta kasa Saka baki a hirar, Wani irin nauyi da kunyar su take ji, anan ne Abbah ke tambayar Daddy cewar, "Wai ni Adnan ba za ka yi aure ba ne, shekara da shekaru ka qi kula kowa,ai ba ka zauna haka ba,kar ka manta har yanzu fa kana da sauran quruciyar ka, dan ba zaka wuce 46 ba ,to dan me zaka tauye kan ka?" Sosa qeya ya yi irin na samarin da aka wa maganar aure sun ji kunya,kawai se kowa ya saka dariya,Adnan kallon Abbah ya yi ya ce, " Abba na ga wadda ta kwantamin a rai a yau d'innan a airport, amma ban magana da kowa nata ba, ko ita bata sani ba,aban wani lokaci tukunna,Abba in ka ganta,kamar su d'aya da marigayiya, komai nasu iri d'aya, banbancin su wannan tafi margayiya tsaho da haske, hatta shigar da margayiya ke yi itama wannan irin ta na ga ta yi, " Cike da mamaki kowa ke sauraran bayanan shi, fatan alkairi Abba da mama suka yi.masa, sannan Auwal ya yi magana cike da Jin kunya, ya ce, " Abbah ina ganin in ya fiddo mata ai sai a had'a da namu ayi ko, tinda Sulaiman ya samu mata shima qanwar wanda ke neman Afrah yake so, gani nima na samu macen da zan qara, a kusa da mu take, yarinya ce sa'ar Sulaiman," Ya qarasa maganar yana sinne kai, wai shi kunya, dariya aka saka a wajen,mutuniyar ku kuwa suman zaune ta yi, cikin wata iriyar muryar da kowa ya kasa fassara ta ta ce, " Aure? Aure fa Auwal? Da yaushe ka qulla wannan abun ban da masaniya?" "Da lokacin da ki ka rufe ido kina cin zarafin marainiyar Allah, kuma ki ke qoqarin hana d'an ki auren d'iyar da ya kamata ace ke kk had'a auren su da kan ki tin fil azal" Cikin matsanancin kuka Rasheedah ta ce, "In dai dan haka ne ka yi wa Allah ka yi hakuri na amince a yi auren su amma kar ka min kishiya,ka sani aduniya bana son kishiya Auwal na tsani komai da zai zama kishiya a wajena dan Allah kar ka min kishiya na canja hali na ba zan sake ba, Mama Abbah dan Allah ku bashi hakuri na sauya daga mummunan halin da na d'orawa kaina na zab'i kyakkyawan hali, dan girman Allah kar ka min kishiya Auwal "  Mama ce ta tashi tsaye ta na nuna Rasheedah da yatsa ta ce, "Ai kuwa sai ki fara son kishiya tin yanzu, mara mutunci, wato halin naki zaki dawo da shi ko? To in baki fasa ba baki cika Rasheedah me mugun hali ba," Abba ne ya riqe Mama dake tashi tsaye tana masifa, Rasheeda kuka take sosai da ya fi na d'azu, ita za a yi wa kishiya yanzu, ba a mata kishiya ba tin da yarintar ta da ruwan jikin ta se yanzu da ta tara manyan yara?..... . *Hahaiiii cassssssssssss Rasheedancy za ai mata kishiyancy, su waye zasu yi qawayen uwargidancy, 🤣🤣🤣🤣🤣* [07/07, 6:15 pm] asiyahabibu93: 💅🏼 KAI NE JARUMI 💅🏼 WRITTEN  BY HAERMEEBRAERH *Ina masu tambayar yaushe za a gama Littafin KYAKKYAWAR FAHIMTA?   To ina mai yi maku albishir da samuwar Littafin KYAKKYAWAR FAHIMTA dan kuwa ya kammalu ya zama ready, ga masu so su mallaki nasu ku yi min magana ta 09031416423 idan an yi payment ɗin #500 ta wannan account ɗin 0006366584 Ja'iz bank, Hamida Sanusi Ahmad,zan tura wa mutum nashi da yardar Allah...kar ku bari labarin Muid'o da Jiddah ya wuce ku💃🏻❤️* *Duk mai son ta koyi yanda zata haɗa kayan gyaran jiki domin  sana'a ta neme ni a 09031416423 Dan ta mallaki LITTAFIN MAIDA TSOHUWA YARINYA A FARASHIN #1000 kacal* Page 33: Se da ya gama lallab'a ta sannan ya tambaye ta abinda take so ta karya da shi, nan ta shiga zayyano masa abubuwan da take so Cike da shagwab'a shi Kuma ya na haddacewa , da kyar ya samu ta yi bacci sannan ya rufe ta ya ja mata qofar a hankali ya fito. Yanda suka barta a haka ya tadda ta, be damu ba ya hau bata umarnin ta dora abin karyawa saboda kar amarya ta tashi ba abinci,  Kuma amarya ta na so a yi mata farfesun kayan ciki dan tana buqatar abu me d'an yaji yaji da ruwa ruwa,ta had'a da chips sannan ta soya qwai, sai ta mata kunun gyad'a, yanda yake fad'an saqon amaryar cike da umarni da izza abun ya gama gigita Rasheedah yau ita ake bawa Umarnin yi wa kishiya girki? Ga shi a yanda yake mata maganar ba wargi bata isa cewa dan me ba shiru ta yi dan tana gudun ya liqa mata duka ya qarasa zubar mata da d'an mutuncin da ya yi saura gaban 'yar cikin ta, ita yanzu gaba d'aya tsoro ma yake bata, ba qaramin canjawa ya yi ba, yana juyawa zai tafi ya yi Wani mugun murmushi, dan tabbas ya san amaryar shi mai Suna Khadeejah na da kirki sosai da sanin ya Kamata, ga ilimin addini da na zamani daidai misali, amma fa ya san tana da wani hali guda d'aya wato tsanar duk wani mai mummunan dabi'u wanda kuskuren da ya yi kenan wajen neman auren ta da ya yi ta hanyar zayyane mata halayen matar shi, a da yayi haka ne dan ita in tazo ta tausayawa Atiyyaerh ta bata kulawar da Rasheedah ta gaza bata,se ga shi ma bata ci gaba da zama da su ba ta koma wajen su Mama, amma yanzu ya gane kuskuren da ya yi na fad'a wa macen da zai aura halin matar shi ta gida,dan ya kula amarya so take ta ci qaniyar Rasheedah da kyau, zai bar su kuwa har zuwa lokacin da Rasheedah zata yi hankali Yana tafiya ya na magana shi kad'ai, "Ai ko ba zan hana ba, yanzu ne zata san a ina ya kamata mace ta yi kishi sannan shi kishin ya ake yin shi," Ya sake yin wani murmushin mugunta ya fad'a d'aki, Khadeejah kuwa har ta tashi ta shiga wanka sai shima kawai ya fada suka yo wankan su fes bayan soyayyar su da suka sha, dik da ta na Jin kunyar shi a matsayin ta na mace Kuma budurwa, burin ta a gidan yanzu shine ta na so ta yi maganin Rasheedah dan haka in Auwal ya yi mata wani abu musamman wanda ya ke sata dariya topa zata ware murya ne tai ta dikar dariya,sedai ba irin dariyar nan mara dad'in sauraro take yi ba,ah ah ta na Yi ne cike da salo da yanga a ciki,Auwal d'in duk na kula da ita,ya kan sha dariya sosai shi d'aya ya jinjina kaidi irin na mata a ran shi. Bayan sun kammala shiryawa ne ta ce Masa, " Honey ni na gaji da zaman d'aki, muje Parlour, yunwa nake ji sosai, kaga tana gamawa kawai sai muci ko," Ta fad'a tana wani rausaya, aiko Auwal kamar raqumi da akala haka ya rungume ta a jikin shi suka nufi Parlour, Rasheedah kuwa da ta d'akko palates zata aje a dinning ce ta d'aga Kai ta hango su suna fitowa manne da juna, Khadeejahn ta Wani maqalqale shi sai shagwab'a take ta na Washhh ita jikin ta ciwo yake, suka samu kujera suka baje, suna maida nunfashi, cikin dariya Khadeejah tace, " Honey kasan me?" Ya girgiza kai dan ba qaramin kai shi duniyar wata take ba, "Lips din ka wani zaqi suke da shi kamar zuma, bana gajiya da sumbatar su" Ta qarasa maganar ta da Kai bakin ta nashi, ba wata wata kuwa Auwal ya cafke nata ya na Wani lumshe idon, Khadeejah kuwa ta haka ta yi dabarar d'agawa Rasheedah hannu tare da zaro ido kamar tana yi da wata 'yar ta ta mata nuni da ta bar wajen, da sauri ko Rasheedah ta yi gaba dan ba zata Iya jure ci gaba da kallon su a wannan halin ba, zuciyar ta kamar zata fashe haka take ji, hankalin ta a matuqar tashe yake, yau wace irin jarabawa take gani? " Oh Allah ka min maganin wannan tashin hankali da nake ciki, ashe haka zafin kishi da radad'in shi yake?" Aje plates din ta yi ta koma, ta qarasa soya kwai tana yi ta na sharar hawaye, bayan ta gama ne, ta kai komai zata wuce Auwal yace ta tsaya ta karya, taso yin musu Khadeejah ta sa baki, "Habaaa Yaayaah ki yi wannan aikin sannan ki tafi baki ci ba pls ki zauna muci, kinga cin abinci a tare ya na qara hadin kan iyali" Cike da kissa take maganar tana kashe idanu, mamaki yarinyar ke bawa Auwal dan kuwa kowa ya San ta da kunya da girmama na gaba da ita mutane na tsananin yaba mata, shine dalilin da ya Kai shi neman aure wajen ta, wata zuciyar ke Sanar da shi cewa. 'laifin ka ne Auwal, ka riga ka b'ata matar ka uwar 'ya'yan ka a gaban wadda ba ka aura ba, dole raini ya shiga tsakanin su' Zama Rasheedah ta yi kamar wadda kwai ya fashewa a ciki,ga masifa tana son yi, amma sai ta kula wannan da gani ta ci uwar ta a bala'i da kissa gashi ba dama ta yi magana Auwal zai mata rashin mutunci a gaban kishiya, sannan in suka yi fad'a da Khadeejah da alama ita zata kwana a ciki, dan kowa laifin ta zai gani musamman Mama zata ga bata sauya halin ta ba dama qarya take, duk girman ta da manyan yara ace wai wata na juyata haka hummmm rayuwa kenan? Amarya ce ta debi chips ta had'a da kwai ta kai bakin Auwal, cike da jin dad'i ya bud'e baki ya amsa,cikin ran shi ya ke ayyana... ' Oh rayuwa kenan ashe nima da rabona a soyayya' A hankali ya tauna yana lumshe ido, ji yayi an sumbaci saman idanun shi dake rufe,ya bud'e ido se ya ga Khadeejah ce cikin yanga ta ce, "An kuwa tab'a fad'a maka kai d'in kyakkyawa ne? Da kai haka baka ji yanda kasa zuciya ta gudu ba, tab'a ma kaji," Kafin Auwal ya yi magana ta ja hannun sa ta dora akan qirjin ta, shiko yana jin ya damqi cikakku kuma tsayyayun na fillos har wani danna hannun shi yake wai zai jiyo zuciyar ta ta, dukan table d'in Rasheedah ta yi da hannayen ta biyu ta miqe tsaye,nan take suka maida hankalin su kan ta, " Ba zan iya d'aukan wannan barikancin ba Auwal akan me....," Maganar ta ce ta katse saboda kallon da Amaryar ta wurga mata me matuqar rikitar wa,ai kuwa ba qaramin kidimata kallon ya yi ba, anya yarinyar nan ba asiri ta musu ba dika? Ta mallake miji dan kawai ta gana mata azaba,kamar daga sama ta ji Amarya ta fashe da kuka, harda shessheqa, cikin b'ata rai Auwal ya ce wa Rasheedahn, "Bata hakuri," Rasheedah kuwa Imani ya mata yawa kawai se ta sake baki,cike da wata gigittaciyar tsawa da tinda suke bata tab'a ji ya yi irin ta ba ya maimaita cewa ta bawa Amarya hakuri,a rud'e ta ba Amaryar hakuri, kamar an kashe redio kuwa ta yi dif, ta lafe a jikin Auwal, sannan ya umarci Rasheedah da ta koma ta zauna, hawaye ne kawai ke gudu a idanun ta, quncin da take ji a zuciyar ta bata Jin zata Iya ci gaba da zama a gidan nan, saboda da dikkan alamu amaryar nan ta zo ne da niyyar kassara rayuwar ta,Auwal d'in ta ne fa, Wanda ke shanye dik Wani rashin mutunci da wulaqanci ta, Auwal d'in ta da ke susucewa akan ta ya b'ata lokaci wajen gwada mata soyayya, Auwal d'in ta ne fa uban yaran ta, amma a yanzu Yana neman fin qarfin ta, cikin kwana d'aya yarinya qarama ta gigita shi ta sa ya fita hayyacin sa, anya zata Iya rayuwa a haka kuwa? A hankali ta koma ta zauna ta na share hawayen ta da suka kasa dena zuba "Zauna ki ci abinci da kyau Ina Gani salon ki zo yunwa ta kama ki ki rame ko ciwo ya kama ki ace bana adalci a tsakanin ku ko?" Zama ta gyara tana hawaye tana tura abincin, yau 'yar cikin ta ke mata mugun abu haka? Oh duniya kenan juyi2, Auwal ne ya d'ebi farfesu ya Kai bakin shi sannan ya deb'o ya ce wa amarya ta bud'e baki ba zafi, ta na bud'e wa ya zuba mata a bakin ta hau taunawa cikin yanga, itama ta d'auki spoon ta d'iba ta bashi,  a haka suka ciyar da juna suka qoshi, Suna ta zuba soyayyar su,zuciyar Rasheeda kamar ta daina aiki haka take ji,ango da amarya sun lula duniyar soyayya ta

Chapter 19 of 21