a Yi wa yarinyar, rungume shi ya yi sosai a jikin shi dan ya yi kukan shi ba me hana shi, sun fi minti 5 a tsaye, sannan ya kamo hannun shi suka qarasa shigowa, zaunar da shi ya yi a kujera kusa da Sulaiman da idon shi har yanzu yake kamar gauta, duk da yayi kukan amma har yanzu zuciyar shi na nan da takaicin wannan had'in auren, ji yake kamar yaje ya batar da Ahmad din, in ba a ga ango ba wa zai aure ta d'in? Afrah ce ta je ta debowa Abban nasu ruwa da abinci, zama ya yi yaci tukunna, yaran na mai kallon lallai Abba har abinci kk iya ci? Bayan ya gama ya yi hamdala sannan ya fara magana kamar haka,
" kuyi hakuri, kuyi hakuri, kuyi hakuri, shine kalmar da zan iya had'a ku da ita, ku sani uwa ta wuce wasa, kar kuce zaku yi fushi da mahaifiyar ku, tabbas uwa ba abar wasa bace, ku yi hakuri da hukuncin da ta yanke, ni kaina zan so hana wa, amma a wannan karon ina son, itama ta ga irin abun da Sakeenaa take son ta gani, na fahimci inda komai yake dosa yanzu haka, ku qara hakuri, zuciyata tafi taku b'aci, badan komai ba sai dan ganin nine mai gidannan, ina da ikon sawa kuma na hana, amma qiriqiri gidana yafi qarfi na, dan haka dole na bamu hakuri dika, Yousuf kai hakuri a daura aure sai ka koma,"
Yana kaiwa nan ya miqe da jakar shi ya wuce ciki, wata qara yousuf ya saki ya koma da baya ya kwantar da jikin shi akan kujerar, sunan Allah kawai ya fara ambato, dan yasan shine kawai mafitar shi a halin da yake ciki cikin iKon Allah kuwa sai ya ji ya fara samun sauqin zuciyar shi, umarni ya ba Afrah akan taje wajen Atiyyaerh, ita kuma bata son zuwa kunyar ta take, wannan zalinci har ina, me zata ce mata? Da wanne idon zata kalle ta to? Amma haka ta miqe ta shiga dakin, tana zuwa ko taga Atiyyaerh na rawar sanyi, tab'a tan da zata yi se ta ji jikin ta rauuuu, kamar wuta, sai karkarwa take, miqewa tai a kid'ime zata fita, ita kuma ta tattare duk qarfin ta da ya rage ta cafko ta,
" Kar ki sanar da kowa, in kk fita raina zai fi haka baci, ki barni wataqila mutuwa tace tazo dan ta sauqaqa min komai dake faruwa dani, ina zan saka kaina, na zama marainiyar qarfi da yaji da ubana, ina mahaifina? Meyasa bai waiwaye ni ba ya nunan ina da uba? Me yasa bai zo ya tsaya min ba? Afrah ba mai jin kukana ko nayi, a banza, ko nai roqon a taimakan a banza, amma ba komai, akwai Allah, kuma baya barci,"
Afrah kuka kawai take ba qaqqautawa, Atiyyaerh ko idon ta yanzu ya bushe, bata jin kukan ma, sai suyar zuciya, a haka aka kira sallar isha'i suka miqe, dan ranar ko magrib ba wanda ya yi,alwala Atiyyaerh ta d'auro da taimakon Afrah, mazan suka yi jam'i suka rama magrib da ke Kan su sannan suka maida isha'i, tinda suka yi sallah Atiyyaerh ke zaune a wajen bata motsa daga wajen ba, domin ta kula sallar da ta yi ta yaye mata wani kaso mai tsoka daga damuwar ta, miqewa ta yi ta ci gaba da jero nawafil, bata samu ta zauna ba sai da taji qafafun ta sun kasa tsaiwa, saida taji idon ta na rufewa sannan ta kwanta a wajen, cikin zuciyar ta addu'a kawai take na neman zabin Allah, tana roqon in laifi ta yi wa Allah ya ke mata wannan horon ya yafe mata, in jarabawar rayuwar ta ce haka tana roqon Allah daya bata ikon ci, kar ya sa ta sab'a masa,a haka bacci ya dauke ta,Afrah ita kuma sai wajen hudu ta tashi ta yi ta nata nawafil din da addu'o'i, kowa a gidan bai rintsa ba banda Rasheedah da ta yi d'aid'ai a gado, tana ta kwasar barci harda saleba.
A yau ne aka daura auren Atiyyaerh da Ahmad, akan sadakin su da suka bada dubu goma,bakin shi kamar zai tsage dan murna,hakoran nan nashi farare da suka rine da hayaqi sai kyalli suke , ba laifi Ahmad na da dan kyau,daidai misali, but he is not that extremly handsome, abokan shi 'yan ganye kamar ruwa a wajen, haka aka tashi Abban su Rasheedah kamar zuciyar shi ta fashe, ko gidan su Atiyyaerhn bai shiga ba ya sa kai ya tafi gidan shi Mama kuwa dama bata zo wannan auren baqin cikin ba, ta dai Kira Yousuf a waya ya had'a ta da Atiyyaerh, ta mata nasiha sosai Kuma ta bata hakuri akan abinda ke faruwa, su Yousuf da Sulaiman daga wajen suka yi makaranta, dama Sulaiman a shekarar ya shiga first semester yake ya na so ya Maida hankali dan ya samu GP me kyau kamar yanda Yousuf ya ke nuna masa mahimmancin hakan, ba wanda ya dauki ko tsinke a cikin su suka wuce,kafin Sulaiman ya San Kiran da ake musu ya sa ran samun wani abu wajen Abban su amma yanzu ji yake in ba kud'in makarantar da ya zama dole ba bai da buqatar komai wajen su ba qaramin haushin su yake ji ba dikan su, Auwal ne ke ta gaisawa da abokan Ahmad, sai abun qauraye suke masa, a haka taron ya tashi, Auwal ya shige gida, direct d'akin shi ya nufa, dan gidan kamar ba aure ake ba, a dangi ba wanda yazo, sai wasu qawayen Rasheedan su uku, suma d'aya ce halin su ya zo d'aya da ita, sauran biyun ne suka samu suka gyara Ablaerh, suka sa ta ta yi wanka, bata masu musu ba ta yo ta fito, bayan ta dauro alwala, zama ta yi suka shafe ta da mayuka masu kyau da suka zo da shi, masu qamshi, a cikin su wata tayo mata humrah mai qamshi sosai, suka shafe mata da turaruka , suka mata kwalliya daidai yanda kyaun ta zai qara fitowa, mamakin kyaun ta suke, the more suna kallon ta the more suna qara ganin kyaun ta, Afrah kam ko jambaki bata saka ba bare kwalli, haka ta zauna kamar wadda take takaba, fuskar nan ba walwala ko ta sisin kwabo, haushin ma Ablaerh da ta zauna ake mata wannan shirmen take, murmushi ta mata ta dafa ta bayan qawayen Umman su sun fita,
" Bana son damuwar ki, in na tafi ina tinano fuskar ki cikin damuwa hankalina zai dinga tashi ne, ki sassauta wa zuciyar ki, ni yanzu na sallama wa Allah ragamar rayuwata na san ba zai tsaran abinda zai zama cutarwa a gare ni ba, zan shiga gidan aure na da son zaman gidan mijina ba da wata niyya ba, tinda ya zama mijina ba zan masa musu ba, zancen halayen shi da kk tsoro kuma kar ki damu, duk fa wanda yaso zama lfy shi yaso,ki sama min nutsuwa ta ganin kyakkyawar fuskar ki cikin annuri,ta haka ne inna tafi zan dinga jin dad'in tunawa da ke, ki min alqawarin zaki dinga zuwa wajena Ina ganin ki, ta haka ne kewa ta zata ragu,"
Afrah gyada mata kai kawai take cikin kuka,daga qarshe suka rungume junan su, Atiyyaerh ta yi matuqar qoqari wajen maida hawayen ta ta hadiye su, dan bata son ta bawa Afrah qarfin guiwar ci gaba da kuka, bud'e qofar aka yi aka shigo, qawayen Umman su ne da umman tasu, dayar mai halin Ummar tasu ce tace,
" Yar nema mai kan buta meye na kukan? Ke za a aurar ko neman gindin zama a wajen ta? Kar na qara ganin kin zubda hawayen ki a banza,"
kallon tsana suka bi ta da shi, ba wanda ta tanka ta a cikin su,
" To Ablaerh kin ji dai abubuwan da muka fada maki d'azu, aure ibada ne, ki jaddadawa zuciyar ki haka kar ki saka mata wani tinani bayan wannan Allah ya albarkaci rayuwar auren ki ya kare ki daga dikkan Sharrin da ke cikin ta ya had'a ki da alkhairin da ke cikin ta,"
Daga nan suka miqar da ita dan raka ta gidan auren ta dake maqotaka da su, d'an tsayawa ta yi sannan ta tafi wajen Umman su ta durqusa,
" Ummana na gode da kulawar ku Allah ya qara girma ya biya maku buqatun ku na alkairi, Ummana ki yafen dukkan bacin ran dana kasance ina saka ki a ciki a dik sanda ki ka kalle ni, ki yafe min dan na tafi da albarkar ku,"
Sheqe2 ta kalle ta tace,
" Na yafe maki Allah ya maki albarka, ai wa miji biyayya a zauna lfy dan nasan halayen ki kaf na taurin kai,"
kallon ta Afrah ta yi ta kauda kai, sannan ta fice, miqar da ita qawayen Umman suka yi sai gidan su Ahmad, ba laifi, an masu tarbar mutunci, an girmamasu, d'akin Atiyyaerh kam ya sha kaya,Auwal ba qaramin qoqari ya yi ba wajen cika d'an madaidaicin d'akin da kaya masu tsada, dakin ciki da parlor ne,sai wani d'an kewayayyen waje nan ne toilet, sannan kitchen din su na kwano ne waje ne na had'aka dika matan gidan nan suke girki, a haka kowa ya fara watsewa, dan atiyyaerh bama ta san sanda Afrah ta zame ta tafi ba, tana komawa gidan dakin su ta tafi ta fada gado ta yi ta kukan baqin ciki, kukan tausayin halin da 'yar uwar ta zata shiga anan gaba.
Ango ne ya shigo da ledar shi a hannu, ya ajiye, direct wanka fad'a ya na gamawa ya fito daga makewayin nasu,ya saka wasu kayan, ledar da ya shiga da ita ya janyo ya kuma kamo hannun Atiyyaerh ya zaunar da ita a gaban ledar dake daf da shi, budewa ya yi se ga qatuwar kaza ta bayyana,
" Amarya kin sha qamshi , amar ya baki laifi ko kin kashe dan masu gida,"
Murmushin yaqe ta d'an yi masa, dan gaba daya tsoron shi ma take ji,
"To bismillah amarya mu ci kazar amarci dan ni dai yunwa nake ji"
Yankowa ya yi ya miqa mata a baki cikin Jin kunya ta d'an kauda Kan ta gefe, dariya ya yi yace,
" Yarinya gwanda ma ki ci dan ga qarar da cikin ki yake yi nan kema,alamar kin bar kan ki da yunwa, na riga Kuma da nasan gidan ku ba yunwa, in baki ci bama ni ba fasa wa zan ba atoh,"
"Menene ba zaka fasa ba? Ni fa bana Jin yunwa ne kawai na qoshi"
"Lallai yarinya yarinya ce, wato baki san ma me za a yi ba, tabdijam, to ke dai ci ko ba Kya Jin yunwa ci Dan Allah ba Dan ni ba"
karb'a ta yi a kunyace ta fara ci, murmushi ya mata, ta mayar masa itama, a haka suka gama ci, bayan sun gama ne, ta tashi ta d'aga komai ta goge qasan da aka saka maiqo, ta je ta yi alwala ta wanke bakin ta, shima wanke bakin ya yi ya zo ya kwanta, sallah ta yi ta zauna ta jira ta ji ko zai ce zasu yi nafila tare, kaya taga yana cirewa, daga shi sai gajeren wando, duk halittar jikin shi tana gani, wani wawan faduwar gaba ne ya kamata, cikn in ina tace,
"Ammmm naaa zaci....zaaa mu yi nafila neee, irin na sabon aure da ake yi?"
Tashi ya yi zaune yace,
" ke ni kyale ni, yau dai saboda na aure ki Allah ya ban iko har isha'i na yi,amma ni kam ba wata nafila da zan yi gaskiya"
Wani baqin ciki ne ya kama ta,da ace Ahmad ba jahili bane haka, da wataqila har son shi zata daure ta koya wa zuciyar ta bayan biyayyar auren, amma inaaa ba zata iya son shi ba samm, cikin kwantar da kai ta miqe ta je gaban shi ta durqusa, ta kamo hannayen shi,sannan ta ce,
"Haba miji na, kai da ka yi raka'a har hudu wannan kuma biyu ne fa kacal, kuma godewa Allah zamu yi akan baiwar da ya mana ta aurar da mu ga junan mu da ya yi, ka ga ai ya Kamata mu nuna godiya da farin cikin mu ta hanyar bauta masa tinda ka ga dai ba za mu yi rawa da waqa ba, magana ake ta Allah,ba Wani ba"
Da Jin haka sai ga Ahmad ya miqe ya zura riga ya je ya yo alwala, yazo ya jasu sallah tayi mamakin yanda ya dan iya ba haka ta zata ba ma sam,a zaton ta komai be Iya ba,
"To yanzu munyi sallah sai gado ko?"
Ya fada yana kamo ta jikin shi ya na qoqarin cire mata hijabin ta,Wani mummunar fad'uwar gaba ne ya kama ta Jin ta a jikin shi da ta yi,a hankali ta saki jikin ta ta kwanta a nashi tace,
"To ai baka min addu'ar da na ji ance angwaye na wa amaren su ba na neman tsarin Allah daga sharrin matar da suka aura da neman Allah ya hada su da alkairan da ta ke da shi, ko so kk na dinga ma rashin kunya ko qin bin umarnin ka?"
Kad'a kai Ahmad ya yi, sannan yace
"Nan da d'aya Atiyyaerh ke kin San da ya na iya karatun sallah ma? Ni ai ban wani iya addu'ar ba, se dai in ke Zaki koya min"
Ba musu kuwa ta koyar da shi, nan take ya dafa Kan ta ya yi mata sannan ya fara mata wasanni, cike da tsoro cikin zuciyar ta, amma ta dake, dan bata son ta yi zaman k'unci a gidan Ahmad, koma me zai je yazo so take kar ta walaka a wajen shi, taurin kan da zata mai shi zai nuna yanda ta zab'i ta zauna a gidan tinda aure dai an riga da an d'aura shi ba Kuma fasa kusantar ta zai yi ba, ko ba jima ko ba dad'e se anyi, to gwanda ma ta hakura ta sawa zuciyar ta salama,ji yake kamar zai had'iye ta, ko ina tabawa yake, yau wai shine da wannan zuqeqiyar a matsayin mata, dole a tanadi addu'a ta godiyar Allah, tun suna wasanni a qasa ya miqar da ita ya kaita gado, ina ganin yazare masu komai na jikin su na basu waje,nace a ci amarci lfy🤭
Ablaerh ta wahala ba kadan ba wajen Ahmad, ta yi kuka ta gode Allah, kukan takaicin rasa budurcin ta ga wanda ba ta taba zata ba shine yake dawainiya da ita, rarrashin ta yake sosai, yace,
"Ashe ku da ku ka yi boko ake cewa yan iska duk qarya ne, wanda basu yi makarantar ba sune yan iskan, dan kinga fiddausin bayan layi gaba daya a bude take,"
zaro ido Atiyyaerh ta yi waje, cikin razana da tsananin tsoro ta kalle shi ashe har neman mata yake bayan shaye shaye????????
[07/07, 6:15 pm] asiyahabibu93: 💅🏼 KAI NE JARUMI 💅🏼
WRITTEN BY HAERMEEBRAERH
*Makaranta ku yi hakuri ku jira ku ji ya abun zai kasance har zuwa qarshe,sannan kar mu na manta cewar kowa fa da qaddarar shi a rayuwa, ba lallai ne a halicce ka ka ji daɗi all ur life ba, we ar not in this dunya to have fun, we ar here to worship Allah, kuma a cikin bautar shi ne ya ke jarabtar mu da abubuwa kala2, in ma ya jarabce mu da arziqi, ko talauci, ko ya haɗa mana dika, gaka mai arziqi amma ma talauci, ko gaka talaka amma mai arziqi, (mai wadatar zuci talaka,da mai kudi mara godiya) dan haka nake cewa ku qara hakuri, akan kome zaku karanta har mu Kai qarshen labari thank you.*
Page 24:
Ahmad a kwanakin nan ji yake duk duniya ba wanda ya fishi morewa da matar aure, ta bangaren Atiyyaerh kuwa ta sani bata yi irin auren da take so ba, Kuma har yanzu bata son Ahmad a ranta, amma ta na Jin dad'in yanda yake kula da ita, yake nuna mata soyayya, ta bangaren surukan ta ma bata da matsala da su, Inna Abu da Baba Garba basu da wata matsala, su suke ci da su ita da Ahmad d'in, dan haka ta kan fita ta ya Innar aiki bayan ta gama da na bangaren ta,Ahmad yana da Yayah da matar shi, wadda take da qananan yara biyu,Sadiq da Umar,yaran ba qaramayen marasa kunyan yara bane, yanda uwar su take ba kunya komai a tsattsaye haka suma yaran suke, Yayan Ahmad Muhammad sunan shi kowa na ce masa Yayah, bai da matsala, amma wani lokacin akan yaran shi sai a buga da shi a tsakar gida, nan ma yana samun pampo ne wajen matar shi,me suna Hajar, Hajar ko sunan surukar ta katsal take fadan shi ba sakayawa wato Abu, shiyasa yaran suma suka dauka, Abuu, Baba Garba ne kawai suke ce wa Baba, su abincin su daban suke yin shi a gidan, in ta ga dama ta zuba ta bawa surukan in bata yi niyya ba suci da yaran ta da mijin ta.
Atiyyaerh ta kasa ce ma surukar ta Abu, sai take ce mata Inna kamar yanda taji Ahmad da muhammad na kiran ta, ta kula da yanda surukan ta ke son ta, har Yayah, sannan kuma ta kula da yanda Hajar ta tsane ta, sai tana yada mata magana akan kyaun ta ai na d'an maciji ne a Jira lokaci kad'an mummunan halin Atiyyaerhn zai bayyana ne nan gaba, amma ba ta taba tanka ta, to yaushe ma tazo gidan? Kuma ma in ta dad'e me zai kaita biye mata? Ita fa a rayuwa bata son hayaniyar fad'a, rayuwar bala'i da masifa a ciki ta taso, to me zai dame ta kuma? Dan haka ganin halayen Hajar take nafila akan inda ta baro ba Wani damuwa bane a wajen ta.
Ta gama wanka kenan ta yi kwalliya daidai ita abin ta, dan rashin sabon da ta yi ne ma da Kwalliyar yasa wataran sai ta yi wanka sai ta manta bata yi Kwalliya ba se ta tina yanzu fa a gidan miji take sai ta dan yi kwalliyar kadan, to ranar Kuma an yi sa'a Ahmad a gida yace zai wuni, ita kuma kullum tana nuna masa fita neman na kai ya na dojewa dan be Saba ba, sai ya ce mata shi fa ba sana'ar da bai gwada ba basa kar bar shi ne, haka take hakura, ta biye mai ya yi ta jagwalgwala ta, bata so amma bata tab'a nuna masa ba,kuma bata taba kyamartar shi ba, dan daidai misali bai da qazanta yanzu, tana sashi gyara a inda taga bai mata ba, da dabara da Jan hankali zata nuna masa me take so ya gyara, misali wata rana suna zaune yana ta bata labarin yan ganyen abokan shi, ,
" kinga kafin na aure ki ,nida Baba Qarami sai mu sha ganye nadi shida a rana, ba abinda ya mana zafi, amma kinga nine yanzu har na d'au sati biyu ban sha koda sigari ba, sai sau d'aya,randa kk shiga yiwa Inna tuwo na sha da kk dawo na buga qasa nace ban sha ba🤣 , kika yi kika yi na kafe na ce miki ban sha ba, kin san me?"
Kada masa kai ta yi tana dariyar tina kafiyar da ya mata yana zaro ido kamar mage ta sha wanka,
"A ranar sai na ji wani haushin kaina dan me zan sha abinda ba ki so, bayan ke tinda na aure ki ba ki da burin da ya wuce na ki faranta min? Shiyasa na yi ta qoqari na daina, dana ji ina son shan Wani abun maye gwanda na zauna a gida na yi ta Koda kallon ki ne Ina Jin nishad'in da bana Jin irin shi a cikin kayan Mayen, shine zakiga na dame ki na maqale maki, ke kuma nasan kin gaji amma a haka ki ke hakuri dani,na gode Atiyyaerh 'yar aljannah ki ta taya ni da addu'a kin ji? Watarana inshaa Allahu zan dena ne"
Tausayi ya bata ta daga masa kai kawai alamar "To" tare da tsagaita dariyar ta, a hankali ya ja ta jikin shi, bakin shi ta ji yana wani bugawa, zuciyar ta ta hautsine kamar zata yi amai, tabbas ta bari ya kai bakin shi nata zata yi amai ne kawai,dan haka cikin dabara ta janye ta na murmushi, ta ce Masa,
"Mijina ina zuwa na je na yi brush, nazo na maka wani abu, dan yau sai na baka ladan qoqarin ka na daina shaye2, duk kuma randa ka min alqawarin daina neman mata ni kadai na san me zan maka a gidannan,"
Ta shi ta yi tana taku mai Jan hankalin da ita Kan ta se da ta yi mamakin yaushe ta Iya hakan? ya kwanta yana hango ta yanda take tafiya jikin ta na juyawa cikin salo, hankalin Ahmad in ya yi dubu to Atiyyaerh ta d'age shi, brush din ta ta d'auka ta saka toothpast, sai ta juya tana kallon shi, tace,
"Mijin Ablaerh na saka maka ne kaima ko na bari?"
Cikin zumudi yace,
"Saka min nima , ai dole nima na tsaftace nawa bakin kar naiwa kaina mugunta, bansan dad'in da za a ban a ciki ba,"
Dariyar samun nasara ta yi, suka je suka wanke baki, a zuciyar ta tana mamakin ina ta iya irin wadannan abubuwan?( niko nace Ablaerh ko wacce mace jaruma ce, mai ilimi ce, kuma mai fasaha ce, dan haka mace mai wayo da dabara ita zata iya sarrafa wadannan abubuwan, kowa Allah ya halicce ta da kissar ta a tare da ita, ya dangan ta da wacece ke kafin ki mori abinda Allah ya baki na baiwa, in ke cikakkiyar mace ce zaki amfana da sirrikan dake tattare dake, in mata kk rako to komai kina zaune ki na jiran sai an fada maki, sai kin ce baki iya ba a koya maki, bayan a take zaki iya maganin matsalar ki da kalaman ki, da jikin ki, sannan da kallon ki,) can na hango malama Atiyyaerh na kwance saman jikin Ahmad, Ahmad ya rude sai sambatu yake, ta gama susuta shi, qara maimaitawa yake,
"Daga yau na maki alqawarin bani ba shan ganye,bare sigari, har abada, Ablaerh ki dinga min irin wannan kullum,"
Hajar ce ta zo wucewa ta ji duk abinda ke faruwa, kad'a kai ta yi ta tafi, bayan sun gama.abinda suke ne, suka yi wanka a makewayin su, ta saka wasu kayan tace masa bari ta shiga ciki ta taya Inna aiki, dama tin dazun take son zuwa , suka zauna hira, cewa ya yi da shi za a, ta yi iya yin ta kar ya bita amma inaa ya qi, hakura ta yi suka shiga ciki tare, tankad'e ta tarar Inna nayi, ta yi sauri ta karb'a ta ja kujera ta miqa masa dan ya zauna, ita Kuma ta tsugunna ta ci gaba da tankad'en, Innace ta bata ta ta kujerar amma taqi karba, tankad'e take suna hira, sannan tana duba ruwan tuwon, dan yawanci abincin su baya wuce tuwo miyar kuka, se juma'a a dafa shinkafa ko taliya 'yar murji, Atiyyaerh ce ma data zo ta sa ake d'an canja miyar kala2,in yau an yi kuka gobe a Yi kubewa ko ayoyo, Hajar ce ta shiga sashen Inna Abun itama ta samu bakin qofar d'akin Innar ta zauna ta ce,
" Au nan ku ka shigo ashe, ai zuwana wajen ku wajen sau uku kenan ina komawa, gaba d'aya kun rikita mana gida da sambatu kamar Kan ku aka fara aure"
Wata uwar kunya ce ta kama Atiyyaerh kamar ta tsaga qasa ta shige, hannun ta kasa riqe rariyar ya yi, sai ta ji ta mata nauyi, kula da hakan ne ya bata ran gogan nata,cikin son baqantawa Hajar Shima ya ce,
" Eh muna can muna abinda muka yi aure domin shi, kin ganta nan na san ba sona take ba, amma bata rowa,kuma 'yar albarkar ba sai an siyo mata tsiren Talle mai nama ba kan a kusance ta, a bata so na take hakuri da babu na, duk da ita gidan ubale akwai, kuma a......"
" Dan Allah ka yi hakuri ka rabu da bata amsa irin haka, baka kula Inna ta tashi ta bar wajennan ba sabida kunyar maganganun ka? Ni kaina ka ja min kunya yanzu da wanne ido kk son na kalle ta?"
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 14 Chapter of 21