tun lokacin.
"What!" Ta ce cikin mamaki tana kallon alert ɗin.
"Miliyan ɗaya a ka turo mini! waye ya turo?" Ta yi tambayar cikin mamaki tana nuna wa Affrin wayarta da ta tsaya tana kallonta cikin mamakin abin da ya sanya ta razana.
"Waye shi Hilah?"
"Ban sani ba domin kamar ba da account ɗinsa aka tura ba ta banki ne."
"Ok, kuma babu tsaƙon da ya turo? Ki duba wataƙila ya tura miki baki gani ba."
Ba tare da musu ba ta shiga cikin inbox ɗinta jikinta na rawa.
Ganin saƙon ya ɗan sanyaya zuciyarta amma ganin an rubuta anonymous sai ta ɗan ji faɗuwar gaba.
"Ga message na gani sai dai da alamar wanda ya yi turo tsaƙon, ba ya son bayyana kansa domin anonymous ne." Ta ce tare da buɗe tsakon wanda ta fara karantawa sai dai ba ta ƙarasa ba ta tsaya cikin tsa
Labarin ya zo da wani irin salo da nishadi, karku baru a ba ku labari. Ku biyo ni domin it’s just like a little introduction part, and guess what? You will really enjoy it. Believe me, my dear readers. Your happiness is my concern. Follow me on Facebook, Whatsapp, Wattpad, Arewaboo, and Bakandamiya. Ta ku, Jamila Lawal Zango (Jamsy).
FOR WHATSAPP: 07072971093
CALL: 008144072423
*RANAR WANKA...*
NA
JAMILA LAWAL ZANGO
"JAMCY"
☀️ *First Class Writers Asso* ☀️
Hame of Qualities And Trusted writer's of The Nation
*GARGAGAƊI*
Ban yarda kuma ban amince a juya mini labari ko ta wace siga ba, sannan ban bada lamuni a ɗora mini littafi a kowane kafar sadarwa ba sai da izinina a kiyaye⚠️
JAN HANKALI
Kirkirarran labari ne ban yi shi don wani ba, idan har ya yi daidai da labarin ki/ka to arashi ne.
SADAUKARWA
Kwacakwan labarin daga farkonsa har karshe sadaukarwa ne ga ƙawata sahibata Aysha Na Lado. Allah saka miki da alkairi ya raya zuri'a.
PAGE 4
BISMILLAHIR RAHMANINR RAHIM
Ganin saƙon ya ɗan sanyaya zuciyarta, amma ganin an rubuta anonymous sai ta ɗan ji faɗuwar gaba.
"Ga message na gani, sai dai da alama wanda ya yi baya son bayyana kansa domin anonymous ne." Ta ce tare da buɗe tsakon, wanda ta fara karantawa sai dai ba ta ƙarasa ba ta tsaya cikin tsananin mamaki.
"Waye wannan mahaukacin masoyi da ya tura miki tsako haka?" Afrin ta tambaya cikin tsananin mamaki.
"Tabbas ya cika mahaukacin masoyi! Domin babu mai hankalin da zai bayyana soyayyarsa a ɓoye da alamar matsoraci ne." Ta ce cikin tsananin mamaki. Sai kuma ta ɗora da cewa kafin Afrin ta yi magana.
"Kin ga shi ma da kansa ya sawa sunansa mahaukaci masoyi." Ta kashe wayar tare da maida ta cikin jaka tana jinjina lamarin lokaci guda kanta ya kulle ta shiga cikin duniyar tunanin.
"Ni fa ina tunanin wani ne da yake can yana fama da sonki, amma ya kasa zuwa gareki kin san ke ɗin ba kowane namiji, zai iya tunkarar ki da maganar so ba; saboda baiwarki da da ilminki uwa uba kyau tamkar ke kika yi kanki."
Shiru ta yi ba tare da kalamanta sun yi tasiri a ranta ba, domin hasashenta ne wannan. Besides, dukanninsu mutane ne kuma babu wanda ya fi wani a gurin Allah sai wanda yafi tsoron shi, don haka ba ta ganin wannan a matsayin hujja da zai sanya ya kasa bayyana kansa gareta.
"Wannan ba hujja bace, amma ko ma mene kyautar kuɗi da ya yi haka dole ya bayyana kansa, bari na je gida na sanar wa Ya Huwais, na san shine kawai zai bani shawara da mafita." Sai ta miƙe tana saɓa jakarta tare da cigaba da cewa,
"To amma ta ya ya akai ya samu account ɗina? Tunani nake ya san ni duk wanda ya turo wannan tsaƙon."
"Eh, ai ba abin mamaki bane saboda kamar yadda duniya ta sanki haka account ɗinki. Mutane nawa suke turo miki da kyauta su ce sun karɓa a musabaƙa da kika cinye."
"Haka ne." Ta ba ta masa sai suka fara tafiya tana cewa,
"Bari na wuce da wuya na dawo tun da surmiting assigment za mu yi, in ban dawo ba ga shi kawai ki ba da." Sai kuma ta canza shawara ta ce,
"Kai bari ma zan dawo kawai."
"Ok." Ta masa tare da miƙa mata assignment ɗin, wanda ta karɓa ta mayar cikin jakarta tare da ciro makullin motarta ganin sun iso gurin.
Da ta isa gida sai ta yi farking a ƙofar gida ta shiga cikin gidan wanda cikin sa'a Ummu na bacci.
Kai tsaye ɗakinsa ta nufa da yake kwance wayarsa a hannunsa ya rungume yayin da ya tafi duniyar begenta.
Ƙamshin turarenta ya dawo da shi da duniyar da ya lula.
Da sauri ya jawo laptop ɗinsa ya zauna ya buɗe tare buɗewa ya fara daddanawa fuskarsa a ɗan ɗaure.
Kallonta ya yi da ta yi sallama tare da ƙarasawa inda yake ta zauna.
"Lafiya sis, ba kin ce sai 4 pm za ki dawo ba?" Ya yi mata tambayar cikin tsannin mamaki duk da ya san dole ta dawo saboda shawarar shi kawai take nema, don baya manta ko a lokacin da ta fara menstration ɗin shi ta fara nuna wa mawa.
"Haka ne Ya Huwais, amma ba zan iya zama har lokacin ba domin tsakon da aka tura mini." Sai ta ciro wayarta ta nuna masa tsakon ta ɗora da cewa,
"Abin da yafi bani mamaki shine har da kuɗi ya tura mini miliyan ɗaya."
Zare idanunsa ya yi cikin tsananin mamaki tamkar bai san abin da ke faruwa.
"Miliyan ɗaya! Waye shi kuma mai yake so daga gare shi, ko kin san shi kike ɓoye mini?" Ya yi mata tambayar cilkin ɗan ɗaga murya har lokacin idanunsa a xare.
Rau-rau ta yi da idanunta lokaci guda hawaye suka fara sintiri kan kyakykyawar fuskarta.
"Kaicona! Sai na yi tur da ni in har zan fara ɓoye maka sirrina." Ta faɗa tana kallonsa.
"To mene ne abin kuka?" Ya ce tare da jawo tissue yana ɗauke mata hawayen
Hannunsa ta kama ta riƙe gam wanda sai da ya ji ɗumin jikinta, har cikin bargon jikinsa, ya rintse idanunsa yana jin yadda yake jin ɗumin na ratsa ko ina na jikin shi yana saukar masa da natsuwa, wanda ya sanya shi zare hannun da sauri yana istigifari da ta'awizi kan Allah ya kawo masa ɗauki tunkafin sheɗanin da ke ƙoƙarin galaba a jikinsa ya yi.
Ba tare da ta fahimci halin da ya shiga ba ta ƙara kama hannun a karo na biyu ta riƙe sosai.
"Ya kafahimce ni wallahi bani da masaniya kan lamarin nan."
"Ok." Ya ce cikin basarwa ya cigaba da aikin shi yana tunanin mai zai ce mata.
Ganin shirun da ya yi ya sa ta fara magana da cewa,
"Ko ma waye wannna tabbas ya cika mahaukacin masoyi, domin ina ya taɓa ganin an yi soyayya a ɓoye? Wataƙila kuma mahaukaciyar zuciyarsa ta gaya masa zai iya siyen soyayyata da kuɗi ne, ba tare da ya san bani cikin makwaɗaitan matan da suke sayar da rayuwarsu saboda kuɗi ba. Namiji mai ilmin addini da boko nake nema, wanda zai amfani da ilminsa duka a cikin rayuwar aurenmu. Kuma ai ina da wanda zai aura don haka ya kama kansa."
Wani kallo ya juyo ya watsa mata, take zuciyarsa ta fara zafi na kishinta, sai kuma ya juya zai ci gaba da aikin wanda ya sanya ta kama hannunsa.
"Yaya, ka yi shiru ba ka ce komai ba."
"Me kike so na ce domin na ga lokacin da Hammad ya ce yana sonki ba ki gaya mini ba." Ya jefo mata maganar cikin bazata.
"Bani da zaɓi ne, bisa umurnin Ummu da ta ce kar na sake na gaya maka, ganin yadda kake tada hankalinka kake nuna kai xaka saɓa mini miji da kanka. Cewarta shi na gida ne, kuma ya cika criteria da kake son mijin da zan aura ya cika." Ta ba shi masa.
Shiru ya yi dama ya san tursasawar Ummi ne har ta fara kula wani ba ta gaya masa ba.
Karɓar wayar ya yi daga hannunta ya ɗan tsaya yana karanta tsaƙon tare da dogon nazari game da abin da zai ce mata.
Bayan ya gama nazarin sai ya ije wayar saman cinyarsa yana ƙare mata kallo ganin yadda ta wani firgice.
Tattara dukkan hankalinsa ya yi gareta ya ce,"Wa ki ka gaya ma wa?"
"Babu kowa sai Afrin ƙawata, bayan ita babu wanda ya sani."
"Good! To kiyi shiru karki gaya wa kowa har muka mai zai yi nan gaba. Ki bar wannna kuɗin a account ɗinki."
"No Yaya, sai dai na yi maka transfer ba zan iya ije maƙudan kuɗi haka ba." Ta ba shi amsa cikin sauri.
"Ki barshi dai gurin ki kafin na gama tunani sai na san yadda za mu yi da kuɗi."
"Tom, amma kana tunanin ɓoyewar ba zai kawo matsala tsakaninmu da iyayena ba? Musamman Ummu don Abu ba zan samu sausauci ba."
"Duk da hakan mu jira muga abin da zai yi kafin mu sanar musu ba. Sannan ki kwantar da hankalinki kar ya taɓa karatunki kin ji sis? Kin san kina da musabaƙa. Kwana uku ne ko?" Ya ce mata cikin tsigar rarrashi.
"A,a biyar ne sun tura mana tsaƙo sun ƙara kwana biyu."
"Masha Allah! Kin ga kin samu ƙarin kwana biyu za ki yi karatu sosai."
"Na ma gama kawai dai ƙarin kwanar zai bani lokacin na ƙara bita."
"Yauwa ma za tashi ki tafi makaranta ko na kai ki?"
"Karka damu zan koma da kaina." Ta ce tare da miƙewa.
Murmushi ta yi tana kallonsa wanda shima ya miƙe yana miƙa mata wayarta.
"Mahaukacin masoyi!" Ta ce tare da jan tsaki da ƙarfi.
"Mutumin nan ya raina mini wayo sosai Ya Huwais. Ga shi gabakiɗaya ya ɓata mini mood ɗina zai sanya na raba tunani gida biyu."
"No kar mu yi haka dake, ki kauda lamarin kin san dole sai kin ciyo mana tropy ɗin nan." Ya faɗa yayin da yake jin babu daɗin kalaman da ta furta amma sai ya daure bai nuna koma ba ya ce.
Ajiya zuciya ta saki mai ƙarfi tana ƙoƙarin comforting ɗin kanta domin gabakiɗaya ta ruɗe.
"In sha Allahu, bari na tafi na yi wanka na koma school."
"To shikenan, 'yar ƙanwata."
Fita ta yi wanda tana yin nisa ya durƙushe a gurin yana jin yadda zuciyarsa ke masa zafi. Ji ya yi idanunsa sun cika da ƙwallah shi kan ya san yana cikin jarrawa, domin ya sanya a ransa ita ce jarrabawarsa.
"Tabbas na cika mahaukacin masoyi! Domin soyayyarki gab yake da fallasuwa cikin raina, wanda zai sanya mutane sun tabbatar da na haukace game da sonki, amma kuma a shirye nake da na amshi duk wani ƙalubalen da zan fuskanta, domin ba zan yi sakaci ba ina ji ina gani wani ya aure ki. Kece farincikina kuma zuciyata."
Kamar yadda ya gaya mata kar ta sanar da kowa. Ba ta gaya wa kowa ba, amma wunin ranar ta yi shi suku-suku, domin ta kasa samun natsuwa. Burinta kawai ta san wanda ya tura mata tsakon, amma iya hatsashenta ta yi ta yi hakarta ba ta cima ruwa ba. Don haka ta ga ji ta haƙura da tunanin sakamakon wani irin ciwo da kanta yake yi.
Wuni ta yi tana duba tsaƙon da ta ji muryar Ummu ko 'yan uwanta sai ta yi maza ta kife wayar.
Da ta zo bacci kasa bacci ta yi ta rinƙa juye-juye a kan makeken gadon da ke barazanar cinye ɗakin, wanda da ƙyar da siɗin goshi baccin ya yi nasarar ɗaukarta wanda sai da ta riƙe carbi tana ta Sayyidil istigafari.
Ya rage gasar su saura kwana biyu, ta yi ƙoƙarin watsar da komai ganin tunanin na son zubar da haddar da ta yi. Ga shi ta burin amso wa Ƙasarta tropy da zai zamo abin alfahari ga al'ummar Musulmai.
A ranar da ta kasance ranar tafiyarsu suka shirya da misalin ƙarfe goma suka ɗauki hanya.
Hilah tana tsaye a gurin da za su fara musabaƙar.
Idanunta ta runtse tana yin addu'a samun nasara.
Da ta tuna irin yadda iyayenta da yan'uwanta suka ƙarfafa mata guiwa, sai ta ji wani irin ƙwarin gwuiwa ya zo mata.
Wayarta ce ta yi ƙara wanda ta duba da sauri.
Ganin numbar anonymous ya sanya ta ƙi dubawa, domin ganin tsaƙon na neman rikita tunaninta da matsuwarta. Sai dai, duk iya ƙoƙarinta na kar ta duba sai ta tsinci kanta da son duba tsaƙon, wanda har ta kasa jurewa ta buɗe cikin ƙarfin hali.
"Ina miki fatan alkhairi ma'abociyar ilmi da baiwa. I know that you gonna rock it. Eh tabbas za ki ci. Ina kallon ki domin ina daga cikin mutanen da suka zo, domin sauraron daddaɗar muryarki da fatan ki cinye wannan gasar. Jikina yana bani za ki ci, domin ba bu faɗuwa a rayuwarki. gani a cikin dubban mutane ina murmushi zuciyata cike da miki fatan nasara."
Da sauri ta shiga duba mutanen dake gurin jin gaya mata yana wurin
"Wane ne wannan! Wane ne wannan yake son wasa da hankalina?" Ta furta tana waige-waige.
Iya hangenta ba ta kowa ba sai Ya Huwais da yake sakin mata murmushi tare da ƙarfafa mata gwiwa da idanunsa.
Da ta kalli sauran 'yan'uwanta sai ta ga kusan irin murmushi da yake kan fuskarsa iri ɗaya ne, musamman Abu da ta ga ya duƙufa yana ta kwaroro addu'a.
Ta shiga ruɗani sosai tana ta tunanin sa. Zuciyarsa ta kwaɗaitu da ta gan shi. Haka kawai ta ji tana son ganin ko wane ne, amma iya tunaninta da son ganinsa ba ta gan shi. Da ta tuna dubban mutanen da suke gurin sai ta daina wahalar da kanta, domin ta san ya faɗa mata ne don kawai ya wahalar da ita, ko ya sa ta faɗi. Sai ta saka wa kanta anya mahaukacin masoyi sonta yake? Ko an yi amfani da shi ne don ta faɗi gasar. Ganin yadda ta rikice lokaci guda!
A lokacin da ka aka kira ta sai ta ji ta rasa natsuwarta da karatun da ta yi bakiɗaya.
Wani irin tashin hankali ya ziyarce ta har ya sa ta dafe ƙirjinta tana jin gadda yake bugawa cikin rashin ƙa'ida.
Da ta tsaya a gurin ta buɗe baki da nufin ta fara karatun sai ta ji ta kasa. Idanunta suka cika fal da hawaye. Tana jin yadda komai yake neman fin ƙarfinta.
Huwais da yake kallonta cikin tsananin ƙauna da bege. A lokacin da ya tura mata tsaƙon, ta buɗe tana karantawa sai ya ji tamkar ya isa gareta ya kamata ya rungume ya ƙarfafa mata gwuiwa.
Ganin ta tsaya tana duba tsaƙon ya sashi ɗan sakin murmushi yana kallonta. Burinsa bai wuce ace ta zamo ta ɗaya ba. Tabbas hakan zai ƙara masa sonta da begenta, kuma hakan abin alfahari ne ga zuriyarsu baki ɗaya.
Ya fara shiga cikin tashin hankali lokacin da ya ga tana ta wilƙita idanunta wanda ya tabbatar da gaya mata cewar yana gurin ne ya sa take duba shi.
Hankalinsa bai ƙara tashi ba sai da ya ga layi na gab da zuwa kanta amma har lokacin nemansa take yi.
Wani irin juya ya ji yana kama shi a zaunen har ya ji kanshi ya sara. Miyau bakinsa na neman ƙafewa.
"Mai ya sa ta damu da ta ganshi, kuma mai ya sa na tura mata da tsaƙon?" Ya tambayi kansa cikin tsananin mamakin yadda ta rikice har yana jin in har ba ta ci gara ba ba zai yafe wa kansa ba.
A lokacin da ta tsaya za ta yi karatun sai ya ga ta kasa idanunta cike da ƙwallah. Miƙewa ya yi cikin dana-sani zai fita daga gurin, domin yana ji ba zai iya ganin ta kasa cin gasar ba. Rintse idanunsa ya yi ya tsaya jin ta fara karatun cikin rawar murya.
Tsaya wa ya yi tare da kafe ta da idanu wanda cikin ikon Allah sai ta kalle shi.
Da hannu ya yi mata maganar kurame na ƙarfafa gwiya.
Ga mamakinsa sai ya ji muryata ta dake ta fara karatun wanda tun da ta fara ba ta tsaya ba sai da ta dire.
Gurin ya yi sit! Ba ka jin komai sai ƙarar A.C da numfashin mutane. Har ta ƙare karatun cikin murya mai tsananin daɗi.
Huwais da ya koma ya zauna, hankalinsa ya kwanta ya lumshe idanunsa, yana jin yadda take zubo karatun cikin murya mai daɗi, da fitar da tajweed tsantsa. Duk inda aka yanko mata sai ta ɗauka tana karantawa cikin gwanancewa. Ya tabbatar wa kansa a karo na biyu in har ya bari ta kubce masa a matsayin matarsa ya yi asarar da bai zai taɓa mayar da ita ba. To amma ta yaya? Don shi dai ko a garin gaɓa-gaɓa bai taɓa ganin Ya ya auri ƙanwa ba. To amma ya akai zuciyarsa da tunaninsa suke ƙarfafa masa watarana za ta zamo matarsa kuma uwar 'yayansa domin perspective ɗinsa kullum kuma mafarkinsa.
Kabbarar mutanen gurin ya dawo da shi daga tunanin da yake yi wanda shi ma ya ɗauki nasa kabbarar.
Kuka sosai take yi tana ganin yadda mutane suka ƙoƙarin ɗaukar ta hoto.
Labarin ya zo da wani irin salo da nishadi, karku baru a ba ku labari. Ku biyo ni domin it’s just like a little introduction part, and guess what? You will really enjoy it. Believe me, my dear readers. Your happiness is my concern. Follow me on Facebook, Whatsapp, Wattpad, Arewaboo, and Bakandamiya. Ta ku, Jamila Lawal Zango (Jamsy).
FOR WHATSAPP: 07072971093
CALL: 008144072423
*RANAR WANKA...*
NA
JAMILA LAWAL ZANGO
"JAMCY"
☀️ *First Class Writers Asso* ☀️
Hame of Qualities And Trusted writer's of The Nation
*GARGAGAƊI*
Ban yarda kuma ban amince a juya mini labari ko ta wace siga ba, sannan ban bada lamuni a ɗora mini littafi a kowane kafar sadarwa ba sai da izinina a kiyaye⚠️
JAN HANKALI
Kirkirarran labari ne ban yi shi don wani ba, idan har ya yi daidai da labarin ki/ka to arashi ne.
SADAUKARWA
Kwacakwan labarin daga farkonsa har karshe sadaukarwa ne ga ƙawata sahibata Aysha Na Lado. Allah saka miki da alkairi ya raya zuri'a.
PAGE 5
BISMILLAHIR RAHMANINR RAHIM
Kabbarar mutanen gurin ya dawo da shi daga tunanin da yake yi wanda shi ma ya ɗauki nasa kabbarar.
Kuka sosai take yi tana ganin yadda mutane suka dabaibayeta suna son ɗaukar hoto da ita. Tun daga kan larabawa da jajayen fata.
Da ƙyar iyayenta suka samu damar ɗaukar hoto da ita, wanda ana gamawa ta ja Huwais gefe.
"Ya ya sanar da ni yana nan tabbas kuma naji a jikina yana nan, wasa da hankalina yake yi! Anya masoyi ne ko maƙiyi? Domin ba zai tura mini tsaƙon da ya rikita ni a daidai lokacin da zan fara musabaƙar ba." Ta ce tare da kama hannunshi tana kuka.
Jikinsa ya yi sanyi sosai duk da ya san cewa bai kyauta ba, amma sai ya ji kalamanta tamkar dafi na maciji, musamman da kunnuwansa suka ƙara ji masa lokacin da take cewa.
"Na tsane shi bana sonsa! Idan ya yi hakan ne don ya samu soyayyata, haƙiƙa ya yaudari kansa, domin a halin yanzu ba ni da maƙiyi sama da shi, kuma wallahi da ya sanya na faɗi a gasar nan, burina ya tashi a tutan ma'aho da bazan taɓa yafe masa ba, kamar yadda ba zan yafe ma kaina ba, domin lokacin da na fara shiga gasa na sawa burin karɓo wa Ƙasata kabbu!"
"Bai kyauta ba shima ya yi kuskure! Tabbas ya zama cikkaken mahaukacin da baya iya gane komai sai cimma soyayarsa." Ya ce mata domin shi ma ya ga wautarsa.
"Yana nan gurin ta ya ya zan iya gane sa na kikkifa masa mari ko zuciyata za ta yi sanyi." Ta ce tana kallon sa sai kuma ta fara dube-dube.
"Ba za ki iya ganinsa ba duba ga dubban mutanen da suke gurin nan."
"Zan iya Yaya, na yarda mahaukaci ne don haka dole ya fita daga siffar masu hankali." Ta ce cikin ɗan ɗaga murya.
"Anya hanyar da na ɗauko mai ɓullewa ne, domin na gane a maimakon ta soni sai dai na ta tsane ni, tunkafin ta san ko ni wane ne." Ya ce tare da rintse idanunsa.
Ba tare da ya hana ta ba ya koma kujerarsa ya zauna, yana ganinta tana dube-dube, amma bai ce mata komai ba, domin haushin maganarta sun sanya shi jin haushinta.
Ganin ta ɗauki tsawon lokaci tana dube-dube ya sanya shi miƙewa. Cikin rashin ƙarfin jiki ya isa gareta, tare da kama hannunta zuwa mota.
Faɗawa ƙirshijin shi ta yi tare da sakin kuka mai ƙargi ta ce,"I hate him."
Ji ya yi tamkar ta coka masa mashi a zuciyarsa har sai da ya rintse idanunsa, jin abin da ta furta.
Bayanta ya shiga shafawa domin ya kasa janyeta daga jikinsa har tsawon lokaci. Suna a haka ya ga Ummu ta nufo motar da sauri wa da ya sanya shi zare ta daga jikinsa ya nuna mata Ummu.
Da sauri ta fita daga motar tana zare idanunta. Ummu na isowa ta aika mata da mugun kallo cikin ɓacin rai ta juya ba tare da ta ce mata komai ba.
Ganin ta yi tsaye ta kasa bin bayanta ya sanya shi fitowa daga cikin motar. Hannunta ya kama suka fara tafiya zuwa gurin mutane.
Cikin nasara ta samu nasarar lashe gasar domin ta zamo zakaran gwajin dafi a tsakanin rawuna. Ta samu kyautittika da dama ita kanta ba za ta manta da wannan ranar ba, domin rana ce na musamman gareta. A ranar da ta kasance zinariya ga mutane ta amso wa ƙasarta kimarta da darajarta. Iyaye da dama sun mafarkin ace ita 'yarsu ce, wanda har da waɗanda suka tako suka nuna hakan.
Bayan sun dawo sun yi hutun gajiya. Suna zaune a falo suna cin abincin da aka shirya mata.
Gabakiɗaya abincin oder ɗin shi aka yi.
Hira suke cikin nishaɗi da fara'a wanda rabin hirar duk kan gasar da ta ciyo ne. Ummu ne kawai ba ta cika soma baki ba sai dai ta yi murmushi, amma fuskarta cike take da farinciki matuƙa.
Hamsiya mai aiki ce ta yi sallama ta shigo tare da duƙawa cikin girmamawa ta ce,
"Inusa, direba ya ce na kawo wannnan wani ne ya turo tsaƙon a bawa Hilah har da mota a waje."
Gabkiɗaya suka kalleta cikin tsananin mamaki.
Hilah kuwa Huwais ta kalla, yayin da idanunta suka firfito saboda ta zargi tsaƙon daga mahaukacin masoyi ne.
Amma sai ta ga ko a jikin shi domin ba ita yake kallo ba, wayarsa ya maida hankali kanta yana dandannawa.
A daidai lokacin tsaƙo ya shigo cikin wayarta, wanda har sai da ta miƙe a zabure ta kasa kallon wayar, ballanatana ta ga wanda ya turo mata.
Sai da ta ɗan ɗauki sakanni sannan ta duba. Hasashenta ya zama gaskiya domin shi ne. Mahaukacin masoyi ne ya ƙara turo mata tsaƙo kamar haka:
"Amincin Allah ya tabbata ga wannan abociyar haske! Na san na yi miki laifi, don Allah ki yafe mini ga tsaƙo nan. Ina miki murnan lashe gasar da kika yi." Tsanananin tashin hankali ya bayyana a fuskarta.
"Waye shi wanda ya kawo tsaƙon irin wanna tsadaddiyar wayar da mota ya siya mata haka? Kai Huwais, ma za ka je ka gani." Ummu ta furta fuskarta bayyane da mamaki.
"No, bari na je tun da ina nan." Abu ya ce tare da dakatar da shi da ya miƙe fuskarsa babu yabo ba fallasa sai ya koma ya zauna yayin da Ummu ta bi shi da kallo.
"Inusa, ina wanda ya kawo
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 3 Chapter of 17