sannan ban bada lamuni a ɗora mini littafi a kowane kafar sadarwa ba sai da izinina a kiyaye⚠️
JAN HANKALI
Kirkirarran labari ne ban yi shi don wani ba, idan har ya yi daidai da labarin ki/ka to arashi ne.
SADAUKARWA
Kacokam labarin daga farkonsa har karshe sadaukarwa ne ga ƙawata sahibata Aysha Na Lado. Allah saka miki da alkairi ya raya zuri'a.
PAGE 16
BISMILLAHIR RAHMANINR RAHIM
"Mai ya sa zai guje ni bayan ya yi mini alƙawarin kasancewa a tare da shi? Shi kenan ya guje ni na rasa shi har abada?" Ya zan yi da soyayyarsa da ta shige mini zuciyata. Wayyo Allah ka dawo mini da shi a cikin rayuwata, domin shi ne irin mijin da nake masifar so." Haka ta rinƙa addu'a har ta fara jin sauki a cikin zuciyarta.
A maimakon ya kai ta gida, sai ta ga ya ɗauke hanya. Gurin shaƙatawa ya kai ta mai kyau, ya kashe motar ya fito tare da zagayowa inda take.
Hannu ya miƙa mata bayan ya buɗe motar.
"Ya Huwais, mai za mu yi nan, kar ka manta yau ne fa auren ka? Mutane na can na jiranka."
"Karki damu, farincikin ƙanwata kawai na ke so." Ya ce mata tare da kama hannunta da ta miƙa masa.
Cikin gurin suka isa, wanda wurin ya yi kyau matuƙar haduwa iya gaya! Hilah ta sha zuwa gurin, domin yana ɗaya daga cikin guraren shaƙatawa da take so, kuma ya ke yawan kawo su.
Siyayya ya fara yi mata har sai da ta riƙe masa hannu.
"Don Allah ka bar kashe kuɗinka Yayana, hidima ce a kanka. Ko ka manta yanzu kai mai iyali? Ba zan so Anty Wajnah ta sha wahala a gidan ɗan'uwana ba." Ta faɗa cikin sanyin murya tare da riƙe hannunsa.
Harararta ya yi, sai kuma ya ƙwace hannun ya ɗauki ƙaton biskit, wanda yasha cakulate ya saka a kwandon.
"Kar ki damu farincikin ƙanwata kawai na ke so. Sam ban damu da kuɗina su ƙare ba, matuƙar hakan zai sanya ki farinciki."
Murmushi ta yi tare da jan hannunsa suka fara tafiya.
"Haƙiƙa ka zamo ɗan'uwa mai kau da damuwar ƙanwansa. Fatana na samu miji mai irin kyawawan halinka da nagarta, wanda hakan yana da nasa ba da fara soyayyata da mahaukacin masoyi, saboda yana da kyawawaan ɗabi'u irin naka."
Ba tare da ya ce mata komai ba, ya fara tafiya, saboda in har bai bar gurin ba, zuciyarsa za ta iya fallasa abin da ke cikin zuciyarsa, saboda yabansa da ta yi.
Ganin haka ta fara tafiya da sauri har ta kamo shi.
Daga gurin da ake sayar da kayan maƙulashe gurin shaƙatawa ya kai ta.
Tana son ta yi masa maganar su koma gida, amma in ta buɗe bakinta sai ya tsareta da idanunsa, masu kama da an zuba zaiba sai ta kasa cewa komai.
Ganin an ɗauki lokaci suna gurin, kuma ga Najib sai kiran sa a waya yake yi, wanda daga ƙarshe ya kashe wayar ya yi gabakiɗaya.
Wayar Hilah ce ta yi ƙara alamun ana kira. Da sauri ta duba mai kiran. Kamar yadda ta ayyana Ummu ce. Ilai kuwa ita ce.
Da sauri ta kanga wayar a kunnenta."Kina ina tun rana ban ganki ba, kacaniyar biki ya ɗauke mini hankali, ban lura ba ki cikin gidan ba, sai yanzu da na zo ɗakinki?"
"Na raka ƙawayena ne Ummu." Ta shirga mata ƙaryar hakan, tana kallonsa da hankalinsa ya ɗauku gurin tuƙi kuma yana sauraren mai za ta ce.
"Ok, to ki yi sauri ki zo ina nemanki."
"To Ummu." Ta faɗa tare da ije wayar.
Waiwawo ta ya yi yana kallonta, daidai lokacin da take share sauran hawayen da yake maƙale a fuskarta.
"Ya kamata ki wanke fuskarki in da hali ki yi make up kar Ummu ta gane halin da ki ke ciki."
Babu musu ta buɗe jakarta, ta ɗauko kayan kwalliyar wanda ganin haka ya yi parkin tare da kashe motar.
Fita ta yi zuwa waje ta wanke fuskarta ta fito
A ƙofar gida ya ije motarsa ta shiga ciki shi kuma ya yi bangarensa.
Najib da yake zaune cikin tsananin ɓacin rai, da waya a hannunsa. Layinsa yake ta gwadawa amma a kashe.
"Ba ka da hankali ko Huwais? Shin ka san abin da ka aikata yau kuwa? Wannan wulaƙancin da ka yi mana, ko ni kaɗai ka yi wa da na san halin da kake ciki ba zan ji daɗi ba." Najib ke magana cikin tsananin ɓacin rai yana kallonsa da ya buɗe ƙofa ya shigo.
Shiru ya yi masa, ba tare da ya ce komai ba, ya ƙarasa kan kujera ya zauna jaɓar tare da sakin ajiyar zuciya ya dafe kansa.
"Ina magana ka yi shiru? Wallahi ji na ke kamar na rufe ka da duka, saboda takaicin abin da ka aikata. Just see the time, this isn't good."
Jajayen idanunsa ya watsa masa, tare da miƙewa bai ce masa komai ba zai wuce.
"Sam bana jin daɗin abin da kake mini da halin da ka sanya kanka. Ya kamata ka farka da ga mafarkin da kake yi. Toxarcin da kake yi wa yarinyar nan ya isa haka. Ta bani tausayi da ta kira ni tana kuka. Don Allah ka tausaya mata ka amshe ta a matsayin mata, domin aurenku an riga an ɗaura yanzu tana da haƙƙi mai girma a kanka."
'"Please, I need my space." Ya ce tare da yin hanyar ɗakinsa yana tangaɗi kamar wanda ya sha giya.
Najib takaici da ya ibe shi gabansa ya sha.
"I will inform Ummu, Huwais. Bana son ka kai ni iya wuya, domin zan sanar mata da duk abin da ke faruwa. Haka kawai ka sanya wa kanka damuwa da Hilah, don Allah kaɗai ya san halin da take ciki.".
"Then go ahead." Ya ba shi amsa tare da kaucewa, zai shige ɗakin duk da cewa ya ji tsoron abin da ya faɗi.
Tsaki ya yi, tare da kaucewa ya ba shi hanya ya shige ɗakin ya rufo ƙofar garam
Sharaf! Ya faɗa gado yana mai da numfashi, yayin da cikin zuciyarsa Allah kawai ya san halin da yake ciki.
"Ya kamata ka miƙe ka shirya ka san dinner ɗin nan ya kamata a fara da wuri."
Tsaki ya yi tare da janyo wayarsa yana kiran numbar Hilah ba tare da ya tanka masa ba.
"Hello, ƙanwata." Ya furta cikin sanyin murya.
"Na'am Yayana," Ta bashi amsa tare da saukar da zafafen hawaye a ƙuncinta.
"Har yanzu kuka kike yi ko?" Ya yi mata tambayar kamar yana ganin hawayen.
"A'a, kawai ina jin zuciyata kamar za ta fashe in har na tuna da cutar da zuciyata da ya yi."
"Ba na yi miki alƙawarin nemo miki shi ba, ko kina tunanin ba zan iya share miki hawayenki ba?"
"Ina jin babu daɗi ne, amma na san kai Yaya ne da ya cike ko wane gurbi."
"To shikenan, ki daina kuka ki ci abinci ki kwanta."
"To, amma sai dai bana jin zan iya cin komai. Yaya Huwais, yau rana ce mafi daraja. Ranar da kake yin aure ya kamata ace na fi kowa farinciki, amma sai na tsinci kaina akasin haka. Ina maka murnan samun abokiyar rayuwa, Allah ya ba ku...."
"Ina fatan Ummu, ba ta yi miki faɗa ba?" Ya katse ta yana faɗin haka don ba ya son maganar.
"Eh, saboda yau tana cikin farinciki matuƙa, saboda kallonta ka yi kawai za ka tabbatar da hakan."
"To ki ci abinci kisha magani ki kwanta, ko na zo na baki? Na san ba kya son magani."
Dariya ta yi." Kai haba! Gidan a cike yake Yaya, zan sha da kaina."
"Ok, to ki kular mini da kanki. Ni ma wanka zan yi na samu na kwanta."
"Yaya, dinner ɗin fa..."
Katse wayar ya yi jin tambayar da za ta yi masa.
"Wallahi inda uban kuturu ya yi kaɗan kenan." Cewar Najib cikin tsananin ɓacin rai.
"Tun da aka fara shirye-shiryen bikin ka ban huta ba Huwais! Wannan ko ni zan ƙara aure iyakan wahalar da zan yi kenan. In ba ka tausaya mini ba, ka tausaya wa matata da ke fama da laulayi. Ƴan matan amaryar kamar za su yaga ni, suna tambayata inda na ɓoye ango. Yanzu kuma sai ka ce ba za ka je dinner ba?"
Jin ya yi shiru yana kallon wayarsa wanda ya tabbatar hoton Hilah yake kallo, ya sanya shi fara duba contacts a wayarsa yana ƙoƙarin nemo numbar Ummu.
"Ba zan ɗora wa kaina wahala ba. Kai da aure ni da shiga damuwa. Ummu zan kira na sanar mata da wulaƙancin da kake yi a wataƙila ta sanya ka kaje."
"Bana son wulaƙanci Ummun za ka kaiwa ƙarata?"
"To ya kake son na yi Huwais? Kai ma ka san iya rufa maka asiri ai na yi."
"Bana jin zan iya halatar dinner ɗin. Xuciyata xafi take yi na yaudararta da na yi. Halin da ta shiga yau na ji babu daɗi da tsanar kaina."
"I warned you! Na gargaɗe ka several times, amma ka ƙi saurare. Don haka yanzu kai za ka ji da lamarin ai dama duk tsuntsun da ya ja ruwa, shi ruwa kan duka. "
"Bari na yi wanka na shirya na je, amma duk abin da ya faru ka yi kuka da kanka." Ya ƙarashe maganar tare da shigewa bayi.
Najib ajiyar zuciya ya saki mai ƙarfi, domin ya ƙosa a kammala bikin ya huta da kiran Wajnah.
Bayan ya fito ya shirya cikin shadda mai kyau. Kayan sun amshi jikinsa sai ƙyalli yake yi..
Wayarsa da ke kan dressing mirrow ya ɗauka. Numbarta ya kira tare da kanka wayar a kunnensa.
"Yayana, kuma angon Anty Wajnah." Ta furta da dariyarta ƙasa-ƙasa wanda ya san ta yi ne don ya ɗauka babu abin da le damunta.
"Kina ina?" Ya yi mata tambayar yana sanya handsfree a wayar ya ije ta kan gado yana ɗaura agogo.
"Ina harabar gida ni da su Umnah da Yaya Naufal za mu tafi."
"Ki jira ni yanzu zan fito mu tafi a motata."
Jin abin da ya ce ya sanya ta zare ido da sauri.
"Ka rufa mini asiri! Ango kake yau. Kamata ya yi ka je ka ɗauki Anty Wajnah ba ni ba."
"Na damu da halin da kike ciki ne kina buƙatar na..."
"Am ok Yaya, karka damu ka je ka ɗauko ta, kuma in har Ummu ta ji a motarka na tafi za ta yi..."
"Kin..."
"Please Ya Huwais, I insist!" Ta furta cikin muryar shagwaɓa.
"Kashe wayar ya yi da jan tsuka mai ƙarfi.
"Ƙanwarka ta fi ka hankali da sanin abin da ya kamata, ko da yake kai kasan kana cikin haukar soyayya shi ya sa." Najib ya ce tare da ɗaukar wayarsa ya yi masa tsaye aka don ya miƙe su tafi.
Bisa dole ya miƙe suka tafi. A motar Najib ne suka tafi.
Tsananin ɓacin rai ya ninku kan kyakykywar fuskarsa.
"Na gaya maka ba zan je a ɗauko ta da ni ba, amma shi ne za ka kawo ni gidansu?"
"Don Allah karka kunyata yarinyar nan a gaban ƙawayenta." Najib ya ce ba tare da ya amsa tambayarsa ba.
Ƙara tsuke fuskarsa ya yi yana danne-danne a wayarsa, ganin ta fito ita da ƙawayenta.
"Amarya ba kya laifi." Cewar Najib bayan ya fito ya buɗe mata bayan mota.
Murmushin yaƙe ta yi, yayin da burinta ta yi tozali da angonta wanda tun da aka fara hidimar bikin ba ta ga ƙewarshi ba.
Wani wawan ajiyar zuciya ta saki, lokacin da ta hango shi a hakimce yana danna wayarsa tamkar basarake.
"Ni ban san wane irin mutum bane angon nan, sai rowarshi ake magana. Bari dai na ganshi sai na gane ko kina ɓoye shi ne don kar ayi miki ƙwace."
Ƙawarta Hindatu ta furta tare da duƙawa cikin motar.
Da sauri ta ɗago kanta, don ya firgitata musamman yadda ya haɗe girar sama da ƙasa babu fara'a.
"Wai wannan miji na ki ai dole ki yi rowarshi.Kyawu kamar shi ya yi kansa." Ta ce tana mamakin inda ta samo shi duk da ita ma Wajnah ba baya ba, domin har ta fishi hasken fata. Sai dai na shi zallar kalar fatar ce, ita kuma tana haɗawa da shafe-shafe.
A hankali ta shiga cikin motar, tamkar ba ta son ta shiga. Kallonsa ta ƙara yi tana jin kamar ta ji ta a ƙirjin shi yadda ya yi kyau.
Wani irin wawan ajiyar zuciya ta furta ganinsa domin Allah ya jarabce ta da ƙaunarsa.
Najib ya rufe motar yana faɗin,"Ku shiga ga motoci nan birjik sai mun haɗu a gurin dinner."
"No, bamu buƙatar mota saboda ina da tawa." Cewar Hindatu tana wani yauƙi.
Shiga cikin motar ya yi jin abin da ta ce.
Ya kunna motar ya fara tafiya a hankali.
Wajnah shiru tana sanya ran zai yi mata magana, musamman turaren da ta yi amfani dashi na sace zuciyar miji, amma sai ta ga ko arziki kallo ba ta samu ba, yayin da hankalinsa ke kan waya.
"Habibina," Ta furta can ƙasa-ƙasa da wata irin murya kuma cikin salo da ƙissa, amma yadda kasan da gunki ta yi.
Cikin tsoro ta sanya hannu za ta kama hannunsa.
Labarin ya zo da wani irin salo da nishadi, karku baru a ba ku labari. Ku biyo ni domin it’s just like a little introduction part, and guess what? You will really enjoy it. Believe me, my dear readers. Your happiness is my concern. Follow me on Facebook, Whatsapp, Wattpad, Arewaboo, and Bakandamiya. Ta ku, Jamila Lawal Zango (Jamsy).
FOR WHATSAPP: 07072971093
CALL: 008144072423
*RANAR WANKA...*
NA
JAMILA LAWAL ZANGO
"JAMCY"
☀️ *First Class Writers Asso* ☀️
Hame of Qualities And Trusted writer's of The Nation
*GARGAGAƊI*
Ban yarda kuma ban amince a juya mini labari ko ta wace siga ba, sannan ban bada lamuni a ɗora mini littafi a kowane kafar sadarwa ba sai da izinina a kiyaye⚠️
JAN HANKALI
Kirkirarran labari ne ban yi shi don wani ba, idan har ya yi daidai da labarin ki/ka to arashi ne.
SADAUKARWA
Kacokam labarin daga farkonsa har karshe sadaukarwa ne ga ƙawata sahibata Aysha Na Lado. Allah saka miki da alkairi ya raya zuri'a.
PAGE 17
BISMILLAHIR RAHMANINR RAHIM
Cikin tsoro ta sanya hannu za ta kama hannunsa.
Tamkar za ta ɗora masa wuta, ya janye hannun tare da watsa mata mugun kallo, wanda ya sanya ta yi saurin ɗauke hannunta zuciyarta a jagule.
A haka suke tafiyar, babu wanda ya ƙara magana sai Najib da ya ga shirun ya yi yawa, ya kunna waƙar Umar M Sharrif ya sanya sauti.
Huwais rintse idonsa ya yi cikin wani yanayi. Yana jin yadda kiɗan da waƙar suke sanya shi cikin shauki mai wuyar fassarawa. Surarta yake ayyanowa yana fatan ina ma a ce da ita ce a cikin motar nan.
Ƙamshin turaren Wajnah da ya ƙara sanya masa ciwon kai, da ƙarar sautin waƙar suka ƙara birkita tunaninsa.
"Please Najib, ka kashe waƙar nan tana sanya ni ciwon kai."
"Na rage dai saboda na san kanka ya ɗau hayaniyar mutane. Karka manta yau ranar farinciki ne a gareka."
"Sosai Najib! Allah kaɗai ya san farincikin da na ke yi na samun sa a matsayin miji, domin na san na yi dace." Wajnah ta furta tana masa mayataccen kallo wanda ko kallonta bai yi ba, ballantana ya san abin da take yi.
A lokacin da suka ƙaraso gurin, Wajnah ta yi tunanin zai kama hannunta ko don ya cireta kunyar ƙawayenta da suke damunta da tambayar angon, amma sai ta ga saɓanin haka. Ya nufi ciki yana takun isa tamkar an aiko masa da mala'ikan mutuwa.
Da ido Najib ya rinƙa masa nuni da ya kama hannunta, amma sai ya basar ya nufi hanyar shiga. ganin haka ya sanya ta ƙarasa da sauri gurinsa za ta kama hannunsa.
Da sauri ya janye hannu tare da ƙarawa da sauri. Ranta ya ɓace har ƙwallah suka taru a gefen idanunta. Da sauri ta yi ma za ta mayar da hawayen ta bi shi suka jera.
Suna isa gurin ya ɗauki tafi ina ihu yayin da aka saki waƙar Umar M Sharrif.
Hilah yana shigowa duk yanayin da take ciki sai da ta ji wani irin farinciki ya kamata. Wayarta da ke hannunta tana ta turawa mahaukacin masoyi kalamai ta ije kan teburin.
Murmushi ta sakar masa, tana kallonsa har lokacin da suka shigo ciki xa su zauna.
Ganinta Huwais ya ji wani irin tsau a ransa. Duk da babu wani kwalliya a fuskarta, kuma in har ka yi mata kallon ƙurullah za ka fahimci tana ɗauke da damuwa, amma ta yi kyau kamar a sace ta a gudu.
Wani tsadadden murmushi ya sakin mata daidai lokacin da suka zauna.
"Anty Hilah, Ya Huwais ya yi kyau sosai. Ki bani wayarki na yi masa vedio recording." Amnah ta faɗi tana miƙa mata hannu.
"Ungo ƙaramar wayar ki yi masa saboda ni ma ya yi mini kyau har a tashi zan rinƙa ɗaukarsa hoto. Yayanmu mai kyau ne ko ne, haka matar da ya aura ko?" Ta ƙarashe maganar tare da kama mata kumatu tana murmushi.
"Eh kuma sun yi kyau kema kina da kyau sosai." Dariya ta yi bayan ta miƙa mata wayar ita kuma ta tafi.
Kallonta yake yi kamar zai cinye ta gani yake duk babu wanda ya kaita kyau.
A lokacin da M.C ya fara bayani tare da sanarwa abokin ango zaji ba da tarihin ango. Huwais, ya yi wa Najib nuni da ya zo.
"Please, Hilah na ke son ta bada tarihina, domin babu wanda ya sanni sama da ita." Ya furta wa Najib cikin muryar roƙo.
"Kana ganin hakan babu matsala?"
"Bana tunanin akwai don Allah?"
"Ok, shikenan." Ya ce tare da zuwa gurin M.C ya yi masa bayani.
Bayan ya gana jawabinsa ya gyara muryar sannan ya ce,
"A yanzu za mu kira ƙanwar ango wanda ita ce za ta bayar da tarihin Yayanta."
Kowa ya ji wani iri har da ita kanta Hilah.
Ummu kuwa sam ba ta ji daɗin haka ba, domin ta san duk shirinsa ne. Ɓata ranta ta yi daidai lokacin da Hilah ta kalle ta.
Jikinta a sanyaye ta miƙe, tana kallonsa da yake ɗaga mata hannu don ƙarfafawa.
"Gaskiya Wajnah, sai kin tashi tsaye, saboda yadda na ga mijinki na son ƙanwarsa zai iya sakinki saboda da ita."
"Ba ki san yadda na tsane ta ba, duk da cewar ƴar'uwata ce, amma wallahi ko kallonta bana son yi, domin da zan samu ko rabin son da yake mata da na ji daɗi."
"A to ki dai tashi tsaye dangin miji ba a iya musu, musammman yadda yake ta kallonta yana mata murmushi xai nuna yana sonta sosai."
"Ki barni da shi za ki ga yadda zan juya shi. Mai wuyar na mallaka masa kaina." Ta ce cikin ƙuna tana kallon Hilah da take jin kamar ta shaƙeta.
A hankalinda natsuwa ta fara bada labarinsa, wanda ya tsura mata idanu yana kallonta. Gurin ya yi tsit ba ka jin komai sai zazzaƙar muryarta da yake tashi a cikin speaker.
Zuru ya yi mata da idanu yana jin yadda take maganar cikin harshen turanci. Kallonta yake yi da sha'awa yana mamakin yadda ta san kanshi fiye da shi. A ransa ji yake kamar ya tashi ya rungumeta ko ya sace ta su je can wata duniya daga shi sai ita su yi rayuwarsu.
Bayan ta gama bada tarihin, rayuwarsa gurin ya ɗauki tafi da waƙa ban da Ummu da ta ci magani.
Aminiyar amarya ta ba da tarihin amarya, sannan aka saki waƙa. An ci an sha an kuma na ta cashewa sai fatan ba da zaman lafiya.
Hilah miƙewa ta yi tana rangaji ta fita daga cikin hall ɗin, saboda ƙarar waƙar yana hawa mata kai.
Kallo ya bita da shi har fice daga hall ɗin. Tun daga lokacin ya rasa natsuwarsa sai kallon agogo yake yi yana kallon ƙofa.
Wani guri wanda ba a jiyo sautin ta samu ta zauna.
Gorar ruwan dake hannunta take watsa ma fuskarta.
Zama ta yi tare da buɗe bakinta tana shan ruwan. Bayan ta gama ta ije gorar tana kallon ciyayin da suke luf a gurin, kuma suka ƙara ƙawata gurin.
Rintse idanunta ta yi cikin damuwa har yanzu in ta tuna da yaudarar da mahaukacin masoyi ya yi mata, sai ta ji ƙwallah na zubar mata.
Gefen hannunta ta sanya ta share hawaye tare da sunkuyar da kanta ta cusa a tsakanin cinyoyinta.
"Hilah, har yanzu ba za ki cire damuwa a ranki ba?" Ta ji muryarsa da ta yi matuƙar tsoratata.
Da sauri ta miƙe tare da waigawa don ta ga inda yake, amma sai ta ganshi a gefen ta yana zaune.
"Innalillahi Yaya, yaushe ka fito?"
"Hankalina ya kasa kwanciya bayan kin bar gurin kamar yadda na zargi tunani kika fito ki yi."
"Don Allah ka koma ciki ƙarar kiɗan ne ya sanya kaina ciwo."
Hannu ya sanya ya kama kan yana faɗin," Ayya, sorry bari na yi miki addu'a."
"No ka barshi xan je mota na ɗauko magani a jakata." Ta ce tare da sauke hannunsa da ya ɗora saman kanta.
"Ok, to mu je na raka ki."
"Please, don Allah ka koma" Ta ce cikin wata irin murya kamar za ta yi kuka.
"To sarkin kuka bari na koma kar ki yi kuka." Ya ce da sauri tare da juyawa yana waigenta.
Har ya bule tana kallonsa. Haƙiƙa ta san yana mugun sonta. Kullum godiya take yi da Allah ya ba ta ɗan'uwa mai tsananin ƙaunarta, wanda ta san ko bayan babu ran iyayensu ba zai bari su wulaƙanta ba.
Komawa ta yi ta zauna. Kiran wayarsa ya rinƙa shigowa. Da sauri ta miƙe ganin ya turo mata tsaƙo.
Tana komawa gurinta ta zauna, ya saki ajiyar zuciya hankalinsa na kanta duk motsi ta yi sai ya kalleta.
Kafin a tashi taron ran Wajnah ya ɓaci matuƙar gaske. Tun da suka je gurin ko kallon kirki ba ta samu ba. Ko da aka kira su yi rawa. Ransa a jagule ya miƙe shi ma don kallon da Ummu ta yi masa ne.
Da ma shi rawa ba ɗabi'arsa bane don haka ya yi ƙiƙam kamar soja. Yana ganin yadda Wajnah take rawa kamar za ta karye.
Bayan sun gama rawar, aka buƙaci iyayen ango su zo. Ummu ta yi ƙoƙarin manna musu ruwan kuɗi haka Abu. Daga ƙarshe aka kira ƴan'uwan ango. Tun da Hilah ta shigo hankalinsa ya koma kanta.Kuɗi ya ciro ya rinƙa manna mata.
Ganin kuɗin da yake manna mata, ya sanya ta fice da sauri daga filin rawar. Ran Wajnah ya ƙara ɓaci har ta kasa jurewa tana harararsa.
Bayan an gama dinner suka tattaro suka dawo gida. Daga gurin dinner aka wuto da Wajnah ɗakinta.
Cikin tsananin farinciki take kallon gidan da kyawunsa ya yi matuƙar tafiya da hankalinta. Haƙiƙa tsarinsa da yanayin gidan ya burgeta, kuma iyayenta sun yi bajinta ƙwarai!
Zama ta yi kan one seater tana kallon Wahida da take shayar da ƴarta mama.
"Gaskiya gidanki ya yi kyau sosai! Abin da ya rage miki sai ki kama maigidan da kyau, yadda babu wata ƴar iska da za ta shigo miki gida, domin irin mijinki shi ne mace ke hauka in zai ƙara mata kishiya."
"Lallia ma Wahida, har yanzu kamar kallon ƙaramar yarinya kike mini. Kin san yadda na samu har aka yi auren nan? Sau biyu ana sanya ranarmu ana fasawa. Ai yadda na sha fama kafin na shigo cikin gidansa ku ƴan'uwansa sai na ga dama zai rinƙa kula su, ballantana wata kishiya. Ni Allah ya tsare ai gaba da baya zan tsare don no kishiya in my house."
Dariya suka kwashe da shi tare da tafawa.
"Ai ban ga laifin ki ba Wajnah, don ko ni mijina shi da wata sai dai matan aljannah da ban isa na hana shi ba, amma a duniya babu macen da ta isa na yi sharing mijina da ita, in kuwa ta kuskura ta aurar mini miji sai na nuna mata mijin wata ta aura. Don ba zan yi shukar ƴaƴan itatuwa ba mu ci da wata." Mardiya ta ce.
"Yadda mijin ki yake jarumin namiji, dole sai kin zama jaruma in ba haka ba kina ji kina gani za a yi miki sakiyar da babu ruwa."
"Duk wacce ta kuskura ta shigo mini
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 12 Chapter of 17