Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
gida nice ajalinta, don sai na canza mata kammanni ta yadda ko iyayenta suka ganta ba za su gane ta ba ballantana shi." "Ato ai gara ki kula saboda kula da kaya yafi ban cigiya." "Shi ya sa maganin da Hajiya Zauzau ta bani ta ce na sha ƙwara ɗaya tall! Kin san Allah? Guda uku na shanye." "Kan uban nan! Wallahi babu ruwana in kika kashe kanki, kin san ƙarfin maganin mata na bature?" Cewar Wahida tare da zare idanunta. "Ai in za ka sha giya ka sha ta dubu." Ta furta tana dariya. "Wallahi babu ruwana kar ki kira ni." Dariyar ya yi ita ba ta ce komai ba. Huwais da Najib a gaban Abu suna zaune yana mishi nasiha. "Ƴar'uwarka ce Wajnah, kuma yau ta koma matsayin matarka. Tana da haƙƙi da dama a kanka, wanda in har ba ka sauke mata ba Ubangiji xai tambaye ka. Kana da sani kuma kai ba yaro bane, kasan haƙƙin da Allah ya rataya maka, don haka kar na ji na ga abin ƙi a rayuwar aurenku. Ka riƙeta tsakani da Allah Ubangiji zai jiɓanci lamarinka, sannan ka sani zaman aure bauta ne na Ubangiji ba zaman jin daɗi ko san rai ba. Duk abin da ka yi mata na cutarwa Allah sai ya tamabaye ka, kamar yadda in har ta saɓa maka ita ma Ubangiji zai hukunta ta. Don haka a matsayina na mahaifinka ina mai jawo hankalinka da ka riƙe amanar Allah sai Allah ya jiɓanci lamuranka." Shiru ya yi jikinsa ya yi sanyi, har yana jin hawaye na son zubo masa, jin nasihar da Abu ya ke masa. "Shin ko zuciyata za ta aminta na xauna da ita, bayan bana sonta kuma ban taɓa jin ta burge ni ba?" Ya yi wa kansa tambayar cikin damuwa. "Na gama za ka iya tafiya, sai dai in mahaifiyarka na da abin cewa." Ya ƙarashe maganar yana kallonta. "Ai ka gama cewa komai, sai dai na ƙara masa da cewar ya kula da ita, ya san cewa ita ƴar ƴaƴata ce, wacce muka fito ciki ɗaya, sam ba zan lamunci ya cutar da ita ba, kamar yadda ita ma ba zan barta ta cutar da shi ba. Ya riƙe ta tsakani da Allah don ɗorewar zumuncinmu " "To ka ji abin da mahaifiyarka ta gaya maka. Ka tashi ka tafi gidanka Allah ya yi maka albarka." Abu ya ce yama kallonsa. Har ya miƙe, sai kuma ya kasa tafiya ya ɗago idanu suka haɗa ido da Ummu, da tun da ya miƙe take kallonsa. Jikinsa ya ƙara sanyi da ya tuna nasihan da suka yi masa, wanda ba ya tunanim zuciyarsa xa ta iya amincewa ya aikata hakan. Ji ya yi kamar ya xauna ya gaya musu wacce yake so, amma ya san a matsayin mahaukaci za su ɗauke shi. "Zan wuce Abu, Ummu ku yafe mini." Ya furta yana share hawayen da ya fara zubo masa. Ummu ce ta zura masa idanu tana ji ita ma tamkar xa ta yi kuka. "Na san abin da ke ranka Huwais, ina matuƙar sonka da damuwa da halin da kake ciki. Sai dai abin da kake so da muradi sam ba mai yiwu ba bane!" Ta furta tana kallon sa cikin tausayawa. "Ma za ka tafi ga iyalinka Allah ya yi maka albarka." "Amin," Ya amsa jin abin da Abu ya faɗa da shi ma ya miƙe yana gayra zamansa. A kasalance yake tafiya Najib na bayansa. Yana fita Ummu ta sauke ajiyar zuciya. Tun lokacin da yaran nan suka mallaki hankalinsu na daina bacci mai daɗi. Haƙiƙa yau zan rama baccin da na daɗe tsawon shekaru ban yi ba." Ta furta tana kallonn Abu da ya ƙura mata idanu sai ta ɗora da ce wa," Ko da yake an sare kan maciji ne ba a yarda gangar jiki ba, domin matuƙar Hilah ba ta yi aure ba hankalina ba zai kwanta ba gabakiɗaya." "Kar ki damu ita ma aure zan yi mata, karatun na ta saura shekara ɗaya ne." Huwais kuwa yana fita ya shiga mota sai ya kifa kansa a kan sitiyarin motar. Kuka yake son ya yi kuka sai mai ƙarfi. Wataƙila ya samu sauƙin tafarfasar da zuciyarsa take yi, tamkar kwatamin da aka cika shi da ruwan zafin da ya fara tafarfasa za a kaiwa mai jego. Idanunsa sum kaɗa sun yi ja kamar jan gauta. Ji yake wani irin miyau mara daɗi ya taru a bakinsa, wanda ya kasa haɗiyawa kuma ya kasa tofarwa. Ga mamakinsa, sai ya ji hawaye masu tsananin xafi waɗanda suka fi garwashin wuta ƙuna sun wanke masa fuska. "Be a man Huwais! Ka yi addu'a karka karaya." "Na rasata har abada! Ashe dama ba zan aureta ba kullum zuciyata take mini ƙawazucinta!" "Sheɗanne yake ƙawata maka don kawai ya ci galaba a kanka." "No Najib, na yadda da kaina. Soyayar da nake mata ba ta sha'a ba ce. Jikina yana bani kamar a kwai ɓoyayyen sirri ko kuma lamarin da zai iya halasta aurenmu." "Wane hujja kake da shi Huwais? Yarinyar da ita ce ƙanwarka ta uku. A gabanka aka yi rainon cikinta kuma aka haife ta, sannan kai ka yi rainon ta har ta girma. Wace hujja kake da shi wanda zai iya halasta mka ita a matsayin mata?" "Ban sani ba, amma ima sonta ita ce zaɓin raina. Don Allah ka yi mini addu'a zuciyata za ta buga, sam ba zan iya adalci ga matata ba." "Ka ƙoƙarta Allah zai shiga lamarinka."Ya ce masa cikin tausaya. "Ina son na yi sallama da ita. Ina son na ganta kafin na yi bacci. Na san cewa Ummu ta yi mini aure ne, don ta rana ni da ita. Sai dai ta yi kuskure saboda mutuwa ce kawai za ta zamo katanga a tsakaninmu." "Huwais, karka kunna wutar da ba za ka iya kashewa ba, kuma ba ya zama ba ka da mafita a lamarin, bayan ka ɓata sunan ahalinka." Girgiza kansa ya yi, ya kasa ce masa komai domin duk abin da ya faɗa gaskiya ne. Ƙoƙarin buɗe motar ya fara ganin Najib na ƙoƙarin tada motar. "Ba zan iya tafiya ba tare da na ganta ba." Hannunsa ya kama yana kallonsa."Ka kira wayarta karka sanya Ummu ta yi mata faɗa." Kamar umurni ya ba shi, sai ya koma ya yi cikin motar ya zauna tare da ɗaukar wayarsa don ya kiranta. Tana zaune a ɗakinta kan gado ta haɗe kai da gwiya tana hawaye. Abin da mahaukacin masoyi ya yi mata yake ƙara ɓata ranta. Hawaye masu zafi suke ƙara shatato mata a saman ƙuncinta. Wayarta da ke kusa da ita ya sanya ta kai hannu xa ta kashe wayar. Ƙaramin tsaki ta yi domin a tunaninta Hamad ne, amma dai dai ganin mai kiran, ya sanya ta ɗauka tare da yin sallama cikin siririyar murya. Labarin ya zo da wani irin salo da nishadi, karku baru a ba ku labari. Ku biyo ni domin it’s just like a little introduction part, and guess what? You will really enjoy it. Believe me, my dear readers. Your happiness is my concern. Follow me on Facebook, Whatsapp, Wattpad, Arewaboo, and Bakandamiya. Ta ku, Jamila Lawal Zango (Jamsy). FOR WHATSAPP: 07072971093 CALL: 008144072423 *RANAR WANKA...* NA JAMILA LAWAL ZANGO "JAMCY" ☀️ *First Class Writers Asso* ☀️ Hame of Qualities And Trusted writer's of The Nation *GARGAGAƊI* Ban yarda kuma ban amince a juya mini labari ko ta wace siga ba, sannan ban bada lamuni a ɗora mini littafi a kowane kafar sadarwa ba sai da izinina a kiyaye⚠️ JAN HANKALI Kirkirarran labari ne ban yi shi don wani ba, idan har ya yi daidai da labarin ki/ka to arashi ne. SADAUKARWA Kacokam labarin daga farkonsa har karshe sadaukarwa ne ga ƙawata sahibata Aysha Na Lado. Allah saka miki da alkairi ya raya zuri'a. PAGE 18 BISMILLAHIR RAHMANINR RAHIM Wayarta da ke kusa da ita ya sanya ta kai hannu xa ta kashe wayar. Ƙaramin tsaki ta yi domin a tunaninta Hamad ne, amma ganin mai kiran ya sanya ta ɗauka tare da yin sallama cikin siririyar murya. "Ki zo waje ina jiranki muyi sallama." Karo na farko ta ji wani iri a rayuwarta.Ganin Yayanta wanda yake ji da ita da ƙaunarta yau xai bar gidan. Haƙiƙa a rana ta yau ba za ta taɓa mantawa da ita ba, domin ta rasa abubuwa da dama. Ta san cewa duk soyayyar da yake nuna mata zai rage tun da ya yi aure, musamman in ya haihu soyayyar za ta koma kan yaransa. Wataƙila ya manta da ita ba zai damu da lamarinta ba. Tunanin hakan ya ƙara sanya mata damuwa fiye da ta ɗazu, wanda sai da ta ji dama bai kirata don su yi sallama ba. Da sauri ta miƙe, tare da zura dogon hijabinta ƙasa kasancewar kayan bacci ne a jikinta. Ba ta yi fargabar fita ba, saboda Ummu tana can da ƴan bikin da ba su gama watsewa ba. Hannu ta sanya ta murɗa ƙofar get ɗin gidan, daidai lokacin da ya gaji da jira ya ƙara kira. Ganin ta fito ya sanya ya kashe wayar yana kallonta dusu-dusu da hasken watan da bai gama girma ba ya haska gurin Da sauri Najib ya fita daga motar ya koma can baya, wanda hakan ya yi masa daɗi sosai, ta yadda zai samu damar magana da ita sosai. Kallon juna suka yi na ƴan sakanni. Ita ce ta fara cire idanunta ta buɗe motar ta zauna a kujerar gefensa. "Na kasa tafiya har sai na ganki. Ina jin wani iri yau zan bar ƴan gidanmu da gidanmu na koma rayuwa da wata can." "Anty Wajnah ƴar'uwa ce ba bare ba, ka daina kiranta da wata can." Ta furta tana kallonsa. "Haka ne, amma ba kamar jinina waɗanda muka fito ciki ɗaya ba." "Za ka saba da ita kuma ina gaya maka za ka ji daɗin zama da ita." "Hmmmmh!" Ya ce wanda ya sanya ita ma ta yi shiru ta kasa cewa komai. "Zan tafi gidana, amma ki sani duk da Ummu ta yi hakan ne don ta nesanta ni da ku, ba za ta yi galaba ba." "Ummu, fa gata ta yi maka kar ka yi mata mummunar fahimta." "Zan wuce ki yi mini fata na gari. Ina sonki ƙanwata." Hannunta ta zare da ya riƙe cikin nasa."Allah ya xaunar da ku lafiya ya baku ingantacciyar zuriya." Addu'ar da ta yi masa sam ba daɗaɗa masa ba, har ya ji da ya san abin da za ta roƙa masa kenan, da bai roƙi addu'ar ba." "Shikenan, ki kula da kanki, kuma ki cire tunanin mahaukacin masoyinki za mu yi maganar." "To Yaya, Allah ya tsare ka gaida Anty Wajnah sai mun zo." Ba tare da ya amsa ba, ta fito motar wanda ganin haka Najib ya shigo motar suka kama hanya. Sai da suka biya suya spot, sannan suka siya tare da siyan drinks masu yawa suka kama hanya. Bayan sun shiga cikin gidan sauran abokannasu da suke jiransa a ɓangarensa suka fito. Yana ƙoƙarin shiga cikin falon, ya ji darararrakun ƙawayenta wanda ya sanya shi dawowa da sauri ya kalli Najib "Ba na son shiriritar nan ka gaya ma ƙawayenta su tattara su bar mini gida so na ke na kwanta." "Kar ka yi mini haka don Allah. Yau rana ɗaya ka daure mu sayi baki, sanin kanka al'adace ta Bahaushe don haka kar ka wulakanta matarka." Jan numfashi ya yi tare da jan ƙaramin tsaki.Tafiya yake yi tamkar ba shi ba har ya shiga cikin falon. Sallamar su ya sanya suka natsu, yayin da masu gyara zaman gyale su na yi masu ajusting zaman su na yi. Wajnah kuwa jin siririyar sallamar da ya yi, ya sanya ta ɗago idanunta da saurinta zuba masa. Wani iri ta ji a cikin ranta yayin da kwalliyar da ta yi ya tafi da imaninta. Abokannasa suka xauna a sauran kujerar, sai wanda Wajnah take ita kaɗai, wanda hakan ya sanya ba tare da zaɓi ba, ya zauna a kujera. Zamansa ga sanya ta ji ta rasa natsuwarta gabakiɗaya. Ƙamshin turarensa da saukar numfashinsa suka sanya ta shiga cikin wani irin yanayi. Lumshe idanunta ta yi, tana jin kamar ta kwanta a jikinsa. Cikin dubara ta matso kusa dashi ta yadda jikinsu yana gogon juna, wanda yanayin da ta tsinci kanta ta rasa kasa bayyana shi. Huwais yana jinta, amma bai kula ba sai dabara ya yi ya matsa. Ƙara matsowa ta yi sosai. Ganin ya ƙure kujerar ya sanya shi haƙura a zuciyarsa yana alla-allah a kammala siyan bakin ya kwanta. Yayin da yake wannan tunanin Wajnah tunaninta ya tafi ga yadda first night ɗinsu zai kasance. Tunanin yadda za ta rama wulaƙancin da ya yi mata za ta yi, domin sai ta bari ya shiga hannu za ta nuna masa ita ma mace ce da ranarta. Gabakiɗaya ta rasa natsuwarta. Buƙatar mijinta da magungunar da ta rinƙa sha ba tare da ka'ida ba suke ɗawainiya da ita. Najib ne ya yi gyaran murya tare da buɗe taronnda addu'a. Bayan nan sai kuma aka fara tsokanar juna. Duk maganganun da suke yi bai tanka musu ba, duk da cewar a kanshi da Wajnah suke yi. Wajnar ce kawai ta buɗe baki tana kare shi, da ita wanda hakan ya ƙara ɓata mood ɗinsa, domin ya tabbata da Hilah ce a matsayin amaryarsa, kunya da natsuwarta ba zai sanya ta rinƙa magana haka ba. Tunaninsa ya yi nisan kiwo gurin tunaninta ya ji muryar Najib na faɗin,"To ango, zamu wuce da ƴan matan, sai na ce asuba ta gari. Ubangiji ya ba ku zaman lafiya da zuriya ɗayyiba. " Ba tare da ya amsa addu'ar ba, ya miƙe sai ita ta masa da sauri tana faɗin,"Amin," Ɗago manyan idanunsa ya yi, ya kalle ta jin rashin kunyar da ta yi na amsawa, amma bai ce komai ba ya fara tafiya don ya raka su. Ganin haka ta bi bayansa suna magana da ƙawayenta. Maryam ta kama hannunta tana faɗin,"Don Allah karki manta asubar fari ki kiramu ki gaya mana yadda daren zai kasance, domin bana jin zan iya bacci, saboda ƙosawa na ji yadda ya kasance. Wallahi kin yi sa'ar miji da za ki more rayuwarki, kuma ki ci duniyar aurenku da tsinke." "Karku damu da zarar komai ya wakana zan sanar muku conference calls zamu haɗa duka na gaya muku, ai sam ba zan yi wasa da wannan ranar ba. Wannan gayen sai na nuna masa iyakansa, domin sai ya zamo tamkar bawa a gareni." Dariya suka kwashe dashi tare da tafawa. Najib ya kama hannunsa tare da raɗa masa. "Please, kar ka ɓata muku first night ɗinku. Kana ganin amarya ta shirya duba ga irin yadda take yi kamar ta haɗiye ka. Ka ba ta haɗin kai ku samar mana takwarar Hilah." Ƙara ɓata ransa ya yi jin abin da ya ce."Zuciyata da gangar jikina na Hilah ce." Da sauri ya shige motar jin yadda ya yi maganar da ƙarfi domin a tunaninsa wasu sun ji abin da yake faɗi. Bayan sun fita maigadi ya rufe get, Huwais ya ɗan tsaya a farfajiyar gidan yana ƙarewa gidan kallo. Tun lokacin da Abu ya fara ginin gidan ya sanar masa da mallakinsa ne. Ya yi buri da addu'ar shi da Hilah xa su yi rayuwa cikinfarinciki a cikin gidan, amma sai dai ya san da wuya gurguwa da auren nesa. Yau ga shi da macen da ya tsana a rayuwarsa fiye da komai a matsayin wacce za su yi rayuaar aure a cikin gidan. Ko ya ya rayuwarsu xai kasance, domin ya san gangar jikinsa ta aura, amma zuciya da ruhi na gurin ƙanwarsa abin begensa Hilah Rintse idanunsa ya yi ji yake ina ma ace yau ita ce daga shi sai ita a cikin wannan gidan. Da hannunsu na maƙale da juna za su taho. Bayan sun tafi shi zai ɗauke ta har zuwa cikin gidansu. A wannan ranar sam ba xai barta ta rintsa ba, domin zai kasheta da zazzafar soyayyarsa wanda ba zai sa ta manta da wannan rana ba.. Yana cikin wannan tunanin, Wajnah da ta gaji da jiransa ta fara kiran sunansa, amma ta ji ya yi shiru babu amsa. Hannunsa ta kamo tare da kwantawa a kafaɗansa. "Babyna, ina ta..." Maganar ta maƙale sakamakon tureta da fara tafiya da ya yi. Sororo ta tsaya cikin tsananin mamaki. Abin da yake mata yana mugun ci mata tuwo a ƙwarya, musamnan inta duba ta ga babu inda Allah ya rage ta. Duk da cewar ta san namiji ne ingarma a cikin mazaje. Ita ma babu wata makusa a jikinta da xai sanya ya rinƙa wulaƙanta ta, domin duk da cewar ita ba fara sosai bace, amma ta haɗa da na kanti wanda ya ƙara mata haske mai kyau sosai, don ba ta siyan kashama marasa kyau, kuma dama siyen na gari mai da kuɗi gida. Tana da zubin aje bota kalar jikinta kamar fanta. Don da ka ganta kaga jiki duk madara😄😄😄 Idan kuma magana ake ta ƙira, ta kuma ya haɗa duk wani sura da xai jawo hankalin ɗa namiji gareta. Mace ce wacce ta yi amanna da supplements na gyaran jiki masu kyau da in ka sha magani take take siye. Musamman da bikinta ba ƙaramin siye magungunan ta yi ba. Ƙuta ta yi ganin yadda ya kusa shigewa ya barta. Da sauri ta fara binsa a ranta tana faɗin,"Za ka sani in ka shigo hannu, da xarar ka ɗanɗani zumar jikina za ka manta da ƴar'iskar da take ɗauke mata hankali, domin hatta shegiyar ƴar'uwark da kake so da Ummu sai ta gane ɗanta ya canza." Da sauri ta buɗe ƙofar falon da ya buga da ƙarfi. Huwais kuwa cikin ɓacin rai ya buga ƙofar falon ya shige. Yana ƙoƙarin shiga cikin ɗakinsa ta ya ƙaraso inda yake. "Haba mijina, ina ta yi maka magana ka yi banxa da ni. Karka manta yau rana ce ta musamman a garemu." Ta faɗa cikin wani irin murya da zai ɗauki hankalin duk wani ɗa namiji tana ƙoƙarin haɗa jikinsa da nata. "Ke!" Ya daka mata tsawa tare da kaucewa ya ɗauki wayarsa. Labarin ya zo da wani irin salo da nishadi, karku baru a ba ku labari. Ku biyo ni domin it’s just like a little introduction part, and guess what? You will really enjoy it. Believe me, my dear readers. Your happiness is my concern. Follow me on Facebook, Whatsapp, Wattpad, Arewaboo, and Bakandamiya. Ta ku, Jamila Lawal Zango (Jamsy). FOR WHATSAPP: 07072971093 CALL: 008144072423 *RANAR WANKA...* NA JAMILA LAWAL ZANGO "JAMCY" ☀️ *First Class Writers Asso* ☀️ Hame of Qualities And Trusted writer's of The Nation *GARGAGAƊI* Ban yarda kuma ban amince a juya mini labari ko ta wace siga ba, sannan ban bada lamuni a ɗora mini littafi a kowane kafar sadarwa ba sai da izinina a kiyaye⚠️ JAN HANKALI Kirkirarran labari ne ban yi shi don wani ba, idan har ya yi daidai da labarin ki/ka to arashi ne. SADAUKARWA Kacokam labarin daga farkonsa har karshe sadaukarwa ne ga ƙawata sahibata Aysha Na Lado. Allah saka miki da alkairi ya raya zuri'a. PAGE 19 BISMILLAHIR RAHMANINR RAHIM "Haba mijina, ina ta yi maka magana ka yi banxa da ni. Karka manta yau rana ce ta musamman a garemu." Ta faɗa cikin wani irin murya da zai ɗauki ha kalin duk wani ɗa namiji tana ƙoƙarin haɗa jikinsa da nata. "Ke!" Ya daka mata tsawa tare da kaucewa ya ɗauki wayarsa. Ƙarar da ya yi mata, ya santa matsa tana xare idanu. Wayarsa ya ɗauka tare da fara tafiya xai shiga cikin bedroom ɗinsa. Ganin zai shige ya santa ta ƙara sauri ta tsaya a gurin ƙofar. "Wallahi ba xan yarda first night ɗina ya tafi a banxa ba, domin ban san yadda xan yi da maganin da na ɗirka wa kaina ba." Ta furta a cikin zuciyarta tare da kashe masa ido. "Haba Ya Huwais, karka manta ni ƴar'uwarka ne. Ko babu aure bai kamata ka wulaƙanta ni ba. Matarka ce ina da haƙƙi a kanka. Karka ruguza ranar farkon mu domin na yi wa wannan rana tanaji na musamman da ba zamu manta da shi ita." "Ni sa'an ki ne? Kauce ki bani guri." Ya ce tare da sanya hannunsa ya tureta ya shige cikin ɗakinsa. Takaicin abin da ya yi mata ya sanya ta fara hawaye. Ganin kamar haƙarta ba xa ta cimma ruwa ba, bayan cika baki da kuranta wa ƙawayenta yadda daren zai kasance fa ta yi. Tana tsaye sororo tamkar gunki, ya murɗa ƙofarsa ya shiga tare da bugata da ƙarfi. Da sauri ta juya don ta shirya kanta ta shiga cikin ɗakin, domin ta rantse ba za ta bar wannan rana ta wuce a tutan ma"aho ba. Ɗaki ta shiga ta faɗa kan gado tare da sakin kuka. Sai kuma ta miƙe ta tuɓe kayanta ta shige bayi. Wanka ta sheƙa wanda ta ɓata lokacinta tana dirzar jikinta da mayuka masu ƙamshi da kyau. Bayan ta gama wankan, ta zauna zaman shafa. Inda ta ɓata lokacinta gurin ƙyalƙyale jikinta da mayuka da turare masu ƙamshi da daɗin shaƙa. Wata doguwar rigar bacci ta sa mai kyau fari. Rigar har ƙasa take, amma kuma ta na bayyana surar mutum. Ƙara ɗauko turaren da Hajiya Zamzam ta ba ta yi tare da ƙara shafe ko ina na jikinta. Sannan ta sanya a rigar baccin. Wayarta ta ɗauka ta duba kanta a madubi sannan ta rufe ƙofar. A lokacin da ta murɗa ɗakin yana kwance a kan gadonsa, hannunsa riƙe da wayarsa. Bayan ya yi wanka ya canza kayan jikinsa zuwa kayan bacci. Riga ya sanya da ƙaramin gajeren wando. Kyawawan dogayen cinyoyinsa masu ɗauke da zararan gashi ya kwantar a saman filo, sannan ya kwantar da kansa a ɗayan filon. Kallon hotonta yake yi, yayin da hawaye suke zuba a ƙuncinsa. Hannunsa ya kai ya shafa fuskarta, tare da sanya yatsarsa a saman idanunta, yana shafa idanunta da suke ɗaukar hankalinsa ƙwarai. Ya faɗa cikin kogin tunaninta, ba tare da ya san Wajnah na tsaye tana ƙarewa halitarsa kallo ba. Wajnah kuwa ji ta yi kamar xa ta sume. Haƙiƙa Allah ya yi mata tagomashi da samun miji mai kyawu kuma ɗan gayu, musamman da ta kalli yatsun ƙafarsa sai ta ji kamar ta duƙa ta lashe. "Huwais," Ta ce tare da ƙara matsowa kusa da shi. Da sauri ya miƙe tare da kifa wayarsa domin ya ɗauka ta ga abin da yake kallo. "Ke! Uban me ya kawo ki cikin ɗakina?" Ya yi mata tambayar cikin ɓacin rai yana zare mata idanu. Wal ta yi da idanunta tare da yi mata fari."Ni da ɗakin mijina sai na tambayi izinin shigowa? Karka manta da kai da duk gidan nan mallakina nane." Tsaki ya yi, tare da da ɗaukar wayarsa ya fita a cikin galary sannan ya ije wayar. Ganin tana matsowa tana son haɗa jikinsa da nata, ya sanya shi matsawa tare da ƙara daka mata tsawa. Yana ganin zallar rashin kunyarta na shigo masa a haka. Ransa ya ƙara ɓaci sosai, ganin rashin kunyarta da tarbiya, domin ya tabbata da Hilah ce mai kunya ba za ta taɓa bayyana surarta ba. "Ya Huwais, don Allah ka bari mu more rayuwar aurenmu. Wallahi na yi maka alƙawarin yin maka biyayya da zama tamkar baiwa a gareka. Ina sonka duk abin da kake son xan yi maka Yayana." "Ba za ki taɓa samun zuciyata ba, domin na gaya miki tun farko baki cikin jadawalin matan da nake so. Sam ba ki yi mini ba, amm kika na ce sai kin aure ni. Ga gidan nan sai ki zauna a ƙarƙashin aurena, amma ni da jikina ba xa

Chapter 13 of 17