ya yi aure, amma abin gaba ya ci."
Dariya ta yi jin abin da ta ce."Wannan dalilin ya sa na ke son shi sosai."
Suna gama cin abincin kenan, ya kira wayarta tare da sanar mata da ya iso.
"Tashi mu je kar na barshi jira."
"Ki dai je in har kuna tare mantawa muke da kowa."
"To shikenan, tun da ba za ki je ba." Ta ce tana dariya.
A hankali take takunta cikin natsuwa kanta a ƙasa. Yana tsaye ya hangonta. Gyara tsayuwarsa ya yi, tare da zuba mata idanu, tamkar zai cinyeta har ta ƙaraso tana masa murmushi.
"Yayana," Ta ce tana kallonsa.
Yanayin fuskarta ya canza hannunsa ta kamo.
"Lafiya Ya Huwais?" Ta yi masa tambayar cikin damuwa.
"Mu samu guri za mu yi magana." Ya ce mata tare sakin hannunta.
Babu musu ta shiga gaban motar ya ja suka fara tafiya. Sun yi nisa sosai, babu wanda ya yi magana, sai ita da take satan kallonshi cikin damuwa.
Ajiyar zuciya ya saki mai ƙarfi wanda ya sanya ta kalle shi.
"Yayana, mai ke faruwa? Na damu da halin da kake ciki."
Bai ce mata komai ba, sai da ya yi parking sannan ya fito. Ganin haka ya sanya ta buɗe ƙofar ta fito.
Gurin wasu fararen kujeru suka samu suka zauna.
Kimanin ƴan sakanni sun zauna babu mai cewa komai.
"Hilah Abu ya gaya mini xai sanar da iyayen Hamad su kawo kuɗin aurenki."
Ras! Ta ji gabanta ya yi matuƙar faɗi. Miƙewa ta yi, yayin da hawaye ya wanke mata fuska.
Ganin razanar da ta yi ya sanya shi jin sanyi. Hannunta ya kamo ya xaunar da ita.
"Kina son Hamad?" Ya yi mata tambayar yana kallon ƙwayar idanunta.
Kallon da yake mata ya sa ta ji wani irin nauyi. Domin kalar idanun da ya canza ba ta taɓa hango hakan a ƙwayar idanunsa ba.
"Bana sonsa, amma kuma matuƙar xan samu saɓani da Ummu kan auren ba ni da xaɓi." Ta faɗi haka cikin rawar murya.
Ransa ya ɓace jin abin da ta ce."Kenan za ki sadaukar da kanki saboda farincikin Ummu? Karki manta rayuwar aure ana samun natsuwa ne, in har mutum ya auri xaɓin rayuwarsa. Ki duba halin da nake ciki tun da aka ɗaura mini aure ban samu kwanciyar hankali ba."
"Ya zan yi Ya Huwais? Ka san halin Ummu, ko soyayyarsa ita ta sanya na amince har na yarda da zan aure shi."
"Shikenan kin haƙura da mahaukacin masoyinki?"
Ɗago idanunta ta yi da sauri jin sunan da ya kira.
"Zan iya haƙura da shi tun da bai damu da ni ba. Zan yi wa Ummu biyayya na san cewa ba zan taɓa taɓewa. Mahaukacin masoyi ya cuce ni ya yaudare ni. Auren da zan yi shine kawai zan baƙanta masa rai. Ya san cewa ban rasa masoya ba. Hamad yana da nagarta kum...."
"Ya ishe ni! Ban zo nan don ki gaya mini nagartar sa ba." Ya katseta cikin fushi yana huci.
Shiru ta yi tana kallonsa tare da share hawaye.
Miƙewa ya yi, ya fara taku sai kuma ya tsaya ya juya mata baya.
"Na san wane ne mahaukacin masoy..."
"What!" Ta furta cikin tsananin razana tana kallonsa.
Yadda ta ruɗe ya firgita shi. Kama hannunta ya yi ganin ta fara kuka.
"Please, ki zauna mu yi magana na fahimta."
Zama ta yi hawayen na bin ƙuncinta."Haba Yaya, da kai xa a haɗa baki a ruguza farincikina. Dama ka san mahaukacin masoyi ya rinƙa wasa da rayuwata? Haba Yaya! Sam ban yi taɓa tunanin zaka yi mini haka ba why?" Ta ƙarashe maganar tana gurzar kuka.
Huwais ya yi shiru cikin tashin hankali yana kallonta. Irin tashin hankalin da ta nuna ya sanya shi ƙara shiga cikin damuwa sosai.
A koda yaushe gani yake tana ƙara son mahaukacin masoyi. Shin idan ta ji shine za ta so shi kamar haka?" Tambayar ya sanya cikin shi murɗawa.
"Mai ya sa aka haɗa baki aka cutar da ni?" Ta ƙara cewa ganin ya yi shiru.
"Waye shi? Waye wannan mugun azzalimi wanda ya yaudare ni? Na zaƙu da na san ko waye na ɗauki hukunci mai zafi a kansa.".
Miyau ya haɗiye da ƙyar, yana jin yadda maƙoshinsa ya bushe, babu ɗigon miyau.
"Yaya Huwais ka gaya mini wane ne?" Ta ce tana girgiza shi.
"Zan gaya miki, amma ki natsu mu yi magana ta fahimta." Ya ce bayan ya mayar da ita inda ta xauna.
Zama ta yi tana share hawayen da yake xubo mata.
"Tabbas Hilah na san shi. Abokina ne kuma yana matuƙar sonki. Saboda kyawunki da matsalar da yake hango ya kasa bayyana miki soyayyarsa. Saboda yana da hankali kuma ya dace dake shi ya sa na ƙyale shi, ya fito miki a matsayin mahuakacin masoyi don ya samu soyayyarki ya sanya ki bijire auren Hamad."
"Amma mai ya sa ya kasa bayyana kansa a gareni? Mai ya sa ya yi mini alƙawarin xamu haɗu ya ƙi zuwa?"
"Kamar yadda ya gaya miki, mahaifiyarsa babu lafiya za a yi mata aiki a ranar kuma zai sanya hannu."
"Saboda me ya kasa bayyana mini domin zan fahimce shi. Wannan ba hujja bace mai ƙarfi. In har zan iya yafe masa saboda kai ne, da kai ne don na san ba za ka taɓa yadda a haɗa baki a cuce ni ba."
Rintse idanunsa ya yi yana jin babu daɗi jin abin da ta ce.
"Ki yafe mini Hilah ba ni da zaɓin da ya wuce na samu soyayyarki ta haka."
"Na san duk abokananka don Allah ka gaya mini wanne ne daga ciki."
"Ba ki san shi ba Hilah, kamar sau ɗaya ya ganki a taron da kuka yi na musabaƙa tun daga ranar ya nuna yana sonki. Na ba shi shawarar ya fito miki ta wannan tsigar, saboda na san yana bayyana kansa za a dakatar da shi."
"Don Allah ka nuna mini hoton shi." Ta ce cikin zaƙuwa.
"Ba zai yiwu ba saboda ya roƙe ni kar na nuna miki."
Ɓata ranta ta yi jin abin da ya ce." To ya kamanninsa yake?"
"Shin idan kika samu miji mai irin surata da halina ya za ki ji?"
"Zan yi farinciki saboda samun miji kamarka, sai macen da Allah ya yi mata tagomashi. Shi yasa kullum na ke ganin Anty Wajnah a mace mafi sa'a da ta same ka."
Jin abin da ta faɗa kansa ya fasu. Ji ya yi kamar ƙasa ba za ta iya ɗaukarsa ba.
"To ki ayyana surarsa da haliinsa kamar ni, amma kuma ni na fi shi sonki." Ya ce cikin murmushi.
Dariya ta yi cikin farinciki."Aiko na samu mijin aure in har kamanka yake."
"Ba ki da kunya Hilah a gabana kike wannan murnar ko?"
Rufe fuskarta ta yi tana dariya."Amma abokin nan na ka ya cutar da xuciyata."
'Ki yi haƙuri xai bayyana kansa ba da jimawa ba. Yanzu wane shawara kika yanke game da auren Hamad."
"Zan fito fili na gaya wa su Ummu akwai wanda na ke so."
Gabansa ne ya faɗi tuna in har aka ce ta kawo shi ya xai yi.
"Yauwa ƙanwata, karki bari Ummu su yi miki auren dole kamar yadda aka yi mini."
Yadda ya yi maganar ya ba ta dariya."Ya Huwais, ka amshi Anty Wajnah a matsayin mata ku zauna lafiya. In Allah ya sa wacce kake so matarka ne sai ka aureta."
"Ba za ki gane yadda zuciya take ƙuntata ba, yayin da mutum ke zama da abin da ba ka so."
"Na fahimta, amma ka yi mata adalci ko don zumuncin da ke tsakaninku."
Shiru kawai ya yi, bai ce mata komai ba sai ya nisa ya ce,"Ki rinƙa ɗaukar kiransa, kuma ku koma kamar da in sha Allah zai bayyana kansa a lokacin da ya kamata."
"To Yaya." Ta faɗa tare da miƙewa ta maƙala jakarta, ganin shi ma ya ɗauki wayarsa ya miƙe.
Tafiya suka fara yi har suka isa mota suna hira. Daga nan makaranta ya ije ta hankalinsa ya ɗan kwanta, ganin yadda take matuƙar ƙaunarsa, ya san ba za ta yadda ayi mata auren dole ba.
Wajnah kuwa bayan ta shiga cikin ɗaki tana kuka, wayarta ta ɗauka tare da danna kiran numbar Mommy, ta zayyane mata ƙarya har da gaskiya.
Ranta ne ya ɓaci sosai ta shiga rarrashinta.
"Ki kwantar da hankalinki yanzu zan kira mahaifiyarshi, don ba xan lamunta ya rinƙa dukanki ba, daga yin aure ai ba jaka na auro masa ba."
Bayan ta kashe wayar cikin fushi ta danna layin Ummu ta zayyane mata.
Matuƙar mamakin marin da ya yi mta ya kamata.
"Ki yi haƙuri kin barni da shi xai gane ba shi da wayo."
Tana gama waya da mommy ta kashe wayar tare da neman layinsa.
A lokacin da ta kira, yana kan hanyar dawowa da ga makarantar su Hila. Ganin kiran gabansa ya faɗi amma ya daure ya ɗauka.
"Huwais, ashe ba ka da hankali? Amaryar da ko sati ba ta rufa a gidanka ba za ka dake ta."
Ransa ya ɓaci jin abin da ta ce."Umm.."
"Ma za ka zo gida ina nemanka." Ta furta cikin ɓacin rai tare da daƙile wayar.
Wayar ya bi da kallo cikin ɓacin rai, yana tunanin abin da zai yi mata don ba zai lamunta, ta rinƙa haɗa shi da Ummu ba.
Juya motar ya yi zuwa gida. A falo ya same ta, zaune ta haɗe girar sama da ƙasa tun da ta ji shigowar motarsa.
Ganin yadda ta sha kunu, ta amsa sallamar ba tare da ta kalle shi ba, ya sanya gabansa ya faɗi.
Zama ya yi cikin sanyi jiki tare da gyaran murya ya ce,"Ummu ga..."
"Ashe ba ka da hankali? Kan me za ka daki Wajnah?" Ta katse shi cikin ɓacin rai tana faɗin haka.
"Ummu, k..."
"Ba ka da hujjar da za ka kare kanka da shi. Kuma ka ji na rantse maka wannan ya xama na farko na ƙarshe da za ka kai hannunka jikinta. Sannan a matsayina na mahaifiyarka, ina umurtarka da ka karɓe ta a matsayin mata ka sauke duk haƙƙinda ke kanka, matuƙar ka ƙi yin hakan za ka fuskanci fushi mai tsanani. Kan auren nan matuƙar ba ka cire banzar tunanin da kake yi ba, kun zauna lafiya zan iya maka mummunar lafazi, domin ba zan bari a cikin dangina ana yamaɗiɗi da ni, cewar ban isa da ɗan cikina da na haifa ba"
Kansa ya ɗago da sauri cikin tashin hankali jin hukuncin da ta yanke.
"Amma Ummu sam ba a yi mini adalci ba na gaya miki bana..."
"Ai bakin alƙalami ya bushe, tun da aka ɗaura aurenku, ba ka da wani xaɓi da ya wuce ka zauna da ita."
Miƙewa ya yi, cikin damuwa xai fice sai ya ji ta kira sunanshi.
"Huwais, wannan ya xama magana ta ƙarshe kan aurenka. Kar na ji kuma kar ta ƙara kawo mini ƙararka."
Ƙarashe ficewa ya yi cikin ɓacin rai zuciyarsa na tafasa.
A hanya tafe yake, yana tunanin abin da Hilah ta gaya masa. Tabbas Allah ya ba shi damar da xai iya auren mata har huɗu, amma ba ya jin zai iya karɓar Wajnah a matsayin mata. Kalaman da Ummu ta gaya masa, suka ƙara rikita ƙwaƙwalwarsa har ya gaza tunanin mafita.
A lokacin da ya isa gida. Ƙarasa shiga cikin dakin yana huci tamkar mesa."Da ma kin aure ni ne don ki haɗa ni da iyayena?" Ya yi mata tambayar cikin fushi yana tsaye a kanta.
Raurau ta yi da idanunta tana kallonsa."Don Allah kar ka yi mini mummunar fahimta, wallahi ina sonka Ya Huwais."
"Ki ji daɗi kin haɗa ni da mahaifiyata. Ki sani ko zan zauna da ke bisa umurnin mahaifiyata ce, amma bana sonki kuma babu soyayyarki a zuciyata."
Miƙewa ta yi, cikin sanyin jiki tana jin ɗacin kalmar bana sonki, da yake gaya mata.
"In har na ci albarkacin Ummu, zan yi farinciki na sam watarana za ka so ni."
"Kin yaudari kanki domin ba zan taɓa ƙaunarki ba." Ya ce tare da wucewa fuu zuwa ɗakinsa.
Jaɓar ta xauna kan kujera, tana jin babu daɗi yadda yake gaya mata ya tsaneta. Hawayen da ke zuba a ƙuncinta, ta share tare da miƙewa zuwa ɗakinta.
Wayarta ta fara ƙara alamun ana kira. Ganin kirar Ummu ce ya sanya ta ɗauka da sauri ta shige cikin ɗakinta.
Bayan ta ɗauki wayar ta yi sallama ta gaishe ta.
"Ki na jina Wajnah? Dole sai kin yi haƙuri tun da kin san dole aka yi masa. Ki daina rashin kunyar da kike masa sannan ki zama mai biyayya, cikin sauƙi za ki mallake shi a hannunki. Ita wacce yake son hauka yake yi, saboda ko mutuwa zau yi don sonta ba zai aureta ba."
Mamaki ya kamata, domin ba ta taɓa sanin Ummu ta san wacce yake so ba.
Ajiyar zuciya ta yi jin abin da ta ce take hankalinta ya kwanta.
"Ba ya cin abincina kulle ɗakinsa yake yi da na shiga yake koro ni." Ta ƙarashe maganar cikin kuka.
"Kar ki damu ki yi masa girkin, kuma ki shirya kinje ɗakinsa, na yi masa mummunar lafazi matuƙar ya ƙi kula ki."
Zuciyarta fes ta rinƙa murna tana gode wa Ummu.
"Duk abin da xai yi miki karki kula shi ki yi masa biyayya kin ji?"
"To Ummu," Ta ce tare da kashe wayar tana tsallen murna.
Miƙewa ta yi cikin farinciki, ta shiga kicin ɗin, tana kallon ƙaton kicin da aka cika shinda kaya.
Tunanin abin da za ta girka masa ta yi. Buɗe frij ta yi ta ɗauko naman kaza ta kunna famfo don ta saki.
Cikin farinciki take yi masa tuwon shinkafa da miyar taushe. Bayan ta kammala ta koma ta dafa masa farfesun kan rago.
Ɗaki ta koma ta yi wanka ta sanya kaya masu kyau.
A lokacin da ta fito falo shi kuma ya fito don ya je sallar isha'i. Kallonsa ta yi cikin shauƙin ƙauna tana wani tafiya tana yauƙi.
Ko inda take bai kalla ba ya wuce zuwa massalaci. Ganin haka ita ta miƙe cikin gaggawa ta yi nata sallar sannan ta fito tana jiran dawowarsa.
Bayan an idar da sallar zama ya yi, yana tunanin umurnin da Ummu ta yi masa, domin bai san ta yadda xai ɗauke ta a matsayin matarsa ba.
Mace ɗaya kawai yake so kuma yake burin ya yi rayuwar aure da ita. Ita ce wacce yake ganin duk ji da kansa da yake yi, zai xama bawa matuƙar xai mallaki zuciyarta, amma kuma ba zai iya bijirewa umurnin Ummu ba.
Miƙewa ya yi, ya kulle masallacin sannan ya shigo cikin gidan. Zuciyarsa na yi masa nasihar ya bi umurnin mahaifiyarsa.
Jin alamun buɗe ƙofa, ya sa ta miƙe da sauri ta ƙarasa gurin ƙofar don ta buɗe masa, dama ta kulle ƙofar saboda ta san lokacin da xai shigo.
Buɗe ƙofar ta yi da murmushi a fuskarta."Barka da dawowa farincikin rayuwata." Ta faɗa cikin wani irin murya yayin da ta matsa kusa dashi kamar xa ta rungume shi.
Karo na farko ya yi mata kallon tsanaki, domin tun lokacin da ta fara nuna maitarta a fili ya ji babu wacce ya tsana fiye da ita, kuma tun daga lokacin bai ƙara yi mata kallon da xai gane yadda take ba.
Ganin ya kalleta ya sanya ta ƙara matsowa kamar xa ta shiga jikinsa.
Ya buɗe baki da nufin ya magana, amma sai ya ji ya gaza furta kalami.
Wucewa ciki ya yi, ba tare da ya ce mata komai ba, wanda ganin haka ya sa ta bishi zuwa ɗakinsa.
"Ya Huwais, na kawo maka abincin ka ɗaki?" Ta yi masa tambayar tana ƙarasowa inda yake xaune.
Ƙara ɓata fuska ya yi tare da kauda kai.
Kusa da shi ta isa ta rage tsawo."Don Allah Ya Huwais ka ji abincin nan, horas da kanka da yunwa babu abin da zai jawo maka sai cuta."
"Bana buƙata." Ya furta a gajarce yana kauda kansa.
Shiru ta yi take ranta ya ɓace, ganin duk wahalar da ta sha ya tashi a banxa. Idanunta suka ciko amma sai ta jure ta fita daga cikin ɗalkin
"Haƙiƙa duk macen da take son wanda ba ya ƙaunarta, tana cikin jarrabawa." Ta furta hakan tare da warware ɗaurin ɗankwalinta cikin takaici.
Har ta ɗauki waya xa ta kira Ummu, sai ta fasa ta wanke fuskarta, da ruwan hawaye ya gama jiƙata ta gyara kwalliyarta.
Numbar Wahida ta lalubo tare da danna gurin kira,"Hello," Sai kuma ta fashe da kuka."
Cikin takaici Saboda ta zabga tsaki daga cikin wayar ta ce,"Na gaya miki zuba mishi maganin yaci shi kawo zai karkato da hankalinsa gareki. Ki cire tsoro da tunanin komai. Mijinki ne kuma in ba ta haka kika yi masa ba, wannan mutumin ba zai lalle ki ba."
"Ba ya sona ya tsane ni. Ban san ya zan yi ba." Ta ƙarshe maganar cikin kuka tana wurgi da filo.
"Na gaya miki abin da za ki yi kenan, wanda zai jawo hankalin sa gareki, amma kika tsaya kallon ruwa har kwaɗo zai yi miki ƙafa. Maganin yana da ƙarfi, don sai ya raina kan sa."
"Ok, na gode." Ta furta tare da ije wayarta kan dressig mirror.Kayan bacci ta sanya ta koma ɗakinsa.
Bayan fitarta ya bi ta da kallo yana son ganin inda ta gaza, amma ya san Wajnah tana da duk abin da ɗa namiji yake so a jikin mace. Shi kawai babu soyayyarta a cikin zuciyarsa.
Yana wannan tunanin ta murɗa ɗakin sai ta ji a kulle. Fara bugawa ta yi tana kiran sunansa.
Har ya yi banxa da ita sai ya tuna umurnin Ummu. Da sauri ya miƙe tare da buɗe ɗakin ya tsaya a bakin ƙofar ta yadda ba za ta iya shigowa ba.
"Lafiya?" Ya yi mata tambayar fuska a ɗaure.
"Ummu, ce ta ce na shigo na kwanta in kaƙi buɗe ƙofar na kira ta."
"Ke zan yi mugun ɓata miki rai, matuƙar za ki rinƙa haɗa ni da iyayena." Ya faɗa cikin ɗaga murya.
"Ni fa bani na kirata ba ita ta kira ni yanxu, kuma ta ce za ta ƙara kira."
Matsawa ya yi ta wuce yana faɗin,"Ga ɗakin nan sai ki cinye."
TO MASU KARATU.. AN CE LAIFIN DAƊI ƘAREWA.LITTAFIN RANAR WANKA... BOOK ONE YA ƘARE SAI MU HAƊU A BOOK TWO.
Mai ke faruwa ko na ce mai ya ke shirin faruwa?🙄🙄🙄🙄🙄🙄🙄🙄🙄
Wajnah na yin nasarar sace zuciyarsa har ya maida ita cikakkiyar mace? Ya kuma manta da HIlah a rayuwarsa?
Mai ya sa Huwais ya ke jin kamar Hilah za ta iya zama matarsa?
Wai ku tsaya masu karatu. Hilah dai ƴar Ummu ce ta uku, saboda me Huwais zai rinƙa tunanin ba yar uwarsa bace?
In har ta gane shi ne mahaukacin masoyi ya za ta yi, kuma wane mataki za ta ɗauka?
Shin in Wajnah ta gane Hilah ce wacce ya ke so kuma yake wulaƙanta ta saboda ita. Wane mataki za ta ɗauka?
Soyayyar da suke yi wa junansu zai ɗaure bayan ya bayyano sirrin da zai canza rayuwarta? Duk da cewa ranar wanka, ba a ɓoyen cibi.
To ita ɗin wace ce kuma su waye iyayenta? Sannan mai ya faru ta shigo cikin rayuwarsu?
Shin zai yi nasarar mallakarta a matsayin mata, kuma ya rayuwar aurebsu xai kasance? Hilah za ta zauna da shi a matsayin miji, ko kuma a matsayin ƴaƴanta za ta ɗauke shi?
Huwais zai ɗauke idanunsa a kanta ya zauna da ita ba tare da ya amshi sadakinsa ba? Ko.kuma girma ne zai fadi ya yi rayuwar aure da ita?
Ina Wajnah mai kishin mijinta da sha maganin mata? Za ta iya barin mata Huwais ko kuma za ta zauna a fafata zaman kishinda ita? Sannan burinta zai cika na fatan ya mallaka mata kansa su zamo abu ɗaya?
Ya rayuwarta xai kasance in har ta cigaba da shan maganin mata?
Shin za ta daina sanar da ƙawayenta rayuwar aurensu ko kuma za ta ci gaba?
To ku sha kuruminku domin duk amsar tambayarku. Yana cikin littafin book two wanda yake paid kan Naira 500 kacal, in kuma aka gama ya zama complete 600 wanda Jamsy ƴar baiwar mai son faranta muku ba ta bar amsar tambayoyinku ko ɗaya ba, domin ta wasa ƙwaƙwalwarta ta bayyana muku har abi n da ba kubsani ba.
labarin cike yake da rikita-rikitar soyayya da tausayi haɗe da jimami da shakwakiya. Ma za ku garzayo ku biya don ku karanta. Kar ku bari a baku labari, domin ya tsari kuma akwai soyayya mai tsuma zuciya. Ƙayataccen littafin naira 500 ne kacal, amma in aka gama rubuta shi 600 ma za ku garzayo ku biya don ya ɗebe muku kewa.
Duk wacce ta shirya biya sai ta tura kuɗin ta a wannan asusun
8144072423
Jamila lawal opay
Sannan a tura shedar biya ta waɗannan numbar nan. 08144072423
FOR WHATSAPP: 07072971093
CALL: 08144072423
Ga masu buƙatar turo katin waya sai ku tura ta wannan numbar 08144072423
Ko kuma wannan 07072971093 a Turi da sheda ta ɗaya daga cikin wannan numbar ta Whatsapp.
Shin kin karanta littafin "SAKACINA KO HALIN MAZA" ko kuma "KURA DA FATAR AKUYA"? In har ba ki karanta ba ma za garzayo ki siya kan naira 600 kacal dob ki more karantunki. Labarine masu daɗi da darasi a cikin su, wanda shararriyar marubuciyar na . Jamila Lawal Zango
Jamsy
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 17 Chapter of 17