bangarensa, amma suka buƙaci su sanya masa kayan.Kaya ne na gani na alfarka aka yi.
Kasancewar mahaifin Wajnah shahararren ɗan kasuwa ne, da yake da shoping mall da yawa a garin Abuja. Ya yi bajinta sosai gurin yin mata kayan, musamman da take ita ce ƴa ta farko da zai fara aurarwa.
Mahaifiyarta ma ba a barta a baya ba, saboda ita ma tana business na atamfa less sa sauran kayan amfanin mata.
Haƙiƙa gidan ya tsaru matuƙar gaske.
Ya rage saura sati ɗaya biki hankalinsa ya tashi matuƙar gaske! Domin abu biyu suka haɗe masa tare da rikita ƙwaƙwalwarsa.
Cikin dare sam baya bacci, yana tunanin rayuwar da zai yi da Wajnah da kullum ƙara tsanarta yake a cikin zuciyarsa. Sannan ga shi Hilah ta takura masa kan yazo bikin. Abin duniya sun haɗu sun yi masa yawa. Gabakiɗaya ya rame ya fita hayyacinsa, wanda ya tsorata iyayensa, amma kuma hakan shi ne kawai zai kawo maslaha.
Wata shawara ta bijiro masa take ya amince da zai zo. In ya so ranar ɗaurin auren sai ya yi mata wani ƙaryar. Duk da ya san cewa za ta yi fushi dashi mai tsanani, amma ba za ta iya rabuwa da shi ba, saboda kamar yadda yake jin sonta a cikin zuciyarsa, ya tabbata tana jin kwatankwashinsa duba ga yadda take gaya masa yadda ta damu da shi, kuma ya san Hilah ba za ta taɓa gaya masa ƙarya ba.
Hilah tsaye a kicin tana dama kunun gyaɗa da ta ke son ta kai masa. Har cikin zuciyarta tana matuƙar tausaya masa domin rashin masoyi babu daɗi. Tana ji a ranta yadda take son mahaukacin masoyinta, matuƙar aka raba ta da shi za ta iya shiga kwatankwacin halin da yake ciki.
Bayan ta dama masa kunun ta ɗauka ta nufi sashinsa. Yana kwance da waya a hannunsa. Hotonta yake kallo yayin da hawaye suka taru a gefen idanunsa.
Ƙwaƙwansa ƙofar ta yi tare da kiran sunansa wanda ya yi maza ya aje wayar.
Yana buɗewa suka zura wa junansu idanu.Tausayinsa da damuwa da halin da yake ciki suka ƙara kamata
Tsayawa ta yi cikin yanayi na jimamai, sai kuma ta ɗauke idanunta ganin ya ƙi cire nasa.
"A haka za ka yi angwancin?" Ta yi masa tambayar cikin tausayi.
Ƙaramin tsuka ya ja jin tambayar da ta yi masa.
"Ya Huwais, ka ga yadda ka koma? Dubi gashin ƙasumba da ka tara. Don Allah ka cire komai a ranka ka yi addu'a kar ka janyo wa kanka cuta mu shiga uku."
"Ina jin zuciyata tana zafi! Ummu ba za ta gane ɗacin da na ke ji ba, saboda auren soyayya ta yi da Abu. Hilah, Ummu ta gama kashe mini farincikin rayuwata tun da ta hana ni da wacce zuciyata ba ta muradinta."
"Please, ka daina faɗin haka. Aurenku sai family ɗinmu sun yi alfahari da shi. Anty Wajnah na da kirki ba za ka yi dana sanin zama da ita, kuma Ya Huwais, Allah ya ba ka damar ƙarin aure, in har ka samu damar auren wacce kake so za ka iya ƙara aure."
"Ta yi mini nisa ba za ta aure ni ba, amma na san sonta shi ne ajalina."
"Ka so abin da ka san za ka samu ba wanda ba za ka samu ba. Na ce ka gaya mini inda take zan je na gaya mata yadda kake son ta na kuma roƙe ta ta aureka."
A ransa ya ce,"Ke ce Hilah! Kece wacce zuciyata take mafarkin samu a matsayin mata, amma kuma ba zan taba mallakarki ba."
A fili kuwa zura mata idanu ya yi, wanda ya sanya ta ɗauko kunun gyaɗar ta iba ta miƙa masa a baki.
Kauda kansa ya yi, yana faɗin,"Ba na jin ɗanɗanon abinci na rasa ɗandanon bakina."
"Ka ci kar ka yi wa kanka horar yunwa."
Babu musu ya karɓa jin abin da ta ce. Yana cikin sha su Abidin suka shigo.
"Yauwa Hilah, dama neman ki muke a cikin gida. Tun ɗazu muka kawo masa break amma ya ƙi ci. Yaya yana son ya yi mana asarar kansa, bayan ya san in har babu shi ba zamu iya rayuwa." Affan ya ce tare da zaunawa a gefensa
Tausayin ƙannin na sa ya kamashi ganin yadda suka nuna tsantsar damuwarsu.
Hankalinsu bai kwanta ba, har sai da ya shanye tas! Hilah ce ta miƙe don ta gyara ɗakinsa.
"Bari muje zamu karɓo ɗinki mu a gurin tela. Hilah ki kula da shi."
Murmushi ta yi tare da ɗaga kanta ta ci gaba da gyara falon.
Tana aikin duk ta ɗago idanunta sai ta ga yana kallonta.
"Gaya mini Hilah in har mahaukacin masoyi ya bayyana yana da mata zaki aure shi?"
"Mai yasa ka tambaya Yaya?"
"Saboda ni ma na gane, in har wacce nake so ta ji ina da mata za ta iya aurena." Ya ba ta amsa jin tambayar da ta yi masa a maimakon amsar wace ya yi mata.
"Eh, zan iya aurensa saboda ina matuƙar sonsa, in har zan auresa matuƙar ya cika duk sharuɗan da ya kamata na aure shi a addini ban damu ba."
Labarin ya zo da wani irin salo da nishadi, karku baru a ba ku labari. Ku biyo ni domin it’s just like a little introduction part, and guess what? You will really enjoy it. Believe me, my dear readers. Your happiness is my concern. Follow me on Facebook, Whatsapp, Wattpad, Arewaboo, and Bakandamiya. Ta ku, Jamila Lawal Zango (Jamsy).
FOR WHATSAPP: 07072971093
CALL: 008144072423
*RANAR WANKA...*
NA
JAMILA LAWAL ZANGO
"JAMCY"
☀️ *First Class Writers Asso* ☀️
Hame of Qualities And Trusted writer's of The Nation
*GARGAGAƊI*
Ban yarda kuma ban amince a juya mini labari ko ta wace siga ba, sannan ban bada lamuni a ɗora mini littafi a kowane kafar sadarwa ba sai da izinina a kiyaye⚠️
JAN HANKALI
Kirkirarran labari ne ban yi shi don wani ba, idan har ya yi daidai da labarin ki/ka to arashi ne.
SADAUKARWA
Kacokam labarin daga farkonsa har karshe sadaukarwa ne ga ƙawata sahibata Aysha Na Lado. Allah saka miki da alkairi ya raya zuri'a.
PAGE 15
BISMILLAHIR RAHMANINR RAHIM
"Gaya mini Hilah in har mahaukacin masoyi ya bayyana yana da mata zaki aure shi?"
"Mai yasa ka tambaya Yaya?"
"Saboda ni ma na gane, in har wacce nake so ta ji ina da mata za ta iya aurena." Ya ba ta amsa jin tambayar da ta yi masa a maimakon amsar wace ya yi mata.
"Eh, zan iya aurensa saboda ina matuƙar sonsa, zan auresa matuƙar ya cika duk sharuɗan, da ya kamata na aure shi a addini ban damu ba."
Da fari murmushin jin daɗi ya yi, amma da ya ji ta ce sharuɗa, sai ya tuna da matsayinsa a gurinta, wanda ya faɗar masa da gaba.
Ba tare da ya ce komai ba, ya kwanta a kan kujera bayan ya ɗora filo a samar ƙirjinsa.
Bayan ta gama gyaran ɗakin ta ja masa ƙofa ta fice ganin bacci yake yi.
Ya rage saura kwana biyu biki, Hilah ta cika da matuƙar murna. Shirye-shiryen haɗuwa fa mahaukacin masoyi take ta yi.
Ta je ta gyara kanta, ta yi ƙunshi mai matuƙar kyau. Sannan har dilka ta sanya aka yi mata. Duk lokacin da ta shigo masa tana murnar zasu haɗu da mahaukacin masoyi sai hankalinsa ya ƙara tashi.
"Yaya, zan ɗauko maka hotonsa, na san zai kasance kyakykyawa kamar kai." Ta furta mishi lokacin da take bashi indomie da ta dafa masa.
Murmushin yaƙe kawai ya yi masa, amma yama jin babu daɗi sosai.
"Ya ce zai gaya mini sunan shi, kuma na san cewa sunan yana da daɗi. Ni fa ina jin kamar na sanshi, domin na tana zuwa gasar musabaƙa ƙawata ta ce wani matashi ya tambaye ta sunana da inda nake. Jikina yana ba ni shi ne."
"Huhm!" Ya ce cikin damuwa yana mata kallon tausayi.
Miƙewa ta yi ta ce,"Yaya, bari na je na yi wanka. Za muje walima gidan su Anty Wajnah."
Ɗaga mata kai ya yi ta fice tana ɗaga masa hannu.
Siraran hawaye masu tsananin zafi suka wanke masa fuska." Haƙiƙa na zama mayaudari, kuma na biyewa zuciyata na sanya ƙanwata cikin wani yanayi. Ban san ya ya za ta ji ba, in har na ƙi zuwa." Ya furta maganar cikin nadama da damuwa.
"Ka yi kuskure Huwais, tun farko sai da na gargaɗe ka da hakan, babu abin da zai haifar sai ɗa mara ido." Amin ya furta cikin wayar ransa a ɓace.
"Ban san ya zan yi ba Najib, ko na yi ninyar daina kiranta, sai na ji ba zan iya rayuwa ba in ban ji muryarta ba." Ya furta jin abin da ya ce.
"Ka daure ka karya layin, sannan ka daina kiranta ka rungumi matarka da za a aura maka. Wajnah na da kyau za ka sota. Sheɗan ne ke yi wa rayuwarka ingiza mai kantu don ya kai ka duniyar nadama."
"Kana da gaskiya Najib! Kuma in sha Allah zan bi shawarar ka." Ya ce tare da rintse idanunsa da suka yi masa nauyi.
Rana ba ta ƙara, sai dai uwar ɗiya ta ji kunya. A yau ranar Juma'a ya kasance family ɗin gidan Alhaji Nadabo suke cikin matsanancin farinciki. Ganin dubban mutanen da suka fara zuwa don halarta bikin Huwais da Wajnah.Kowa fuskarsa ɗauke da farinciki. Gurin ya cika maƙil da manyan mutane. A masallacin Juma'a za a ɗaura auren, daga nan sai a wuce gurin cin abinci.
Abu zuciyarsa fara ƙal tamkar gonar auduga. Sai haba-haba yake da mutane yana tarbarsu cikin karamci.
Ummu kuwa tafi kowa murna, domin ji take babu wanda ya kaita farinciki. Tun safiyar sai dai kawai ta ji hawaye sun zubo mata na farinciki. In ta tuna dargar da ya sanya ta da tashin hankalin da ta fuskata kafin bikin, da ƙalubalen da ya rinƙa faruwa sai kawai ta zube ta yi sujjada shukuriya. Shikenan daga yau ta huta Huwais ba xai ƙara sata damuwa ba, don ta gama yadda sha'awace take damunsa wanda kuma ya ɗora kan ƴar'uwarsa.
A ranta duk ta ƙosa a ɗaura auren ya tattara ya bar mata gidanta.
Najib ne zaune a cikin ɗakin Huwais, da sauran abokanansa suna ta fama da shi ya shirya, za su inda suka kama don masaukin baƙinsu bayan ɗaurin auren amma ya ƙi.
Cikin ɓacin rai Taufiƙ ya kalle shi,"Wannan abin da kake yi sam ba ka kyautawa Huwais, ni wallahi zan iya yarda da aljana da aureka, saboda babu yadda za a yi ka kai har wannan lokacin baka yi aure ba." Ya tsagaita ko zai ce wani abu, amma sai ya ga ko kallon arziki bai samu ba.
"Please, ka tashi."
"Ka barni domin babu inda zan je."
Caa suka yi masa ganin ya ƙi tashi ya yi wankan ballanatana su sanya ran za shi.
Banza ya yi dasu, yana ta tunanin halin da Hilah za ta shiga, in har ta kira wayarsa ta ji a kashe, domin saura minti talatin lokacin da suka sanya za su haɗu ya cika.
Ganin sun kaɗa sun raya, amma ya ƙi tashi sai Najib ya kalle su ya ce,"Ku ƙyale shi na san wanda za ta sashi ya yi wankan."
Wayarsa ya ɗauko tare da fara neman numbar ta. Huwais ya ɗauka Ummu ce har zuciyarsa ta fara bugu.
"Yauwa, ƴar halak ƙin ƙi ambato." Ya furta lokacin da ya ji muryar Hilah na yin sallama.
Jin an bata damar shigowa ya sa ta shigo cikin natsuwa.
Gabakiɗaya idanunsu suka hau kanta. Wani irin tsau ta ji tare da kunya ta lulluɓe ta.
Kanta ta duƙar ƙasa cikin sanyaruar murya ta gaishe su.
"Wow! Huwais ƙiri-ƙiri ka hana ni auren ƙanwar nan na ka." Ya furta yana mata kallo tamkar zai cinyeta.
Zumbur ya miƙe cikin ɓacin rai ya ce,"Ba na hanaki shigowa ba in na yi baƙi?"
"Ka yi haƙuri Yaya, zan tafi ne kuma ina ta kiran wayarka ba ka ɗaga ba."
Muryarta ba shi kaɗai ba, duka mutanen ɗakin sai da ta ɗauki hankalinsu.
Sai a lokacin ya tuna wayarsa, na cikin bedroom ɗinsa, tun safe da Wajnah ta kira ya yi wurgi da wayar.
Hannunta ya ja cikin tsananin jin haushin yadda suke kallonta. Bedroom suka shiga.
"Kai anya na taɓa ganin mace mai kyau irin ƙanaar Huwais?" Adnan ya faɗa shakku.
"Dole ya rinƙa kishinta sosai. Wannan fulawar tun da babu aure a tsakaninsu, dole ya kula da wanda zai ba shi ya amanarta." Sudais ya ce.
"Yayana, zan tafi saura minti ishirin mu haɗu da mahaukacin masoyi."
Idanu ya zura mata na tsawon lokaci ya kasa cewa komai. Kwalliyar da ta yi da kyaunta, suka tafi da imaninsa. Ji yake kamar ya rungumeta ta rarrashe shi.
"Har kin yadda da shi, da ya ce zai zo? Gani nake kamar yaudararki yake yi. Kuma in har da gaske yake yi gida ya kamata ya zo. Ki haƙura da shi ki manta shi a cikin rayuwarki."
Raurau ta yi za ta yi kuka, sam ba ta son ya hana ta tafiyar."Don Allah ka barni na je, ni da Afrin zamu. Kasan Ummu ta hana ni kula sa, matuƙar ta ji ina tare da shi ranta zai ɓace."Ta ƙarashe maganar tare da kama hannunsa.
"Ok, ni ban ce kiyi mini kuka ba." Ya ce yana xare hannunsa.
"Yauwa Yayana, sai na dawo. A ɗaura aure lafiya."
Tsaya ya yi, tare da zura hannunsa a cikin aljihun wandon, kayan baccin da yake sanye da su ba tare da ya ce mata komai ba.
Har ta buɗe ƙofar za ta fita, sai kuma ta tsaya tare da ƙare masa kallo.
"Yayana, ango sukutum guda bai yi wanka ba?"
Ɓata fuska ya yi, jin abin da ta ce tare da gyara tsayuwarsa.
"Yauwa, gara ki san ya shi ya yi wankan, domin tun ɗazu muke fama da shi, ga kayan shi can wanda Affan ya kawo ya ƙi sakawa." Cewar Najib da ya shigo.
Ɓata fuska ta yi tare da kama hannunsa."Don Allah ka yi wanka..."
"Je ki kar ki ɓata masa lokaci kinga lokaci ya kusa."
"Pleas.."
"Hilah, ki je na yi miki alƙawarin zan yi."
"Promise?"
"Sure," Ya ce mata to sai ka shiga bari na haɗa maka ruwan wankan.
Da sauri ta nufi bayinsa, wanda ko minti uku ba ta yi ba ta fito.
"Yayana, na haɗa maka. Ka yi mini addu'a zuciyata na bugu."
"Fatan alkhairi sis." Ya furta cikin wani irin yanayi.
Ba tare da ta kula ba ta fice da gudu.
Kallon ƙofar da ta fice suka yi." Ka cutar da yarinyar nan Huwais! Shin me kake tunanin za ta ji in har ba ta gan shi ba?"
"Za ta ji babu daɗi na yi kuskure, amma yanzu zan tura mata da tsaƙon haƙuri, kuma ba zan ƙara kiranta ba."
"Hakan shi yafi,"
Da ya shiga cikin bayin sai ya tura mata da tsaƙo kamar haka;
Ina ba ki haƙuri bisa laifin da na yi miki. Haƙiƙa na cutar dake, amma soyayyarmu ba za ta yiwu ba.In a roƙon ki yafiya don a yau zan bar Ƙasar nan ki yafe mini na ɓata miki lokacin da na yi. Sai dai ina son ki sani ina matuƙar ƙaunarki daga Muhammad na ki.
Sai ya tura hoto wanda daga baya ya goge.
Wayar ya ije cikin ƙunci sai kawai yaji hawaye na zubar masa a ƙunci.
"Da gaske ba zan auri Hilah ba za ta zamo mallakin wani? Innnalillahi wa inna ilaihir raju'un!" Ya furta a cikinn zuciyarsa.
Wankan ya yi, sannan ya shirya cikin tsadaddiyar shadda. Haƙiƙa ya yi kyau duk da ramar da ya yi bai hana shi kyawu ba.
Yana shiga cikin gidan, abokan wasa suka yo kanshi wanda ko murmushi ya kasa yi musu.
A mota Hilah da take tuƙi cikin rashin natsuwa ta waiwayo ta kalli Afrin ta ce,"Har yanzu gabana faɗuwa yake yi, ji na ke kamar a mafarki zamu haɗu, da mahaukacin masoyina. Ko ya ya haɗuwarmu zai kasance? Ina fatan wannan haɗuwar ya zama sanadin da zai jagoranci zamanmu a inuwa ɗaya."
"Amin," Afrin ta ce cikin zaƙuwa, domin ta ƙosa ta ganshi wanda ya sanya ta fara samun saɓani da ƙawarta.
Parking suka yi ta tsaya tare da fitowa. Ganin babu motarsa a inda suka yi za su haɗu ya sa ta jingina da motar ta ɗan bashi lokaci ƙila yana hanya.
Minti goma sha biyar bai iso ba, sai ta ɗaga waya don ta kira shi. Gabanta ya faɗi jin wayar a kashe, saboda ko da safe sun yi waya.
Datar wayarta ta kunna, tare da shiga Whatsapp don ta yi masa magana. A nan ta tsinci tsakonsa da sai da ta yi taga-taga za ta faɗi Afnan ta riƙe ta.
Hawaye shar! Suka wanke mata ƙuncinta. "Innalillahi wa inna ilahir raju'un!" Ta furta tare da dafe kanta da take jin juya na ibanta.
"Lafiya Hilah?"
"Don Allah ki riƙe ni kar in faɗi."
Da sauri ta kamata, ta buɗe murfin motar ta shigar da ita, ganin yadda take haƙi kamar wace ta yi gudun famfalaƙe.
"Wayyo Allahna!" Ta furta tare da rushewa da kuka.
"Lafiya, don Allah ki yi mini bayani."
"Mayaudari ne mahaukacin masoyi! Ya turo mini da tsaƙon, na manta da shi a rayuwata zai bar ƙasar."
Jikin Afrin ya yi sanyi, har ta kasa cewa komai, musamman yadda ta ga ta ruɗe matuƙa ta fita hayyacinta.
"Don Allah ki natsu, ni dama tuntuni zuciyata ba ta aminta da shi ba, saboda bai kamata ki mallaka masa zuciyarki ba tare da haɗuwa ta zahiri ba.!"
"Ya cuce ni ya sanya mini soyayyarshi ya guje ni ya zan yi?" Ta yi mata tambayar tare da kama hannunta.
Wayarta ta zaro ta danna numbar Huwais, da yake cikin taro, zuciyarsa a cinkushe tunanin halin da za ta shiga yake yi.
Ganin kiranta gabansa ya faɗi matuƙa. Ya kasa ɗaukar kiran har sai da ta yi masa yafi goma. Ganin ba za ta daina ba, ya kai hannu zai kashe sai ya ga rashin adalcin yin hakan.
"Ya Huwais, mahaukacin masoyi mayaudari ne, ya tura mini da tsaƙo na manta da shi ya bar ƙasar." Ta furta cikin tsananin kuka.
Rintse idanunsa ya yi, cikin wani yanayi yana jin babu daɗin yaudararta da ya yi, saboda shi da zaɓin da ya wuce haka.
"Ni ma na zama mahaukaciya kamarsa, tun da na aminta da soyayyarsa." Ta ƙarasa faɗin hakan cikin kuka ganin ya ƙi cewa komai.
"Ki natsu Hilah, ki bawa Afrin motar ta tuƙa ki ku da... Ko kuma ki faɗa mini inda kuka na zo."
Wayar ta miƙa wa Afrin." Ki yi masa kwatance ba zan iya ba."
Afrin ta yi masa kwatance tare da kashe wayar, tana rarrashinta da take kuka kamar ranta zai fita. Wani irin ƙaunarsa take bijiro mata ganin ta rasa shi.
Duƙawa a gurin ta yi, ta saki kuka duk irin rarrashinta da take yi ta tashi taƙi.
Huwais kuwa cikin tashin hankali ya miƙe xai fice.
"Ina za ka ga baki kana da su?"
"Ka kula da su, ina zuwa Najib." Ya furta hakan ba tare da ya amsa kiran ya juya ba.
Yana isa guri ya buɗe motar ya fito. Tana ganinsa, ta fashe da kuka tare da miƙe wa ta isa gareshi ta faɗa jikinsa.
"Ba zan yafe masa ba, domin ya cutar da zuciyata ya yaudare ni."
Kama hannunta ya yi suka shiga motar bayan ya bawa Afrin umurnin ta tuƙa motar ta dawo gida.
Ganin irin kukan da take yi, ya yi matuƙar daga hankalinsa matuƙa. Yana tuƙi amma shi kansa ba shi da natsuwar da zai mayar da hankalinsa ga titi.
Kukan na ƙara mishi ƙunci a zuciyarshi sosai, musamman in ya tuna shi ne sanadin zubar hawayenta.
Gangarawa ya yi ƙasan titi ya sauka, tare da paking ɗin motar ya kifa kansa a sitiyarin
"Ya Huwais, ba zan taɓa yafe masa ba, domin ya cutar da zuciyata. In har ya san ba ya ƙaunata mai xai sanya ya shigo cikin rayuwata?" Kukanta ya ƙara tsananta bayan ta furta hakan.
Jiyowa ya yi yana kallonta, yadda ta ci uban kuka, abin ka da farin mutum fuskarta har ta canza ta ƙara haske.
"Hilah," Ya kira sunanta can ƙasar murya, wanda ya sa ta ɗago kanta da sauri tana kallonsa.
Girman idanunta da suka canza kala, ya sanya ya kasa rarrashinta da ya yi ninyar yi, wanda ganin hakan ya sanya ta ci gaba da kukan har da ƙara sauti.
"Please, don Allah ki daina kuka domin zuciyata na zafi." Ya furta cikin sanyin murya.
Jin ta rage sautin kukan, ya sanya shi buɗe motar ya fito. Ta inda take zaune ya zagaya ya buɗe motar.
A gabanta ya tsuguna yayin da ya yi narai-narai da fuskarsa.
"Kina son damuwa ya sanya na mutu kuma ki ga hawayena ko?" Ya yi mata tambayar cikin wata irin murya tare da saukowar tagwayen hawaye a fuskarsa.
Hankalinta ya tashi sosai! Da sauri ta share hawayenta tana kallonsa.
"Don Allaah kar ka yi kuka na daina."
Ajiyar zuciya ya yi lokacin da ya ji muryarta na faɗin haka.
"Ina jin rayuwata wani iri Hilah. Yau ake mini auren dole, kuma ƙanwata wacce na fi ƙauna tana cikin wani yanayi. Ban san da wani irin kalamai zan rarrashe ki ba, amma na yi miki alƙawarin nemo mahaukacin masoyi duk inda ya ke, tun da na fahimci ya riga ya sace zuciyarki."
A yadda ya yi maganar, ta kasa gane ko bai ji daɗin irin yadda ta nuna tashin hankalinta ba ne, ko kuma tsananin tausayin halin da take ciki, ya sanya shi shiga cikin yanayin.
"Ka yi haƙuri ka gafarce ni, na sanya mahaukacin masoyi a raina, amma halayensa da iya kalamansa suka sanya na mallaka masa zuciyata ba tare da dogon nazari ba, kuma Yayana, duk wanda zai shiga rayuwata, ba zan taɓa ba shi matsayinka ba."
"Na fahimta yadda kike ji, da kuma yadda soyayya take tasiri a zuƙatan masoya, ba tare da tsimi ko dubara ta masoya ba. Sam ban yi miki mummunan fahimta ba, saboda ni ma ina jin kwatankwacin ɗacin da kike ji."
Miƙewa ya yi, tare da sanya hannu sa ya riƙe murfin motar, sai kuma ya saki ya kama gefen hijabinta.
"Share hawayenki ƴar ƙanwata kin manta na gaya miki matuƙar ina raye ba za ki taba yin kuka ba?"
Ɗaga masa kanta ta yi tana murmushi tare da saukowar hawaye a fuskarta.
Gefen hijabinta da ya ɗauke hawayen da suke zuba, ya ƙara sanyawa ya ɗauke mata wasu da suka ƙara zubowa.
Rufe motar ya yi, bayan ya sakar mata murmushi, ya zagaya ya koma ta bangaren mai tuƙi ya shiga.
Bayan ya tada motar sai ya tsaya yana kallonta yadda ta ƙurawa titi idanu.
"Yayana, ina sonka." Ta furta daidai lokacin da ta juyo ta kalle shi.
Rintse idanunsa ya yi tare da jin wani irin tsau a ransa.
"Ba irin wannan soyayyar na ke so ba Hilah;wace za ki zamo murfin asirina kuma farincikin rayuwata uwar ƴaƴana."
Murmushin ya mayar mata sannan ya fara jan motar.
"Ni ma ina sonki ƙanwata."
A hanya suna tafe Hilah ranta a ɓace. A ranta tana jin in har ya ƙara kiranta, sai ta yi masa rashin mutunci, duk da cewar ba halinta ba ne.
"Mai ya sa zai guje ni bayan ya yi mini alƙawarin kasancewa a tare da shi? Shi kenan ya guje ni na rasa shi har."
Labarin ya zo da wani irin salo da nishadi, karku baru a ba ku labari. Ku biyo ni domin it’s just like a little introduction part, and guess what? You will really enjoy it. Believe me, my dear readers. Your happiness is my concern. Follow me on Facebook, Whatsapp, Wattpad, Arewaboo, and Bakandamiya. Ta ku, Jamila Lawal Zango (Jamsy).
FOR WHATSAPP: 07072971093
CALL: 008144072423
*RANAR WANKA...*
NA
JAMILA LAWAL ZANGO
"JAMCY"
☀️ *First Class Writers Asso* ☀️
Hame of Qualities And Trusted writer's of The Nation
*GARGAGAƊI*
Ban yarda kuma ban amince a juya mini labari ko ta wace siga ba,
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 11 Chapter of 17