are right sis Umnaah, kuma ba ta duba ɗaukakarta da nasararta. Abin na ci mini tuwo a ƙwarya, ya kamata muje har ofis ɗin Abu mu yi mishi complaining, saboda a gida muna fara magana za ta hana mu." Naufal ya faɗa yana gyara zamansa.
"Eh, mu je gaskiya don abin na ci mini tuwo a ƙwarya." Cewar Abidin da yake danne-danne a wayarsa.
Wani irin tsananin ƙaunar 'yan'uwansa ya ƙara kama shi, ganin ba sa son abin da take mata ya kalle su zai ce daidai lokacin da Fu'ad. ya tari numfashinsa.
"Mu ma yana ci mana tuwo a ƙwarya kuma na sha ganin su Umnaah sun je za su taimake ta, amma sai ta hana su. Ni kaina mun taɓa zuwa a tare taki. Kuma ban san dalilin da kullum take maganar ya kamata ayi mata aure da wuri ba, domin ta so ace kafin ka dawo an yi aurenta da Hammad."
Idanunsa ne suka kaɗa bayan shi sheda ne kan Hilah 'yar'uwarsa ce na jini, domin a gabansa aka samu cikinta aka kuma haifeta ta girma sai ya ce a kwai lauje cikin naɗi, amma shi sheda kan hakan."
"Bari gobe zamu same shi a ofis mu yi mishi magana karku damu kun ji 'yan ƙannina."
"To." Suka haɗa baki gurin faɗi tare da bin sa da kallo lokacin da ya miƙe ya nufi hanyar kicin.
A hankali ya tura ƙofar kicin ɗin tana tsaye a gaban gas tana juya damen tuwon semonvita da ta yi.
Ba tare da ta san ya shigo ba tana aikinta tana rero karatun qur'ani suratul Maryam kasancewar tana matuƙar son surar.
Bagan ta juya sai kuma ta koma ta zauna ta leƙa duniyar tunani wanda kusan 'yan mintina ta yi nisar kiwo.
Kamar wacce aka tsikara ta miƙe da sauri ta ƙarasa gurin talgen da har ya fara zuba.
Buɗewa ta yi tana juyawa sai kuma ta mayar da murfin ta ije muciya ta ɗauki garin za ta tuƙa.
Tana tuƙin yana kallonta, kamar wanda ya kunna fim har ta kusa gamawa, sai cikin rashin sa'a tuwon ya fallatsar mata a hannu, wanda ta yi ɗan ƙara ta yarda muciyar tana tsallen azabar zafi.
Da sauri ya ƙarasa gurinta tare da kama hannu ta yana hura mata wanda ta kalle shi idanunta tab da hawaye.
"Ya Huwais, ashe ka shigo."
"Ki rinƙa aiki a hankali kar kije ki rinka cutar da kanki. Kinga ga shi nan har kina ƙona kanki." Ya faɗi cikin ɗan ɗaga murya ganin yadda gurin ya yi ja.
"It pains me." Ta ce tare da saka kuka wanda hakan ya ƙara tana da hankalinsa.
Janta ya yi zuwa tap, ya buɗe tare da tara kyawawan hannuta da suka sha jan lalli, waɗanda suke fisgar zuciyarsa zuwa ƙara ninka sonta.
"Am sorry sis. Bari na ci gaba da tuƙa tuwon." Ya ce tare da ƙarasawa gurin gas ɗin ya ɗauki muciyar bayan ya wanke ya sanya a cikin tuwon.
"No ka barshi zan iya Ummu za ta yi faɗa in ta gani." Ta ce yayin da hawayen da suke maƙale a fuskarta suka gangaro mata.
Mayar da muciyar ya yi, tare da kamata ya zaunar ya kai bakinsa yana hura gurin, kamar sakwan talatin sai ya koma gurin tuƙin yana faɗin,
"Let her do, ciwo kika ji saina kasa taimakon ki."
Kallon da ya yi mata sai ta ji a karon farko ta ji wani abu game da kallon wanda ta kasa tantance ko mene ne shi.
Idanunta ta sunkuyar ƙasa ba tare da ta ce komai ba, sai dai ƙarƙashin zuciyarta tana addu'ar Allah ya sa kar Ummu ta shigo, wanda ta san faruwar hakan ba ƙaramin faɗa za ta sha ba.
"Zan yi wa Ummu magana, ba zai yiwu ace duk kuɗin mahaifinmu ba kina girki ba dare ba rana, kina buƙatar time Hilah, kar ta manta watanni ya rage ku yi musabaƙa, duk da na san you gonna rock it, amma kina buƙatar hutu sosai don kina da 'yancin hakan. I don ma don kar kije gidan aure ba ki kowa ba, zuwa yanzu sai dai ki kowa ya wasu"
"Ummu, uwa ce a gareni wanda ko wane ɗa zai yi alfaharin samunta, domin ta gina rayuwata da gishirin duniya wato ilmi. Ba zan yi baƙinciki don ta sani aiki ba Ya Huwais, don Allah karka ka yi mata magana ko Abu. Ina son mahaifiyata ba na son na ɓata mata rai. Bayan haka ma gani za ta yi kamar ƙararta na kai maka."
Sosai ta ba shi tausayi musamman da mood ɗin da ta yi maganar. Bai amsa mata da zai yi mata magana ba ko a'a ba, ya fara zuba garin tuwon a cikin tuƙunya yana tuƙawa, wanda ganin hakan ya sa ta saki dariya.
"Kai ya Huwais! Dama ka iya girki ne?"
Dariya ya yi jin yadda ta yi masa tambayar cikin zallar mamaki ganin yana tuƙin da ƙwarewa.
Rufe tuwon ta yi bayan ya gama ya rage gas ɗin wanda take kallon shi har yanzu mamaki ɗauke a fuskarta.
Sai ya matsa gab da ita zai ɗauko kular da zai kwashe tuwon wanda ta riƙe hannunsa tana faɗin,
"A ka barshi zan iya kwashe na gode."
Matsowa ya yi kusa da ita har tana jin kusancin ya yi yawa domin a tare suke saukar da numfashi kuma suna jin hushin juna.
Dubara ta yi ta matsa ƙarshen sink ɗin tana mamakin hakan da ya yi mata.
"Mamaki kike yi ko? Ai da na je London na kasa cin abinci na kowa sai tunanin na ki, shine na gwammace gara na yi girki da kaina ya ɗan fi kama da naki, tun da ina lura da yadda kike yin na ki."
"Ikon Allah!." Ta ce da ƙarin mamakin a fuskarta.
"Abincin kowa baya mini daɗi sai nawa. What if ka yi aure ya za ka yi da na matarka?"
Tambayar ta ƙona masa rai domin ya so ya ji tace in suka yi aure ya huta da cin abincin kowa sai na ta, amma to in ta faɗi haka ta ya ya kenan?
"Sai na ɗauke ki na kaiki gidan har sai ta koyi girkinnki."
Jinjina kanta tayi tana mamakin menene a abincin ta da har ya bambanta daɗinsa da sauran na mutane.
"Ai da yake da sauƙi tun da Anty Wajnaah ce duk da cewar tana da girman kai ba lallai bane ta koya, amma ina da yaƙinin ba za ta iya rasa ƙwarewa kan dafa abinci ...."
"Sai kuma aka ce miki ita zan aura?" Ya jeho mata tambayar cikin ɓacin rai, yana miƙa mata tuwon da ya saka a leda tana nannaɗawa tana sakawa a kula.
"Eh, na ga tun kafin ka tafi aka yi emgagement ɗinku, dalilin tafiyarka ya sa aka ɗaga auren sai ka dawo. Ga shi yanzu har ta gama servise kamar ta samu aiki na ji Ummi na faɗi." Ta yi maganar cikin ɗan shakku da rashin gasganta maganar sai kuma ta ɗora da cewa,
"Eh haka ne, Uncle Nauhis na ji yana mata murna a lokacin da muka je bikin 'yar gidan Mummy Binta."
"To ba ita zan aura ba domin bana sonta."
"Haba Yaya! This isn't right. A kan me za ka sa ta ɓata lokacinta for almost two years, kuma yanzu ka ce ba ka sonta? Gaskiya in ka yi mata haka sam ba ka yi mata adalci ba."
Tabbas ya san gaskiya ta faɗa, to amma kuma da ya aureta ya kasa bata haƙƙinta ya cutar da ita, wanda in ba mai iya riƙe kanta bane sai ta faɗa harkar banza ai gara ya ƙi aurenta, domin duk matar da zai aura ba ƙanwarsa ba matar shige take a gurinsa.
"Kin san mene ne soyayya?" Ya tambayeta cikin sanyi tare da barin kwashe tuwon.
"Ban sani ba Ya Huwais saboda har yau ban wani ji ina son Hamad ba, sai don mahaifiyata ta yaba da shi, kuma besides ya cancanci ko wace 'ya mace ta so shi."
"Wannan dalilin ya sa kike ganin baike na, kuma duk abin da zan gaya miki ba za ki fahimata."
"To Yaya, wata ka kamu da sonta?" Ta yi masa tambayar cikin mamaki har zuwa lokacin tana jin bai kamata ya yi mata haka ba.
"Eh, ita ce zuciyata kuma rayuwata. Ita ce nake jin zan iya rayuwar aure da ita, ma kuma zauna da ita ko da ta kasance musaka. Ita ce mace ta farko da zuciyata ta kasa bacci take tunaninta babu dare babu rana har ya taɓa sashi na rayuwata."
Mamakin abin da yake cewa ya kamata duk da cewa ba sa ɓoyewa junansu komai, amma sai take ganin bai kamata ya gaya mata waɗananan kalaman ba. Ita mamakinsa ma take yi da yake bai cika shiga rayuwar mutane ba har ya iya soyayya haka. A she ɗan soyayya ne.
"Hilah ina jin in ban aureta mutuwa zan yi domin ta zamo rai da numfashi a gareni. Kin ga kuwa babu rayuwa in har babu ita, domin rasa yarinyar daidai yake da rasa rain.."
"Wace ce ita, wace ce wacce take son ta yi mana sanadin ɗan'uwanmu? A ina kuka haɗu? In har kuɗi na iya komai ba su Abu ba ni kaina da kuɗin da na mallaka zan nemar maka aurenta ko 'yar shugaban ƙasa ne." Ta ƙarasa maganar cikin hawaye ganin yadda idaunsa suka cika da ƙwalla domin ɓata taɓa ganin abin da ya sa shi cikin wannan yanayin ba.
"Wanne kike so na amsa miki Hilah? Tarin tambayoyin sun yi mini yawa?
"Duka Ya Huwais. Duka nake so domin kawo ƙarshen matsalarka, saboda ba zan iya ganinka cikin wannan hali ba."
'Ba 'yar kowa bace kuma ba ta wuce matsayinmu ba, amma ta yi mini nisa da tazara;tazaran da yake kamar kwatankwacin sama da ƙasa. Ba zan same ta ba har abada.
"To mene ne amfanin tunanin abin da ba za ka samu ba? Saboda abu physical wanda kake da tabbacin samunsa shine za ka yi tunani akai, amma abin da muka san yafi ƙarfinmu ko mallakin wani ne, tunaninsa babu abin da zai sa mana sai damuwa da ƙunci. Ka cire yarinyar a ranka hasashena yana bani ƙila ita ɗin matar aure ce ko kuma budurwar abokinka. Kaga waɗanɗan Allah ya hana neman aure cikin aure."
"Haka ne kina da gaskiyarki na ga wauta na da na kamu da soyayyarta duk da cewa mutum ba shi yake sawa kansa so ba Ubangiji ne, amma soyayya
Labarin ya zo da wani irin salo da nishadi, karku baru a ba ku labari. Ku biyo ni domin it’s just like a little introduction part, and guess what? You will really enjoy it. Believe me, my dear readers. Your happiness is my concern. Follow me on Facebook, Whatsapp, Wattpad, Arewaboo, and Bakandamiya. Ta ku, Jamila Lawal Zango (Jamsy).
FOR WHATSAPP: 07072971093
CALL: 008144072423
*RANAR WANKA...*
NA
JAMILA LAWAL ZANGO
"JAMCY"
☀️ *First Class Writers Asso* ☀️
Hame of Qualities And Trusted writer's of The Nation
*GARGAGAƊI*
Ban yarda kuma ban amince a juya mini labari ko ta wace siga ba, sannan ban bada lamuni a ɗora mini littafi a kowane kafar sadarwa ba sai da izinina a kiyaye⚠️
JAN HANKALI
Kirkirarran labari ne ban yi shi don wani ba, idan har ya yi daidai da labarin ki/ka to arashi ne.
SADAUKARWA
Kwacakwan labarin daga farkonsa har karshe sadaukarwa ne ga ƙawata sahibata Aysha Na Lado. Allah saka miki da alkairi ya raya zuri'a.
PAGE 3
BISMILLAHIR RAHMANINR RAHIM
"Haka ne Hilah, kina da gaskiyarki na ga wauta na da na kamu da soyayyarta, duk da cewa mutum ba shi yake sawa kansa so ba Ubangiji ne, amma soyayya wata aba ce da take shiga zuƙata ba tare da umurni ba ko neman izini. Soyayya wata abace da take girmama a zuciyar mutum. Ta canza maka muƙaminka ko da ace Sarkin da yake kan karagar mulkinsa ne, sai ta sanya ga zama bawa ga abocin begenta."
"Na fahimta amma..."
"Wai Hilah abincin duniya kike girka ma wa da kika daɗe a kicin ɗin?" Muryar Ummu ta katse mata maganar da take yi, wanda ya sa ta yi saurin fara ƙoƙarin karɓar tukunyar da yake wankewa suka fara kokawar sai ya gama har ta shigo ta same su.
Tsananin tashin hankali ya bayyana a fuskarta domin ba ta yi tunanin yana kicin ɗin ba.
Ƙarasowa ta yi cikin tsanannin fushi ta kwashe ta da mari da idanunta da suka firfito tun kafin ta ƙarasa.
Kallonta ya yi zuciyarsa a harzuƙe tare da dafe ƙuncinsa domin ya gwammace ace shi ta mara ƙila marin zai fi masa sauƙi.
'Haba Ummu! Kan me za ki mare ta bayan ni nake da laifin na zo har inda take?"
Ko za ka rama mata ne eh? Saboda na ga yadda kake cika kamar za ka iya rama mata?" Ta ce masa cikin tsananin fushi.
"Allah karya nuna mini wannan ranar." Ya ce muryarsa a sanyaye.
Sai ta ɗora da cewa ganin bai ƙara cewa komai ba, sai ƙasa da idanunsa da ya yi zuciyarsa na suya.
"Na ga 'yata ce ni na haife ta kuma nake da iko da ita."
"A gaskiya abi da kike yi Ummu bai dace ba kin nuna bambanci a tsakaninmu kuma bayan duk ɗaya muke a gurinki. Bayan kina da sani Hadisi ne ingantacce kan bambanta 'ya'ya."
"Ok, ka je waje ka koyo rashin kunya za ka fara yi mini a gaban ƙanninka ko?" Ta tambaye shi tana kallon ƙanninsa da suka yi cirko-cirko Azerh, Umnaah, da Amnaah hawayen tausayin 'yar'uwarsu suke yi.
"Ki yi haƙuri Ummu. Ya Huwais, don Allah ka daina ƙalubantarta ita uwace agare ni." Ta ce cikin muryar kuka tare da durƙusawa sai ta fashe da gigitaccen kuka.
"A'a ki barshi ya yi mini rashin kunya, kin ga sai na san wuyansa ya isa yanka ya kai munzalin da zan kafa doka ya ƙi bi. Tarbiyarku nake dubawa domin boko ba zai sanya na bari ku aikata abin da ba daidai ba. Idan da ƙuruciya a yanzu kun girma ko su Amnaah da Fu'ad ba na barin su cika shaƙuwa sosai ballantana ku da kuka girma kuka mallaki hankalin kanku. Ku ɗin haƙƙi ne a kaina na kula daku, don haka kar ku ga kamar ina takurawa rayuwarku ne" Ta ce musu haka don su daina mata kallon da sam ba ta jin daɗinsa, yayin da fuskarsu take ɗauke da tarin tambayoyin da ba ta da masarsu.
"Ummu, ina da hankali kuma kin bamu tarbiya kar ki bari temptations ya sanya ki zargin 'ya'yanki. Ko da kika ga na fi shaƙuwa da ita ina yi ne saboda ita ce mace ta farko da aka fara haihuwa a gidan, amma bayan wannan babu wani abu saɓanin hakan."
"Munafuki duk mai hankali daga kallonka zai fahimci ƙaunarta kake. Ballantana ni mahaifiyarka da na raine ka na san abin da kake so da wanda ba ka so." Ta ce a ranta a fili kuwa cewa ta yi.
"Na dai gaya maka sai ka kiyaye." Ta ce tare da ficewa.
Ransa ne ya ɓace idanusa suka yi ja sai ya juya ya fice ba tare da ya kalli kowa ba.
Yana fita Ummu da ke ƙoƙarin haye sama ta saki ajiyar zuciya tana jin wani irin tashin hankalin da yana saukar mata da ciwon kai ta nufi ɗakin Abu.
Duƙawa ta yi ta saki kuka sosai wanda 'yan'uwanta suka yo kanta suna rarrashinta
Kuka ta saka masa tare da faɗawa jikinsa wanda hankalinsa ya yi matuƙar ta shi ya fara rarrashinta.
"Yaron nan daga dawowarsa yana son ya cigaba da sani cikin damuwa. Na yi tunanin shekarun da ya ɗauka zai sa ya daina haka, amma abin ci gaba ya yi.
"Lafiya mai kuma ya yi?" Ya tambayeta cikin mamaki wanda ya sa ta share hawayenta ta ce,
"Shaƙuwar da bana son yan nuna mata dai yake nunawa. Wallahi bani da kaffara mahaukacin yaron nan sonta yake. Ko a ina ya taɓa ganin an so wacce babu aure a tsakani? I don sonta da ƙyawunta yake ruɗarshi har yake jin ƙyashin wani ya aureta, ai akwai mata waɗanda suka fita kyawu sai ya je ya nema, amma ba wai ya tsaya yana nuna wa 'yar'uwarsa wacce suka fito ciki ɗaya soyayya ba."
"Haba Laila, har yanzu hasashe kike baki tabbatar ba, kuma bai taɓa gaya miki ba. Yana da hankali ba zai aikata hakan ba. Duk kyawun da take da shi ai dole wani ya aureta tun da babu aure a tsakaninku. Ku dai mata kuna da sauran camfar abu don babu komai a tsakaninsu sai shaƙuwa. Tun suna yara ya kamata ki raba shaƙuwar ba wai sai da suka girma ba don hakan zai yi miki wuya."
"Shiyasa na ce ayi musu aure kawai! Tun da ya dawo a haɗa aurensu tare ga Wajnaah har ta gama karatu aiki take yi. Ta yi haƙurin jiransa."
"Eh, zan yi mishi magana amma ita Hilah gaskiya ba yanzu ba sai ta gama makaranta." Ya ce tare da ɗaukar agogonsa zai ɗaura wanda ta taso ta ƙarɓa tana ɗaura masa.
"Ina kashedi da jawo hankalinka da ka da yaron nan ya kasa controlling emotion ɗinsa ya aikata ba.."
"Haba ke fa uwace don Allah ki daina faɗin haka domin in sha Allahu hakan ba zai taɓa faruwa ba." Ya katseta cikin tsawa wanda ya sa ta yi shiru amma a ranta ita tasan abin da take tunani.
Sai kuma ta ce"Haka ne Allah ya shige mana gaba." Tare da ɗaukar wayarta da ba ta san me za ta yi daita ba sai juya ta take yi.
Huwais, zaune a kan kujera cikin ofis ɗin abokinsa kuma amininsa Doctor Khair.
Kallonsa yake yana jin bayanin da yake masa wanda ya ɗora da cewa,
"Sam bana shawartarka da ka cigabada shan irin waɗannan maganin it been for a while kana sha wanda a shawarce bai kamata ba ace kana sha ba. Duba ga illolinsa da abin da zai haifar nan gaba, saboda za ka kai mizanin da za su zamo maka illa..
Shiru ya yi cikin tunani ganin bai ce komai ba ya ɗora da cewa.
"Please, ka daina shan maganin ɗauke sha'awa ka yi aure. Wata ƙila perception ne kawai na ka kan babu macen da za ka ji feelings a kan ta sai ita. Ta iya yiwuwa negatives ne ba gaskiya bane. Kai namiji ne cikkake mai ba dutse bane, bana tunanin za ka iya kaɗaicewa da mace ba tare da ka ji wani ba. Ka ga ƙila albarkacin auren ya ɗauke maka sha'awarta da ƙaunarta, don ƙila sheɗan ne yake saƙa maka hakan don ya yi nasara a kanka ka aikata ba daidai ba, saboda tun da nake ban taɓa jin wanda ya kamu da son yar'uwarsa biologically.
"Ya zan yi, ya kake son na yi Khair? Ba ka san abin da nake ji game da ita ba shi ya sa kake cewa haka. A irin yadda na ke jin sonta sai zuciyata take kitsa mini akwai lauje cikin naɗi, amma na kan kore hakan ina tuna da rayuwarmu bakiɗaya. A gabama aka haife ta na raine ta ta girma. Ni na san soyyayarta ita ce ƙaddarata wace za ta kai ni kushewata lokacin abai yi ba." Ya ƙarashe maganar cikin murya mai rauni tare da saukar hawaye masu zafi kan ƙuncinsa.
"Yanzu me kake son yi?" Ya tambayesa cikin tsananin tausayinsa na jararabawar da Allah ya yi masa.
""Ban sani ba! Ni ma ban sani ba." Ya faɗa yana watsa hannunsa cikin damuwa sai ya ɗora da cewa,
"Amma sai dai ina jin zuciyata tana bani shawarar da zai iya zama mini ƙadangaren bakin tulu a rayuwata, domin zabbi shawarar da take bani, wataƙila bayan lalacewar lamarin sai na samu mafita a cikinsa. Zanbi makauniyar zuciyata domin samun mafita, duk da ance son zuciya, ɓacinta."
"Karka je ka aikata abin da za ka yi dana sani. Ka amince da aure kawai shine mafita."
Kallonsa ya yi ba tare da maganarsa ta shigesa ba.
"I understand, I know that you are trying to help, amma ka sani kurmar zuciyata ta riga ta yi nisa ba ta jin kira, domin a shirye take ta yi nadama a lokacin da ruwa ya ƙarewa ɗankada! Matuƙar za ta samu muradinta ko da na wucin gadi ne."
Tabbas ya yarda so mahaukaci ne domin ga shi ya mai da amininnasa mahaukaci yana tunani ba tare da ya hangi abin da zai je ya dawo ba, ganin yadda zuciyarsa take masa ingiza mai kantu ya aikata lamarin da ya tabbatar xai yi dana-sani mara amfani.
"Na fahimce ka duk da cewar ba na amince da ka ci gaba da sha bane, amma babu yadda zan yi da kai, don haka ga maganin ka ci gaba da sha Allahu ya kawo maka ƙarshen matsalarka."
"Thanks." Ya ce tare da karɓar maganin ya fice yayin da zuciyarsa ke gasganta masa hakan shine kawai mafita a gare shi.
Hilah ta shiga cikin tsananin damuwa na maganar da suka yi da shi. Tunaninta wa yake so, kuma mai ya sa yake faɗin ta yi masa nisa? Kan me zai ɗauki son mace ya ɗora ma kansa har yana tunanin in ba ita ba ba zai iya rayuwa ba. Bayan namiji ne wanda ko bai samu soyayyar mace ba zai samu wacce ta fita.
A ɗan tunaninta sai take ganin duk ba matsala bace wanda zai tashi hankalinsa har ya saka shi cikin ƙunci domin shi ɗin namiji ne da Allah ya ba shi damarmarki da dama.
Kwanciya ta yi tana tunanin halin da yake ciki. Tana wannan tunanin har bacci ɓarawo na yi nasarar sace ta.
Zaune yake kan sofa daga shi sai gajeren wando. Duk da sanyin A.C da ya cika ɗakin sai yake jin zufa na kama shi ta cikin jikinshi, sakamakon abin da yake son aikatawa.
Miƙewa ya yi, ya ɗauko ƙaton hotonta da ya zana ya rungume a ƙirjinsa cike da begenta. Ya ɗan ɓata lokacin yana rungume da hoton sai kuma ya miƙe ya ɗauko maganinsa ya ɓalla tare da haɗiya bisa ƙa'ida wanda a hankali ya fara aiki ya daina jin sha'awarta.
Sabuwar wayar da ya siya da da sabon layi ya sanya hannunsa ya ɗauko. Bayan ya gama deciding da yanke hukunci zartacce akan lamarin ya aminta da komai ya faru in the future zai ɗauka, domin tsuntsun da ya ja ruwa, shi ruwa kan duka.
Sa layin ya siya wanda ba shi ya yi rigister ba ya ɗauko sai ya kunna wayar yana kallon wayar da ta gama serching ta kunnu.
A hankali ya danna numbarta a cikin wayar da nufin ya yi mata magana ta whatsapp sai kuma ya fasa ya kashe wayar ya koma ya xauna yana tunani.
A ƙalla sai da ya yi haka sau biyar da ga ƙarshe ya yi nasarar tura mata tsaƙo kamar haka:
"Na kasa natsuwa na kasa sukuni kullum zuciya cikin begenki. Kar kinyi mamakin hakan, domin na riga na gama a concluding son ki da ya mai dani mahaukaci shi zai yi ajalina, amma kafin na mutu, akwai buƙatar ki san wani yana can yana begenki da fatan ki zamo ta sa na har abada. Na ki mahaukacin masoyi."
Ya tura mata da hakan tare da kashe wagarsa gabakiɗaya yana jin yadda zuciyarsa ke bugu tamkar za ta fito waje! Ko wanda ya yi gudun kilometer 1000. Bayan ya tura mata alert na naira miliyan ɗaya.
Hilah na zaune cikin hall ɗinsu tsaƙon ya shigo wanda ba ta duba ba, saboda lectured ɗin da ake musu hankalinta na kan malamin, domin sam ba ta wasa da sauraren lecturer in yana lecturing.
Bayan ta fito sai ta nufi cafateria don ta ci abinci saboda yau a makare ta haɗa karin kummallon ba ta samu damar da za ta yi breakfast ba.
Tana zaune ita da ƙawarta Nihal suna cin abincin sai ta tuna da tsaƙo ya shigo cikin wayarta, wanda ta ɗauko wayar da ke cikin jakarta don ta duba.
Da sauri ta miƙe tana kallon alert na one miliyan da ya shiga cikin wayarta
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 2 Chapter of 17