Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
iya samar ma kanta mafita cikin sauri nan take ta shirya ma Fareeda gadar zare, shi kuma ya hau ya zauna daram. Tonuwar asirin maganar cikin ƙanƙanin lokaci haka abu ne da bata taɓa tsammani ba. Ƙara sunkuyar da kai ƙasa tayi bayan ta gama faɗa mishi duk abinda ya faru. Mukhtar kallonta yake babu ko ƙyafta idanu. Zuciyarsa cike da tsoro da mamakin halayen ƴaƴan Adam. Kiyi tarayya da ƙawa zuciyarki ɗaya ashe ita ko kaɗan ba ta ƙaunarki ba ta ƙaunar ci gabanki. Ya kasa haƙuri sai da ya ce "Fatima, ko dai akwai wani abu ne da Fareeda ta taɓa miki na mugunta tun kuna yara wanda har yanzu kike riƙe da shi a zuciyarki?" "Babu komai. Wallahi Allah bata taɓa min komai na mugunta ba. Alkhairi ne tsakanina da ita..." "Dalla rufe min baki algunguma. Ita kaɗai ke nufinki da alkhairi. Me yasa ke ba kya ƙaunarta?" Ɗif tayi, ta kasa cewa komai. Sai mutsu-mutsu take yi tana ƙara sunkuyar da kanta ƙasa kamar wacce tayi ƙarya a gaban sarki. "Ki zauna anan ƙasa har a kira sallar asubah. Ko yunƙurin miƙewa kika yi sai na miki wani hamɓari da zai sa ki faɗi ki karye, ki zubar da haƙora, ki fasa baki, da bala'in ƙarfi zan tokareki ta yadda zan tabbatar kin ƙarasa gaban tsohon madubinki kin fasa kai. Muguwa kawai." Ya faɗa mata maganganun da wani fitinannen haushinta a fuska da muryarsa. Ƙaƙƙarfan ƙwafa yayi, yaja tsaki haɗe da galla mata harara. Kwanciya yayi kan gadon ya juya mata baya, zuciyarsa sai tuƙuƙi yake yi, ko kallonta ba ya son yi. Haka ta zauna a watangare tana kallonsa yana kwance, ga gajiyar kusan kwana ana harraƙawa, ga wannan fitinannen tashin hankali da Mukhtar ya zo mata da shi bagatatan. Ga wani bala'in fitsari da ya riƙe mararta kam! Amma saboda tsananin tsoron kar ta motsa ya ce ya sake ta ko numfashi a hankali take saukewa. Kwatsam, Allah ya taimaketa ladanin unguwarsu ya kwaɗa kiran sallar asubahi. Addu'a take tayi a zuciyarta kan Allah yasa Mukhtar baiyi barci ba, ganin ko ƙwaƙƙwaran motsi ba ya yi. Ana gama kiran sallar sai taga ya yunƙura ya tashi zaune, ya miƙe tsaye zai wuce banɗaki. Da sauri ta janye yatsun hannunta na hagu da yake ƙasa ganin yana ƙoƙarin take ta. Bayan ya gama laƙaiƙaita a banɗaki ya ɗauro alwala ya fito. A gurguje ya shirya saboda yana so ya sallaci raka'atanil fijr kafin a tayar da sallar asubahi. Ya kama hanya zai fice daga ɗakin ta bishi da kallo, idanunta ciccike da hawaye, tana so ta roƙe shi zuwa bayi tai fitsari tana tsoron kalmar da zai fito daga bakinsa. "Kiyi sallah kafin in dawo. Ki tabbatar kin shirya zuwa gidan tsinanniyar matar nan." Ya faɗa mata haka yana gaf da ficewa. Da gudun gaske ta faɗa banɗaki, ko da ta sauke nauyin mararta maimakon ta ɗauro alwala kamar yadda ya umarceta sai ta fito, wayarta da ke ajiye gaban madubi ta ɗauka jikinta na rawa ta lalubo lambar Maman Murad ta danna mata kira. Idanu ta bubbuɗe ta ɗora hannun hagu akai ta fara hawaye jin kamfani na sanar da ita wayar a kashe take. Cikin daƙiƙu ƙalilan ta kira fiye da adadin da ita kanta baza ta ƙididdige ba, amma duk amsa ɗaya take samu, lambar da take kira a kashe take, bata ankara ba sai jin sallame sallar asubah tayi a masallaci. Da sauri ta aje wayar, a guje ta sake faɗawa banɗaki ta ɗauro alwala. Tana raka'ar ƙarshe Mukhtar ya shiga cikin ɗakin. Wani irin faɗi da gabanta yayi sai da ta runtse idanunta, ta cije baki. Nan take karatun sallar ya ɓace mata, haka ta ƙarasa ibadar a daburce har ta sallame. Ta daɗe hannayenta a sama tans roƙon Allah ya rufa mata asiri, Allah ya taushi zuciyar Mukhtar a wannan yini duk abinda zai je ya zo kar Allah ya bashi ikon sakinta. "Ina kwana Haskenah?" Ta faɗa bayan ta shafa addu'ar tana kallonshi da raunanan idanunta da ƙarara suke bayyana irin tashin hankalin da zuciyarta take ciki. Kamar mai gadi, haka yake tsaye ƙiƙam a bakin ƙofa yana jiran ta idar. Ko da ta gaishe shi maimakon ya amsa kawar da kansa yayi, hannayensa biyu naɗe a bayansa ya fara takawa zuwa cikin ɗakin har inda take zaune kan sallaya. "Fatima?" Ya kira sunanta da wata garjejiyar murya. "Na'am Haske..." "Daga yau idan kika sake ce min Haskenki sai na miki ɓarin makauniyar da zai yi sanadiyar zamowarki mai wawulo. Kina ji na?" "Na ji Aban Twince, Allah ya huci zuciyarka." Ta faɗa a sanyaye. "Tashi mu tafi." Yana faɗin haka ya fice daga ɗakin. Haka nan ba don zuciyarta na so ba ta bi bayanshi, gwuiyawunta a sanyaye kamar wacce ta kwana tana zawo. Da duku-dukun asubahi haka suka shiga mota, ya fige ta a guje suka bar gidan. Wani irin tuƙi Mukhtar ke yi na gagari, da yake kuma da duku-duku ne babu cinkoson motoci haka yake ta ƙure malejin mota ba tare da ya fuskanci matsalar go-slow ba. Babu mai cewa uffan a tsakaninsu, Fatima kwantar da kai tayi a jikin ƙofa tana ta jan duk addu'ar da tazo cikin zuciyarta. "A wace unguwa take?" Ya tambayeta sa'adda suka shiga hayin rigasa. "Maƙera" Ta amsa a taƙaice. Ko da suka shiga cikin layin maƙera daƙyar ta gane gidan. Sau uku tana nuna mishi layuka mabanbanta, sai sun shiga ta gama waige da dube-dube sannan ta ce mishi ba nan bane. A ƙarshe dai Allah yasa ta nuna mishi wani gida ta bashi tabbacin nan ne gidan Maman Murad. "Kin tabbatar?" Ya tambayeta yana ƙure ta da kallo. "Eh! Na tabbata, nan ne. Bari in je inyi sallama da ita." Har ta kama hannun ƙofar motar za ta buɗe ta fita ya dawo da ita ta hanyar janye hannunta. A tsorace ta waiga tana kallonshi da alamar tambaya a fuskarta. Wani baƙin gilas da yake ajiye a gaban motar ya ɗauka ya ƙwama a idanunsa. "Kin ga na miki kama da ɗan'iska wanda bai san abinda yake yi bane?" "A'a!" "To Idan ba haka bane ta ya kike tunanin zan barki ki shiga bayan tun ɗazu ina kallon yadda kike ta danna ma lambar matar kira? Ni da kaina zan je inyi sallama da ita. Fita muje." Jiki babu ƙwari ta buɗe ƙofar ta fita, yabi bayanta bayan ya kulle motar. Ko da suka isa ƙofar gidan a gefe ta tsaya, shi kuma ya matsa ya ɗauki wani ƙaton dutse ya fara ƙwanƙwasa ƙyauren gidan da yake a kulle. Bai ɗauki minti ɗaya ba ya ji ana ƙoƙarin zare sakata ta ciki. Don haka yaja gefe ya tsaya, hannayensa naɗe a ƙirji, fuskarnan a ɗaure tamau, kamar bai taɓa sanin wata aba wai ita dariya ba. "Malam lafiya da sassafennan kake mana irin wannan bugun? wa kake nema?" Wanda ya buɗe gidan ya tambayi Mukhtar. "Maman Murad muke nema. Tana ciki? Allah yasa bata nan ta tafi garinsu." Fatima tayi maganar a daburce cikin rawan baki. Jin abinda Fatima ta ce yasa Mukhtar dafe bangon gidan yana kallonta da mamaki, sai kuma ya ɗanyi murmushi, zuciyarsa cike da tunanin irin tsiyar da zai shuka ma Fatima idan ba'a samu wannan matar a gida ba. Shi kuwa wannan mutumi da ya buɗe gidan kallon ƙurilla yake ma Fatima, irin kallon nan na anya wannan lafiyarta ƙalau? Ta faɗi ga wacce suka zo gurinta, amma kuma take fatan ace matar ba ta nan? "Maman Murad tana nan, jiya da daddare ta dawo daga garinsu. Amma ba ni da hurumin da zanyi muku sallama da ita kai tsaye, bari in kira muku mijinta sai ku nemi izinin ganinta daga gare shi." Ya amsa musu bayan yayi tunanin lafiyar Fatima ko akasinta ba abinda ya shafe shi bane. Cikin gidan ya koma. Minti biyar tsakani wani dattijo ya fito ƙofar gidan. Fuskarsa cike da kamala, hannu ya miƙa ma Mukhtar suka yi musabaha. Ko da Mukhtar ya faɗa mishi sun zo ganin mai ɗakinshi ne ɗan jim yayi, sai kuma ya ce "Malam Muntari Allah yasa dai lafiya?" "Lafiya ƙalau Baba. Wata harƙalla ce ta shiga tsakaninta da wannan matar a kwanakin baya. To an samu matsala, shi ne muka zo takanas ta kano don a warwara wannan matsala cikin maslaha ba tare da tashin-tashina ba. Amma fa idan ita mai ɗakinka ta bayar da haɗin kai." Uzuri dattijon ya nema a gurin Mukhtar, ya shiga cikin gidan, can sai ga shi ya sake fitowa, a bayansa Maman Murad ce. Fuskarta dagaje-dagaje da yawun barci, da alamun ko sallar asubah bata samu gabatarwa ba saboda yadda take ta sakin hamma tana mutsuttsuke idanu, alamu ne na wacce aka taso ta daga nannauyan barci. A ƙyamace Mukhtar yake kallonta, sai kuma ya mayar da hankalinsa kan Fatima da ta raɓe jikin bango ƙirjinta na bugun tara-tara ya ce "Ita ce wannan?" Yai mata tambayar yana nuna Maman Murad da yatsarsa manuniya. A kasale ta ɗaga kai alamar eh, ita ce. Sai a lokacin idanun Maman Murad ya faɗa cikin na Fatima, faɗaɗa fuskarta da fara'a tayi ta ce "Maman Ummee, ke ce yau a gidan namu? Bismillah shigo mana? Baban Murad baka gane ta ba? Maman Ummee ce fa wacce na yi ma aiki shekarun baya a unguwar rimi, baƙin alkhairi ne ba na tsiya b..." "Idan kin so, shi ne za mu zame miki baƙin alkhairi. Idan baki so ba kuwa akasin haka ne zai kasance." Mukhtar ya katse ta da sauri jin yadda take ta zuba tana cika mishi kunne da zantukan da bai ɗauke su a komai ba sai shirme. Kafin ta ce komai ya cigaba da cewa "Tunda duk kun gane juna to Alhamdulillah! Ke baiwar Allah, kin tuna aikin da ƙanin mamanki yayi ma wannan matar da kike kira Maman Ummee ko? Ba komai ne ya kawo mu a daidai wannan lokacin ba sai don sanin ta inda aka hau ta nan ake sauka." "Ban gane ba." Maman Murad ta faɗa tana yamutsa fuska, bayan ta haɗe girar sama da ƙasa. Gilashin idanunsa ya cire ya riƙe a hannu, ya sake haɗe fuska sosai, babu alamun rahama ko ƙanƙani a tattare da shi. "Za ki gane yanzunnan. Ta faɗa min, a wancan lokacin ta waya kawai kika kira kawunki suka gama maganar mugun aikin zaluncin da take so ayi mata kan Uwargidana. To a yanzu dai wannan aikin ba ta buƙatarshi, ni ne mijinta. Don haka ina umartarki ki kira Kawunki yanzunnan ki faɗa mishi ya warware wannan ƙullin da yayi..." "Taɓɗijan! Wasa ma kenan! Ai wannan aikin aka yi shi anyi kenan. Makarinsa kawai ka saki ita waccan matar ne ka zauna da Maman Ummee ita kaɗai, ina tabbatar maka ko wata matar ka auro haka za ka ji ta Salam, mahaɗar jin daɗi da gamsuwar buƙatarka na auratayya an haɗa shi da Maman Ummee ne..." Maganarta ya ɗauke ɗif ne, sanadiyyar wani ɓarin makauniyar mari da Mukhtar ya sauke mata ba zato ba tsammani. Ɗif ta ɗauke wuta, babu abinda take ji a kunnuwanta sai wani irin wiiiiiiiiii kamar jiniyar ƴan sanda. A idanuwanta kuwa babu abinda take gani sai wasu taurari masu bala'in haske da ƙyalƙyali suna shige da fice a jikin junansu. "Baba kayi haƙuri na ɗora hannu kan iyalinka Na rantse da girman Allah idan matarka da ɗan'uwanta basu warware wannan mummunan asirin da suka yi tsakanina da matata ba hukuma ce za ta shiga tsakaninmu. Daga nan state CID za mu wuce kai tsaye, tun ɗazu na kira babban abokina da yake can na faɗa mishi abinda yake faruwa. Yanzu haka kiran wayata kawai yake jira, zai turo mota yanzunnan a tafi da ita. Idan mun je can aka je har can garinsu aka ɗauko ɗan'uwan nata luguden mintuna goma ya isa su samo hanyar warware wannan ƙullin da suka yi." "Kayi hakuri Malam Muntari, abin duk bai kai haka ba..." Ihun da Maman Murad ta ƙwalla cikin azaba shi ya ankarar da su ta dawo cikin hankalinta. Ta buɗe baki za ta sake ƙwallah ihu a gigice da sauri Baban Murad ya janyo ta ya rufe mata baki. Cikin gidan ya ja ta, bayan yayi ma su Mukhtar umarnin su bi bayanshi zuwa cikin gidan. Duk da gidan haya ne jin irin gaggarumin maganar da ke tafe da su Mukhtar shiga da su cikin gidan shi yafi alkhairi da tsayuwarsu a waje. Ga unguwar irin ghetto ɗinnan ne, duk da safiya ce mutane masu wucewa har sun fara tsayuwa ganin kafcecen marin da aka saukewa Maman Murad. A tsakar gidanma mata da maza ne tsaitsaye suna hum-hum-humm! "Baban Murad lafiya kuwa?" Biyu daga cikin mutanen gidan suka haɗa baki wurin tambayarsa. "Lafiya ƙalau." Ya amsa a gundure. Ya bankaɗa labulen ɗakinsu ya shige ciki, su Mukhtar suka bi bayansa. Maman Murad kwance a jikinsa ranga-ranga kamar sumammiya. *Ba fa anan naso tsayawa ba Wlh😪😪😓😓 caji na 3%, kar in tsaya iyayin ƙara yawanshi wayar ta ɗauke. Idan na samu wadataccen caji za ku ji ni gobe, idan baku ji ni ba a cigaba da min uzuri masu karatu🥰🥰🥰🙏🏽🙏🏽🙏🏽. Customers ɗina masu kira na su sayi data I loviyu wujiga-wujiga😘😘😘😘* Assalamualaikum Barkanmu da wannan lokacin AUNTY ZEE TAKU CE ,Ina uwar gida Amarya da yanmata albishir gareku BONONZA; BONONZA;BONONZA; Nazo maku da SAHIHIN MAGANIN CIRE TUMBI CIKIN SATI DAYA ZAKI BAN LABARI,KINCI GAYU ANA TAMBAYARKI YAUSHE ZAKI HAIHU TUMBI YA HANAKI ADO DA KWALLIYA SHA KURUMINKI NAZO MAKI DA MAGANI CIKIN SATI DAYA ZAKI BAN LABARI ZAN DANDANA MAKU SHI AKAN RABIN KUDINSHI DAGA NAN ZUWA SATI DAYA 7K DUK ROBA DAYA KI BIYA 3500 KI MALLAKI NAKI NAN DA SATI DAYA ZAI KOMA 7K MAGANIN BREAST WANDA ZAICIKO MAKI DA TUWON NONO DAN ALLAH KIJARABA ZAKIZO KINA GODIYA DAN DUK WADDA TA GWADA SAITA DAWO MANYAN MATA SUKE GYARA KAMAR YANDA KUKASANI 8K YAKE ZANKARA TALLATA MAKU SHI KI BIYA 4K KI MALLAKI NAKI KI BIYA TA WANNAN ACCOUNT DIN KITURA MAN SHAIDAR BIYA 3968303018 ZAINAB SHU AIBU FCMB 08162859027 *RABON AYI* *30* *©Fareeda Abdallah* *_Ƴar'uwa ki tuna, kafin saukar da ko wace irin cuta, sai da aka saukar da maganinta. Don kinyi magani da yawa baki dace ba ba shi zai sa ki yanke tsammani daga samun waraka ba. Ki gwada maganin da muke karɓa ma al'ummar Annabi SAW, wata ƙila warakarki a wannan maganin yake baki sani ba. Haihuwa kike nema? Baki taɓa yi bane ko kuwa jinkiri ne kike samu tsakanin haihuwar? Sanadiyyar planning ne kika samu jinkirin ko kuwa sanyi ne yake damunki ko haka kawai? Matsalar rashin haihuwar daga mijinki yake? Muna da ingantaccen magani garanti wanda aka gwada muka tabbatar da aikinsa, in Allah ya yarda ko me ya shafi mahaifar mace da mararta wanda ya hana ta haihuwa in dai tayi amfani da saiwoyin maganinmu za ta samu biyan buƙata da yaddar Allah. Matsalar mace ko namiji 2k ne.* *Akwai ƙullin maganin da muke sayar da shi 500, in dai matsala ta shafi nonon mace da yaddar Allah za ki samu waraka. Mai ciki, mai shayarwa, mare shayarwa duk za su iya amfani da wannan magani. Ko da matsalar ciwon daji ne da ya shafi nono in sha Allah za ki sami waraka sanadiyyar amfani da wannan magani. Akwai garin maganin sanyi da za ki haɗa a cikin yaji, shi ma 500. Akwai ingantaccen maganin sanyi da za ki saya muku ke da Oga, 2k ne. In Allah ya yarda za ki sha mamakin yadda lafiya zai wadace ku ke da Oga, za ki ga yadda za ku dawo kamar sabbin amaren da suke mararin junansu😍.* *Akwai ingantaccen haɗin magani na gyaran nono wanda ni Fareeda Abdallah nake sayarwa, bokiti 1litter 2500, ƴar'uwa in dai za ki juri dama kunun garin maganin safe da dare, za kiga yadda ba cikowar nono kaɗai ba, hatta fatar jikinki sai ta canza, za kiyi kuɓul-kuɓul😍, sa'annan ni'ima bazai taɓa yanke miki ba in Allah ya yarda saboda irin haɗe-haɗen da ke cikin wannan magani. Ga duk mai buƙatar ɗaya daga cikin maganinnan da gaske ta tuntuɓeni ta whatsapp a 07039080978, idan kira ne a kira ni ta 09077591726. Don Allah ƴan'uwa🙏🏽🙏🏽🙏🏽idan ba da gaske kike yi ba kar mu ɓata ma juna lokaci.* Ko da suka shiga cikin ɗakin da yake falle ɗaya, sai suka tarar da kujeran zama mazaunin mutum uku ita kaɗai ce a ajiye ta bakin ƙofa. Can daga cikin ɗakin gado ne, a gefe guda da sauran tarkacen kayayyaki. Kan kujera Baban Murad yayi musu umarnin zama, shi kuma ya ƙarasa gefen gado ya zaunar da Maman Murad. Jikinsa na rawa ya ƙarasa kusa da fanka ƴar tsaye ya kunna ya matsa da fankar kusa da Maman Murad da tayi wata dagwalooo kamar wata wawuya ta ƙura ma guri ɗaya idanu. Fatima ce ta ɗan ɗofana mazaunanta kan kujerar, kamar ace ƙyat ta zura a guje. Shi kuwa Mukhtar tsaye yayi a bakin ƙofa ya harde hannaye a ƙirji, fuskarsa a ɗaure tam yana kallon abinda dattijon ke yi. "Maryam, Maryam, kina ji na?" Baban Murad ya tambayi Maman Murad bayan ya tsuguna a gabanta, ya riƙe hannayenta biyu cikin nashi. Tsawon wasu daƙiƙu kamar baza ta motsa ba. Sai kuma ta sauke ajiyar zuciya a zabure ta damƙe hannayen mijinta da ƙarfi. Idanu warwaje take kallonshi, sai kuma ta kalli Mukhtar a tsorace ta nuna shi da yatsa manuniya tana surutai "Baban Murad kana ganin ya kafta min mari da hannunsa mai kama da dutse baka rama min ba? A gabanka za'a ci zarafin uwar ƴaƴanka baza ka ɗauki mataki ba? Ashe haka soyayyar da kake ikirarin yi min..." "Maryam! Saurara don Allah! Ki nutsu ki fahimci abinda zan faɗa miki. Kinga wannan mutumin ba da wasa yazo ba. A matsayina na mijinki, ina mai baki shawara tun kafin hukuma su shigo cikin zancennan ki kira Kawu Bello yanzu ki faɗa mishi ya warware aikinnan." "Hukuma kuma Malam? Me kuma ya kawo hukuma a cikin wannan maganar?" Ta faɗa jikinta a sanyaye. "Ƙwarai kuwa hukuma. Ashe ɗazu baki ji abinda na ce ba kenan? Ke na ga ma kina neman ɓata min lokaci, bari in kira kawai azo a tattara min ke zuwa can, shi ma kawun naki duk inda yake a ƙasar nan cikin ƙanƙanin lokaci za'a damƙo shi" Har ya fara daddana wayarsa da saurin gaske Maman Murad ta ce "Dakata Alhaji, Allah ya huci zuciyarka. Don girman Allah maganar ba sai ta je gaba ba. Yanzu zan kira Kawun nawa." A duniya idan akwai abinda Maman Murad take tsoro bai wuce harkar hukuma ba. Duk baki da tsananin bala'i irin nata ko fadar mai unguwa aka kaita ta dinga rusa kuka kenan tana bayar da hakuri. Ko da kuwa ita ce da gaskiya, balle ace gurin ƴansanda? ba ta fatan ko maƙiyinta a jarabceshi da zuwa gurin ƴansanda. Duk da kawun nata ya sha sanar da ita irin wannan aikin bai da makari. Haka nan ta ɗauki wayarta ta kunna, ta lalubo lambarsa ta danna mishi kira, a amsa kuwwa ta saka wayar don Mukhtar ya ji da kunnensa abinda kawunta zai faɗa. Ringing ɗaya, biyu, ya ɗaga daga can ɓangaren. Duk da jiya ta bar gida, amma ba ya ganin kiranta yaƙi ɗagawa ko me yake yi, saboda ita ɗin abokiyar cin mushensa ce. Hajiyoyi take amso ayyukansu daga birni tana kai mishi yana samun na cin abinci. "Assalamu alaikum! Mariya? Daɗa in ce kau kin koma gida lahiya? Wallah tun jiya nika biɗat nambarki ba ni samu, nicce ko shigiyat abinga ta sadarwar garinmu tayi mana tsiyat da ta saba..." "Kawu kana ji na?" Tayi gaggawar katse shi sanin da tayi shi ɗin uban surutu ne. Yana amsa yana jin ta ta cigaba da cewa "Ina wannan matar Maman Ummee da nicce maka ita uwarɗakina ce? Har nihhaɗaka da ita ga waya kun kayi magana ta ƙara whaɗi maka yadda taka biɗar aikin da za'ayi ga kishiyarta ya kasance. Ka tuna ta?" "Ƙwarai kuwa na tuna ta Mariya. Ta ina zan manta wannan muguwar mata da tacce tana biɗat inyi gagarumin aikin da kishiyatta za tayi muguwar wulaƙanta irin wulaƙancin da bata taɓa ganin wata ƴa mace tayi a duniya ba. Ko ba ita kika magana ba? Wacce har tacce sunanta Fatima kau? sunan mijin da za ta aura Mutari, sunan uwargidan nata Fidda'u take ko Fareeda? Na dai manta. Mi shinka faru? Ko wani aikin taka biɗar a sake yi mata? Kin san dai ko ga wancan lokaci na whaɗi miki ita wannan kishiyar tata ba ta taɓuwa sai wani ikon Allah. Macece mai yawan Ibada da addu'a, ko aikin salamta kasa yi niyyi ga ita, daɗa shi nassa nayi aikin langwai ga mijinta yadda ko kusa ba shi iya kusantar ita matar tasa..." "Kawu ka saurara mana." Maman Murad ta katse shi, idanunta ciccike da hawaye. Tana kallon fuskar wayarta tana satar kallon Mukhtar da izuwa yanzu sai girgiza ƙafafu yake yi, tana ganin yadda yake ta dunƙule hannu a fusace kamar zai kai naushi sai kuma ya buɗe hannun. "Kawu, ita wannan Fatima da ta baka aikin, Ga ta zaune a gefe na ita da mijinta wai ba ta buƙatar aikin. Don Allah kawu ka taimaka min, ka warware wagga aiki da kayyi kan mijinta Mutari, ka ganshi nan tsaye bisa kaina riƙe da bindiga mai jigida a hannunsa. Ɗazu da ya kafta min mari ina rantse maka da Allah tsawon lokaci nikkasa tantance shin a duniya nike ko har na mace ne an whara min hisabi ga munanan ayyukan da niyyi. Daɗa Kawu ashe shi mijinta soja ne, ya ce idan baka warware wagga aiki ba zai kashe ni sannan ya zo har nan garinmu ya kashe ka da duk iyalinka. Daɗa ga Baban Murad yayi maka ƙarin bayani. Don girman Allah kawu ka taimaka min." Hannunta na rawa ta miƙa ma mijinta wayar. Wasu zafafan hawaye suka gangaro daga idanunta, ta kalli Fatima da duk ita ce ta janyo mata wannan bala'in tana zaman zamanta ta galla mata wata matsiyar harara, har yanzu ɓangaren kumatunta da Mukhtar ya mara bai daina raɗaɗi ba. Fatima dai bata san tana yi ba, ta rasa inda za ta tsoma ranta ne. Tunda ta ji Malam Bello ya faɗi irin aikin da tace a yi kan Fareeda bata san sa'adda ta sauka daga kan kujerar da take ɗofane ba, ta tsuguna a dandaryar sumintin tsakar ɗakin kamar mai jin kashi. Hannunta na hagu ɗore a tsakiyar kanta. Idanunta a rufe amma hawaye ne ke tseren gudu a kumatunta. Zuciyarta cike da wani iri da-na sani mai bala'in yawan da ko kusa baki bazai iya baiyanawa ba. Bata taɓa tsammanin lamarin zai juye haka ba, bata taɓa zaton Malam Bello kawun maman Murad mutum ne mai masifaffen surutu har haka ba. Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un! Ita dai tata ta ƙare, ta san yau babu abinda zai hana Mukhtar ya lakaɗa mata tsinannen duka sa'annan ya sake ta saki uku!! Baban Murad ya san halin Malam Bello da taurin kan riƙe amanar aikin bokancin da yake yi. Don haka ya cigaba da ɗorawa kan inda matarsa ta tsaya, sosai ya cigaba da tsoratar da Kawu bello ta hanyar tabbatar masa lallai fa ga Mariya nan an rutsa kanta da bindiga mai jigida. Matserar rayuwarta kawai a warware wannan aikin ne. "Daɗa amma wannan mata Fatima anyi walakantacciya. Ita ta san mijinta soji ne tammiƙo sunanshi garen da cewa in mata aiki akan matarshi? Ni wha ko lokacin na ga Mutarin mai bala'in zafin zuciya ne. Ni Bello na ga ta kaina, yanzu ya zanyi? ta ina zan whara aikin warware wagga aiki da ban taɓa yi na kunce ba..." "Au!!! Don abu kaza-kazanka baka san ta inda za ka fara warware aikin ba ko?" Mukhtar yayi maganar a fusace cikin tsawa bayan ya lailayo wata ƙatuwar ashariya ya maka ma malamin. Da takalmin ƙafarsa ya taka har inda

Chapter 22 of 26