Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ɗore akai, mata da yawa sun fara kokawa ne da ƙarfi suka zube a ƙasa suna roƙon Hajiya Mariya ta rufa musu asiri, daga masu cewa idan aka kaisu station aurensu zai samu matsala, sai masu cewa tunda suke a rayuwarsu basu taɓa zuwa ofishin ƴan sanda ba, tayi haƙuri kar su fara zuwa daga sha'aninta. Hajiya Mariya kuwa ta shafawa idanunta toka tana tsaye tana karkaɗe jiki ta ce bata san kalmar haƙuri ba, za tayi haƙuri ne kawai idan ɓarauniya ta fito mata da jakarta. Masu ɗan ƙarfin zuciya a cikinsu ne suka zaro wayoyinsu da nufin su kira makusantansu don sanar da abinda yake faruwa, amma ƴan sandan nan suka katse musu hanzari ta hanyar ƙwace wayoyin hannayensu. Cikin waɗanda aka karɓewa waya har da Hajiya Balaraba. Haka nan suna ji suna gani aka tarkatasu a motocin ƴan sanda shiga ba biya fita da Allah ya isa a cuccushe wata kan wata a wulaƙance ba tare da banbance talaka da mai kuɗi ba zuwa Ofishin ƴan sandan gidan gayu. A gurin kashi biyu da rabi cikin uku na matan wannan abin da Hajiya Mariya tayi musu shi ne ƙarshen tozarci da wulaƙanci da aka taɓa yi musu a rayuwarsu. Masu arziki a cikinsu sun ɗauki munanan alwashi da yawa a kan Hajiyar, talakawan cikinsu kuwa a zukatansu suke ja mata miyagun alkaba'irai iri-iri. Wani ƙarin abin haushi da Hajiyar tayi shi ne na ƙin shiga ɗaya daga cikin motocin ƴan sandan a tafi da ita, da ƙyamar shiga motar ƙarara a fuskarta ta ce su tafi, za ta biyo su yanzunnan ita da direbanta, ta ja kunnen ƴansandan ko da sun isa bata ƙaraso ba kar a kuskura a fara wani bincike sai ta ƙaraso, da haka suka bar gidan. ******* Sun shafe awa biyu cur a cikin cell kafin Hajiya ta ƙaraso, tafe take tana taku ɗaiɗaya irinna manyan mata masu duniya. Ta canza wanka, ta cancaɗa gayu a fuskarta wanda ya taka muhimmiyar rawa gurin ɓoye shekarunta. Saɓanin ɗazu da take sanye da leshi, yanzu wata ɗanyar shadda ce a jikinta wacce aka yiwa ɗinkin doguwar riga, an ƙawata rigar da aiki irinna zamani. Tana shiga cikin gurin da sauri aka bata kujerar zama, a ƙasaice ta zauna tana huhhura hanci. "Ya ake ciki? sunyi bayani?" Tayi tambayar idanunta ba kallon ƴansandan. Ko da suka tuna mata ta ce kar ayi komai na bincike sai ta ƙaraso taɓe baki tayi, irin alamun rashin damuwar nan. Ta buɗe baki za ta sake yin magana aka kira ta a waya, ko da ta duba fuskar wayar mijinta ke kira, wanda take yiwa inkiyar His Excellency saboda takarar gwamna da yake yi. "Excellency barka da yamma." Tayi maganar a tausashe fuskarta na bayyana murmushi. "Yauwa Hajiya. Na dawo gidan sai ban tarar da ke ba, ko har kun wuce mothers day ɗinne?" Ya tambayeta daga can ɓangaren. Yanayin alhini ta sakawa fuskarta sannan ta bashi labarin abinda yake faruwa, ta kuma ƙara da faɗa mishi inda take a halin yanzu. "Hajiya? kinyi hauka ne?" Abinda ya fara cewa kenan cikin fushi daga can ɓangarensa. Da mamaki ta buɗe baki tana kallon wayar kamar shi ne a gabanta, ta buɗe baki za tayi magana ya katseta cikin fushi. "Wane irin haukar tunani ne ya shiga cikin ƙwaƙwalwarki da za ki wulaƙantar da mata masu yawa haka waɗanda muke saka ran ba ƙaramin muhimmiyar rawa za su taka mana a zaɓen da ke tafe ba? To in dai wannan jakar taki mai ruwan madara ce ga ta nan ajiye akan gado cikin ɗakina. Ki gaggauta sakawa a sallami matannan yanzunnan, ko da yake ga ni nan zuwa in basu haƙuri da kaina." Kafin ta ce komai ƙit ya katse wayar. Ya barta riƙe da tata wayar a hannu, baki sake, zuciyarta cike da maɗaukakin mamaki jin cewar a ɗakinsa ta bar jakar. Sai kuma ta tuna ƙasa da mintuna sha biyar kafin ta ankara da ɓacewar jakar tabbas ta shiga ɗakinsa, don ta ɗauka ma Amarya Jidda set ɗin sarƙar da uban ya siya mata, za ta ba direba ya kai mata can gidan ƙanwarta inda suke tare da ƙawayenta. Ashe can ta ajiye jakar? Inna lillahi wa'inna ilaihi raji'un! wannan wane irin abin kunya ne ta aikata ga ƴan uwa da abokan arziki har ma da manyan aminanta? Da wane ido za ta sake kallonsu tayi musu magana, ya rabbi ya rabbi. Ta ɗaga idanu ta hango su can cikin cell, wasu daga cikinsu na tsaye, wasu kuma a zazzaune sun haɗa kai da gwuiwa. Fuskokinsu damalmale da matsananciyar damuwa da tashin hankali. "Hajiya? Mu fara basu jikinsu ne ta yadda ɓarauniyar za tayi gaggawar bayyana kanta?" Ɗaya daga cikin ƴansanda mata ta faɗi haka da salon cusa kai gareta. Wani mugun kallo da ta aikawa ƴarsandannan ba shiri ta ja da baya tana sosa gefen wuya. Da wata irin muguwar kasala da sanyin jiki ta miƙe tsaye ta tambayesu ina ne ofishin DPO? An nuna mata kenan za ta shiga sai ga isowar mijinta Alhaji Lukman Mai Dala, a bayanshi motoci ne masu yawa. Tun kafin direbanshi ya gama daidaita fakin a harabar gurin ya buɗe ƙofa ya fita zuwa cikin ofishin, sai saɓa babbar riga yake yi cikin tashin hankali. Cikin masifa ya bada umarnin a fito da matannan yanzunnan, saboda yawansu sun cike gurin taf. Ganin yawan matan da Hajiya ta sa aka kulle a wulaƙance saboda rashin tunani da rashin hankali irin nata ba ƙaramin sake ɗaga mishi hankali yayi ba. Irin mugun kallon da da yawa daga cikin matan suke aika musu shi da matarshi da take rakuɓe a gefenshi ya bala'in ɗaga mishi hankali. A matsayinshi na babban ɗan siyasa mai neman takarar kujeran gwamna ko ƙanƙani ba ya fatan abinda zai janyo mishi matsala tsakaninshi da jama'a, ya san idan bai ɗauki mummunan mataki nan take ba lallai aikinshi ba ƙaramin jiƙewa zaiyi ba. Ya juya inda Hajiya take ya aika mata da wani haukataccen kallo mai cike da tozartawa, cikin fushi da fusata ya balbaleta da bala'i kamar bai san daga inda ta fito ba, ba kuma tare da ya duba yawan mutanen da suke gurin ba. A ƙarshe ya dire maganganunshi da cewar lallai tana buƙatar saiti tunda har ta iya wulaƙanta iyaye da yayye da ƙannenshi mata haka akan abinda bai taka kara ya karya ba, nan gaba bai san me za ta ƙara yi ba na tozarci da rashin hankali. Idan ya haye gadon mulki haka za ta tafiyar da al'umma a wulakance. Ta tafi gidansu ya saketa saki ɗaya. Duniyar ce ta fara hajijiya da Hajiya Mariya, tunaninta ya tsaya cak! saki shi ne kalma na ƙarshe da ko a mugun mafarki bata taɓa tsammanin zai shiga tsakaninta da maigidanta ba. Wannan abu da Excellency yayi ga Hajiya shi ya wanke kaso tamanin cikin ɗari na baƙin cikin da matannan suka ƙunsa. Rai fes sunan wata zani. Hatta ƴan'uwanta na jini sun ji daɗin wannan saki da aka yi mata, daman tuntuni ta ishe su da kaɗifiri da girman kai na tsiya, ko cikin dangi sai abinda tace ake yi, ko babu komai yanzu an karya alkadarinta. Da kallo ɗaya yaga sassaucin tsana da ɓacin ran da yake kwance a fuskokinsu. Duk a ƙoƙarinsa na sake wanke zukatansu nan gabansu ya zube gwuiwarsa a ƙasa yana sake basu haƙuri. Idanu suka bubbuɗe, alamun mamaki. Babban mutum irin wannan shi ne ya durƙusa musu a ƙasa? bakinsu har rawa yake gurin cewa "Honorable don Allah ka miƙe tsaye. Wallahi har ga Allah mun yi haƙuri, mun yafe abinda tayi mana. Yanzu kawai babban burinmu a sallamemu mu koma gidajenmu." Talatin da biyunsa a waje ya dinga yi musu godiya da fatan alkairi. Ya umarci direbansa ya ɗauko masa jakarsa a mota, ko da ya buɗe envelope ne ɗauke da kuɗi naira dubu ashirin-ashirin. Haka ya bisu ɗaya bayan ɗaya ya damƙa ɗai ɗai a hannayensu, sannan ya umarci direbobinsa su kwashe su ko wacce a aje ta a gidan mijinta. Mata masu sukunin cikinsu kuwa waɗanda Allah ya huwacewa arzikin mallakar mota gidansa ya ce a mayar dasu, idan suka ɗauki motocinsu sai su wuce gida. Sai a wannan lokacin aka damƙama su Hajiya Balaraba wayoyinsu da aka ƙwace. Suka fita daga gurin fuskokinsu babu yabo ba fallasa. Farida da Fatima hanyarsu ɗaya ne, ita Fatima tana da mota, direbanta ne ma ya ɗaukota suka je gidan Fareeda aka ɗauketa daga can ya ajiye su gidan bikin. Kasancewar yaranta suna daf da tashi a islamiya sai ta sallami direban da cewa yaje ya kwashi yara ya mayar gida, ƙarfe shida na yamma ya koma gidan bikin ya ɗaukosu. To yanzu ƙarfe biyar da rabi, wannan abu da ya faru yasa jikinsu a sanyaye yake kamar an lakaɗa musu duka. Har gara ma Fatima akan Fareeda, ita kam har wata ƙwarya-ƙwaryar rama tayi kamar wacce ta yini tana amai da gudawa. Idanunta sunyi ƙozai-ƙozai saboda kukan da ta kusan yini tana yi, wannan uban kwalliyar da tayi kafin su taho yanzu ko ɓurɓushinsa babu. Duk da an sallamesu har da ladan kuɗaɗe hankalinta ya ƙi kwanciya, tana ji a ɗazu yadda Mukhtar yaita kiranta akai-akai, ta kuma ji shigowar saƙonni a jejjere, saboda fargaba da tsoron abinda za ta tarar ta ma kasa ciro wayar ta duba abinda saƙonnin suka ƙunsa, babban burinta da fatanta bai wuce ta buɗe idanu ta ganta a tsakiyar falon gidanta ba. *_Ina sayar da datar MTN mai aminci da ƙarko. 1GB👉🏽N300, 2GB👉🏽N600, 3GB👉🏽N900, 4GB👉🏽N1200, 5GB👉🏽N1500. A tura kuɗin sayen data ta 5407827015, Farida Abdullahi, FCMB, sai a tura screenshot na shaidar biyan kuɗi da kuma bayanin yawan datar da ake so ta nan whatsapp a lambar wayata 07039080978_* Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/EjmQJ7W13K97BCI2wgWNWY *RABON AYI* *©Fareeda Abdallah* _*Littafin TUBALIN TOKA ya zama complete Document. Ga duk wacce take buƙata akan N400 ta tura kuɗin ta 5407827015, Farida Abdullahi, FCMB. Sai ta tura shaidar biya ta lambata 07039080978*_ _*3*_ Duk da mota ɗaya suka shiga wajen komawa gida zaman ƙuda ne a tsakaninsu, kamar ma waɗanda basu taɓa sanin juna ba. Ko wacce ta jingina kai da ƙofar mota ne suna kallon can waje. Ita Fatima babu wani fargaba da damuwa a tattare da ita, babu nauyin miji a kanta balle ta shiga ɗimuwa, shekarar mijinta biyu da rasuwa, shi yasa take dama kununta yadda take so. Ganin yadda Fareeda ta ɗaure fuska ta juyar da kanta ɓangaren ƙofa ne yasa itama tayi hakan, don kar ƙawartata taga kamar bata damu da halin da take ciki ba. Gidan Fareeda aka fara isa, da wata muguwar kasala ta buɗe ƙofar motar tana ƙoƙarin fita, hannunta ɗaya da Fatima ta riƙe yasa ta juya a hankali ta kalleta. "Na san duk inda Mukhtar yake ya dawo duba da yadda yaita kiranki akai-akai, ko in raka ki cikin gidan in taya ki ba shi haƙuri?" Murmushin yaƙe tayi, ta zare hannunta a hankali. "Babu komai, ki ƙarasa gida kawai. Zanyi masa bayani, babu abinda zai faru sai alkhairi in Allah ya yarda. Za muyi magana a waya" Bata jira komai ba ta mayar da ƙofar ta rufe, ta juya ta nufi ƙofar gidanta da sassarfa ƙirjinta yana luguden daka. Bakinta ɗauke da addu'o'i kala daban-daban. Ganin ƙaramar ƙofar gidan a buɗe saɓanin rufewar da tayi kafin ta fita shi ya ƙara tabbatar mata da Mukhtar ya dawo, ko da ta shiga cikin gidan sai ta rakuɓe a jikin ƙofar. Idanunta tsaye ƙyam akan motarsa da yake fake a tsakar gidan, jikinta babu inda ba ya rawa. Mara gaskiya aka ce ko a ruwa gumi yake, duk da sanyin iskar hunturu da ya fara kaɗawa bai hanata jiƙewa sharkaf da gumi ba. Ta lumshe idanunta, wasu zafafan hawaye suka silalo daga idanuwanta, zuciyarta cike da takaici da Allah wadai na wannan taurin kai da rashin jin magana irin nata. Ba sau ɗaya ba ba sau biyu ba sun sha samun saɓani da Mukhtar kan fita unguwa mara muhimmanci. Ya sha zaunar da ita yayi mata karatun dalla-dalla kan ra'ayinsa na rashin son ganin matarsa tana fita unguwa barkatai. Ko sha'anin ƴan'uwanta ko nasa idan ba mai matuƙar muhimmanci bane bai cika barinta ba, ballantana sha'anin ƙawayenta waɗanda kai tsaye yake kiransu da tarkace. Ta kai tsawon mintuna biyar a gurin tana tufka da warwara ba tare da samun hanyar da zai ɓulle da ita ba, daga bisani kawai sai tayi shahadar ƙuda ta mayar da ƙofar ta rufe, ta nufi cikin gidan ƙafafunta na harharɗewa saboda rashin gaskiya. "Daga ina kike?" Ta jiyo fusatacciyar muryarsa yana tambayarta cikin tsawa. Ƙam ta tsaya guri ɗaya, a hankali ta ɗaga idanunta ta kalleshi, yana zaune kan kujera mazaunin mutum ɗaya yana fuskantar ƙofar shigowa. Ya ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya yana karkaɗawa, alamun da ke nuna tabbas tsiya yake ji. Ƙyifƙifta idanu tayi, lokaci ɗaya suka cicciko da hawaye. "My de..." "Na ce daga ina kike?" Ya katse ta tun kafin ta ƙarasa faɗin abinda tayi niyya. Runtse idanu tayi, ta haɗiye wani kakkauran miyau sannan tayi ƙarfin halin cewa "Daga gidansu Jiddah..." "Na je har gidansu Jiddar ban same ki ba, ban tarar da kowa a gidan ba. Ki faɗa min gaskiyar daga ina kike yanzu Fareeda, idan ba haka ba Wallahi tallahi zan nuna miki wani ɓangare nawa da baki taɓa sani ba." Idanunta ta sauke ƙasa, cikin sanyin murya ta kora mishi bayanin zallar gaskiyar daga inda take a halin yanzu. Tun daman can ita ba gwana bace a ƙarya, ko tayi nan da nan ake ɓaro jirginta, shi yasa ako wane irin hali ta gwammace ta faɗi gaskiya duk abinda zai faru ya faru. "Ofishin ƴan sanda? Ke Fareeda? daga Ofishin ƴan sanda kike yanzu? Taɓɗijan! Lallai ma!!!" Ya faɗi kalaman da wani irin yanayi mai bayyana kaiwa ƙololuwa a takaici da baƙin ciki haɗe da mamaki. Fareeda ta goge mishi hadda, ko da ya dage ta faɗa mishi daga inda take yayi tsammanin za ta faɗa mishi sun fito gidan walimar Amarya ce. Matarsa a ofishin ƴan sanda sanadiyyar fita da tayi ba tare da izininshi ba shi ne ƙarshen tozarci da cin mutuncin da Fareeda ta taɓa yi mishi mai bala'in ƙuna a iya zamantakewar aurensu na shekaru shida. Tabbas zai ɗau mataki, ya zama dole ya ɗauki ƙwaƙƙwaran mataki kan Fareeda, ta yadda nan gaba ko da da amincewarsa ba ko wane karabitin unguwa za ta dinga tambayarsa ba. Tsam ya miƙe tsaye daga kan kujerar da yake zaune, hannayen rigarsa ya fara nannaɗewa yana yi yana ciccije baki. Idanu warwaje take kallonsa 'Rufe ni da duka zaiyi?' Ta tambayi kanta a zuciya. A iya zamantakewar aurensu duk bala'in Muktar ko dungurinta da ƴar yatsa bai taɓa yi ba. Lallai yau ta kai ƙololuwa wajen ɓata masa rai. A tsorace ta zube ƙasa ta ɗora hannaye biyu a kanta ta runtse idanu haɗe da fashewa da ƙaƙƙarfar kuka. Cikin kukan ta fara magana tana yi masa magiya "My dear... don girman Allah da darajar fiyayyen halitta SAW ka yi haƙuri... ka yafe min don Allah, wallahi in Allah ya yarda daga rana mai kamar ta yau bazan sake fita ba da izininka ba, kayi haƙuri don Allah kar ka duke ni..." "Yi min shiru Fareeda!!!" Ya katseta ta hanyar daka mata wani gigitaccen tsawar da yasa ta fara sakin fitsarin da tun ɗazu yake cike dam da mararta. "Na yi shiru, wallahi na yi shiru, don Allah ka yi haƙuri..." Wani murmushi mai bayyana matsanancin takaicin da zuciyarsa take ciki ya sakar mata, kan hannun kujerar da ya tashi ya ɗan ɗofana mazaunansa, da hannu yayi mata alamun ta tashi daga ƙasa ta hau kan kujera. Da rawar jiki ta cika umarninsa. Tsawon daƙiƙu casa'in yana ƙare mata kallo, Allah ya sani yana tsananin son Fareeda, soyayya kuma ba na wasa ba. Daidai gwargwado akwai zaman lafiya da kyakkyawar fahimtar juna tsakaninshi da ita. Babban abinda yake haɗa shi da ita taurin kai ne da rashin jin magana, ba sau ɗaya ba ba sau biyu ba ya sha sanar da ita yawan yawon zuwa gidan biki da suna shi ba shi a tsarin rayuwar zamantakewarsa da iyalinsa. Idan tana so su cigaba da tafiya cikin farin ciki da ɗasawa to tabbas ta bi abinda yake so, a lokacin za ta ce ta ji, har ma ta ƙara da ƙasƙantar da kanta ta bashi haƙuri, ta kuma ɗaukar mishi alƙawarin in Allah ya yarda baza ta sake ba. Wannan ba shi ne karo na farko da ta fita ba da izininsa ba, ta sha yin haka babu adadi, lallai wannan karon idan bai ɗauki hukunci mai bala'in tsaurin da zai jijjiga duniyar Fareeda ba baza ta san Annabi ya faku ba. "Ba dukanki zanyi ba Faree, a iya tsawon zamantakewarmu na taɓa dukanki?" Da sauri ta girgiza kai alamar a'a! "Kuma ba sau ɗaya ba ba sau biyu ba kina ƙetare iyakar dokokin da nake gindaya miki ko?" A kasalance ta ɗaga kai alamar eh! "Ki buɗe bakinki ki amsa min." "Eh! Don Allah..." "Saurara Fareeda, ki daina haɗa ni da Allah, na yi haƙuri, na kuma yafe miki." Da mamaki ta ɗaga idanunta tana kallonshi baki buɗe. "Eh tabbas na yafe miki. Rufe bakin." Kamar wata sakarya ta rufe bakinta, wani tsinkakken miyau da ya taho mata ta haɗiye da sauri. "Ki shiga cikin ɗaki yanzu kiyi wanka, kiyi alwala, ki gyara jikinki kiyi sallar magriba. Sai ki nemi abu mai sauƙi ki dafa min, rabona da abinci tun karin safe." Yana gama faɗin haka ya naɗe hannuwansa a baya, da wani irin taku na ƙasaita ya nufi cikin ɗakinsa, saɓanin ɗakinta da in dai yana gari anan suke gudanar da kusan komai na rayuwarsu. Ko da ya shige ta fi minti biyu tana kallon hanyar da ya bi, mamaki take yi, mamaki mai matuƙar yawa. 'Me yake damunsa ne? kai ko dai ba shi lafiya? Duk faɗa irinna Muktar shi ne za ta mishi irin wannan laifin kai tsaye ya ce ya yafe mata? Me yake faruwa?' Ire-iren tunanin da ke cikin zuciyarta kenan har ya ɗauro alwala ya fito ya tarar da ita a inda ya barta. Idanu ya buɗe da mamaki ƙarara a fuskarsa. "Menene haka kuma Sweety? Na faɗa miki fa yunwa nake ji." Yayi maganar da sanyin murya idanunsa a kanta. "Yi haƙuri, yi haƙuri Dear, yanzu zan samar maka abinda za ka ci." Tayi maganar cikin sauri, a zabure ta miƙe tsaye ta ɗauki jakarta da mayafin da ya faɗi ƙasa ta nufi cikin ɗakinta da sauri, har tana harɗe ƙafafu. Tana ɓacewa ganinsa ya ɗaure fuska tamau, yayi ƙwafa, ya cije gefen bakinsa na dama ya ƙanƙance idanu. Hannun rigarsa da ya naɗe don yin alwala ya warware sannan ya nufi hanyar fita daga ɗakin don zuwa masallaci. Tunani yake, tunanin irin matakin da zai ɗauka akan Fareeda. Lallai ya kamata ya ɗauki ƙwaƙƙwaran mataki, zai buge ta irin bugun daga kai sai me tsaron gida, ta inda zai lallasata tayi laushi, laushi kuma na har abada. Wani tunani da ya kurtso zuciyarsa lokaci guda ya saka shi sakin wani tattausan murmushi, ya girgiza kai alamun samun gamsuwa. *_Kar dai ku manta ina sayar da Datar MTN, mai so ta tuntuɓeni ta private 07039080978_* *RABON AYI* *©️Fareeda Abdallah* _*Littafin TUBALIN TOKA ya zama complete Document. Ga duk wacce take buƙata akan N400 ta tura kuɗin ta 5407827015, Farida Abdullahi, FCMB. Sai ta tura shaidar biya ta lambata 07039080978*_ _*4*_ Kasancewar tana da lafiyayyiyar soyayyar miyar da tayi jiya da daddare, sai kawai ta ɗora sanwar farar shinkafa. A gurguje ta faɗa bayi tayi wanka ta ɗauro alwala, tana fitowa ta wanke shinkafarta ta zuba sannan ta tayar da sallar la'asar da basu samu damar gabatarwa ba suna gurin ƴan sanda. A mafiyawancin lokuta in dai yana gari idan yayi sallar magriba ba ya fita daga masallaci sai ya sallaci isha'i, akwai karatun littattafan addini da Limamin masallacin yake musu tsakanin magrib da isha'i, in dai yana nan ba ya son rasa karatun. Ko kafin ya koma gida ta kammala girkinta tsaf, tana da ƙanƙarar pure water a frig, sai tayi amfani da wannan damar ta dafa zoɓo da kayan ƙamshi ta jejjefa ƙanƙara a ciki. Ya shiga falon ne a daidai lokacin da ta gama shirya komai kan ɗan madaidaicin teburin cin abincinsu da yake can gefe ɗaya a cikin falon. "Sannu da dawowa Masoyi." Tayi maganar a tausashe, fuskarta ɗauke da lallausan murmushi, tana kallonshi cikin ido. "Yauwa" Ya amsa a taƙaice, da fuska kadaran kadahan. A taƙaice ya kalleta ya ƙara kalla, ta yi kwalliya cikin wasu riga da wando na shan iska, kayan ko a ido basuyi alamar nauyi ba, kuma roba ne duba da yadda suka bi fatar jikinta suka lafe, sun fitar da ainihin shape ɗin jikinta. _'Fareeda ba dai ƙirar jiki mai kyau ba, tubarkallah ma sha Allah, baƙa ce a kalar fatar jikinta, amma ba irin baƙinnan ƙirin ba, baƙinta mai kyau ne da ɗaukar idanun mai kallonta._ _Doguwa ce a yanayin halittarta, sai dai irin tsawonnan da bai yi ma mace yawa ba, ga kuma ƴar ƙiba da cikar baya da ƙirji da take da shi, waɗannan abubuwa uku su suka taka muhimmiyar rawa gurin daidaita tsawonta._ _A fuska baza a kirata kyakkyawa ta gaban kwatance ba, amma kuma baza a jefata layin munana ba, tana da kyau daidai gwargwado._ _Kuma kasancewarta wacce ta laƙanci sirrin gayu da iya ɗaukar wanka idan ta fito baza'a taɓa cewa bata yi ba, za'a kalleta a ƙara kallah, ba kuma wai ɓata lokaci take a gurin shafa wannan goga wancan a fuskarta ba, a'a!_ _Ƴar powder kawai take shafawa sama-sama, sai ta goga man baki a laɓɓanta da suka kasance masu ɗan tudu, sanin sirrin gayun ƴa mace kuma yasa take ɗan ƙara tsuke bakin, lokaci bayan lokaci kuma tana ɗan tura leɓen ƙasa gaba sak na shagwaɓaɓɓun mata._ _Idan ta ɗan zizara kwalli a idanuwanta, kasancewarta mace mai yalwar gashin gira tana ɗaukan wasu daƙiƙu gurin tacewa da daidaita kwanciyarsa._ _Har yanzu da take cikin shekarunta na ashirin da tara fuskar ƴanmata ƴan sha takwas take da, idan ba sani aka yi ba baza'a taɓa cewa ita ce tayi haihuwa uku ƴaƴa huɗu ba saboda kyawun jikinta._ _Haihuwarta na farko da na biyu duk basu zo da rai ba, sai na uku ne ya tsaya, da lokacin haihuwar yayi ta haifi ƴan biyu duk maza._ _Sun shekara ɗaya da wata takwas cif kafin mahaifiyarsa wacce suke kira Hajiyarmu ta ɗauki ƴaƴan yaye, a yanzu haka suna can gidanta a unguwar dosa. Ta ko wane ɓangare Fareeda ta kai irin macen da ko wane namiji mai hankali zai so aura a matsayin matarsa, babban matsalarta rashin jin magana da taurin kai. Shi ya ƙi sakar mata mara ta dinga fita yadda take so, ita kuma a matsayinta na wacce take ƙasansa ta ƙi haƙura ta watsar da tsarin rayuwarta ta bi abinda yake so. Sai yaushe ne za ta gyaru...?'_ "Masoyi lafiya dai ko? ga abincinka na gama haɗa duk abinda za ka buƙata" Saukar muryarta shi yayi nasarar dawo da shi daga duniyar zurfin tunanin da ya afka. Bai ce mata komai ba, kuma a maimakon ya nufi ɓangaren da ta jera mishi abinci sai ya kama hanyar zuwa ɗakinsa. Da sassarfa ta bi bayanshi, yana shiga ɗakin ta ɗora ƙafa a inda ya cire tasa. "Ya aka yi?" Ya tambayeta da mamaki a fuskarsa. Narai narai tayi da idanu suka cicciko da ƙwallah, ta riƙo hannayensa guda biyu a cikin nata. "Na san na ɓata maka Mijin Fareeda, don Allah kayi haƙurii..." "Na zaci mun gama wannan maganar?" Ya katse ta idanunsa a cikin nata. Ƙwayoyin idanunta ta saukar da su ƙasa a hankali, sai a lokacin ta ba hawayen damar sauka zuwa kumatunta, sai ta sake ɗaga idanu ta kalle shi "Walwalarka nake buƙatar gani Masoyi, idan baka huce ba don Allah kayi min faɗa, kayi ta faɗa idan ta kama ma ka haɗa min da duka har zuwa sadda za ka ji sauƙin zuciyarka. Wannan yanayin damuwar da nake gani shimfiɗe a kyakkyawar fuskar mijina sam ba na jin daɗinsa." Sai kuma ta fara ɗan jan hanci tana shessheƙa, hawaye wasu na korar wasu. Ya buɗe baki zaiyi magana ta yi saurin katse shi da cewar

Chapter 2 of 26