Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
titi yana kallon ta "Shine abinda ya fara zuwa kai na..." Ya fadi yana maida hankalin shi kan titi, wata irin dariya Madina ta kwashe da ita "Da gaske Hamma?" Lubna sufyan Hausabook.com 223 Ta tambaya, kafadu yadan daga yana rausayar mata da kai "Kinki mun hira... Bansan me zance ba" Yayi maganar da dukkan gaskiyar shi, hannu takai ta gyara gilashin fuskarta tana sauke numfashi, har lokacin da murmushi a fuskarta. Kawai ba zatace ga asalin abinda yake damunta ba duk satin. Ta san zazzabi, da shine zata gane, babu inda take ji yana mata ciwo, kawai tana jin kamar dai akwai wani abu da babu a cikin rayuwarta a satin. "Bajjo zaiyi aure" Daada ta fada mata, ta zabi ta fada mata lokacin da ta cika bakinta da ruwa tana shirin hadiye wa, ta kuwa sarke tana tarin da ta kusan shafe mintina biyar bai tsagaita mata ba, idanuwanta duk sun tara hawayen wahala "Cikin satin nan idan Allah ya bamu aron rai" Daadar ta sake fadi, ko da taso yin wata tambaya bata san ta inda zata fara ba, tambayoyin nata da yawa, wata na danne wata haka suka dinga tasowa cikin kanta. A lokaci daya kuma tana Lubna sufyan Hausabook.com 224 nemar ma maganar wajen zama a tare da ita cike da son gane me hakan yake nufi da tata rayuwar ko wata dangantaka da take tsakanin auren na shi da ita. Shisa sai komai yayi mata yawa, abu dayane take jin zata iya cewa, kamar Nawfal din bai kyauta mata ba, kamar daga bakin shi ya kamata ta fara ji. Kamar ya kamata ace tasan maganar. "Kunyi shakuwar da zai gaya miki zaiyi aure ne?" Wata murya ta tambayeta, ta so tayi gardama, taso ta zayyano ma muryar shekarunta na kuruciya, lokuttan da Nawfal yake daukota akan bayan shi daga makarantar islamiyyar su zuwa gida kamar bata da wani nauyi, lokuttan da take jiran zuwan shi dan ta zayyana mishi duk wasu kananun bukatunta ya kuma cire kudin shi ya biya mata su. Sai ta tuna da shekaru biyun da suka ja layi a tsakanin su, abubuwa da yawa zasu iya fara a cikin awanni biyu, balle a tsallaka awannin da suke cikin ranakun da suka shude tare da shekara biyu. "Ma shaa Allah. Allah ya tabbatar da alkhairi" Lubna sufyan Hausabook.com 225 Tace maimakon furta ko da daya daga cikin tambayoyin da take da su ne. Hidimar da ta fito da ita ta cigaba dayi, ba dai tasan dalilin Daada na binta da wani irin kallo mai cike da ma'anoni ba. Ba zatace tausayawa kawai ta gani a cikin kallon ba, kamar Daada na son sanar da ita auren Nawfal din yana da alaka da rayuwarta ne, ta kasa fahimtar kalaman da Daada ta zabi tabar su cikin idanuwanta maimakon ta furta mata su. A ranar da ta shiga dakin ta, bayan ta zauna ta dauki agogon Nawfal kamar yanda sabonta yake sai ta tsinci kanta da saukowa daga kan gado tana neman waje ta jefa agogon a ciki. Har yau da take zaune a cikin motar Salim da yazo daukarta zuwa restaurant din da suka yanke hukunci zuwa yasu-yasu dan gudanar da yar walima ta taya Nawfal din murnar auren shi da aka daura a safiyar Asabar din ba zatace ga dalilinta na adana agogon ba. Hannun Salim da taji a gefen kuncinta na sata saurin janye jikinta kamar wadda wuta ta taba, sake mika hannun shi yayi kamar bai ga yanda ta hade da murfin motar ba, ji yayi babu zazzabi a jikinta. Sannan Lubna sufyan Hausabook.com 226 ya janye hannun shi yana gyara zaman shi yana fadin "Shirun ki yayi mun yawa" Numfashi ta sake saukewa a karo na biyu "Banda labari ne fa... Yau zan missing karatu a islamiyya, bana fashi in ba rashin lafiya ba sai bikin Adee, zasu ga banje ba yau ma kuma ban fada ba" Kai ya jinjina "Zasu dake ki ne?" Saboda tunanin wani zai taba lafiyarta na sa jikin shi daukar dumi da wani yanayi na bacin rai "A'a, ba su cika dukan fashi ba inba kana yawan yi ba" Duk da haka hankalin shi yaki kwanciya "Kin tabbata?" Yayi tambayar cikin harshen turanci "Na tabbata" Lubna sufyan Hausabook.com 227 Ta bashi amsa cikin harshen itama, yana shan wata kwana ya dan rage gudu alamar yana son samun damar da zai tsallaka titi ne, tana kuma iya ganin sunan restaurant din Tasty Corner. Sai da ya tsallaka ya samu waje yayi ajiye motar yana kashewa tukunna take kara ganin kyawun restaurant din tun kafin ma su shiga. Da yake banda makaranta babu inda take zuwa, sai nan cikin unguwar su, sai kuma gidan Julde da shima tana dadewa bataje ba, a garin Kano tsaf zaka siyar da ita. Babu inda ta sani, yanzun ne ma da Salim ke yawon dauko ta daga makaranta yakan biya wani wajen yayi mata siyayya, har wani wajen saida litattafai sukaje da bata san a ina bane ba, amman yayi mata kyau matuka. Da kan shi ya zagaya ya bude mata murfin motar ta fito. Sai lokacin ya kalli kayan jikinta, jeans ne baki, kamar yanda ta saba ta nannade shi har kwaurinta ya dan fito, sai fararen kambas, rigace ta sanyi mai dogon hannun da taja baya, itama farace kamar hijabin kanta. Ta dora wata farar hular sanyi a saman kanta. Murmushi yayi yana tsayawa a gabanta yana kara mamakin gajartar Madina, da kadan kanta ya wuce cikin Lubna sufyan Hausabook.com 228 shi, kama hular yayi yana cire ta daga kanta ya duba kamar mai son gano wani abu a jiki. Murmushin dai ya kasa barin fuskar shi har lokacin, gyara hular yayi a cikin hannun shi yana dorawa saman kanta kafin ya gyara mata ita saman kanta, ganin yanda take kallon shi yasa shi amfani da dan yatsa ya tura mata gilashin da yasan gab take da dago nata hannun ta gyara mishi zama. "You look like a Mug" Salim yace muryar shi dauke da wani irin yanayi da yake jin fitowar shi daga zuciyar shi, kai Madina take girgiza mishi tana kokarin danne dariyar da take son yi saboda hada tsayinta da kofi da yayi "Ba zaka fara kirana da Mug ba Hamma" Girar shi daya ya daga mata "Gargadi ne?" Kai ta girgiza da sauri tana saka shi lumshe idanuwan shi yana bude su a kanta "Mug it's then... Muje" Lubna sufyan Hausabook.com 229 Juyawa tayi kuwa, wani murmushin na kara kwace ma Salim, da gaske tayi kama da yan kofinan nan masu kyau da ake zuba coffee a ciki, masu murfin da marassa murfi, amman masu kyan cikin haka yake ganin tsayinta a gaban shi "Mug" Ya furta dai-dai kunnuwan shi da murmushi a labban shi, har takai kofar wajen ta juyo tana kallon shi da tunanin abinda ya tsayar da shi, taku biyar yayi ya karasa inda take suna shiga tare, can wani teburi da yake karshen wajen ya hango su Khalid, sai kuma hannuwan Adee duka biyun da take daga musu kamar yace bai gansu ba. Baima san me yasa mijinta yabar ta fitowa ba duka sati daya da aure, dariya take tana sake daga musu hannuwa, dakuwa Salim yayi mata daga inda yake yana kallo ta sake kwashewa da dariya kamar wadda ya bawa kyauta. Suna karasawa tana tashi daga wajen da take zaune ta kama hannun Salim din da yake kokarin kwacewa yana daure fuska "Wallahi nayi kewar ku sosai" Lubna sufyan Hausabook.com 230 Ji tayi kamar tayi waya bakwai bata gansu ba "Sakeni dalla" Tabe baki Adee tayi, matsalar Salim ba'a mishi gwaninta, tana zame hannuwanta daga nashi ya daga ya dillar mata bakin da ta tabe mishi "Dan kinyi aure zaki mun rashin kunya" Dafe labbanta tayi babu shiri "Ouchh... Hamma" Kallon da yayi mata yasa ta koma ta zauna, kujera yaja shima ya zauna yana dan kara janta gaba, kafin ya kalli agogon hannun shi "Minti talatin..." Ya fadi yana kallon su, yana da hidimar da zaiyi, ko bashi da ita baida hirar da zaiyi da su, hayaniyar zata dame shi. Gara yaci abinci ya barsu suyi hirar su cikin nutsuwa. Kallon juna Khalid da Nawfal sukayi, dan sunyi gulmar shi, babu ma wanda ya kawo zaiyi minti talatin din duk a cikin su Lubna sufyan Hausabook.com 231 "Ni nace maka Hamma ba zai minti biyar a wajen nan ba" Cewar Khalid "In za'a iya mishi takeaway din duk abinda yake so a kasa da minti biyar ba zai kai ba" Nawfal ya kara, basu taba tunanin zai zauna a waje irin haka yaci abinci ba "Nasan kunyi gulmata" Ya fadi kasan makoshi yana duba menu din da waiter din wajen ya kawo mishi bayan ya dan daga hannu cikin alamar kira, dankali da kaza ya zaba sai bakin lemo yana kallon Madina da tunda ta zauna idanuwanta na kan Nawfal, bata ganshi ba tun da akayi mata zancen bikin, bai kwana a gidan Daada ba, sanda yazo tana makaranta sai dai inta dawo Daada tace mata Nawfal ya zo. Yanzun da ta ganshi kawai sai take jin kamar abin wasanta da ta dade tare da shine aka fisge daga hannun ta. Kai tsaye ba zatace ranta ya baci ba, amman kuma bata farin cikin da kwacen, wani yanayi ne Lubna sufyan Hausabook.com 232 a tsakanin abu biyun da bata san wacce kalma zatayi amfani da ita wajen fassara shi ba "Madina..." Salim ya kira a hankali yana dan daga mata Menu din da yake hannun shi bayan ta kalle shi "Abinda duk aka baka" Ta ce cikin sanyin murya, su Nawfal ya kalla, kowa ya fara jero abinda za'a kawo mishi "Madina yaushe zaki zo gidana? Kinsan ina fushi daman, baki je kaini ba, na kula ai" Murmushi Madina tayi, har ranta tayi niyyar zuwa kai Adee din tunda harda Daada, a wajen motocin daukar amaryar taji an riko mata hannu ana janta, kafafuwan shi ta fara kallo ta gane waye "Hamma..." Ta kira, bai amsata ba ya cigaba da janta har suka inda motar shi take ya bude murfin yana sakin hannunta, yanayin fuskar shi yasa ta shiga batare da tayi musu ba, ya ja motar da bai tsayar ba sai a kofar gidan Daada, nan sukayi zaman su Lubna sufyan Hausabook.com 233 a ciki suna hira, ko tace tana mishi surutun da yake amsawa dai-dai. Har fita suka kara yi ya siyo musu tsire mai yawa da lemo. "Zan zo, Hamma zai kawo ni. Kibari kunshin ki ya karasa gogewa, sai ki kira Daada kinga idan nazo sai in miki sabo" Kai Adee ta jinjina "Kin kusa ki wanke laifin ki" Yar dariya tayi tana kallon Nawfal "Hamma Ango" Hararta yayi "Yanzun ne zaki kula ni? Bana so" Hannuwanta ta hade waje daya cikin ban hakuri "Ance angwaye basa fushi fa ko Hamma Khalid?" Dariya Khalid yayi "Ni zan shiga fadan ku? Ku shirya ku ware ni yanda kuka saba? Babu ruwana, sai dai babban Yayaa" Lubna sufyan Hausabook.com 234 Ya karasa maganar cikin sigar tsokana. Wani kallon kashedi Salim ya watsa mishi yana saka shi gyara murya "Idan na taso saina mare ka" Salim ya fadi yana sa Adee kwashewa da dariya "Me nayi ni kuma?" Ko da ba'a fara kawo musu abincin su ba yasan ba amsa zai samu ba. Hira ce ta barke tsakanin Nawfal, Khalid da Adee, Salim abincin shi yake ci duk da maganganun su da yake ji har cikin kwakwalwar shi, Madina ma abincin take ci tana tsintar dankalin dai-dai. Salim na kallonta ta gefen idanuwan shi, dan ture plate din shi yayi yana jan nata bai damu da kallon mamakin da take mishi ba, wuka ya dauka yana yayyanka mata cinya guda biyu kanana yanda zata iya dauka kafin ya tura mata plate din batare da yace komai ba yaci gaba da cin abincin shi. Lemon da yake gabanta ma shi ya bude yana zuba mata a kofi ya tura mata kusa da ita. Da ya gama cin nashi abincin ma ita yake kallo. Lokaci zuwa lokaci takan dago su hada ido, ta saba ciye- Lubna sufyan Hausabook.com 235 ciye a gaban shi, tasan dai idan ta ajiye cokalin magana zai mata tunda ba wani ci tayi ba, ita kuma tana turawa ne badan tana gane dandanon abincin a bakinta ba, sai da taci kusan rabin naman da yayayyanka mata tukunna ta ajiye cokalin a ciki tana dan ture plate din. Ganin girar da Salim ya daga mata cike da alamar tambaya ya sata fadin "Na koshi Allah, tuwo Daada tayi mana" Baice komai ba ya mike yana karasawa inda zai biya kudin ya kuma bama Madina damar yi musu sallama, idan yabarta zasu mayar da ita gida ya sani, bai san ko tana so ta zauna ba, ba tambayar ta zaiyi ba. Yanda suka zo tare haka zasu koma tare, saboda hakan yake jinyi badon yana da wani kwakkwaran dalili ba. "Allah yasa alkhairi Hamma, Allah ya kawo zuri'a dayyi ba" Madina ta fadi tana rasa dalilin da yasa take jin wani iri "Zan zo anjima" Lubna sufyan Hausabook.com 236 Nawfal ya amsa, kai ta jinjina mishi tana mikewa, Khalid ne ya kalle ta da fadin "Ki bari mu tafi gabaki daya mana, ba sai mu sauke ki ba" Kai ta girgiza mishi "Hamma zai ce a'a" Dakuna mata fuska Khalid yayi "Ka kyaleta Khalid, kiyi tafiyar ki Madina, saina kira Daada..." Numfashi ta dan sauke bata ma amsa ba ta juya "Kai ina ruwan ka? Baka ga tare suka zo ba?" Ruwa Nawfal ya kurba ya hadiye sannan yace "Ni kadai naga Hamma ya yankawa Madina nama?" Dariya Khalid yayi "Wallahi kiris in shake da taliya... Anya Hamma?" Kai Adee ta girgiza Lubna sufyan Hausabook.com 237 "Kuna da bala'in gulma yaran nan, ina ruwan ku? Sai na fada mishi" A tare suka kalle ta, dan kasa tayi da murya kamar tana tsoron Salim din zaiji ta "Amman da gaske me yake faruwa ne?" Kallon 'maganar da nakeyi kenan ai' Khalid yayi. Hirar suka dan karayi kafin su saki zancen suna kama wani tunda sun san koma menene ba zai wuce su ba, suna zaune zai zagayo kowa ma ya gani. * "Yanzun wanne mai hankali ne ya dauki yarinya yaba Bajjo?" Saratu ta fada tana tabe baki "Mai irin hankalin wanda ya daukeki ya bani" Julde ya amsa ta, amsar kuma tayi mata zafi "Ubana kenan?" Bai ce komai ba, sakon ya isa baya bukatar jan magana kuma Lubna sufyan Hausabook.com 238 "Idan wulakanci abinyi ne ka cigaba da wulakantani Julde, Allah ya baka sa'a, hirar arziki ma ba zan taba samu inyi da kai ba saika gasa mun magana" Shirun dai shi ya kara yi mata yana cigaba da neman kayan da yake son sakewa dan ya fita yabar mata gidan ma gabaki daya, a gajiye ya dawo daga Abuja tunda acan ya kwana aka daura aure da safe ya tsaya wata hidima da ta shafi kasuwan cin shi tukunna ya juyo "Kuma sanda na aure ka aika girmi Bajjo, shekarar ka wajen ashirin da biyar" Gani tayi da gaske bashi da niyyar amsata, wasu hawaye taji masu zafi sun taru cikin idanuwanta. Duk kawayen ta haka suke cewa tayi sa'a, mijinta ga arziki ga kyau "Ko yanzun mijinki yaso zai auri budurwa wallahi da zata bi kyawun shi" Wata kawarta ta taba fada, dan yanzun ma sun raba jaha, daina sakar mata fuska tayi tun da aurenta ya mutu, saboda matar ba karamar gogaggiya bace ba. Ko da aurenta ma duk yanda Lubna sufyan Hausabook.com 239 kuke karka fara yaba kyawun mijinta yanzun zata daina sauke girarta a gabanka. Wani irin kishin shi takeyi na ban mamaki, shisa duk idan taga zai fita haka take jin kamar baza'a waye safiyar ranar da ita ba saboda bacin rai. Da mutanen da suke mata kallon tana zaune a wannan tankamemen gidan tana kuma auren namiji kamar Bajjo sun san me take hadiya da ta daina basu sha'awa. Ita a bakin yaran da ta haifa da cikinta ma bata ji zancen cewa Nawfal zaiyi aure ba. Yara kamar ba daga jikinta suka fito ba, yanda suke nanike ma Nawfal din yana bata takaici. Sai jiya da Julden zai tafi Abuja yace mata "Gobe da safe za'a daura auren Bajjo" Tambayar duk da tayi mishi kuma bata samu amsa ba. Haka ya tsallake ta ya wuce, son da take mishine abinda ya sata yi mishi addu'ar dawowa lafiya. Sai Adee ta kira, itace take fada mata kowa zai aura da inda suka hadu. Duk da bangare mafi rinjaye a zuciyarta na tare da bakin cikin kalar matar da ya samu, sauran karamin kashin yaji dadi da kuma fatan su Lubna sufyan Hausabook.com 240 karata can, ta rike shi karya dawo. Kar ya sake waiwayo su, inda yake ya zauna kamar Bukari, danma yanzun zamani ya canza ko ba'a ga fuskar juna ba za'aji muryoyi, da tace aji shi dif, ayi zaman makokin da babu gawa idan anyi cigiya an gaji. Ya zamana sunan shi ma zaiyi ma kowa nauyin ambato kamar yanda na mahaifin shi yayi. Wannan shine fatanta, Nawfal yayi ma rayuwar ta da ta ahalinta nisa Wannan karin ma kaddara ce ta riga fata Kaddarar da take bibbiyar mutanen da ta kira ahalin ta da Nawfal din da ta zabi ta ware a cikin su Bata sani ba Bata san shi din haske bane a tare da su Bata san shi zai zame musu katanga a lokacin da tarihi ya maimaita kan shi ba "Sai da safe" Julde ya fadi yana nufar kofa, hannu tasa tana share hawayen da ya zubo mata. Yana fita yaja Lubna sufyan Hausabook.com 241 mata kofar, a jagule yake jin zuciyar shi harya fice daga gidan, inda ya tsaya ya siyi lemon zaki yaji wani yace "Mero!" Sai da zuciyar shi ta nemi fitowa daga kirjin shi saboda tsallen da yaji tayi, da sauri ya waiga yana ganin yarinyar da bata wuce sa'ar Adeen shi ba da take tattare kwanoninta da alama abinci ta gama siyarwa a wajen, lumshe idanuwan shi yayi ya bude su "Maigida ga canjin ka" Mai lemon ya fadi, karba Julde yayi ya karasa motar shi ya zauna a ciki yana dora kanshi da abin tukin, har lokacin numfashi yake fitarwa cikin kokarin dai-dai ta bugun da zuciyar shi "Naji maganganu kala-kala akan ka, wanda duk yake tunanin ya isa dani yace mun kar in aure ka... Ya zanyi da zuciyata Julde? Ya zan fito musu da ita su fahimci hakuri da kai baya cikin zabin da nake da shi?" Lubna sufyan Hausabook.com 242 Kalaman Mero suka dawo mishi kamar tana cikin motar a tare da shi, sake runtsa idanuwan shi yayi "Na yadda kowanne rai da nashi kaddarar, kai ne kaddara ta Julde..." Ya rasa yanda lokaci zai zama mai adalci kuma marar adalci a lokaci daya, yanda yake wucewa batare da ya jira kowa ba shine babban adalcin shi, amman yanda idan ya wuce baya dawowa kowa a wajen Julde hakan rashin adalci ne, ya zaiyi da kadan daga cikin kurakuren da yake jin zaiso ya sake samun aron lokaci dan ya sauya zabukan da yayi? Yau bama wani waje yake son komawa ba, rana daya ce, dakika ne kayadaddu a cikin ranar da zai sauya amsar da ya bama Mero, so yake ya kalleta ya fada mata ita ce kaddarar shi bashi bane kaddararta. "Mero tayi aure" Labarin ya riske shi shekaru hudu bayan rabuwar su, labarin da saida yayi yar karamar jinya a kan shi, hangota da wani, hango rayuwar da tayi da shi tana yinta tare da wani ba zai daina kassara zuciyar shi ba. Shi kadai yake Lubna sufyan Hausabook.com 243 dawainiya da ita a ran shi, ita ta shafe babin shi daga rayuwarta harta bude wani sabon shafin tare da wani. Bai tambayi a ina ko wa ta aura ba, abubuwan da yake gujema cikin sanin masu yawa ne. Da duk rana da yanda yake jin kusancin ta a zuciyar shi yana kuma jin nisanta da rayuwar shi Da ya san kaddara ta adana musu shafin sake haduwa a titi daya da ya sauya tunani In da yasan haduwar da zasu sake yi da Mero zata tono mishi abubuwan da za'a hada da rayuwar shi ta baya da ta yanzun a waje daya daya duba zabukan da yake da su Dago kan shi yayi yana sauke wani irin numfashi ya tayar da motar fitilar ta na haske wajen har yana shirin kashe mishi idanuwan daya dan jima da su a runtse, sai da yasa hannu ya murza idanun, duk da haka ji yake hasken kamar yayi mishi yawa Da yasan duhun da yake bibiyar shi watakila da ya nemi duk wani haske da zai iya kafin lokaci ya kure mishi Lubna sufyan Hausabook.com 244 Kaddara Kaddarar dai... Ya baro tushen shi saboda ita Tana biye da shi har wajen da yake tunanin ya boye mata Bai san ko ya kamata ace yana jin shi wani iri tun safiyar ranar ba, da Julde ya kira shi yace an daura ma baiji wani abu ba. Wasu kance sunji su kamar suna yawo kan gajimare saboda farin cikin an daura musu aure. Shi baiji duk wannan ba, farin ciki, yana cikin shi tunda ya samu goyon bayan su Julde akan auren, na rana daya bai taba jin ba zai samu Murjanatu ba, sai dai in rashin tabbas na rayuwa, mutuwa ta raba tsakanin su. Shi da ita din basu fara soyayya lokaci daya ba, daya ganta in da ance zaiji wani abu a kanta, ko zai kirata matar shi wata rana zaiyi mamaki. "Ka zauna mun a waje" Lubna sufyan Hausabook.com 245 Shine maganar farko da tayi mishi a coffee shop din daya shiga cikin harshen turanci , an kuma hado mishi irin yanda yake so da kankaru a ciki. Ya zabi teburin ne saboda yana can lungu, kuma mai kujera biyu ne da ba lallai inka zauna kaga wani ya zo ya zauna kusa da kai ba. Harya hango yanda Coffee shop din zai zamana wajen zuwan shi duk rana. Yanda take kallon shi haka shima ya daga kai ya saka nashi idanuwan cikin nata, da yake lokaci ne na sanyi, shigar sanyi ce a jikinta, iya abinda yake gani na daga fuskarta ya gane ita din me kyau ce, kyau irin wanda zaka gani a kallo daya. "Banga sunan kowa a wajen ba kafin in zauna" Hannuwanta da babu safa ta murza kamar sun daskare mata "I'm a regular a wajen nan. Kowa zai fada maka corner dina ce nan" Ta karashe maganar da hausa wannan karin dan yayi mata kama da bahaushe "Kaga karfin hali" Lubna sufyan Hausabook.com 246 Ya fadi da fulatanci a muryar da yayi tunanin dai-dai kunnen shi ta tsaya "Ba karfin hali bane ba, gaskiya ce" Ta amsa shi da fulatancin tana ganin mamakin daya bayyana akan fuskar shi, dayar kujerar taja ta zauna "Bafullatana ce ni, tunda kaji nayi hausa bai kamata kayi mamaki dan nayi yare na ba" Dariya yayi, ba dan akwai abin nishadi a muryar ta ba, sai kwarin gwiwar ta da yanda take mishi magana kamar ta dade da sanin shi. Kamar ta san cewa ita da shi din ranar ne labarin su ya fara, sai da aka kawo mata abinda tayi order harda cookies ya gani sannan ta sake ce mishi "Murjanatu Faruk" Kai ya jinjina mata "Nawfal Bukar" Ba zaice sunyi hira ba, ta dai riga shi tashi daga wajen dan lokaci zuwa lokaci tana duba agogon da yake wajen, yanayin ta ya nuna cikin sauri take. Lubna sufyan Hausabook.com 247 "Next time ka nemi wajen ka, this is my spot" Dariya kawai yayi, kafin ma ya amsata tabar wajen. Ko da ya tafi ba zaice yayi tunanin ta ba, daga ranar ma zuwa safiya ko sau daya bata fado a ran shi ba. Watakila duk littafine da finafinai ke zuzuta wannan kalar soyayyar. Sai ace idanuwa sun sarke cikin na juna shikenan har soyayya ta kullu, ko an gogi juna jiki da ruhi sun girgiza. Watakila kuma kaddara ta hada hanyar shi da Murjanatu ne dan su kafa tarihin da zai karyata wannan kalar soyayyar. Sunyi haduwa wajen goma bayan nan, ta shigo Coffee house din shi zai fita, ya shigo ita zata fita, banda gaisuwa babu wani abu da yake hada su. Maganar su ta fara tsayine randa ta same shi zaune da sketch book dinshi yana nazarin wasu zanunnuka "Kai Artist ne?" Ta tambaya, zai tuna ya girgiza mata kai, kamar ba zai ce mata komai ba kafin ya amsa "I'm a furniture designer, ko ince abinda nake karanta kenan" Lubna sufyan Hausabook.com 248 Gabaki daya hirar su akan abinda yake karantawa ne har suka rabu. Zaice ita ta fara neman shakuwa da shi, ta fara neman alakar su ta wuce haduwa a Coffee Shop din bayan ta gayyace shi wani furniture showcase da za'ayi a cewarta baban dan ajin su ne a wajen ko wani bayani da ba zaice ya fahimta ba gabaki daya, an gayyace ta, ita kuma ta gayyace shi. Ya amsa ta da cewar zaije ta rubuta mishi lambar ta a takarda tana ajiye mishi sukai sallama. Ranar ta bude musu sabon shafi, dan duk wani yunkuri da zaiyi sai ya gan su a tare a wani wajen, sai yaji kamar dama can ya santa ne, babu wata bakuntar juna a tare da su. Kamar yanda a cikin duk wata dariya da zasuyi ya fara jin ba ita bace ta karshe. A cikin shekara daya sunyi wani irin sabo da kalamai zasuyi karanci wajen fassara shi, dan a gidan su Murjanatu babu wanda bai san shi ba, har idan an nemeta ba'a samu ba, yana cikin jerin abokanta da Mamanta ko babanta zasu fara kira suji ko suna tare ko kuma ta fada mishi inda taje. Rana daya ya tashi da safe yaji baya son hango tana da kayadadden lokaci a rayuwar shi, baya Lubna sufyan Hausabook.com 249 son hango wasu ranaku a cikin rayuwar shi da babu ita a cikin su "Ina son kasancewa da ke, fiye da abokanta" Ya fada mata batare da shakku ba, ta dauki mintina biyar, har saida shirunta ya fara tsoro ta shi kafin ta dago tana saka hannuwa ta dauke kwallar dake cikin idanuwanta "Na dauka ba zaka taba tambaya ta ba" Tayi maganar muryarta na rawa "Ka san tun yaushe nake son ka" Kai ya girgiza mata, jin tayi shiru na sa shi fadin "Wannan na da muhimmanci ne yanzun?" Dariya tayi mai sauti "Babu, kana jin yanda nake ji, shine a saman komai" Daga nan suka fara, bai san a inda zasu tsaya ba. Ya dai san zai karasa sauran rayuwar shi tare da ita yana mata godiyar yanda ta yarda da shi da zuciyarta, da farin cikinta harda abubuwan da tasan shi kan shi bashida tabbaci akan su. Lubna sufyan Hausabook.com 250 "Zan sauke ka gidan Daada ko in wuce?" Khalid daya turo dakin ya fadi yana katse mishi tunanin da yakeyi "Hamma mana, ba zaka dinga kwankwasa daki ba zaka shigo" Dan karamin tsaki Khalid "Har wanka na maka Bajjo" Dafe kai Nawfal yayi yana fadin "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un" Kafin ya dago ya kalli Khalid din "Zan wuce wallahi ina da abinyi..." Mikewa Nawfal yayi "Da zan kara watsa ruwa ne" Ganin yanda Khalid yaja kofar ya rufe yasa shi karasawa wajen kofar da gudu yana budewa "Yi hakuri ka jirani in dauko jakata" Dariya yayi ganin hararar da Khalid ya watsa mishi. Anan cikin falon Khalid yake tsaye yana Lubna sufyan Hausabook.com 251 jiran shi dan baiji shigowar Salim ba sai ture shin da yayi yana furta "Tashi dalla" Sake matsawa Khalid din yayi, dan Salim ya tsani ka tsaya akan hanya, ya dan fara rage saurin hannu da ya mare shi, ko kuma sun fara girma ne a idanuwan shi, Khalid din ba zaice wanne bane a cikin biyun, dakin shi Salim ya wuce yana rufo kofar, dai-dai lokacin da Nawfal ya fito yana janyo tasu kofar dakin "Uban

Chapter 9 of 18