Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ka karo uku ka ajiye mu zama mu hudu, zamu isheka, mun isheka Julde, dan Allah..." Murmushin da baka raba fuskar shi da shi yayi mata, ko ranshi a bace yake kuwa zaiyi murmushi "Ajiye mata hudu ba zai hanani hangen wasu ba Saratu, ke dinma ya na kare dake? Aure, yarana kawai da nake kallo suke hanani dana sanin zaman aure dake, ko dan irin wannan surutan da kike yawan yi mun. Zan sake maimaita miki in ba zaki iya zama dani ba furtawa kawai zakiyi...kiyi harkarki inyi tawa, zaki iya nemar mun shiriya idan kina da wannan lokacin, in baki dashi kibar ni da halina..." Lubna sufyan Hausabook.com 28 Ba dan tana da wani ilimin addini ba, sallah da tsarki ma yanda zatayi su a tsarin addini a gidan Radio ta koya. Anan taji kalar kuskuren da take tafkawa a rayuwarta, amman zata iya cewa jahilci na daya daga cikin babbar cutar da take damun Julde. Watakila da yayi makaranta, ta boko ko ta addini zai rage wasu abubuwan. Yanzun ma lokaci bai kure mishi ba idan har yayi niyya, tunda ita ma takan saurari kasakasai da ta siyo na wa'azi kala-kala kuma tana karuwa. Shisa halayen shi suka hadu suna mata ciwo biyu yanzun, kishin shi da kuma matsayin abinda yakeyi ga makomar goben yaran su. Komawa tayi ta kwanta, bata koyi kokarin share kwallar da take zubo mata ba. Sosai kirjinta yake zafi, musamman da zuciyarta ta shiga hasaso mata hotunan inda Julde yake da abinda yakeyi. Idanuwanta taji sun bushe rayau, ko alamun bacci babu. Tana jin hawayenta tun suna zuba har suka daina, banda ajiyar zuciya babu abinda takeyi, ko juya kwanciya batayi ba, ta dai ja jikinta sosai ta dunkule waje daya ko zata samu saukin zafin da kirjinta yakeyi. Ba duba agogo takeyi ba balle ta san ko karfe nawa, Lubna sufyan Hausabook.com 29 kawai dai taga daren yayi mata wani irin tsayi ne. Kiran sallar asuba kawai take saurare taji an turo kofar. Tana jin kai kawon shi, tasan kayan jikin shi yake ragewa. Bata dai motsa ba, kwan dakin daya kunna kafin ya fita yaje ya kashe ya dawo yana hawa gadon. Jin da tayi ya rikota yana juyawa da ita ta fuskance shi ya sa ta fara kiciniyar kwacewa, sai dai karfin su sam ba iri daya bace ba, ko sirantaka irin ta yawancin fulani Julde ba shida ita, ba zaka kira shi namiji mai jiki ba, amman dogone na misali, ko ina a jikin shi bai nuna rama ba. "Kina son gwada karfi dani Saratu, in kin ganni a irin yanayin nan ki daina mun gardama kar inji miki ciwo wata rana" Wasu hawayen ne masu zafi taji sun cika mata ido, da daudar zinar daya kwaso yake neman hada jiki da ita, ko wankan tsarki baiyi ba, lokacin da taji yanda zata tsarkake jikinta tayi kokarin ganin shima ya sani, kwanaki ta jera kullum sai ta karanta mishi yanda zai tsarkake najasar da yake yawo da ita, bai nuna mata Lubna sufyan Hausabook.com 30 alamar ya dauka ba, amman yaji ta, kuma tana fatan ya dauka din. "Dan Allah ka kyaleni..." Ta furta a raunane, ta san halin shi, abinda yayi niyya ba zai fasa ba, kuka takeyi sosai, kukan ta bai karu ba sai da bayan ya gama abinda yayi niyya ya juya mata baya cikin wani irin yanayi da ya fito da tsantsar kunar rai ya furta "Babu kamar Mero, har yanzun banji irin Mero ba" Kamar ita tayi sanadi ko ta zama dalilin da ya rasa Mero kuma ya kasa samun madadinta ba har yanzun. Kukanta kara mishi kunar rai yakeyi. Mata uku ita cikon ta hudu a dare daya amman ko kusa da natsuwar da yake samu da Mero basu kusanta ba balle su cike mishi ramin da ta bari. Akan yaran shi yasan menene soyayya, akan Nawfal yasan asalin kauna da dukkan zuciyar shi. Mace, ita din a wajen shi kamar riga ce da zai saka wadda yake so don biyan bukatar shi ya cire ya sauya a lokacin da yayi niyya. Me yasa Mero ta kasa barin ran shi? Zuciyar shi babu wajen kaunar wata mace Lubna sufyan Hausabook.com 31 banda Daada, amman yana jin wani rami a cikin kirjin shi inda baisan Mero ta zauna ba sai da tabar shi. "Baka taba sona ba Julde, da akwai soyayyata a ranka ko yaya ne ba zaka zubar mun da mutunci har haka ba, ba zaka mayar dani abin nunawa a dangi ba..." Maganar Mero ta dawo mishi tana saka shi runtsa idanuwan shi yana hango fuskarta, idanuwanta, jan bakin da baka raba labbanta da shi. Ita da kanta ta fada mishi baya son ta, me yasa zata manne mishi har haka? Mata nawa ya sani kafin ita? Mata nawa ya sani bayan ita, me yasa ta fita daban? Me take da shi da ya kasa samu tare da sauran? Kullum, tun bayan ita kullum saiya nemi gamsuwar da yake samu da ita a tare da mata daban-daban amman ya kasa samu. Baya bibiyar mata da yawa haka kafin Mero, ta sake bude mishi sabon shafin da babu kalaman da zasu iya fasaltawa. Bai bude idanuwan shi ba har bacci ya dauke shi cike da mafarkin Mero, ya kuma bude su da wayewar gari cike da tunaninta. Da yake Juma'a Lubna sufyan Hausabook.com 32 ce shi yake kai yaran makaranta in ba wani babban uzuri ba, a gaggauce yayi wanka ya shirya sannan yayi sallar asubar da ba kullum ya damu daya sameta a cikin jam'i ba. Duk tare suka karya yana hira da yaran kamar bashi da wata matsala in har yana ganin su a kusa da shi. Salim ne dan shi na farko, Fadila da itace ta biyu kuma tana makarantar kwana ta Science and Technical da take nan garin Kano, Khalid sai Lukman. Suna gamawa ya saka su a gaba suna fita tare, daya sauke sune ma Khalid yace mishi "Daddy idan na dawo zanje gidan Daada acan zamuyi Weekend tare da Bajjo..." Khalid din ya karasa yana kallon Julde da yake girgiza kai "Har kwana biyu zaku je kuyi, ka dai je idan na dawo daga kasuwa da dare in biyo in dauke ku... Shima Nawfal din zan hadu da shi daya tafi bai fada mun ba" Gardama ba halin Khalid bace ba, duk a cikin yaran shi kadaine ba zai ja magana sau biyu da Lubna sufyan Hausabook.com 33 babba ba. Hakan yasa shi jinjina kai kawai yayi ma Julden sallama yana bin bayan yan uwan shi ya shige cikin makaranta. Julde kuma yaja motar shi yana nufar kasuwa, zuciyar shi tayi mishi nauyi fiye da kowanne lokaci. * Yanda yake cin abincin Daada take kallo, ya tattara hankalin shi kamar bai taba yin wani abu mai muhimmanci kamar wannan ba. Tausayin shine cike da zuciyar ta, daren jiya da ta zubo mishi taliya da miyar kifin da tayi ta zallar tumatiri da albasa taga ya kalleta "Tumatir ne kawai da albasa Bajjo" Ta fadi tana kiran shi da sunan da ta makala mishi kasancewar shi da daya tilo a wajen mahaifin shi. Tana dadewa bata kira shi da Nawfal ba. Tana gani ya saka cokali ya fara dibar miyar da kifin yana kaiwa bakin shi, saida ya sauke numfashi tukunna ya fara cin abincin. Yau ma haka, kwano ta samu daban tana zuba mishi miyar da tayi saboda shi kawai. "Daada abincin nan yayi mun dadi" Lubna sufyan Hausabook.com 34 Cewar Nawfal yana jin kamar ya samu waje ya adana dandanon abincin ya dinga daukowa yana tunawa a ranakun da zaici mai da yaji ko ya sha shayi saboda Nanna ba zatayi abincin da zai iya ci ba. Ya dade idan ya kalleta yana so ya tambayeta laifin shi, yana so yaji me ya taba yi mata mai zafi da ta dauki karan tsana ta dora mishi ba. "Yarana da gidan uban sune ma abinda na dafa shi suke ci, ba zaka sakani girki biyu saboda baka cin yaji ba wallahi, ba zan iya wannan jidalin ba" Ta kan yawaita fada mishi, ko a makaranta Nawfal Bukar yake amfani da shi ba Isiyaku ba. Ya san bashi bane baban shi ko bata tuna mishi ba, amman shi din yake ma kaunar da ya kamata yayi wa baban shi da bai san komai game dashi ba bayan suna. Sai dai abu na farko daya fara koya bayan magana shine yin shiru, akan abubuwa da yawa, musamman abubuwan da suka fi karfin fahimtar shi, da kuma wanda suke damun shi. Shiru yafi komai saukin yi, furta wasu abubuwan baya kawo gyaran su, ya taba Lubna sufyan Hausabook.com 35 furtawa Julde cewa Nanna tace gidan ba gidan uban shi bane ba. Fadan da sukayi a gaban idanuwan shi harya mutu ba zai manta ba, yana da tabon dukan da Saratu tayi mishi a bayan shi har gobe. Shiru yafi komai sauki a wajen shi, yanzun ya kara fahimtar duk abinda ake so yaji za'a iya fada mishi ba saiya tambaya ba, abinda yake son ji kuwa koya tambaya idan ba'a son fada mishi ba zaiji ba. "Kar dai ka fado daga kujerar nan wajen santi" Daada ta fadi tana mishi dariya "Ba dai zai hanani yabon girkin nan ba dan yayi mun dadi... Idan zan tafi kika dibar mun miyar nan zata dade bata lalace ba?" Kallon shi Daada tayi "Zata iya kwana biyu dai tunda ba sake dafawa zakayi ba, ko akwai fridge a dakin ku?" Kai ya daga mata saboda ya cika bakin shi da shinkafa Lubna sufyan Hausabook.com 36 "To bari sai ka karo kayan miya da kifin in maka da yawa, idan kaje saika saka cikin fridge ka dinga diba" Murmushi yayi, matsayin Daada daban yake a wajen shi, ko ganinta yayi sai yaji wani sauki a cikin ran shi. Da duk wani abu da zatayi kuma da yanda take faranta mishi. Mikewa tayi tana shiga daki ta fito da hijabi a hannunta "Gara inje barkar nan sai ma in biya in taho da Madina..." Cewar Daada tana saka hijabin ta "Kibari zanje in dauko ta" Kai ta girgiza mishi "Ba nisa da inda zanje... Sai na dawo" Kai Nawfal ya daga "Allah ya tsare. A dawo lafiya" Daada ta amsa tana ficewa daga dakin. Abincin shi ya gama ci ya dauke kwanonin ya kai kitchen, ya dawo ya zauna yaji sallamar Khalid daya amsa, uniform din da yake jikin Khalid din Lubna sufyan Hausabook.com 37 na tabbatar mishi daga makaranta kai tsaye nan din ya nufo "Da baka jirani mun taho tare ba gashi na zo ai" Dariya Nawfal yayi "Ka kyauta. Daman bance ba zaka zo ba ai, kawai jiyan na so tahowa..." Takalma Khalid ya cire yana sake yin sallama ya shiga cikin falon, jakar shi ya fara saukewa dan a cikin ya zubo duk wani abu da yake tunanin zai bukata, yaji me Julde yace, amman yasan wahalar dai yazo gidan Daada. Idan ta saka baki dole yabar su su kwana biyu. Fada ne Nanna zatayi idan ya koma, to ko bai zo ba Nannar shi ba zata rasa dalilin yin fada ba, shisa bai koma ta gidan ba yayi tahowar shi, zaice mata Daddy ne yabar shi. "Ina Daada?" Ya tambaya "Wai zatayi barka sai ta taho da Madina daga makaranta kuma..." Kai Khalid ya jinjina yana mikewa Lubna sufyan Hausabook.com 38 "Ni yunwa nake ji" Kitchen ya wuce ya zuba abinci iya wanda yake tunanin zai iya cinyewa yana hadowa da wani filet din daban ya dawo falon, kan kafet ya zauna ya ajiye filattan a gaban shi yana janyi jakar shi ya bude. Mangwaro ne manya guda biyu ya dauko "Mangwaron ne a jaka Hamma?" Nawfal ya fadi yana dorawa da "Ko dan meye ba za'a samu a jakar ka ba" Dariya kawai Khalid yayi, inda sabo ya saba jin suna mishi wannan surutun. Kawai yafi yarda da ya saka duk wani abu da yake tunanin zai iya bukata a cikin jakar shi ta makaranta. Har paracetamol zaka samu cikin jakar, inka tambaya zaice maka "Idan naji kaina yana ciwo fa? Tunda ba sanar dani zaiyi kafin ya fara ba" Akwai ranar da suke dawowa daga islamiyya takalman Salim suka tsinke. Khalid ya zage aljihun gaban jakar islamiyyar shi ya zaro Lubna sufyan Hausabook.com 39 takalma silifas yana mikawa Salim din yayi gaba abin shi. Su duka binshi sukayi da kallo na wasu dakika kafin su kwashe da dariya. Wata rana dan tsokana ko sabulu ne ya kare musu a bandaki zakaji suna "A duba jakar Khalid ba za'a rasa ba" Shiru yake ya kyale su kamar yanda yayi ma Nawfal din yanzun. Abincin shi ya gama ci ya tashi da filattan yana zuwa ya wanke mangwaron, a fridge ya saka saboda Nawfal ya siyo daman, ya kuma san ba zai sha ba sai yayi sanyi ko yaya ne, idan ma yayankawa akayi zai dauki na shi ya saka a fridge. Yanda Nawfal baya mura har mamaki abin yake ba Khalid, idan ya sha sanyin da Nawfal yake sha na rana daya a sati saiya kwanta gadon asibiti. Da ya fito ma bai zauna ba, dakin da suka saba sauka ya nufa, wanka yayi ya fito ya dawo falon daga shi sai gajeran wando "Geez Hamma..." Nawfal ya fadi yana kare idanuwan shi, kallon kan shi Khalid yayi, yanda Nawfal din yayi wani Lubna sufyan Hausabook.com 40 zai iya zaton babu kaya Khalid ya fito, karamin tsaki yaja "Kasan shekara bata fi daya ba a tsakanin mu ko? Ba zaka daina ce mun Hamman nan kana dora mun girma ba" Batare da Nawfal ya sauke hannun shi daga kare idanuwan shi da yayi ba yace "Ka dai girmeni, zan daina in ka daina ce mun Bajjo" Wucewa kawai Khalid yayi abin shi. Mikewa shima Nawfal din yayi, sai da ya kara watsa ruwa, lokacin daya fito har Khalid ya gama shirin shi ya fita. Shima shiryawa yayi cikin farin yadi harda hula bula ya saka kamar takamin shi daya dauko. Kafin ma ya fito yaji dawowar su Daada saboda rakadin Madina da take kwala mishi kira, sanda ya fito Khalid na fadin "Lallai Madina, kamar baki ganni ba ko?" Ko kallon shi batayi ba ta ruga da gudu tana fadawa jikin Nawfal hadi da zagaya hannuwanta jikin kafafun shi Lubna sufyan Hausabook.com 41 "Hamma na dauka ka tafi kabarni" Kanta ya shafa "Nace miki ina nan har ki dawo makaranta ai... Masallaci dai zamu tafi ni da Hamma yanzun mu dawo, me zan siyo miki?" Daga kai tayi tana kallon fuskar shi "Biskit" Khalid da yake zaune yace "Ni ina da biskit din ai, ba zan baki ba tunda baki kulani ba" Juyawa tayi ta kalli Khalid "Hamma na zai siyo mun ai dai, ko Hamma?" Kai Nawfal ya jinjina yana dariya "Ki je ki cire uniform, Daada tayi abinci mai dadi" Murmushinta ne ya fadada "Tuwo ta dafa?" Lubna sufyan Hausabook.com 42 Wannan karin har Khalid dariya yayi da Madina bata ga dalilin su nayin dariya ba. Nawfal yace anyi abinci mai dadi, shisa tayi tunanin tuwo ne "Shinkafa" Lokaci daya fara'ar fuskarta ta dishe tana raba jikinta da Nawfal din "Shinkafa kuma" Ta furta ranta a bace tana sake saka su dariya. Daki ta wuce harda jan kafafuwa a dole ranta ya baci da aka dafa shinkafa ba tuwo ba. "Daada zama dake yarinyar nan kaf ta kwashe halin tsofaffi, ace ga shinkafa amman tuwo ne a ranta" Khalid yace yana dariya "Ku da bakuyi halin tsofaffin ba ai sai kuyita fama da shinkafar ku, amman ni tuwo zan mana anjima" Mikewa Khalid yayi "Tafdin, aci tuwo lafiya..." Lubna sufyan Hausabook.com 43 Dan shi baya so, tuwo da danwake na cikin abincin da yunwar da zata saka shi cinsu ba karama bace ba. Sallama suka yiwa Daada suna fita masallaci. "Adee..." Ya kira ta da sunan da Khalid ya saka mata tun lokacin baya iya kiran sunan ta, maimakon Fadila din sai ya gajarce shi zuwa Adee da kowa yake kiranta da shi yanzun "Ke bakya jin rana?" Kai ta girgiza mishi, duk rashin magana irin ta Nawfal bai kai Adee ba. Dan ta ita duniya bata tashi ba, komai da sanyi-sanyi takeyin shi. Kusan ita ta kwaso jikin fulanin. Yanzun haka idan kaganta ita da Nawfal din babu wanda zaice itace babba, kanta da wahala idan ya kai kafadar shi, bata da tsayi kuma bata da jiki. Sai hasken fatar da kusan gadon shi sukayi. A gajiye take jinta, ta rasa inda Daddy ya tsaya da yau baizo daukar su ba. Ta riga da ta saba da anyi hutu ta fito a bakin gate take samun motar shi yana jiran ta. Lubna sufyan Hausabook.com 44 "Yau Daddy ya dade..." Tayi maganar cike da kosawa. Nawfal bai amsa ta ba, baisan me zaice mata ba. Inda yana da zabi zai zauna a makaranta abin shi. Duk satin duniya sai Daddy yazo ya gansu. Wasu satikan da Khalid yake zuwa. Sai dai a wani bangaren idan ya tuna zai ga Daada sai yaji komawa gida ba abu bane mai muni kamar yanda zuciyar shi take fadi. Sati ukune kawai hutun nasu, idan ya rike numfashin shi kafin ya sauke zaiga kwanakin sun wuce kamar ba'ayi su ba. Zai kokarin gujema Nanna a satikan. "Daddy muna ta jiran ka" Muryar Adee ta katse mishi tunanin da yake, yana daga kai ya kalli Daddy da yake mishi murmushin da yake mayar mishi. Sai yaji kamar anfi sati rabon da yaga Daddyn saboda yanda yayi kewar shi "Ba kun gujeni kun zabi boarding ba yaran nan?" Dariya sukayi gabaki dayan su. In da zasu biye Julde sam ba zasu hada hanya da makarantar Lubna sufyan Hausabook.com 45 kwana ba. Ya fiso ya dawo gida ya gansu kafin ya kwanta, idan ya tashi da safe ma ya gansu kafin ya fita. Saboda su baya tafiya ta wuce kwana biyu, kewar yaran shi zata fara tambayar shi. Sai dai a lokaci daya kuma bashida zuciyar hana su abinda yaga muraran suna so. Da zai iya da ba zasu zo makarantar kwana ba, musamman Nawfal da baya kaunar yaga yayi mishi nisa. Su Adee yaran shine, jinin shine, daga jikin shi suka fita. Ba zai karya ba suna da matsayin da za'a kai ruwa rana kafin wani ya taka shi a zuciyar shi. Amman Nawfal, matsayin Nawfal abune da ba zai iya furtawa ba, babu kalaman da zai iya amfani da su ya misalta yanda yake jin Nawfal gab da zuciyar shi. "Amana ta ne Julde, yaron nan amanata ne" Abinda Daada ta dinga jaddada mishi, abinda yake so ya kalli ba ita ba har kowa yanzun yace "Nawfal amanata ne, ni ya kamata Bukar ya ba amana..." Saboda Nawfal ya fito daga jikin bukar ne kawai, amman dukkan wata kauna da uba zai yiwa dan Lubna sufyan Hausabook.com 46 shi itace yake yiwa Nawfal. Kuma yana godewa Allah idan yaga irin murmushin nan a fuskar Nawfal. Idan yaga yanda Nawfal yake nuna mishi ko duniya zata hade waje daya tare da mutanen cikinta in dai zata sake budewa to zai riko hannun shi a matsayin Uba. Soyayyar da take tsakanin su mai girma ce Sai dai rubutacciyar kaddarar da take tsakanin su tana son danne girman soyayyar "Bajjo jiba idanuwan ka, kana ma cin abinci?" Dariya Nawfal yayi me sauti "Baka ga yanda Adee ta koma ba" Kallon su Adee tayi "Rabon da in koma wani abu anfi shekara uku, ina nan yanda nake... Da gaske idanuwan ka sun rame" Akwatin shi daya tashi daga kai yake kokarin dauka kafin Julde ya karasa ya karba, baiyi musu ba ya sakar mishi. Ko siyayya ya fita dasu shi yake rike ledojin, duk yanda zasuyi su karba zai ce Lubna sufyan Hausabook.com 47 "Yaushe hannuwan ku zasu iya daukar wannan kayan. Da nauyi sosai" Da akwatin Adee ya hada ya saka su bayan motar "Yanayin abincin ka ya sa bana son ka da makarantar kwana Nawfal, nasan wahala zaka sha" Gaban mota Nawfal ya bude ya shiga. Adee ta hau baya. Daddy ya zagaya ya zauna mazaunin direba ya rufe murfin. Har ya tayar da motar ya juya yana mitar yanda Nawfal din baya cin abinci duk ya rame. Murmushi kawai Nawfal yayi "Ina ci fa Daddy, dan baka gani na kullum ne shisa..." Kai Julde yake girgizawa, ko satin daya fita da yazo ganin su bai ga yayi zuru-zuru haka ba. Shiru kawai Nawfal yayi, dan baisan me zaice ba. Julde baisan cewa yafi koshi a makaranta fiye da gida ba. Tunda yana da zabin na yaci abinda aka dafa ko akasin haka. Idan shinkafa da miya ne, ya amshi fara yana da kifin gwangwani zai juye a Lubna sufyan Hausabook.com 48 ciki yaci abin shi, wata rana zaici snacks. A gida bashi da wannan zabin, akwai kifin gwangwani da Daddy kan ce saboda shi yake siyowa. Kamar kuraye haka su Khalid suke akan nama, shine kawai bayacin nama Kwata-kwata. Ba allergy bane ba, kawai bayajin zai iya cin nama tun yana da karancin shekarun shi. Da yagan shi a cikin miya ma hankalin shi tashi yake, daga kaza har sauran nau'in nama. Baisan a shekarun yarintar da ba zai iya tunawa ba ko yaci, iya wanda zai tuna kawo yanzun baya hada hanya da duk wani abu nama. Amman kifin nan bai isa ya taba ba. Idan danyene aka kawo dan ayi miya. Nanna zata sarrafa shi yanda zai zama haramiyar shi. Shisa bai taba saka rai a duk wani abu da saiya fito ta hannunta sannan ya iso wajen shi ba. Idan Adee tazo hutu yana jin dadi, yana cin abinci da miya, da kanta take shiga kitchen tayi mishi miya ta kuma juye a rubber ta kai mishi dakin shi. "Me yasa kike haka Nanna?" Lubna sufyan Hausabook.com 49 Shine tambayar Adee duk idan Nanna tayi kokarin hanata. Wasu ranakun harda duka amman ko bandaki Nanna ta shiga sai tasan yanda tayi ta kaima Nawfal din wani abu da zaiji dadin shi. Kifin gwangwani kuwa ita da Khalid suna diba su kai mishi ya ajiye a dakin shi, Khalid da dai-dai zai dauka. Adee zata iya daukar kwalin gabaki daya, wata rana nata na makaranta randa ta dawo hutu take zuwa ta kai mishi. Kamar bata ci kwata-kwata tana tarawa ne don shi. Kananun abubuwa irin wannan yasa yake jinta har ran shi. "Ka daina jira sai Nanna ta baka abu, idan kagani kana so ka dauka ka tafi abinka" Ta kan fada mishi wasu lokuttan idan ta kai mishi wani abin. Sai dai yayi dariya, baya son tashin hankali sam, duk wani abu da zaiyi ya gujema fadan Nanna zaiyi, wani lokacin zai rantse ganin shi kawai harzuka matar yakeyi. In ba Daddy yana nan ba baya shiga bangaren ta. Ko yunwa zata kusan halaka shi daya leko ta window yaga tana falo saiya koma, in Khalid yana nan zai mishi magana ya zubo mishi abinci. Lubna sufyan Hausabook.com 50 Idan baya nan kuma zaici duk abinda yake da shi a bangaren shi. Yanzun ma da suka karasa akwatin shi yaja zuwa zai nufi na shi bangaren "Kamar jira kake Nawfal? Ba zaka shiga kaga Nannar taka ba?" Murmushi yayi "Daddy nagaji, zan watsa ruwa tukunna..." Kai kawai Julde ya daga ya rufe bayan motar yana daukar akawatin Adee da tayi saurin kamawa tana fadin "Bajjo zaka ba, akwai wasu kayan shi a ciki, idan ya kwashe naje in dauka" Ta karasa maganar tana kallon Nawfal da fuskar shi take dauke da alamar tambaya. Kai ta dan daga mishi, cikin sanyin jiki ya karaso yana jan akwatin nata ya hada da nashi ya nufi bangaren shi. Ita da Daddy suka wuce cikin gidan tana bashi labarin da bashi da kan gado dan kar ya tambayeta wanne kayan Nawfal ne a akwatin ta. * Lubna sufyan Hausabook.com 51 "Takardun meye wannan?" Saratu ta tambaya tana rarraba takardun a tsakanin hannuwanta, a karo na babu adadi tana jin takaicin rashin ilimi, daya daga cikin rashin gatan da maraici yayi mata. Duk da boko ce karshen abinda aka damu dashi a inda ta tashi, amman ko bakomai an sa taje makarantar allo, babu wanda ya damu da yanda rayuwarta zata kasance. "Takardun filayen Bajjo ne za'a siyar da wasu a sai mishi gida" Wani abu taji ya taso da ba zata ce ga daga inda yake ba, amman dacin shi har akan harshen ta. Filaye Julde yace, hakan na nufin ba daya ba ba biyu ba tunda yana kiran wasu daga ciki za'a siyar a sai mishi gida. "Yana da dukiyar shi Saratu, Nawfal na da dukiyar da tunanin ki ba zai taba hangowa ba. Ba taimaka mishi nake ba dan ina biya mishi kudinn makaranta, ganin dama ta ne kawai..." Kalaman Julde suka dawo mata wani lokaci can baya da tayi tsegumi akan yanda zaman Nawfal Lubna sufyan Hausabook.com 52 din yake karin nauyi akan shi. Ba zata daina wahalar da kwakwalwar ta wajen tunanin inda Bukar ya samu arziki har haka ba. Bukar fa, Bukar dai daya bar kauyen su da sunan zuwa neman ilimi. Tsoron kar tunanin ta yayi karadin da wani zaiji shisa take tausar shi, amman akwai ayar tambaya mai girma akan wannan kudin da Bukar yabar wa Nawfal kamar yanda akwai babbar tambayar da kowa yaki yarda ya furta akan asalin haihuwar Nawfal. "Dukiyar Nawfal bata karewa ne? Har nawa yake da..." Sauran maganganun suka koma mata saboda yanayin juyawar da Julde yayi yana kallon ta "Meye matsalar ki da dukiyar shi? Sanin yawan ta amfanin me zaiyi miki?" Kauda kai tayi gefe, abinda take ji yana kara ninkuwa, wannan dukiyar da yake kira Nawfal na da ita da su Salim take hangota, duk wani jin dadi da yake gidan duniya rayuwar yaranta take hangowa a ciki. Lubna sufyan Hausabook.com 53 "Su Khalid ma ya kamata ace suna da gidajen su yanzun tunda kana da halin" Karamin tsaki Julde ya ja kafin ya taka ya fisge takardun da suke hannunta yana mayarwa cikin jakar shi. Bai san me yasa daya dawo hannunta kan jakar shi yake fara sauka ba, sai kuma ta dame shi da tambaye-tambayen da bayaso kan duk wata takarda da zata gani kamar ya aiketa. "Duk takardar da zaki gani in ba zaki iya karantawa kiji ko ta mecece ba karki sake damuna da tambaya" Maganganun shi sunyi mata zafi ba dan kadan ba, duk da ba yau bane rana ta farko da yake amfani da duk damar da zai samu na goranta mata rashin ilimi kamar laifin nata ne. Karatun hausar da ya koya daga bayane da dan kalaman turanci daya tsinta akan titi suke kara bashi damar zaginta haka. "Ka sama mun makaranta ko ta yaki da jahilci ce..." Ta furta cikin wata irin sanyin murya. Sosai Julde ya kalleta wannan karin kafin ya kwashe Lubna sufyan Hausabook.com 54 da dariya yana girgiza kai kawai. Har ranshi dariya ta bashi. Duk tsayin shekarun nan batayi tunanin shiga makaranta ba sai yanzun? Saboda tana son saka ma shige da ficen shi idanuwa fiye da yanda takeyi yanzun. Takardun shi ya mayar tsaf ya gyara ya karasa yana samarwa jakar waje ya ajiye. Fita yayi daga dakin baccin nasu zuwa falo yana jin motsin Adee a kitchen, hakan yasa shi tunkarar kitchen din ya kuwa ganta tana wanke-wanke. "Sannu da aiki..." Da murmushi a fuskarta ta juyo "Daddy Am... Ba wani aiki bane ba fa" Kai ya jinjina, komai ma in dai ya danganci hidimar cikin gida amsa daya Adee zata baka, dan wajenta ba aiki bane ba, har mamakin kokarinta yakeyi a kankantar da take da shi, gashi sanyin halinta baisa tana da sanyin jiki ba "Ni ma zan leka Daada ne" Wannan karin fuskarta cike da roko tace "Dan Allah zanje... Saura kadan in karasa..." Lubna sufyan Hausabook.com 55 Dan jim Julde yayi sannan ya amsa "Bari to in duba su Khalid, nasan zasuje suma sai su shirya duk mu fita gabaki daya" Murmushi tayi har

Chapter 2 of 18